acikinka
To momy yaushe Zaki kawomin ita?
Momy ta kalli anty jidda, cikin fada akace tun dazu kince Zaki kirashi, nazuba Miki ido, Naga alama bakida niyyar Kiran kema de jidda
Anty jidda cikin ranta tace yau de yar hucewa ce akaina🤣🤣🤦🏻♀
Takira number Bilal
Yana ganin Kiran kuwa yadaga da sauri Dama da tashi da ita
Doctor yagida ya aiki?
Aiki ai Yana wajanki matar aboki 😒
Wanne irin aiki kuma? Aikune da aiki doctor
Yace a a ai yanzu kece da aiki, kidauki yar tawa qwaya daya jal, kikaita gidan aiki, Kinga kuwa ai ke kikai aiki🤣🤭aini bakimin adalci ba jiddah, 😳
(kaikai jiddah Kai tsaye 🤭😳)
Doctor bazaka gaaneba, dogon labari ne, idan muka hadu zanyima bayanin komai
Wallahi doctor akwai matsala, qanina Yana kwance a asbiti saboda yarka, but doctor yace dole sai an Nemo masa abinda yakeso ko hankalin sa zai kwanta, dan Allah doctor na roqeka, kayi hakuri, nayima alqawarin zanyima bayanin komai idan muka hadu
Amma yanzu yaya za'ayi mu ganka yanzu?
Saida yagama shan qamshi sannan yace gaskiya yanzu na tashi daga aiki ne, saide ku Bari zuwa gobe, kusameni a office saimuje
No bani zanzo ba doctor su momy ne
Saida yayi hamdala a ransa Jin iyayen Yaron ne zasuzo, dadin yanda zai nuna musu yarinyar tanada daraja tana amfani
Yace babu damuwa, zan turo Miki adrees din asbitin sai suzo gobe dasafe su sameni
Toshikkenan doctor godia nake
Dahaka sukai sallama, aikuwa a lokacin yaturo musu adrees din komai
Ita Kuma tabawa momy
Sai a lokacin hankalin haneef yadan kwanta
********
Momy tace hajiya hafsat babu lokacin bayani, Ina haneefa?
Tace haneefa tana daki, Afrah jeki Kirata
Afrah na zuwa suka futo tare, ganin su momy yasa gabanta yafadi, lokaci daya tahade girar Sama data qasa
Mami Tana ganin yanayin ta tasan cewa ba lafiya ba
Har qasa ta tsugunna tace daddy ina kwana, momy Ina kwananku
Atare suka amsa Mata, momy tace haneefa kiyi hakuri kinji? Dan Allah ki yafe mana abinda muka Miki, dan Allah naroqeki kiyi hakuri kizo muje kiga haneef, kina sonsa Yana sonki, mukam indan Tamu ne mun amince wallahi🤣🤣
Duk falon ita aka zubawa ido, Kanta aqasa tace momy kiyi hakuri, ni yanzu Bana Sansa
Kowa yayi mamakin furucinta, daddy yace yata kiyi hakuri, yanzu de kizo muje kiganshi Asamu lafiyarsa daga baya ayi maganar komai
Yadubi hajiya hafsat yace kiyi hakuri hajiya mun barki aduhu, kutashi muje asbitin nan gaba dayanmu tunda kuma nan Kuka nufa
Wayar Safah ce tayi qara, tace Excuse me, zan yi magana
Tana futowa daga falon adede lokacin Ameer Shikuma zai shigo, aikuwa sai jikake garam sunyi Karo
Wayarta tafadi qasa, itama tatafi zata fadi Ameer yayi sauri yatarota
Zubawa juna ido sukai, cikin ransa yace cute
Qwace jikinta tayi, tadauki wayarta, Shima cikin sanyin jiki yace Mata sorry, yayi gaba.
