tadora kafa daya Kan daya, tana girgiza jiki, alamun ashirye take d kowa, kara ta riqe a hannunta tana karkadawa tana Kallan Shalele da Rana take gasawa
Baba yayi sallama yashigo gidan, turus ya tsaya yana Kallan Shalele, itama dasauri tace baba sannu da Zuwa
Da mamaki afuskarsa yace, a a Shalele nah kece kike wanki yau Kuma?
Bata bashi amsa ba sai Daria datayi alamun Ko ajikin ta
Qarasawa yayi cikin rumfar inna take zaune tana kallansu d'ai-d'ai
Yace mezan gani haka Marka?
Asheqale inna t kalleshi tace au Wai danna saka Shalele wanki? Masassara ce ta kamani shiyasa Naga bazan Iyaba nabata, Ko akwai damuwa akan Hakan?
(nikwa nace tofa wata sabuwa 🙄meyake shirin faruwa a gidan baba ne?
Please Dan Allah Sharhi da comments 👏🏻
Amnanku ce ✍🏻
💕SHALELAN BABA💕
(Romance)
Writing by Amnah El
7&8
Baba yace babu damuwa, Allah yabaki lafiya
Ko ajikinta tace amin
Shalele nagama wankin ta shanya, tace inna nagama
Can ciki ta amsa mata, alamun aikin bewani dadata da qasa ba
Baba ya kalleta shide duk mamaki yakama shi
Be gama mamaki ba yaji tace, idan kinyi ga tukwane can, kije kidora abincin dare
Dasauri tace Kai inna tun yanzu? Bazai huceba kuwa?
Haka nayi niyya, idan zakiyi kiyi, idan Kuma ban Isa nasaki bane saiki fadamin
Jin wannan furucin nata ne yasa jikin Shalele yayi mutuqar sanyi, dariyar yaqe tayi tace a a Bari in Dora
Shikuwa baba yayi Shiru yanaso yaga gudun ruwan Marka, yaga yau wani take take takeji na rashin mutunci acikin gidansa
Wanke tukwanan tayi ta Dora tuwo da miya, dayake girkin nasu bawani me yawa bane nan da nan tagama, a lokacin baba yana Daga cikin daki yana jiyosu, tazo tace inna angama Shima
Tana karka da kafa tace saiki share gidan ai, ba Tsayawa zakiyi akaina kina kallo ba
Daga murya yayi daga cikin dakin yace ke Shalele, kama hanya ki shirya kitafi islamiyya, kada wanda yake daukar ki Yazo yaga yau kinyi latti
Saida ta kalli inna, Ko zata ce wani Abu, Taji innan tayi Shiru, danhaka tashige cikin dakinta domin shiryawa, tana shigewa ta riqe bayanta alamun wajan ya amsa, saboda rashin Sabo da aiki, agogon dakin ta kalla da sauri ta tashi tashirya cikin uniform dinta, tadau jakar da littattafan islamiyyar suke ciki ta futo, tace inna natafi
, Amma Kamar da qasa take magana, haka inna ta shareta, baba yasake Daga murya yace jeki Shalele nah, Allah yakaremin ke a duk inda kike, Allah yabada sa'ah, Saida tasaki Murmushi saboda jin dadin adduar dayayi mata sannan tace amin baba, tafice da sauri, Zuciyar ta cunkushe da tunanin laifin me tayiwa innarta take wannan fishin da ita, aide aiki ne tabata Kuma tayi, Amma meyasa yau gaba daya ta sauya mata Kamar ba innarta ba?
