Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

azzalumi, Allah ya isa na, wuta balbal Dan iska
Ta kwasa da gudu tashige dakinta, tasaka sakata, sai huci take, jikinta ko'ina yana rawa
Tana jinsa Yazo gaban dakin nata yadaga murya Yanda zata jishi yace yarinya dakin tsaya kema aida kinji dadi, abin nakima babu laushin kirki da alama nine nafara tabawa, saide Kuma da alama zasuyi girma sosai, kinyiwa kanki, yajuya yafice Daga gidan
Tanajin fitar sa tasaki Ajiyar zuciya, Bai Dade da fita ba su inna suka dawo, tanajin ta tana kwala mata kira, tadaga murya tace inna zazzabi nakeji na kwanta Saida safe

********
Washe gari da safe ta shiga gidan baba Malam suka gaisa, sannan tadawo gida, babu wani Abu da inna ta nuna mata, suna zaune lafiya, Har la'asar, ta shiga daki tana sallar la'asar inna tace Shalele!!!! Dasauri tashafa Addu'ah ta futo, tana futowa taga inna dawata mata gabjejiya, taci kwalliya taci uban mayafi, ta Cewa matar Ina wuni

Ladidi tace lafiya, sannan ta kalli Marka tace to ni zan wuce Marka, inna Marka tace Shalele baki gane wannan bako? Daga Abuja take, maqociyar Hajiya Hafsat ce yayar mamanki, jiya muka hadu nake cemata muma ai Gobe zamuzo

Cikin tsananin murna tace laaaaa Dan Allah kinsan yayar mamata? Ladidi tace yanzu hakama dazaki bini Har wajanta zan kaiki

Inna tace ah meze Hana, Shalele kawai kibita, Tunda muma gobe zamu biyo bayanku dasu Malam yahai, saiki dauki wasu kayan ma kiyi gaba dasu, sauran nakawo Miki goben

Dasauri tace to, tashige dakinta Bata dauki komai ba sai kayanta Kala biyu da photon baba, ta futo suka tafi, inna tace insha Allah muma da safe zaki ganmu kinji? Shalele cikin murna tace to inna saikun zo

Sun futo Daga gidan ta dubi ladidi tace Dan Allah zanyi sallama dasu baba Malam, ladidi tace to shiga amma kiyi sauri
Shalele tashige gidan baba Malam ta inna sabuwa Ina baba Malam, sabuwa tace Malam yafita Shalele, Ina zaki da kaya ahannu?

Tace Abuja zamu, inya dawo kice masa sai sunzo

Inna sabuwa Malam yahai baiyi mata bayanin komai ba jiya, tayi tunanin da wannan baqon likita zasu tafi, danhaka tace to Allah yakiyaye Shalele, tace amin tafice da gudu

Suna fita suka yi bakin titi, suka tare mota suka shiga sai cikin Abuja, tafiya anayi da dadi ba dadi Har dare, mota duk aragargaje, tun tana Kallan hanya harta dawo ta daina ta kwantar da kanta acinyar ta

Sai dare suka isa gidan ladidi, gidane Dan qarami Mai kyau madedeci, daki biyu da falo da tsakar gida,ladidi tafada cikin kujerun falon nata tace wash Allah nagaji wallahi

Shalele kuwa ta zauna akan hannun kujera tace Toni intafi idan kin huta kyazo? Inane gidan Daga ciki? Nagaba ne kokuma wannan na Bayan damuka Bari?


Ladidi ta kalleta tace kije Ina? To Marka aikatau tace nadauko ki nakawo ki Abuja






Kekam Shalele kina ganin dalala 🤣🤣🤣


(tab gaskiya gobe akwai kafce, 💪🏻, menene zai faru idan Bilal Yazo ya iske wannan labari? Anshaqe mata wuya ma yayi mari to inaga ya nemi yarsa 😃😃😃😃yarasa??

Yaya makomar inna Marka gobe?