(um yau Naga india🤣🤣)
Gaba dayansu suka tafi asbitin Mota uku sukai
Shalele sai kumburi take, wallahi badan Mami tace dole saitazo ba, wallahi da bazata zoba
Anty jidda da Ajmal ne a Dakin nasa, sai gani sukai baqi suna shigowa
Haneef Yana dago kansa yayi ido hudu da shalele, yakafeta da kallo, Ajmal na zungurinsa Amma inaaa🤣🤣hankalin yatafi
Hajiya hafsat na ganin kallan da haneef yake Mata ta fahimci komai, Kenan haneefanta ce take Aiki a gidan su? Kenan haneefa haneef yadauka suka fita qasar waje? Ita din tagani a TV Kenan? Itace momy suka Kora agidansu?
Lalle akwai matsala, dole sai haneef yagane kuransa, aiko ameer dinta ne yadauki haneefa suka tafi wani waje batare da sanin taba dole zata masa hukunci
Dan haka bataga laifin shalele ba, datace Bata sonsa yanzu
Anty jidda tana kallan Samah da Bilal suna hararan juna, tace to yau kuma masifa ce tahadu daa San girma kenan🤣🤣
Tana juyawa taga Ameer Yana satar kallan Safah, itama tana Kallansa qasa qasa 🤣🤣
Tasake juyawa taga shi haneef ya kafe haneefa da kallo
Tayi murmushi wannan tun kafin ayi abin kunya agaban surukai Gara su fice, Allah yaso babu sajidanta 🤣🤣🤣da abin yayi yawa, Dan haka tace daddy, momy, Mami muje waje mudan basu waje
Aikuwa duk suka fice daga Dakin
Suka barsu su biyu
Zama tayi Akan kujerar tana zumbura baki
Shikuwa sai Kallanta yake kamar yaga sabuwar halitta 🤣
Cikin gunguni tace kawai nace bazan zoba bazan zoba sai anmin dole
Yajita Sarai, murmushi yayi yace congrats Ina tayaki murnar samun mamanki, but banji abinda kike fadaba
Cikin fishi tace cewa nayi ni Bana sonka, kuma abiyani bakina, bazan yardaba
Kallanta yayi yace oh really?
(naji korafinku, kuma ngd Sosai, insha Allah zamuci gaba kamar yanda muka saba, nagode Sosai da kaunarku agareni 🙏🏻)
Wanda sukaga banyi musu refly Akan comment dinsu ba suyi hakuri,massages ne sukamin yawa wallahi
Menene zai faru tsakanin Dr Bilal da Samah? Me damo sarkin hakuri Ameer yake nufi da daya sarkin hakurin Safah?
Anya kuwa Haneef zai Samu haneefa cikin sauqi dangane da furucin hajiya Hafsat?
Muhadu gobe idan Allah ya Ara mana lokaci 😃
Mrs Usman ce✍🏻💕SHALELAN BABA💕
(Romance)
Writing by Amnah El
(🙏🏻kuyi hakuri Dan Allah bisa mistek din Dana Samu jiya wajan rubutu, akwai inda ya goge atsakiya, inda su daddy sukaje suka nemi Bilal, da irin Jan ajin daya musu kafin yakaisu gidan hajiya hafsat, dakuma sabanin da suka Samu shida Samah Har suke hararar juna a asbiti, da irin yanayin da momy tashiga itada daddy lokacin dasuka tabbatar shalele yar'uwarsu ce, sannan ne akayi inda daddy yace a Kirata kuma aka Kirata tace bataso, kungane yanzu? To wajan me ya goge wallahi, babu yanda zan gyara saboda nariga nayi posting dinsa, Amma wasu sunce sun gane ahakan, ngd, dafatan za'a Fahim ceni 🙏🏻)
39&40
Yunqurawa yayi yatashi Yana yamutsa fuska, alamar baijin dadi Sosai
Yataso yazo gaban kujerar da take Kai, ya tsugunna, yakafeta da lumsassun idanunsa, sannan yasaka hannunsa yakama face nata, yamatso da bakinsa dab da nata, Cikin sauri ta qwace Fuskarta, takawar da Kanta gefe, murmushi yayi, kikace nabiyaki bakinki, to tayaya zan biyaki idan banyi Miki irin nada ba?