Acan makaranta ma, anayi musu akdari haka malamin yagama yafita Amma abinda ta fahimta Dan qalilan ne, sabira qawar ta dake gefenta, ta fahimci ba kalau takeba, Dan haka tace HANEEFA SURAJ ADAM, meyake damunki ne yau gaba daya Kamar kina tunani
Ajiyar zuciya tasauke tace wallahi sabira, inna ce yau take fishi Dani, Bansan me nayi mataba
Kafadarta ta dafa tace haba de, keda innarki da ba'a jin kanku? Nafi tunanin wani laifin kikai mata, wanda ke baki saniba
Tace wallahi sabira babu abinda yafaru yau dinnan de
Sabira tace to idan kin koma gida kibata hakuri, insha Allah komai zai wuce, Amma yanzu de ki nutsu akan karatun daya kawomu
Murmushi tayi tace to Qawata godia nake
Cikin gida kuwa Shalele na fita inna tahau fada, amma de Malam kasan abinda kake yi a gidan nan baka kyauta wa Ko? Yanzu Kenan ni ban Isa da wannan yarinyar ba? Shikkenan komai sai abinda kace zatayi? Yarinya babu wanda isa da ita, harni zansa ta aiki Amma kasa yarinya qanqanuwa ta bijiremin
Hularsa yake kokarin sakawa da alama fita zaiyi, yace yanzu Marka mekike so ince dake? Yarinyar Nan de kina gani lokacin tafiyar ta islamiyya ne yayi, yanzu Marka saboda aiki can maras tushe zan daure mata gindi akan ta zauna tayi aiki kada taje makaranta? Toni bazan dauki wannan ba, idan ma wasu ne Daga gefe suke hure Miki kunne to kifada musu sudena, ba'a gidanaba, yana gama fadar haka yasakai yafice yabar mata gidan
Yana fita inna tafashe da kuka, akan Shalele yake fada mata wannan maganganun? Hakika yau tayi DANA SANIN auren surajo, ita Kuma Shalelen ai zata dawo gidan ta sameta, da ita suke zancen
Shalele na dawowa gida gab da magrib tayi sallama tace inna nadawo
Daqyar ta bude baki tace Aina ganki
Murmushi tayi, aranta tace inna Bata huce ba Kenan, buta tadauka ta shiga bayi tayi tsarki, sannan ta futo tayi alwala, tabarmar da inna take zaune anan taje tatada kabbarar sallah, tana idarwa tace inna kiyi hakuri
Mekikamin dazaki bani hakuri
Shalele tace Naga yau duk ranki abace yake, Bansan laifin danayi Miki ba innata Amma kiyi hakuri
Aikin nunamin ban Isa dakeba haneefa, inda na isa dake bazan sakaki aiki kiqi yiba
Da tsananin mamaki afuskarta ta kalli innar Tata, yau inna ce Dakanta take kiranta da Haneefa?
Meyake faruwa ne? Kota manta ne baba yace Sunan mahaifiyarsa ne? Amma Tafadi sunan haka Kai tsaye?
Murmushin dole ta qirqiro tace to inna kiyi hakuri, Bari in tashi in share gidan, kiyi hakuri
Yunqurawa tayi zata tashi, tana tsammanin inna zatace dare yayi tabarshi, Amma sai Taji sabanin haka, domin kuwa inna amsa tabata da Cewa "Dade yafi Miki"
Share gidan tayi tsaf, Daga nan tashige dakinta take ta aikin kuka, Bata sababa, batasan metayiwa inna haka me zafi ba
Koda baba yadawo ma, bece inna takawo masa abinci ba, Shalele ya qwalawa kira taje takai masa abincin sa, haka de ta kwanta ranar jikinta duk yayi sanyi, baba kuwa Baisan abinda yayi yaqara qona ran inna ba, haka nan takejin wata irin tsanar Shalele aranta
*******
Washe gari dataje makarantar islamiyya, haka take fadawa sabira Cewa tabawa inna hakuri fa Amma babu abinda yasauya, sabira tace "kedan bakya karanta littafin hausa nefa, infada Miki akwai wani Novel Dana taba karantawa naji ance Wai masu ciki wani lokacin cikin yana sakasu masifa"
Shalele tace "Dan Allah da gaske kike?"