Duk kubiyoni gobe danjin mezai kaya









Dan Allah Sharhi da comments 👏🏻




Amnanku ce ✍🏻

💕SHALELAN BABA💕
(Romance)

Writing by Amnah El

17&18

Tsananin mamaki ne yahanata magana, aikatau? Batasan lokacin data zame dagakan hannun kujerar datake zaune ba, sai jinta tayi jagwab aqasa
Ladidi tijara tace menene abin faduwa, nabata dubu hamsin kudin aikinki Kenan na wata daya, saboda akan haka nake bada farashin yaran danake bayarwa aiki

Zuwa yanzu Kam Zuciyar ta ta tsike, idanunta qamas babu alamar kuka, meta yiwa inna Marka ne haka datakesan ganin bayanta?tukunnama su waye dangin mamanta? Su waye? Huci tafara Kamar zakanya, idan tayi karatu tazama lauya! Idan tayi karatu tazama lauya saita kashe inna Marka (😠😣😠gaskiya Shalele yau rai yakai mutuqar baci)

Ladidi tijara ganin yarinya ita kadai tana huci Kamar kububuwa tace, zaki dakenine saboda nafada Miki gaskiya? Kinga yarinya ni babu abinda yadameni dake, bazaki rasa ci da shaba agidana, Abu daya nasani bazan barki kije ko'ina ba, batare dakin biyani kudi naba, ki danqamin dubu hamsin indanqa Miki kudin Mota kikoma gidan ku, inba haka ba kuwa Sunana ladidi tijara wallahi tijara zan nuna Miki

Hawaye ne yazubo mata, Bana komai bane saina haushin kanta dataji saboda rashin karbar number uncle Bilal jiya, Allah sarki, yanzu haka yaji ajikinsa ne bazai sake ganinaba shiyasa jiya yacemin shi tuban inna Bai kwanta masa Arai ba
Hannu tasa ta goge hawayen idonta, yanzu Kam Ko ance mata ga hanya Takoma Garin kuje babu inda zata, da masifar yawale zataji Daga karshe ma ya lalata mata rayuwa kokuma da rashin dangin uwa da uba? Yanzu dama inna batasan inda dangin mamanta suke ba shine jiya tayi tuban muzuru ta nuna musu zata kaisu gidan?

Bazata taba komawa kujeba sai tayi aikin da inna ta Dora ta akai, tasamu kudi tazama lauya, Daga karshe taje takashe ta
Allah yakareka Aududu, Allah yakareka a duk inda kake


Kayan hannunta ta zubar aqasan ledar falon ta futo tsakar gida, ladidi na kallanta batace komai ba, aranta tace yarinya bani kudi na, nabaki hanya
Ita kuwa Shalele alwala tadauro tadawo falon ta kunce Dan kwalin kanta ta shinfida tafara rama sallolin dake kanta na magrib da ishsha'i
Ta Dade tana ma kanta Addu'ah itada Aududu, sannan tashafa, ladidi ta tashi takawo mata abinci jallop din shinkafa tace ga abinci kici, girgiza kanta tayi batare da tace mata komai ba, tabe baki tayi ta dauke abincin ta

Awannan wajan datayi sallah anan ta kwana, ladidi tabata wajan kwanciya tayi banza ta qyale ta, itama kuwa ta shareta tashige daki ta dauko katifa babba tashinfida a falon tayi kwanciyar ta, Shalele na zaune akan Dan kwalin ta, anan wajan tazame ta kwanta itama

********
Washe gari da safe wajan karfe goma, wani Alhaji yayi sallama yashigo sai kada key din motar dake hannunsa yake, Bayan sun gaisa da ladidi yace ladidi akwai yarinya kuwa wadda zata dinga yiwa iyalaina wanki da guga ? Shalele tana jinsa tana zaune agefe Ko ina kwana batayi masaba (lalle Shalele ankaita karshe😅😂🤣)
Dasauri ladidi tayi zuruf tace ah haba Alhaji Yusuf ai ba'a rasasu a gidan nan, Bana rabo dasu ai, yanzu ma ga wata nan a zaune idan tayima, ta nuna masa Shalele 😃😃kallanta yayi, yaga yarinya Kamar dutse Ko motsi batayi, yace no ladidi wannan tayi qarama dayawa, bazata Iya daukar nauyin aikin gidanaba, zan dawo wani lokacin Ko za'a samu wata, haka yafice,Shalele tabi bayansa da harara, Dan renin hankali, in banda ma rayuwa harya isa ya kalleta yace tayi masa wanki? Tona ubanta ma batayiba bare nawasu iyalansa😀😃😀

ladidi tazubawa Shalele ido, tayi qwafa

********
Sabuwa yi kokari ki daukomin asuwaki na a daki in samu in fita kofar gida injira Yaron nan likita, nasan yanzu duk inda yake yakusa Zuwa mutafi

Sabuwa tace a a Malam Ina zakuje? Yace Abuja zamu shiga, zamu Kai Shalele wajan yayar mahaifiyar ta

A a Malam ba jiya jiya shi Likitan Yazo yadauki shalelan ba da yamma? Jiya tazo tamin sallama zata tafi,harma ta tambayeka nace kafita, Dama batare take dashi ba?