Kallansa tayi tafashe da Kuka, ta Dora Kanta Akan jinyarta tana Kuka Sosai harda shashsheka, Shikuma gashi a tsugunne a gabanta, Hakan da tayi saiya qara musu kusanci Sosai
Meyasa take Kuka? Anya kuwa su momy basu zagi yarinyar nanba? Jin kukannan nata yake Har cikin ransa, jiyake kamar yajata ya rungume ta a jikinsa ko zaiji dadin lallashinta
Sumar kansa yashafa, yayi ajiyar zuciya, kansa yamatso dab da nata datake sunkuye tana Kuka, saitin kunna ta yasaka bakinsa, "kiyi hakuri, nasan iyayena sun Bata Miki rai, kuma nasan cewa abinda suka Miki ne Nima yashafeni Har kika fadaamin wannan maganar,
(aikwa de hakane shazali tunda a lokacin Ina ganinta ta lumshe ido 🤣🤣🤣)
Yaci gaba da cewa amma kiyi hakuri, nizaki duba basuba, Dani Zaki zauna ki rayu kiyi Zaman aure Dani basu ba, Koda ace kowa baya sonki aduniyar nan ni Ina sonki haneefa, kiduba kiga halin danake ciki, soyaiyarki ce tasa na kwanta a gadon asbiti, kiyi shiru, insha Allah komai zai wuce, watarana su momy zasu soki, kiyi hakuri, kada kisake cewa bakya sona, inba hakaba wallahi zan tabbata a gadon asbitin nan
Yahade hannayensa kiyi hakuri, ki yafewa iyayena 🙏🏻
Adede lokacin iyayen nasu suka dawo Dakin, anty jidda na ganin qaninta a tsugunne agaban shalele mamaki yakamata, lalle soyaiya Mai gyara mutane, yau haneef dinta ne agaban qaramar yarinyar nan, kome yake rokonta? Oho musu
Jin sun shigo dakinne yasa yatashi yakoma gefen gadon sa ya kwanta
Mami tace a a Dana wanne kwanciya kuma Bayan ka ware Sarai, Saida ka ganmu zaka koma Kan gado ka nade 🤣🤣
Duk Dakin sukai Daria
Daddy yayi gyaran murya yace to alhmdlh, godia ta tabbata ga Allah daya bamu ikon haduwa a wannan wajan, yadubi shalele da idanunta sukai jajir saboda Kuka yace Haneefa takanki zan fara, kiyi hakuri dangane da sabanin fahimta da aka saamu, munsan cewa mu masu laifi ne agareki, Amma kiyi hakuri komai ya wuce, kada kisake cewa bakya son haneef, Koda bakya yimasa so na aure aayanzu Kam haneef dan'uwanki ne, dole Zaki soshi kuyi zumunci
Kiyi hakuri kinji yata? Ahankali ta share qwallar idonta, tadaga masa Kai, haneef Yana Kallanta, bayasan kukannan datake, jiyake kamar Shima yayi, Amma tayaya ta zama yar'uwarsa?
Daddy yakatse masa tunani da fadin, haneef, Samah, Safah, dakuma ke jidda, Haneefa yar'uwarku ce, itace yar gidan qanwar mahaifiyar ku, ke jidda da haneef zaku Iya saninta, nasan iklas da fadilama zasu Santa, yanayin rayuwa ne yasa tazo Aiki gidanmu, kuma alhmdlh mungodewa Allah dayasa zuwan nata yazama me mana alkhairi gaba dayanmu,
Sannan ya nuna musu Mami yace nasan kun Santa, duk da ba ziyartar juna akeba, wannan itace wadda suke ciki daya da zainab mahaifiyar haneefa, ga babban danta Ameer, dakuma qaramar Afrah
Hajiya hafsat kiyi hakuri, munsan cewa abin babu dadi, Amma idan Zaki duba zakiga komai yafaru ne bisa rashin Sani, kuma munyi DANA SANI Akan Hakan
Mami tace babu komai Alhaji, Allah yakiyaye gaba, Dukansu sukace amin, doctor yazo zai duba jikin haneef sai gani yayi daki yacika dam da mutane, yace a a, yau ko Dan qaramin biki ake a Dakin ne?