Sosai makuwa, inji sabira
Hauka da yarinta irin tasu yasaka Shalele yarda da maganar qawarta
********
Kwanci tashi babu wuya awajan Allah cikin inna ya tsufa, daqyar take zama daqyar take tashi, halin datake nunawa Shalele kuwa babu abinda yasauya saide ma qaruwa dayayi, baba yana lura da duk wani take takenta, jira kawai yake yaga ta haihu lafiya, yanzun yana Daga mata kafa ne akan larurar datake jikinta,sauqin Shalele daya, shine makaranta datake Zuwa da safe, dayake yanzun Suna ss1 ne, Amma dazaran tadawo gida tofa babu zama, aiki ne zai biyo baya, tun maganar sabira na yaudararta akan Cewa haka masu ciki suke Har abin yadawo Bata mamaki, domin kuwa qarara inna take nuna tsanar datake yimata
********
Yau takama Laraba, Kuma a yaune inna ta haihu da namiji, baba yayi mutuqar farin ciki, daya Daga cikin qannan inna ne sukazo domin temaka mata
Kayan da akayi haihuwar dashi, aka Bata da jini murja ta meqo mata shi, tana zaune a tsakar gida, ta dungurar da bahon tace ke gashinan dauki kije ki wanke shi
Shalele Bata kawo komai aranta ba, asalima murnar tasamu qani yahana bakinta rufuwa, daukar bahon tayi tace to anty murja, tashige bayi dashi, kwata Kwata batada qyanqyami haka ta wanke wannan kayan jinin tas, ta shanya, ta wanke hannunta da omo, dakin innar Tata ta shiga hankalinta yanaga Yaron tace anty nagama, tameqa hannu zata dauki jaririn
Dasauri inna tasa hannu tace mezaki masa? Kinga barmin yaro na, bazakije ki jagwalgwala Shiba, Har yaushe da hankalina zan Bari ki dauke shi
Idan akwai abinda yafi sanyin jiki Tona Shalele yayi, Kallan anty murja tayi Ko zata yi magana Amma Bata sami komai Daga wajan murja bama sai amsar harara
Haka tataso ta futo jiki asanyaye, salalo salalo
Awannan Karon Kam Bata Iya tsaida hawayen dayake shirin zubo mataba, kuka ta zauna ta rizga, idanunta sukayi jajir, tanajin baba yashigo yabawa murja sako yace murja ga wannan ki dafa mata Ko zataji dadinsa, yafice
Yana fita anty murja ta qwala mata kira, dasauri ta goge hawayen idonta tace gani anty murja, ledar da Baba yabawa murja ta wullo mata Har naman dayake ciki yafara zubewa, tace dauki wannan wulaqantaccen naman ki wanke kidorashi awuta
Wulaqantacce? Naman da baban nata yafita yasiyo da kudin sa ake Kira sa Wulaqantacce?
Batada ikon magana haka tadauka taje ta wanke shi, tadora awuta, albasa ta yanka aciki tasa Maggi da gishiri dasu citta, nan da nan kuwa Qamshi yafara tashi
Haka ta zauna Saida dafawa inna naman, sannan tazuba mata shi a flas, takai tace inna gashi, Ko azuba Miki?
Hararar ta murja tayi tace ke awa? Eye nace ke awa? Kinga jeki ni karki cinyeni da wannan idanun naki me kama Dana mage, gayyar na ayya
Haka yafuto Daga dakin ranta duk ajagule, inna kuwa da harara tabita, tun kafin ta zauna, inna da kanta ta qwala mata kira tace Haneefa futo kidora muku abinci keda ubanki
Ahankali tace "nida ubana"
Sake futowa tayi, tadora musu abincin harta qare, zama tayi domin ta huta, ta tuna da shara, Gara ma tayi, saboda inma batayiba zasu sake tasota
Tana gama sharar, tahada kwanukan gidan zata wanke, randar gidan ta bude taga babu ruwa, taje gaban dakin inna, suna zaune itada murja sun bararraje sunacin farfesun data dafa, cikin tsoron fadansu tace inna dama zanyi wanke wanke ne shine Naga babu ruwa acikin randar
Banza sukayi da ita, babu wanda ya tanka mata acikinsu
Kallansu tayi tasake Cewa Inn... Bata qarasa fadar sunan ba, innar ta hayaiyaqo mata, to Haneefa Bari nazo nasaka hijabi na nadebo Miki ruwan kinji, tsaya gani nan Zuwa
Jiki ba qwari tabar kofar Dakin, dakinta taje tadau hijabi, tazari boket tafice Daga gidan, tuqa tuqa taje tadebo ruwan tadawo, tana dawowa ta shigo zauren gidan tahadu da Baba
Kallanta yayi yace menake gani haka Shalele nah?
Murmushi tayi tace baba babu ruwa a gidan, Kuma baka nan, naduba wajan baba Malam Kuma baka nan shine nace kawai Bari nadebo
"sauke bokitin nan "abinda yace mata Kenan
Laaa baba babu nauyi fa
" nace ki sauke "
Bata sake magana ba ta sauke boket din, yasa hannu yadauka yace mata muje cikin gidan
Itace tayi gaba, yabiyota Abaya, tun kafin su karasa shiga yafara qwalawa inna kira
Marka! Marka!!
