Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
mishi ba, duk da kyanta nashi gurin kyawu inya cika yawa hadari ne.*** hafis lady ta dubi farida amarya tace in fata kin gama amfani da duk kayan da inno ta hada miki? farida tace ke dai bari,kinsan Allah , saida na gama komai dan iskan nan ahj sambo ya rusa komai, da sauri hafsi lady ta mike tana fadin amma ke farida Allah yayi 'yar iskar baiwa, yanxun dan jaraba da rashin hakuri ke da za'a kawo gidan miji sabon jini shine kikaje kika mika kanki ga wannan tsohon ya shanye duk dan tattalin da tanajin da aka ma ango? farida ta dubi aminayarta ta cikin damuwa tace wlh kawata ba da son raina bane bana ce miki yana ta damuna da waya ba? tace bana ce miki kada ki daga wayar ba? tace in ban daga damun da yakemin dole na daga, cemin yayi in har banzo munyi na bankwana ba , zai min tuggun da soja zai gane kinsan ko ba zan so haka ba. hafsi lady tace me ya hana ki kira ki sanar dani? yanda kike son soja haka yake son mulki sai kice mishi kema zaki fito ki fada ma 'yan jarida alakarku tace kash, duk tunanin baizo min ba , to yanxu na danyi amfani da wasu, tace inma ya gane ki hada da kissa da kuma kisisina, sai kice fade aka miki tun kina karama, inko bai gane ba ki share shi. farida taja filo tace aiko kin kawo shawara kawata nasan zai gane yanda yake kurin ya auri salihar mace ya sameni fanko dole hankalinshi ya tashi sukayi dariya sannan suka tafa hafsi lady tace sauaran yanda kike son shin nan ki nuna zakewarki da zalamarki zai iya ganewa, kiyi ta nokewa kina....sllamarango da abokanshi ya katse hirr tasu, nan take farida ta ja gyale ta rufe fuskarta,sun gais bayan barkwanci aka sai baki haka ango ya raka abokanshi sannan ya dawo. sun gabatar da sallar ma'aurata yayi 'yan tamboyoyi game da addini babu (not clear) dama ya zaci haka kasancewar ta kamila a nashi tunanin. soyayyarshi ya shiga nuna mata tare da wasanni tana nokewa tare da nuna tsoro hakan yasa shi binta a hamkali, yana da ilmi musamman na fikihu yasan sirrin mata da yanda halittarsu take hakan ya shiga bin komai a sannu amma sanda ya kai kofar da ya jima yana raya ma ranshi yanda zai bude ta, sai kawai yaji ta a bude, hakan ya saka jikinshi sanyi take komai ya lafa, ruf da ciki ya kwanta sai yana ji tamfar mafarki, kuka ta saka tana fadin innalillahi wa inna ilaihir raji'un dama nasan haka zata kasance a kaina, ya daure ya dube ta amma ya kasa magana, ta mike tare da neman kaya tasaka sannan ta dauki gyalenta ta rufa ta tsugunna gaban gadon inda yake kwance ka yafemin kuma Allah ya baka hakuri nasan ban caacanci ka zana dani ba ta mike zata fita yayi karfin hali ya tashi zauna a kua bakofayc z n,ta jyo fuskashi tamkar bai taba dariya ba gaban ta ya fadi. [1:56PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1----17 Yace xonan ki gaya min dalilin bada kanki ga wani,ta soma kuka, ban bada kaina ga kowa ba, ta xauna ta daga kai tamkar mai tunani hawaye na xuba kan kumatunta,tun ina yar shekara takwas wani mlmnm bayan mun tashi mkrnt ya amshi jakata sannan ya bani wasu takardu ya ce in kai mishi su ofis.bayan na