Ajmal yace ai wannan yawuce qarami doctor saide babba 🤣
Yace to masha Allah, Bari na dubashi, Yana juyawa sai yaga Dr Bilal, yace a a kamar babban doctor nake gani
Bilal yayi murmushi yace wallahi nine, nazo ganin marar lafiya ne tare da yata
Wacece yar taka? Yanuna haneefa yace gatanan a zaune, ai itace yarinyar da marar lafiyar taka yake nema
Cikin Daria doctor yace alhmdlh, gaskiya naji dadi, to ai kawai Bari nabaku waaje saika dubashi
Dr Bilal yace a a haba doctor qarasa aikinka wlhy, Nima daganan wucewa zanyi nakoma wajan aiki
Likitan ya dubi daddy yace Alhaji wannan abokin aikinmu ne, Amma sune manyanmu, Aida nasan kun sanshi da tun farko ma can wajansa zan turaku
Samah tayi sauri tace ai doctor nan dinma yayi, mungode
Tajuya ta kalli Dr Bilal tasaakar masa harara, Shima anasa bangaren hararar yasakar Mata
Doctor na dubashi yace zasu Iya tafiya, idan wani Abu yataso zasu Iya zuwa wajan Dr Bilal
Tashi sukai suka tafi, haneef farin ciki yacikashi, ashe ma yar'uwarsa ce, aikuma yanzu maganar momy taqare, saura ta daddy, Shima insha Allah komai zai wuce
Suna zuwa harabar hospital din, momy tace ai hajiya hafsat saimu wuce gida gaba daya ko, Kinga yau sai mu wuni tare
Mami tace hajiya muje
Shalele ko kallan haneef batayi, Ana cewa a shiga Mota ma cikin sauri tashige, haneef na ganinta, yasan saboda shi take komai
Mazan ne suka dakata, sukuma Matan suka tafi,shima Bilal yayi musu sallama yatafi, Saida su momy sukaje gida sannan saminu yazo yadaukesu
Suka tafi gidan suma, direct part din haneef sukayi, Ajmal yace lover boy, yanzu shikkenan ka ware ko? Wai Dan Allah abokina me kake rada Matane muka shigo Dakin
Hararar sa yayi yace to bazadai kajiba, wannan sirrin Wanda suka kusan shiga daga ciki ne 🤣
To idan tayi tsami maji☺
Ai bazatayi Bama
Ameer yayi Daria yace wa Ajmal tokai kaji sai kayi hakuri sirrinsu ne
Ajmal yace rabu dashi Ameer, zaiyi bayani ne
********
Yanmatan Dukansu suna dakinsu Samah, afra ta miqe agado tana daddanna waya, Samah takamo hannun shalele tace kiyi hakuri yar'uwata, nasan nayi Miki laifi Mai yawa, Amma kiyi hakuri ki yafemin, Kodan yayana da yar'uwata
Nima wannan masifar tawa tana damuna wani lokacin 🤣🤣wallahi, kuma duk saurayinki ne yagogamin wallahi, dan Bahaka yanbiyu na takeba Safah
Afrah Tai Daria takalli shalele tace toke saiki zauna tana fadawa saurayinki magana
Safah tace kiyi hakuri antynmu, komai yawuce, adena tuna baya
Murmushi tayi tace babu komai Safah, Allah yakiyaye gaba kuma
Bari inje wajan baba Hanne, ta yunkura tatashi, Samah tariqeta tace a a wallahi, babu inda zakai zama zakiyi muyi fira
Safah tace ni wallahi harna matsu ma Inga aurenku keda Yaya, saboda Inga yanda zai nuna Miki soyaiya, idan kaganshi haka kamar bazai yiba
Amma nasan mutane masu shiru shirun nan, sun Iya soyaiya Sosai, akwai lokacin Dana ganku afalo kuna Daria, sainaga kamar ba yayan Dana saniba
Samah tace Nima sun birgeni lokacin Dana gansu afalo tana mopping Shikuma Yana gefenta yawani Matso Yana Mata rada, baki gansu ba wallahi
Afrah tace Amma ku kuwa kuncika Yan sa'ido wallahi 🤣
Samah tace a a barmu mugani, taa kalli shalele tace wannan baban naki yacika son girma dayawa wallahi, kamar shi yafi kowa, jiyafa da zamuje gidan Mami nazauna akusa dashi amota wallahi haka yasa kafa ya danne min kafata, bakiji zafi ba, gashi fari tass Amma zuciyar sa baqa😏
Shalele tace kede Samah kifadamin gaskiya idan kina ciki, Kinga Dan fari zubin larabawa
Haba de sister haneefa, harfa cewa yayi zai zaneni, idan na aureshi kuma ai dukana zaiyi
Afrah tace Nima ina ganin ku a asbiti kuna hararan juna, wasu kuwa kallan kallo suke qasa qasa waisu ustazai 🤣🤣
Safah tayi murmushi laaa Wai Yaya ameer ke babu komai wallahi, kawai Kallansa nayi sai aka Dace Shima ya kalleni
Afrah tace um wannan kallo kuwa da yawa yake🤣🤣
Samah tace waike Afrah dawa za'a yi?