Tana Daga cikin dakin ta amsa tace Malam inajinka
Marka wanne irin rashin adalci ne wannan zaki saka Shalele diban ruwa? Har me zakiyi da ruwan dazabaki tsaya nadawo gidan nadauko muku ba?
To yanzu Malam nikakeso nasaka hijabi naje nadebo mata ruwan? Bafa ayimin adalci acikin gidan nan ehe
Qwafa yayi be sake cemata komai ba, yanufi randa yazuba ruwan, sannan yajuya zai ficedaga gidan ya kalli Shalele da ke tsaye Kamar kazar da qwai yafashewa aciki, cikin tausasa murya yace karna qara ganin kinfita waje wani diban ruwa, inde ba makaranta zakiba, bakason naqara ganinki da makayin diban ruwa kinji Shalele nah
Batace masa komai ba illa girgiza masa Mai datayi alamun to
Yana fita inna tadaka mata wata uwar Hararar datasa Shalele sunkuyar da kanta qasa Kamar wata munafuka
Ruwan da Baba yajuye aranda ta Diba tafara wanke kwanukan datayi amfani dasu
********
Ranar Suna yaro yaci sunan kakan Shalele na wajan uwa, mahaifin inna Kenan Abdallah
Amma inna na kiransa da aududu (🤣)
Anyi taron Suna lafiya angama kalau, taro yayi taro, inda baba yayanka wa inna raguna Har biyu saboda hidimar Suna
Yau baba yana gida, suna zaune Dukansu arumfa anty murja Takoma gidan ta, Aududu ne yayi fitsari inna tace Haneefa zoki sakawa Yaron nan ruwa yayi fitsari
Baba ya kalleta da tsananin mamaki, Ko kadan yanzu Bata shakkar fadar sunan mahaifiyarsa agabansa, Ko babu komai ai sirikarta ce, duk da bata a Raye
Hannunta ta dauraye Daga wankin tsarin tuwonsu datake yi, tazo tadauki Yaron ta wanke masa jikinsa, tasaka masa wani wandon, Bata taba daukar Aududu inde ba wahalar sace ta tashi ba, tarasa meyasa inna Bata barinta ta dauke shi, kawo mata shi tayi Takoma taqarasa wankin tsarin ta bazashi akan wani babban tabarman zana
Sannan ta wanke wandon da Aududu yayi fitsarin ta shanya, tun kafin ta zauna, Yaron yayi Kashi
Baba yayi tunanin inna zata tashi Dakanta tagyara Yaron, Amma saiyaji tace Haneefa zoki daukemin Yaron nan ki wanke masa Kashi
Tace to inna, ta tashi tadauki Yaron sukayi Bayan gida
Hannu bibiyu baba ya zabga tagumi (🙉) Yama kasa Cewa komai
Futowa sukai Daga bayin itada Aududu tana da gashi sama ta nayi masa wasa, sai babbaka Daria Yaron yakeyi, dasauri inna tace "Ke karki lahanta min yaro mana, ke mahaukaciyar inace!? Eye nace ke mahaukaciyar inace zaki dinga cillamin yaro sama kina cafewa saikace wanda kika dauki Leda
Da karfi baba yace Marka!!!
Mrs Usman ce ✍🏻
💕SHALELAN BABA💕
(Romance)
Writing by Amnah El
9&10
Itama cikin fishi tace zaka dakenine? Malam nace zaka dakenine akan nayi mata magana saboda Dana? Idan ta kashemin shi Kaine zaka bani wani Ko ita? Da wannan din dayaya na sameshi? To bismillah, aiga fili ga me doki, kana yin kuskuren sake fadamin baqar magana Akan yarinyar Nan zakaga mummunan matakin dazan dauka akanta
Dukda yana cikin halin masifa, lokaci daya jikinsa yayi sanyi dajin furucin Marka, Gabansa ya tsanananta faduwa, cikin mamaki yace subhanallah, subhanallah Marka mekike nufi da kalamanki? Wai nikam in tambyeki, su waye suke hure Miki kunne abayan idona?Shalele datayi tsaye tana Kallan abinda Bata taba ganiba, idanunta babu abinda yake zuba banda hawaye, ita ya nuna da hannunsa Sannan yace Marka me kika dauki Shalele ne? Kishiyarki ce Ko yarki?