Gaban Malam yahai yafadi yace Wai wacce shalelan kike nufi ne sabuwa? 😳

Sabuwa tace Shalele nawa ce damu Malam?

To meyasa baki sanar daniba tun jiya sabuwa?

Kamarya? Wai kana nufin baka saniba?

Wajan zama yanema yazauna jagwab aqasa yadafe kansa dake masa ciwon nan take yace sabuwa kin kasheni🤦🏻‍♂🙆🏻‍♂😃

*******
Nnamdi Azikiwe international Airport

Cikin takunsa na qaqqarfan namiji yafuto Daga cikin Airport din, yana dauke da brief case dinsa ahannu

Matum biyu ne majiya karfi suka qaraso gareshi da sauri, daya Daga ciki yayi sauri yakarbi jakar hannunsa, dayan kuwa sai muzurai yake yana Kalle Kalle awajan
Kamar kullum yauma wankan Suit yayi, Amma fara, sosai yayi masifar kyau, Kamar ka saceshi, suna futowa waje yanufi wajan da motocin sa suke jere guda uku, daya Daga cikin guard din ne yayi saurin bude masa motar tsakiyar Prado launin ash color,number motar ansa SHAZALI NO.4 yana shiga suka rufe sukajashi Zuwa gida

Megadi najin dirin motocin yatashi yabude da sauri, suka shigo, bude masa motar sukai yafuto, aka biyo bayansa da brief case dinsa

Saida suka kawo shi Har bakin kofar falon sannan yakarbi jakar sa, yace zaku iya tafiya, yajuya yayi cikin falon
Momy na zaune dawasu yara yanmata guda biyu, daya na danne danne awaya, daya nayiwa wani yaro karami home work
Salamu alaikum

Gaba dayansu suka dubi maiyin sallamar, dasauri yaran suka fara Cewa Yaya sannu d Zuwa, daya tashige daki, itama dayar takama hannun Yaron zasu tafi daki, momy tace ke samah, barmin yarona anan, kude kuje

Murmushi Haneef yayi yace to Yanzu momy ni Daga dawowata kinji nayi musu magana ne?

A a ai Kai dinne halin ka nasani Haneef, yanzu zaka fara masifa babu gaira babu dalili

Murmushi yayi baice mata komai ba dama itama batasa ran zaiyi maganar ba

Tace Yaya tafiya? Ansha Italy

Lallausar sumar kansa yashafa yace momy kwana biyun? Ko kinyi missing Dina ne?
A a wanne missing? Inrasa wazan yi missing sai tsohon tuzuru?

Momy I'm tired, zanje part Dina, dasauri yafice yabar falon yayi part dinsa

Yana shiga tun daga falo ransa yafara baci, hannunsa yasa akujerun falon farare, sannan yaduba hannun yaga qura ajiki
Dakin yashiga, ya cire takalmin kafarsa, Taku daya biyu yayi, sannan yakai dubansa ga safar kafarsa, ya cire safar yayi jifa da ita, yafuto yanufi part din momy rai abace, meyasa yaran nan suka renashi ne? Koda yaushe sude kawai burinsu subar masa dakinsa da datti, daki duk ya lalace ko'ina qura

********
Yana parking motarsa yaga Malam yahai zaune a kofar gida yayi tagumi, futowa yayi daga motar yabashi hannu suka gaisa, yace a a yanaganka a zaune anan, tashi mu qarasa mana, yakamata ai su futo mutafi da wuri
Baba Malam yace likita akwai matsala

Wacce irin matsala Kuma? Meyake faruwa ne? Baba Malam yakwashe komai yafada masa Kamar Yanda sabuwa tabashi labari

Becewa baba Malam komai ba yanufi gidan Marka, baba Malam yayi sauri yariqoshi yace tsaya likita mekake shirin yi?
Baba Zuwa zanyi intisa qeyar Marka takaini gidan da takaimin yarinya, domin na tabbata dole akwai saka hannunta aciki, nide banzo na dauke taba, Toda wanne shege zatayi tafiya? (tofa kaji masu yarinya😃😀🤣)

Baba Malam ya lura idan yabar Yaron nan yashiga to za'ai batacciya Dan haka yace muje, muje wajanta tare
Suna shiga gidan kuwa inna na zaune Atsakar gida, ta Dora kafa daya Kan daya, tana ganinsu ta turo Dan kwalin ta Gaba, dama tasan wannan lokacin yana nan Zuwa

Bilal sai huci yake yace ke Ina Haneefa?
Kallansa tayi asheqe tace oho

Zaki fadamin inda take kokuma saina dauki hukunci dakaina?