Saida tayi fari da idonta 🙄wallahi wani Dan abokin daddy ne, Yana Lagos, a India nahadu dashi
To Allah yakaimu musha biki, inji shalele
Duk sukai caaa akanta, bikinku de
Rufe kunna ta tayi tace nashiga uku, to naji🤣
********
Dukansu sun hadu a dining suna cin abinci, haneef Kam babu kunya yaje ya zauna akusa da kujerar da shalele take
Sunacin abincin wasu na satar kallan juna su ameer Kenan 🤣
Wasu kuma suna Saka ido irinsu afraah da Ajmal 🤣🤣
Shikam haneef ko kallan shalele bayayi, itama haka
Mutanan wajan kuwa kowa Yana mamakin wannan sharewa tasu, shi kansa Ajmal yayi mamaki
Garin Kalle kallan nasa yaje ya qware🤣
Yafara Tari,ya sunkuya yariqe kirji
Safah dake kusa dashi tabashi ruwa
Wai kawai dagowar dazaiyi saiyaga kafar haneef Akan ta haneefa 🤣🤣tab gaskiya shazali Dan duniya ne
Shine asama ya nunawa mutane babu ruwansa da ita, Amma daga qasa Yana abinda yaso, ashe shiyasa ya maqa daga gefen ta
Shazali na ganin Ajmal yaqi dagowa yasan cewa yaga komai
Safah tace Yaya Ajmal ga ruwan, sannu
Dagowa yayi yace yawwa qanwata, ya kalli haneef, kallan nasan komai 🤣
Shima yadaka masa harara
Yaci gaba da shafa kafarta da tashi kafar, Sarai tana jinsa, Amma ta shareshi, duk wani iri takeji, tajanye kafarta yasake Dora Mata, kowa ya kalleshi bazaice wani Abu yana faru ba, Amma itakam ta naji ajikinta, sai kuma Ajmal daya gansu🤣🤣
Al'amarinsa Yafara fin karfinta, Bata isa tace yabiyata ba🤣, tunda dazu ma data fadi haka taga abinda ya biyo baya
Dan haka ta share shi, Har suka Gama, da zasu tafi ameer yakoma wajan Mami ya yi Mata rada
Tace Dan Allah ameer ya kyaleni
Momy tace meyake faruwa ne hajiya hafsat?
Ameer naji momy tayi magana yayi wuf yafice daga falon
Mami tace tun dazu Yaron nan yadameni Wai a fadawa daddy shi Yana son yanbiyu, shine yanzu yake sake cemin Wai kada namanta de🤣
Momy tayi murmushi tace towa yakeso acikin su?
Koshi Yana Iya banbancesu?
Afrah tace momy Safah ce wallahi
Safah kuwa kamar tashige cikin qasa Dan kunya, cikin gudu Takoma dakinsu 🤣
Momy tace to ai shikkenan, kuma menene abin boye boye baanda abin ameer, ai Dani yasamu Kai tsaye ya fadawa
Mami tace ai ameer dakike ganinsa Har yafi wata macen kunya
Momy tace ita ma Safah haka take, Allah yasa ayi Damu
Duk sukace amin
Momy tace Amma de hajiya ai zakibar shalele anan gidan kukutafi ko, tunda Dama anan take
Mami tayi murmushi ai hajiya an maidata makaranta, gobe zata fara zuwa, yauma abinda yasa batajeba saboda zuwanmu nan ne
Lokaci daya kunya takama momy, meyasa ma tayi wannan tambayar, duk Zaman yarinyar agidansu Basu taba tunanin Sakata a school ba, Allah de yakiyaye gaba
Tace toshikknn yaushe abbansu zai dawo?