dawo yana qofar ajinmu sai yace in shiga cikin ajin in dauki jakata,ina shiga sai ya biyo ni ya rufe qofa....ta rushe da sabon kuka tankar gaske,taci gaba da fadin ya min fyade yayi kaca kaca dani ya gudu sai da aka min dinki a asibiti,ta kifaka kai tana ta kuka mai ban tausayi,uaji makira,ya taso da sauri yaxo xa rungume ta,tausayinta ne ya kika ranshi yana ji aranshi da yaga wannan tsinannan mutum babu abin da xai hana shi saka bindiga ya harbe shi,daga lallashi ya xarce soyewa,ranshi fes.duk da yaji haushin yanda ya sameta amma haka ya daure bai nuna ba tunda ba laifinta bane,soyayya suka shiga xabgawa a satin inda yaga shi qaramin dan wasane a wannan fannin itace take nuna mai salosalo na soyayya. Abin ya ta bashi mmk hr ya kai ga tambayarta a ina ta koyo wadannan salon,sanar da shi ta yi ai ma'abociyar karance-karancece, dan haka sai ya yi murna da jin haka ta mantar da shi komai. dani da ke mkrnt muka gama jarabawa a ka bamu hutu. kamar nasan ba zai zo dauka ta ba na ce Balkisu in direban ku yazo daukarki zai sa min hannu ku sauke ni kaduna.Ta ce in an zo daukarki fa? Na ce bros dina na Abujan nan ne zai zo daukata,kuma gidan shi zai kai ni ni ko ina son ganin Momy,Mina ta ce kai Queen ki tsaya a Abuja nan basa sai muna ziyartar juna ba? Na ce kin sani ne? ba ma shi da shi ne sosai zai matsa min gara in je gurin Momy haka ko direba su ya zo suka sauke ni har gida Murna gurin Momy kamar me musamman ganin yanda na koma.Sun gaisa da Balkisu sannan suka dauki hanyar jigawa ko na ce Kano,Momy ta ce me ya hana Soja yaje ya dauko ki? Na ta6e baki sannan na ce kila ya manta,ta ce wane irin ya manta? Na ce ina wayata ne? Ta ciri min ta ce gata sai kin saka a caji na ce zan kira Rahma ne ta san na dawo. Momy ta ce ina ruwan Rahma in taje gaida Mama ta kan shigo mu gaisa ai Usman ya yi sa'ar mata,na ce sosai ma ita ce dai ba ta yi sa'ar miji ba,Momy tana dry ta ce shima ai ba ruwanshi na ce ni kam gare ni ba shi da kirki,Anty ta shigo ta ce 'yan mkrnt hr kin iso? Na ce eh ina yini Anty? Muka gaisa ta ce ke da maigidan ne? Na ce a'a kawata ce suka rage min hanya,Momy ta ce shi ne zai zo ya dauko ta yana fama da Amarya? Ai zai zo ya same ni, Anty ta ce a"a Momy kin san ko bayan ta taho yaje? Ta ce ba wani zuwa da zai yi wannan kawar tata da suka kawo ta tun da daga jigawa aka je dauko ta amma na cikin Abuja bai je ba ki ce yana da niyya.Tunda nazo kaduna bai ta6a zuwa ba,Momy kuma bata neme shi ba don koda ya yi mata waya bata ta6a mishi zancena ba, Ko ta ce yaya ba muyi hutu ba? Ko kuma nazo bai zo ba sannan ta lura bai ta6a kirana ba, don haka ta ce ta san maganinshi. Abbada ya nemi ba'asin zamana a kaduna,Momy ta ce nazo ganin gida ne.Hutun mu na sati 4 ne saboda SS2 zamu shiga rannan na shiga gidanmu mun gaisa da su Mama,sai ga Rahma. Na ce yauwa kawata,dama ina ta jiranki ne kizo ki raka ni saloon,ta ce muje nima ki biya min na wanke nawa na ce lallai Momy zata ba ni sai dai kije gurin Ya Usman ko ke ma Mama ta baki? Mama ta ce zo gashi Rahma,Rahma ta fita tana dry tare da fadin wasa nake Mama,gidan su Momy shiga na yi wanka