Tashi tayi tsaye tace ai Bansan Kai qaramin Dan iska bane sai yanzu, kana nufin shekaran jiya Marin dakamin yatashi a banza Kenan? To fansa nadauka, ni Bansan wata Hajiya Hafsat ba, sunan ta kawai nakeji awajan surajo, Sim card dinsa Kuma nice nacireshi na taune, sannan Haneefa dakake tambaya naturata aikatau birni, Bansan awacce duniya takeba yanzu sannan..... Kafin taci gaba da wata maganar ya cire belt din jikinsa yafara dukanta dashi

Ihunta sabuwa Taji, itama tayafa mayafi tabiyo bayansu, Malam yahai tatarar yana riqe Bilal wanda yake dukan Marka haiqam Kamar Allah ya aikoshi, dasauri ta cire mayafinta taci damara dashi, tafara kokarin cetar inna Marka, daqyar Malam yahai ya tsaida Bilal Daga dukan Marka, ransa abace yana huci yafice yabar gidan jikin motarsa ya tsaya, wannan matar meyasa batada Imani ne?
Dasauri yadauko wayarsa yakira police, sannan ne yaji ransa yadan fara yin sanyi, yana tsaye a kofar gidan Har Saida motar police din tazo sannan ya nuna musu gidan, Aikuwa suka shiga aka tisa qeyar inna Marka, Shima yabisu Abaya tareda sabuwa da Malam yahai duk suka rankaya Zuwa police station din

********
Yana komawa part din momy yagansu sundawo falon gaba dayansu, nunasu yayi da hannu yace ku!!! Dukansu suka kalleshi lokaci daya cike da tsoron masifar sa
Ni zaku yiwa rashin kunya Ko? Yaushe nafara wasa daku? Eye yaushe nafara wasa daku?
Momy dake zaune tana ganin ikon Allah tace haba Alhaji shazali 😃me yayi zafi ne haka ido zaici wuta? Me sukayi ma Daga dawowar ka kahau minsu da fada?
Yanda kasan yayi kuka, cikin takaici da shagwabar dashi kansa Baisan ma yayi ba yace shekaran jiya da zanyi tafiya nacewa Samah su tabbatar sun gyaramin part Dina Amma yanzu Ina shiga ko'ina qura, ni Dan qazamin inane dazan kwanta ahaka?

Samah tayi sauri tace ni?😳
Wallahi Yaya bani bace saide in Safah ce, itama Safah dasauri tace Kai Samah ittaqillah

Nunasu yafara yi da hannu yace kingani Ko? Kinga irin renin hankalin nasu Ko momy? Kasa yarinya aiki saboda tagama renama hankali tace ba ita kasaba

Momy tayi Murmushi ganin yanda yadage yana shagwaba agaban qannansa kokuma Baisan yanayi bane?

Tace to Kai Haneef mashirmacin inane da za'a Haifi Yaran agabanka Amma ace Har yanzu kakasa banbance su?

Yaga alama momy Bata dauki maganarsa serious ba, danhaka ya kallesu yace Dan Allah ku Bari natashi Daga bacci nakoma part din na ganshi da datti, yasa kafa yayi ball da wayar wata acikinsu dake qasan kafet, itama Baisan ta wace ba acikinsu , saboda wayar ma iri daya suke riqewa,🤣 yayi dakin momy yana masifa cikin ransa, da wannan masifar harkokin nasa zaiji kokuma da tsayawa yana banbance wasu yara
********
Acan police station kuwa, d.p.o ya kalli Dr Bilal yace meke tafe daku ranka yadade? Dr Bilal yadauko ID card dinsa ya nuna musu sannan yabasu labarin duk irin azabar da inna tabawa Shalele, ya Dora da Cewa, yallabai Hakan datayi be ishe taba, Saida ta yaudaremu tace yau muzo zata kaimu wajan yayar mahaifiyar yarinyar Nan, ashe batasan inda takeba, Sim card din babanta dazamu samu kowanne information aciki ta cire ta taune, Kai Daga qarshe ma ta tura yarinyar Abuja Wai aiki
Dpo ya kalli Marka yace hakane baiwar Allah?