Gobe zai dawo
Toshknn Allah yakaimu, muma zamuzo idan yadawo din
Haka suka tashi suka fara haramar tafiya, haneef ya matsa kusa da Afrah yace qanwata idan kunje gida Dan Allah kice tabude wayarta
Afrah Tai Daria tace to yayanmu
Shalele taje kusa da anty jidda tace mama zamu tafi, kicewa sajida da ayaz zan kirasu
Aimunyi fishi haneefa
Kiyi hakuri mama, naso nazo gidanki Bayan nabar nan, Amma kiyi hakuri,
Toshikknn haneefa ki kiramu iidaan kunje
Duk sukai rakosu wajan Mota, suka shiga suka tafi, Ajmal da haneef sukayi hanyar part din haneef din
Ajmal yace Wai Naga mutuniyar taka sai fishi take dakai
Meyake faruwa ne Naga mutuniyar taka sai basar wa take
Murmushi yayi, zata Dena, fishi take Dani
Ajmal ansamu abinda akeso, shide arayuwarsa Yana so yadinga Jin dramarsu 🤣🤣🤣
Yace fishin me?
Wai fishi take saboda nayi kissing dinta
Kiss haneef😳😳
Innalillahi....
To sarkin kwakwazo, menene aciki danna fadama gaskiya, kissing dinta nayi, shiyasa take fishi kuma nabata hakuri, itama abin dayasata fishin nasan abinda su momy suka Mata ne, Amma a lokacin ai batama nunamin komai ba,
Ajmal yace lalle haneef Kai Dan duniya, inbanda iskanci kayi abun kazo kana fadaamin haka
To Kai nasan me kakeyi da yata?
A a a a, mezan Mata shazali? Inda nine nayi Mata ai sai ka daure ni
Babu wani dauri Ajmal, kawai ni abinda nasani shine da inje inyi Abu aboye, Gara inyishi afili, Wanda suka nuna basayi din ai ba'asan me sukeyi aboye ba, itama kuma nasan fishi ne yasata fadar haka, insha Allah zata yi hakuri
Ajmal yace eto kanada gaskiya
To shine take fishi, Wai dazu ma ita Bata sona, nabiyata bakinta
Me Ajmal zaiyi inba Daria ba, bakin zaka biyata?
Haneef yace to yarintarfa, Aida ta tsaya Dana biyata, kaga daga nan ma nasake tsotsa
A a shazali kafi karfina, wannan Gara ayi muku auren nan muhuta
Ayima na gaba daya de muhuta, dan renin wayo
********
Bayan kwana biyu su daddy sukaje gidan hajiya hafsat, nemawa haneef auren haneefa shida makusantan abokansa
Daddy yace to Alhaji Tahir, kaji kaji abinda yakawomu
Alhaji Tahir yace to ai Alhaji bukar, wannan ba abin damuwa bane,saide wannan yarinyar akwai babanta Bayan ni, mahaifinta tun kafin yarasu yace yabashi ita halak Malak yariqe ta amatsayin Uba, dan haka Bari nakirashi nasanar dashi halin da ake ciki, nan kuwa aka Kira Bilal yace zaizo daga baya, yabashi Dama yayi komai, ai Shima mahaifinta ne,
Nan daddyn Afrah yayi masa godia yaakashe wayar, sannan yadubi su Alhaji bukar yace, Dama Nima inaso inzo da tawagata nemawa Dana ameer auren yar wajan ka
Daddy yace toshikknn, Kunga saiku bamu mu Baku 🤣
Alhaji Tahir yace to munbaku haneefa, Shima daddy yace muma munbaku Safah
Babu Bata lokaci anan wajan aka tsaida ranar aure nanda wata daya
Alhaji Tahir yace saide kuma wani hanzari ba gudu ba kasan yarinyar tana ma karanta a yanzu
Daddy yace a a wannan ai ba abin damuwa bane, Nima yaran wajena University suke shirin tafiya, kaga kowa sai tayi karatunta a Dakin mijinta