Inna na girgiza jikinta irin tanaji da masifar nan tace masa oho shafa kaji
Gaskiya ne Marka, zan shafa, zansha fa naji yanzu kuwa, Kallan Shalele yayi idanunta sunyi jajir sabida kuka, Bata taba ganin iyayenta Suna fadi infada da junaba sai yau, ita kuwa wacce irin yace da zatayi silar samun sabani tsakanin iyayenta da ba'a jin kansu Ko kadan?girgiza kansa yayi alamun ta dena kukan datake, Saida ya sassauta muryarsa alamar rarrashi sannan yace share hawayen ki Shalele nah, ajiye Yaron nan
Bata ajiye Shiba, ta qanqame Yaron ajikinta, ahankali baba yasake Cewa ajiye mata shi nace, inna na kallansu tana karkada jiki tana auna musu harara
Still Bata ajiye Yaron ba, cikin tsawa, wadda tsawon rayuwar ta Bata taba ji mahaifin ta yayi Mata ba, yace "nace Ki ajiye Yaron nan!!!"
Lokaci daya jikinta yahau kyarma ta ajiye Aududu tashige dakinta da gudu tana kuka
Baba ya kalli inna Marka yace kin kyauta, sannan yasa Kai yafice Daga gidan
Bai zarce ko'inaba sai gidan maqocinsa Malam yahai, kafin ya qarasa gidan yar qaramar wayarsa tahau qara
Yana dagawa yace eh insha Allahu Ina nan tafe, zaku ganni Hajiya, Yauwa nagode, sanan ya kashe wayar
Sallama ya qwala a kofar gidan, amininsa Malam yahai yanaji yasaka hularsa yafuto kofar gidan, ayanayin da yaganshi yasan Cewa ba kalau ba, akwai damuwa, danhaka yace a a Malam surajo, qaraso mana, mu qarasa ga dakali nan mu zauna, bece komai ba sai zama dayayi, yakama kansa da hannunsa bibbiyu
Dafashi Malam yahai yayi yace meyake faruwa haka Malam surajo? Yanayin ka ya nunamin ba lafiya kake ba
Cikin damuwa baba yace Marka
Malam yace me markan tayi?
Marka ta sauya Malam yahai, nan take yabashi labarin duk abinda yake faruwa, Daga qarshe yace kaji abinda yake faruwa
Innalillahi wa inna ilaihirraji'un gaskiya Malam surajo wanan ba qaramar matsala bace, yanzu ya za'a yi a shawo Kan wannan matsalar?
Baba yace yanzu Kam kaina yariga daya kulle Malam yahai, Amma dole zan dauki babban mataki akan Hakan, ba wanan ne damuwa ta bama, Hajiya takirani Daga Abuja, tana son ganina, Amma idan bazan samu damar zuwaba to tanaso tazo da kanta, tanason zamu yi wata magana Mai muhinmanci dangane da Shalele nah, Amma nafada mata Cewa bama sai tazo da kanta ba, zansa lokaci naje cikin satin nan
Malam yahai yace to ai ta kwana gidan sauqi Malam surajo, ni Ina ganin mezai Hana kawai katafi da ita Shalelen can wajan hajiya, ai zaifi
Malam yahai tana zuwa makaranta yanzu, banaso Ko kadan na katse mata karatunta, idan natafi da ita bazasu Bari nadawo da ita ba,, zan Bata hakuri kawai,idan Naga gidana yagama dedeta yadawo Kamar da, sainaje, Amma yanzu bazan Iya barin Shalele Daga ita sai Marka awannan halin ba
Malam yahai yace eto wannan dinma tunani ne Mai kyau gaskiya, babu damuwa, kada kadamu abokina,kakira Marka ku zauna kaji menene damuwar ta, insha Allah komai zai warware, saika kira hajiyan kabata hakuri kayi mata bayanin komai
Baba yace zan kirata insha Allah, nagode sosai da shawararka a gareni
Malam yahai yace haba abokina babu godia a tsakaninmu
Da wannan shawarar ta Malam yahai baba yaji ransa yadanyi masa dadi
Tashi yayi yace zanje gewaya gona, saina dawo Malam yahai
Malam yahai yace to shikkenan Nima Bari in koma gida
Daga nan baba Bai zarce ko'inaba sai gonarsa, Saida yagama dubata da kyau sannan yadan ciccire mata ciyayin dasuka Dan futo, yahau kekensa ya wuce wata gonarsa ta shinkafa, nanma dubawa yayi yaga ruwa ya wadace ta, sannan yazauna yana hutawa a wata bishiya Mai sanyi, Daga nan Baisan lokacin da bacci ya daukeshi ba