Tace eh hakane

To meyasa kikai Hakan? Ko kina da dalili?

Saboda mijina yana fifitata akaina, ba yayimin komai sai abinda yarinyar takeso, Daga karshe ma yabata saqon saki tafadamin, ta nuna Bilal da hannu tace Sannan shi wannan Dan tsaurin idon harda marina, shiyasa nadauki mataki dakaina

Dpo yace naji, yanzu Ina yarinyar take?

Nakaita wajan ladidi tijara, nace takai ta koma inane tayi aiki, nide fatana kada Taji dadin rayuwa

Dasauri Bilal yace Aikuwa Nima yau zan nuna Miki Sunana Bilal Dan tijara 🤣😂
Dpo yace kayi hakuri ranka yadade
Sannan ya kalli Marka yace yanzu Ina zamu samu ladidi a karbo yarinyar awajan ta?

Tace sun tafi Abuja jiya, Bansan gidan datake ba, Bansan unguwar datake ba

Shi kansa Dpo din mamakin karfin halin ta yake, yace Amma Yaya akai kika Santa Har kika dauki yarinya kika Bata?

Anan Garin take, Amma Bata zama tana zuwa ne lokaci Zuwa lokaci Takoma Abuja

Kin kuwa San girman laifin da kika aikata?
Ya kalli wani dan Sanda yace aje a sakata a cell

Dr Bilal yace dakata yallabai, yasa hannu ya fizge Aududu Daga hannun Marka yace
Yanda kika dauki 'yata kika turata duniya, to Nima zan dauki danki yanzu, mushiga duniya dashi tare, bazaki sake ganin saba Har sai lokacin danaga 'yata, yakalli Dpo yace yallabai bakuda matsala Dani wajan kudi, Ko nawa kuke buqata zan aiko muku, Abu daya nakeso awajan ku shine, kuci gaba da riqe wannan maha'inciyar ahannunku kuci gaba da gana mata azaba, kada kusaketa har sai nabaku umarni

Aikuwa nan take aka tisa qeyar Marka aka kulle, sai ihu take tana Kiran sunan Aududu

Dr Bilal da Malam yahai da sabuwa suka kamo hanya sukayo gida, Malam yace yanzu likita Yaya zakai da wannan Yaron? Murmushi yayi yace ai baba babu abinda zaka yiwa uwa Taji ciwo irin karabata da danta, tarabani da 'yata Nima narabata da danta🤣🤣

Sabuwa tasa hannu ta karbeshi suka shiga mota, da tambaya suka isa gidan ladidi tijara, gidan a kulle yake, Saida suka tambayi duka maqotanta Ko sun San gidan datake a Abuja kokuma unguwar datake, Amma kowa yace baisani ba, asalima Ko number ta basu dashi, saboda batada mutunci yanzu zata nunama tijara
Haka suka dinga yawo Ana tambayar ladidi, kokuma wanda yasan wani nata, Amma babu wani bayani, Har yamma lis sannan Dr Bilal yace yabawa Malam yahai katinsa yace duk lokacin dayaji wani bayani, Toya kirashi yasanar dashi

Yasa hannu yakarbi Aududu ahannun sabuwa, sabuwa tace yanzu yazakai da yaro likita? Ka barshi zan riqeshi ahannu nah
Yace karki damu inna, insha Allah zai samu kulawa sosai, Kamar Yanda zan Bawa yar'uwar sa

Haka sukai sallama dashi rai duk babu dadi, shi kansa yana driving wani qullutun baqin ciki yakeji aransa, yana ganin Kamar yakasa cika burin Malam surajo ne akan Shalele, Aududu kuwa yana zaune akujera sai wasansa yake

Kai tsaye gida yaje yabawa Mai aikinsu Yaron yace ta kula masa dashi idan Baya nan, idan yadawo Daga aiki Kuma zaici gaba da kula dashi, Hajiya ma ta amince da Hakan, yayin da Sady ma tayi murna da Yaron kasancewar basuda qaramin yaro a gidan

Tabbas Addu'ar wanda aka zalunta batada hijabi tsakanin ta da Allah, Allah ya amsa adduar ki Shalele, haqiqa Aududu yafada hannun wanda bazai taba Yada Shiba