Nan da nan kuwa kowa yayarda da wannan hukunci na daddy, aka sake gaisawa sannan suka tafiya gida domin yasanar wa dasu momy hukuncin dasuka yanke
Shima Alhaji Tahir yashiga gida domin sanarwa da hajiya hafsat abinda yake faruwa, yashiga gidan da goron sa da alawa nasaka Rana
(kuyi hakuri da wannan Banda chrgi ne wallahi ngd🙏🏻)
Sharhi, comment, share to others groups Dan Allah 🙏🏻
Amnah El ✍🏻💕SHALELAN BABA💕
(Romance)
Writing by Amnah El yaqoub
41&42
Yau gidan anty jiddah anyi baqi, yanbiyu sunzo sai fira suke da sajida, kasancewar ba zuwa suke Sosai ba, sai zuwan nasu yayi Mata dadi
Anty jidda na waya da mijinta adaki, Bayan sun Gama takira Bilal
Tace doctor Har yanzu Baka zoba Akan maganar danace zamuyi shekaran jiya
Jiya kuma bakabimu gidan momy ba daga asbiti saika wuce wajan aiki
Yace eh wallahi, bansamu lokaci nazo ba, Amma yanzu Dama zanje gidan hajiya hafsat, kawai zan shigo tanan, daganan Saina wuce
Tace to saika zo
********
Yana shiga cikin falon yaganta a harde akujera, cikin fara'ah ya Bata goro da alawar hannunsa yace hafsat riqe wannan
Tasa hannu ta karba tana binsa da kallan mamaki
Na menene wannan Alhaji?
Nasaka ranar yayanki ne, ameer da haneefa, nanda wata daya insha Allah za'a daura musu aure, saiki fara shirye shirye
Wanne irin aure Kuma Alhaji? Yarinyar Dana maidata makaranta?
Ita hajiya Amina Aina fada Mata namaida yata makaranta abinda suka kasa yimata
Kwana da kwanaki tana zaune agidansu, amatsayin me aiki, sun zaunar da ita tana musu bauta, sannan ni da take musu aikinma bantaji haneefa tacemin tana karbar kudinsu ba, saide faman wahala datasha
Tsakani da Allah abban Afrah, gida de kamar gidan Alhaji bukar tayaya zasubar ma'aikatansu batare dasun sakasu a makaranta ba, aiko yar islamiya ce sa sakasu aciki
Kuma haka kawai saboda rashin adalci dason Kai irinnasu suzo dawata magana ta aure?
OK sai yanzu ma nagane, saboda dansu Yana kwanciya jinya saboda ita, shine za'a katsewa yarinya karatunta ace za'a Mata aure, bazai iyuba
Ajiyar zuciya yasaki, to yanzu hafsat me kike so ayi?
Kaje kafada musu cewa ni nan, nace bazan Bawa dansu auren yata ba, ai itama tanada gata ba marar galihu bace, shide ameer din tunda namiji ne kuje kuyi masa, Amma Banda haneefa
Yanzu ni din kike so naje nasamu shi Alhaji bukar da wannan maganar?
Cikin fishi taace toshi kuwa yazo yasameka da ita? Qarewa mafa Yaron nan zuwa yayi yadauki haneefa yafita qasar waje da ita, yarinyar Bata nuna masa korafin komaiba, sannan Bata samu iyayensa tafada musu maganar ba
Saikace wata marar gata, wallahi baban Afrah ko ameer dinane yadauki haneefa suka fita wani waje batare da sanina ba dole zan hukuntashi Akan haka
Idan yarinya bame kamun Kai bace wayasan mezai faru?saboda kawai suna taqamar cewa ita yar aikin su ce? Shin masu aiki basuda iyaye ne? Kokuma idan andaukesu aiki Hakan Yana nufin za'a iyayin komai dasu?