Zafin dayaji aqafarsa ne yasa yafarka da Addu'ah abakin sa, hamma yayi sannan yakai dubansa kan kafarsa, baiga komai ba, wajan dayakejin Zafin yataba da hannunsa nanma de baiga alamun komai ba, danhaka baikawo komai aransa ba yatashi yayi miqa ya wuce gida
Gab da magrib ya isa gida, danhaka ya wuce masallaci Saida yayi sallah sannan yatafi gida, yana shiga ita Kuma tafito zata fita, cikin siririyar muryarta tace sannu da Zuwa baba, yawwa Shalele nah, za'a tafi wajan tulawar ne? Eh baba zan tafi, to shknn Allah yabada sa'ah saikin dawo
Ahankali ta amsa da ameen sannan tafice Daga gidan
Dama haka take safe tatafi makarantar boko, da yamma islamiyya, da dare muma tilawa sai takwas da Rabi zata dawo gida
Atabarmar da inna take zaune anan yazube yana fadin wash, wallahi nagaji sosai
Kamar batason magana tace sannu da Zuwa
Yawwa Marka sannu, tashi ki dubomin rob a daki na shafa akafata ciwo takemin
Batare datace masa komai ba tatashi tadauko masa rob din, ya karba yashafa sannan Yarufe idonsa, shiru sukayi da gashi Har ita, shi yana tunanin rayuwar yarsa gudan jininsa, ita kuwa bacin rai ne danqare acikin ranta
Idonsa arufe yace Marka, inaso zamuyi wata magana dake
Aududu ta kwantar agefe Tace inajin ka
Me Shalele tayi Miki Marka?
Babu abinda tamin, kawai de Ina Bata tarbiya ne akan abubuwan dakake yimata, sannan Malam zamanta a gida haka ai ya isa haka, ayi auranta mana
Murmushi yayi, aransa yace Wai tarbiya, jin dalilin nata bawani Mai tushe bane
Afali saiyace Aure fa kikace Marka, dududu nawa yarinyar take dahar za'a yi mata zancen wani Aure! Idan kin manta lissafin ne saina tuna Miki shakerar Shalele goma sha biyar, ni aganina tayi qanqanta da Aure yanzu, kina gani fa yaran gasunan dayawa anayi musu auren dazaran sunzo haihuwa saisu fara yoyon fitsari, saboda yarinya bazata Iya haihuwa da kanta ba
Yanzu de maigida Tunda ba zakayi mataba ai shikkenan saika sata agaba kana kallo kanajin dadi
Bece mata komai ba sai Murmushi dayayi kawai, yasa hannu yadauki Aududu yafita dashi waje, yanajinta tana sakin wani uban tsaki
**********
Washe gari kafar baba ta kumbura tayi suntum, daqyar yake Iya takawa, Shalele Bata saniba, tun da sassafe data gama share gidan tayi wanke wanke, ta tsaya abakin kofar Dakin ta gaida su ta wuce makaranta Bata dawoba
Shikuwa baba yana kwance a daki yahada uban gumi, Marka tana kallansa ta share shi, ahankali yace Marka!
Tanajin sa ta qyaleshi, Saida yakirata yakai sau hudu sannan ta amsa, yace saka mayafinki kije kikirawo min Malam yahai
Saida tagama abinda yake gabanta sannan tatashi ta leqa ta katangar su tace sabuwa, kice wa Malam yahaya Yazo Malam yanasan ganinsa, kafin sabuwa tace to, Har Marka tabar jikin katangar, habarta ta riqe tace tooo
Tana fadawa mijinta yafuto dasauri yashigo gidan, yace Marka Ina Malam surajon yake? Lafiya deko?
Bata yi masa magana ba Kawai nuna masa dakin tayi da hannunta, yayi bismillah yashiga, yana ganin baba akwance yace subhanallah Malam surajo lafiya kuwa? Yana runtse ido yace kafata ce take ciwo tun jiya wallahi,
Yace subhanallah sannu Malam surajo, muje waje sai Naga kafar, da temakon Malam yahai, yakama baba yafuto dashi Daga cikin dakin, acikin rumfar suka tsaya, ya kalli Marka datake zaune agefe yace Marka temaka ki shinfida mana tabarman nan
Tabarmar ta fizgo agefe ta shinfida musu, Malam yahai yana Kallan ikon Allah, haka ya kwantar da Baba yasaka Fillo Daga bayansa, dage kafar wandonsa yayi, ga kafar nan ta kumbura sosai, yace Malam surajo yaushe kafara jin ciwon ne?