********
Washe gari da safe Suna yin break fast da momy da daddy, Haneef Safah Samah, huzaifa
Safah tanaci tana chtting, yayin da Samah take leqawa tana ganin abinda yar'uwar ta take

Spoon biyu yayiwa abincin, yatashi yabar wajan rai abace
Momy tabi bayansa da kallo Cikeda damuwa sannan ta kalli daddy tace Alhaji Yaron nan bayajin dadi idan ba baba Hanne ce tayi girki ba, Wai yau nasa su Safah ne suyi, shine yanajin dandanon girkin banata bane yatashi, yanzu kaga haka jiya Yazo yayi tayi musu fada saboda gyaran part dinsa
Alhaji Dan Allah asamo wa baba Hanne wata me aikin mana,kaga saita dinga temaka mata

Saida yadau minti biyu sannan yayi magana, (nikwa nace aaaa to inaga Dan awajan uban ya koyi rashin magana😃😂)
Hajiya wannan shine Karo na biyar da ake kawo wa Yaron nan Mai gyara masa part dinsa yana korarsu

Dan haka Nina cire hannu na acikin Al'amarinsa

A a Alhaji ba za'a yi hakaba, kayi hakuri kasa akawo masa, insha Allah wannan Karon ba za'a samu matsala ba
Baice mata komai ba, yadauki waya yakira abokinsa, hello Alhaji Ghali, idan babu abinda kake Dan Allah Mai dakina tanaso kasa a turo mata me Aiki guda daya
Shiru yayi daga yana sauraron abinda ake fada, yace a a idan ansamu din koma yaushe ne, kawai a turo ta, ok, ok to ngd

Yakashe wayar yaci gaba dacin abincinsa, Hajiya tayi Murmushi tace godia Muke Alhaji, Shikuwa baice mata uffan ba

********
Suna zaune Atsakar gida, ladidi ta kalleta tace ow nikuwa zan Dade banga mutum Mai baqin jini irin naki ba😃😒ace kowa Yazo neman Mai aiki basa daukar ki? Koda yake ai na lura da niyya kike musu rashin mutunci, Kuma wallahi dakinqi dakinso sai kinyi aikin nan, yarinya idan bakyason aiki danqamin hamsin Dina na danqa Miki hanya

Shalele najinta tayi banza ta kyaleta, suna wannan zaman doya da manjan wayar ladidi tayi qara, kawai Cewa tayi ah akwai, yanzu ma akwai wata yar ahannu, Dan Allah wannan familyn ne suke buqata? 😳a a yanzu zanje nakaita, ngd Hajiya sai anjima, takashe wayar ta dubi Shalele tace saiki tashi mutafi
Ansamu wani gidan dazan kaiki, Nima cikin satin nan zanbar gari, dama ke kika tsayar Dani, saboda baqin jini

Shalele batace mata komai ba ta tashi tashirya, tadauki kayanta da photon baba, suka fita Daga gidan, taxi suka tare suka shiga, tanaji ladidi nayi musu kwatance Har sukazo kofar wani gida da wani mekeken gate

Suna shiga harabar gidan Shalele tazama yar qauye tuburan domin kuwa Kai bazakace a Nigeria kake ba, shukokin fulawoyi Tako Ina

Batasan dalili ba kawai de tanaji gabanta yana faduwa

Har suka je falon, gaskiya falon yahadu, ita da za'a Barta a Iya falon ma kadai ya isheta rayuwa Allah sarki Shalele 🤣🤣

Wasu yara tagani guda biyu, bazasu girme taba, tsananin Kamar dasuke ne yasa takasa banbancesu , Hakan ne ya tabbatar mata da Cewa Yan biyu ne
Ladidi ce cikin fara'ah tace yanmata sannunku, Safah tace yawwa, Amma Samah Ko Kallan inda suke batayi ba

Ladidi tace Dan Allah Ko zaku yi mana magana da Hajiya?
Batace komai ba ta Daga murya tace momy!!!
Hajiya ta futo tace gani, menene

Ladidi tace Hajiya Ina kwana? Dama anyimin waya ne akan nakawo Miki me aiki, shine nasakota agaba nakawo ta

Momy ta kalli Shalele taganta yarinya, tabe baki tayi tace ok, eh gaskiya muna neman me aiki,akwai aikin da za'a Bata, Amma yanzu de nawa za'a dinga baki kudin aikinta duk wata?