Kuma still yanzu azo ace Wai anbada ita, saboda me? Bazai iyu Bama Alhaji, kamaida musu kayansu, ta watsar da goron aqasa 🙆🏻😭
Hannayenta yakama yace hafsat, kiyi hakuri, nasan Yaron nan da iyayensa sunyi Mata laifi, kuma sunzo Har gida sun Bata hakuri kema kuma sunbaki, sannan sun sake neman yafiyarku
Kisani Allah mafa muna masa laifi kuma yayafe mana
Bare mu Yan Adam, yanzu hafsat idan kikace nakoma namaida musu kayan Saka ranarsu, mekike tunanin zai faru? Kina nufin suma zasu Bawa danmu ameer yarsu ne?
Hafsat bazasu bashi ba, saboda muma mun hanasu tamu yar
Alhaji Dan Allah kadenamin maganar wannan marar mutuncin Yaron 🤣🤣tatashi fuuuu tayi dakinta, Alhaji Tahir ya girgiza kansa sannan ya tsugunna yasaka hannu ya tsince goron da alawar
Cikin ransa Yana cewa nide bazance komaiba kiji babu dadi kice nayiwa Dan yar'uwarki maganar daba daidai ba🤣🤣🤣
********
Yana zuwa yadanna door bell, Sajida tatashi tabude, tana ganinsa tasaki murmushi laaa uncle ashe Kaine, sannu da zuwa
Ashe yau da babban baqo kazo mana, kawoshi, ta meqa hannu takarbi Aududu dake hannunsa
Tajuya tana cewa Bari nakira mama
Yace to Sajida, Yana qarasowa cikin falon
Akujera ya zauna, Safah takalleshi tace uncle sannu da zuwa Ina yini?
Cikin fara'ah yace Lfya Alhmdlh, Yaya school
Laaa uncle ai munyi candy
Yace to masha Allah, kice yanzu sai University
Kafin Safah tasake magana
Samah tace masa Ina yini, batare data kalli inda yake ba
Shima Yace lafiya ataqaice,🤣 wato wannan yarinyar shi zata gaisar asheqale ko,yagama lura bataso ma ta kalleshi, to menene da jikin nasa daza'a qi Kallansa?
Itama anata bangaren takaici ne yakamata, ita bazai tambayata ko Yaya gida ba? Batakai ba Kenan
Safah na kallan su tana Daria cikin ranta
Tasake dubansa tace uncle ashe kaima kana zuwa gidan anty jiddah
Ina zuwa mana, tunda yata tana gidan ai dole nazo
Daria tayi tasake cewa to ai yanzu Bata nan uncle, ko wajan wata kazo🤣🤣
Dasauri yace no, no, nazo wajan antynku ne, daganan kuma zan wuce wajan haneefa
Aikuwa uncle muma saimu bika muje muganta, rabonmu da ita tun shekaran jiya
No kusa driver yakaiku, bancika son damuwa ba wani lokacin 🤣
Haba uncle wacce irin damuwa kuma Ana zaune lafiya?
Kema de da shegiyar jaraba kike wallahi Safah, Ana yageki kina qara liqewa a'inda bakida kwarjini, cewar Samah 🤣🤣
Cikin fishi Shima ya kalli Samah din yace ke wato bakida kunya ko? Ba'a Isa dake ba, ba'a Isa asaki bako?
Dede lokacin anty jidda tazo tatarar da wannan rikicin nasu, Safah kuwa Daria kamar me, in Banda Abu irinna uncle Bilal meya Saka Samah din taqi yi? 🤣🤣
Harda cewa ba'a Isa asata tayi ba🤣🤣
Anty jidda tace sannu da zuwa babban doctor
Yawwa anty
(mamaki yakamata, yau Bilal dinne yace Mata anty🤭to inajin de da biyu🤣)
Ta Kalle su tace kutashi kukoma daki, zanyi magana dashi
Safah tace anty, sannan ta kalli Bilal tace uncle inkun Gama ka tabomu saimu wuce
Suna tafiya anty jidda tace Dr Dama zan Baka hakuri ne Akan komawar haneefa gidanmu, banyi Hakan dawata manufa ba, saide Inada babban dalili na
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 13 Chapter of 17