Tiryan tiryan baba yabashi labarin komai tun zuwansa gona Har abinda yafaru, sake ganin kafar yayi sannan yace to gaskiya Ina tunanin miciji ne ya cijeka, kokuma wani qwaron me mugun dafi, Bari inje gidan Dan makandi na karbo ma magani, dasauri yafita Bai jira amsar baba ba
Maganin yakarbo Yazo yajiqa yabawa baba yasha, sannan yabashi goro yace wannan namijin goro ne kaci, inde hasashen mu ya zama gaskiya macijin ne to insha Allah zakaji sauqi, Allah yabaka lafiya, baba Bai Iya amsawa ba illa kansa daya Daga, ahankali Yarufe idonsa Har bacci ya daukeshi
Sannan Malam yahai yatafi gida da nufin idan anjima kafin nan baba yatashi saiya dawo
Har biyu saura baba Bai tashi ba, yana bacci saboda jiya baiyi baccin kirki ba
Tana shigowa gidan da sallama abakinta, dashi tafara tozali da gudu ta qarasa wajan inna Marka tace inna lafiya baba yake kwance anan? Meyasa mi babana inna?
Inna tace kaji me uba, to sannu yar Baba, gashinan akwance ai saiki tambayeshi
Jiki asanyaye Takoma gefen sa ya tsugunna, maganin data gani ajiqe akofi duk da batasan kona menene ba hakanne ya tabbatar mata da babanta baida lafiya, lokaci daya hawaye yacika idonta, ganin tana kuka Amma innarta ta share ta ko rarrashi babu yasa taqara volume din kukanta, wannan wacce irin masifa ce take cikinta? Ace uwarka tana fishi dakai tsawon lokaci Mai tsawo haka
Shashshekar datake ne yafarkar dashi Daga baccin dayake, ahankali yace Shalele nah kin dawo? Daga masa Kai tayi, tana share hawaye idanunta sunyi jajir, karan hancinta yayi jajir abinka da farar Fata
Cikin kuka tace sannu baba, kanta ya dafa da hannunsa yace kiyi hakuri Shalele nah, insha Allah zan warke kinji? Sake Daga masa Kai tayi
Yace tashi kije kici abinci kihuta, kiwuce islamiyya, cikin muryar kuka tace baba yau Alhamis babu islamiyya, yace to tashi kije kici abinci karki zauna da yunwa
Tashi tayi takai jakar makarantar ta daki, tadauki kwano tace inna akwai abinci?
Inna tace bandafa dakuba, Iya cikina nayi, saide ki dafa muku, bazan Iya ciyar dakuba
Cikin sanyin jiki ta ajiye kwanon tadauki tukunya tadora musu jallof din taliya yar hausa, kasancewar batada wahalar dahuwa nan da nan tagama, tazuba akwano takaiwa baba nasa, agefensa ta zauna ta rafka uban tagumi
Duk abinda yaje faruwa baba yanajinsu Yarufe idonsa ne kawai Amma ba bacci yakomaba
Bude idonsa yayi yace kici abincin mana Shalele nah
Baba ai kaima bakaci ba, bazan Iya ciba
Murmushi yayi yace to Bari inci, daqyar yatashi zaune, yadauki cokali yafara ci, itama tasaka hannu anasa suke ci tare, inna tajuyo ta kallesu ta zuba tsaki
Baba kuwa Ko Kallan inda take baiyi ba, yaga alama Marka tana jiran Jan kati ne(🤣😃)
Suna gamawa tabashi buta yayi alwala, yayi sallarsa a zaune, duk yanayin hakanne domin Shalele tasaki ranta, Amma shi kadai yasan azabar da yakeji aqafarsa
Har dare Suna nan wajan, itade inna ta dauke danta suka shige daki, baba yace Shalele kiramin Malam yahai yakaini daki na kwanta, kema kije ki kwanta kihuta Allah yayi Miki albarka
Girgiza Kai tayi tace baba
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 17