Ladidi tace Hajiya ai mukam bamuda zabi, Ko nawa kika yanke yayi
Tace ok, Jakarta dake kan kujera ta dauka tace to za'a dinga Bata dubu tamanin duk wata
Ladidi ta Washe baki cikin farin ciki

Momy ta kalli Shalele tace Yarinya kudin yayi Miki haka?
Shalele tace a a kawai kibarsh....
Dasauri ladidi ta mintsineta jin zatayi mata katobara, wanne irin a barshi?

Ta kalli momy tace Hajiya yayi, momy ta zaro kudi tabawa ladidi tace to ga kudin ta na wannan Watan, inyaso duk wata saiki dinga Zuwa kina karba mata

Ladidi tace a a Hajiya, adinga Bata abinta, wannan ma abinda yasa na karba nayiwa mamanta alwaqari ne zan Kai mata kudin aikin yarta na farko
(Shalele ta kalleta, jin wannan qarya, aranta tace a a zaki riqe kudin ki de)

Momy tace to shknn za'a dinga Bata insha Allah, Ladidi tayi sallama tatafi

Momy ta kwalawa baba Hanne kira, dasauri tazo, tace Hajiya gani

Momy tace ga yarinya nan aje atufatar da ita, itace sabuwar me aikin dazata dinga gyarawa Haneef part dinsa











Adaure ayi Sharhi Dan Allah 🙏🏻 dafatan wannan shafi ya muku dadi

Ina masoyan shazali? Shikkenan magana ta qare?

Welcome to shazali's house Shalelen baba










Mrs Usman ce 🙏🏻

💕SHALELAN BABA💕
(Romance)

Writing by Amnah El Yaqoub

19&20

Baba Hanne ta kalli Shalele sannan ta rissina tace to hajiya
Momy tace da nayi niyyar ta dinga temaka Miki da girki, but Naga tayi qarama dayawa, kawai zata dinga gyaran bangaren nasa, ki gwada mata komai, gobe zata fara aikinta insha Allah, sannan wannan kayan nata nafada Miki asake mata wasu
Baba Hanne ta rissina tace to hajiya, sannan takama hannun Shalele suka shige daki
Suna zama Shalele tafara Kalle Kalle, baba Hanne tace yarinya Yaya sunanki?

Haka kawai Taji matar ta kwanta mata Arai, Daga gani batada matsala, Murmushi tayi mata tace Sunana SHALELAN BABA

Ah gaskiya ne da alama de wannan yarinyar baban nata yanaji da ita

Shiru tayi, lokaci daya jikinta yayi sanyi, baba Hanne tace menene sunanki na gaskiya?

Kallanta tayi tace HANEEFA

masha Allah, kice ma sunanku daya da uban gidan naki
Kallan rashin fahimta tayi mata, baba Hanne tagane Hakan shiyasa tasake Murmushi tace Ina nufin wanda zaki dinga gyarawa bangaren sa, ai Shima HANEEF sunansa

Shalele tace Allah sarki, menene aikin da zan dinga yi?

Zamanta tagyara tace yawwa kawai zaki share masa ko'ina ne, saiki goge, aikin Iya mopping Ko?

Daga Kai Shalele tayi tace eh na Iya

Yawwa toshi dakike ganinsa bayasan qazanta, yanaso kullum yaga waje tsaf, zaki share ko'ina ki goge, ki wanke masa toilet, ki gyara duk wasu abubuwa da kikaga basu yiba, kiyi Ahankali dashi, Bai cika magana ba, Amma masifaffe ne, qannansa ma Bai barsuba, ni kadai yake ragawa a gidan nan Bayan iyayen sa, Shima Dan yaga na manyanta ne, Haneef bayason qazanta, karkiyi mamaki idan nace Miki sau biyar Ana kawo masa masu aiki yana korarsu

😳😳zaro ido Shalele tayi tace meyasa?

Baba Hanne takama hannun Shalele tace ta farko saboda tayi shara batayi mopping ba, tayi tunanin bazai ganeba, shikuma yagane, hakanne yasa yace tanada ha'inci yakoreta

Ta biyu kawai yace Bata wanke masa toilet da kyau

Na uku sai aka kawo namiji, shikuma satinsa daya yace bazai Iyaba, yagaji da wannan aikin inde baso ake ya mutu ba🤣🤣

Ta hudu Kuma shishshige masa take,

Please Login or Register in order to submit comment