ina kwalliya muna hira da Rahma muka ji sallama gabana ne yayi wani mugun faduwa ban san mai sallamar ba,na gama na saka riga da siket na atamfa 'yar Holan mun fito falo Momy ta ce ga kudin gyaran kan na ce dari biyu ma za ki ban. Ta ce rike dari biyar din na amsa zamu fito kenan akayi sallama kofar Momy gabana ya sake faduwa ta daga labule ta shigo,Nan take na gane ta. Faridar Ya umar don bayan hotonta da na gani hr da kalandar su na gani dakin Mama hr da agogon su sanye take da wani shegen leshi wanda kyawunshi ya nuna tsananin tsadar shi. Ruwan madara ne da ratsin ja dan gyalenta shi ma ja, Haka takalmi da jaka na dauke kaina daga dubanta duk da ba son mijinta nake ba sai na ji kishinta yana yin kallon da take min tana tunanin nice matar mijinta tunda duk sauran taga su lkcn bikinta,sannan taga idon da yake ce mata yarinyae ba kyau ba,sai ido kamar na mujiya.... Ni dai muka fita kofar waje muka yi kici6is da Ya Umar ya dube ni cikin mmk ba komai ya ba shi mamaki ba yanda ya manta dani har ga Allah ya manta da wata matarshi a mkrnt yanzu mai zai ce ma Momy ban ko kuma kallon shi ba na sa kai na fita abina,Rahma ce ta tsaya gaishe shi ta biyo ni me yasa bako gaida shi ba? Na ce yanzu ba da ba ne,ba zan dauki wulakanci ba ko dama don ni sane na jur wani abina. Shi kam da ya shiga gurin Momy sai ya shiga kame-kame yana cewa shi sam mkrntr ba su mishi waya su anyi hutu ba,Aliyu ne. ya dauko ta ba shi ba ne amsar da Momy ta bashi kenan,ta fita daga dakin,Farida ta dube shi Soja na wadda tafi ta yanzu ita ce Asma'u din? ya ce eh kawai shi yasan Momy tana fushi dashi ne don ko gaisawa sama-sama suka yi ta,Ya kai Farida dakin Antynshi sanda na dawo daga saloon na gansu zasu shiga gidanmu.Yanayi tamkar ban gansu da na wuce abina,na samu Momy tana yanka Alayyahu na amshi yankan Anty Amarya tana ciki tana tuka tuwan shinkafa,dama su baka gane mai girki komai tare suke yi..... Gefen baki suka kwana da farko neman masauki ya ce zai yi a hotel,Momy ta ce duk gidan nan ko can gidan Alhj ba gurin kwana sai ka kaita hotel saboda ta raina mana arziki? To kuje sai da safe a gabn Farida ta fadi haka,nan yake ya gyara musu gefen baki tunda Aliyu baya nan haka nan su Jamila.Jamila da Nafisa suna gidan Anty Salima shi ko ya Aliyu sunyi tafiya da Abba ni dai ina can kuryar dakin Momy koma falo na zauna ba zan ta6a gyara musu gurin kwanciya ba,da safe ma sanda suka shigo na gama karyawa kawaye da Mina Turaki ina jin sanda suka yi sallama yi na yi tamkar ban san suna yi ba,Suka zauna Momy ta fita suka gaisa ya Umar sai hararata yake,na mike na shige cikin daki,ina amsa wayata,dakin Anty suka yada zango karfe 2 suka tafi bai ce ma momy komai game dani ba haka nan nima ban ce kala ba dama bana so ace in bishi Momy ma ba ta ce komai da hutun mu yana karewa ta mishi waya bai zo ba ba ya turo kudi wai Aliyu ya yi min shopping sannan yajw ya biya kudin makaranta hakan ce ta kasan ce muka koma makaranta...... Tun daga wannan ganin ban kuma ganin ya Umar ba,har muka gama SS2 muka shiga 3 duk hutu Momy zata aiko a dauke ni ta ce ma Abba ita ce na dinga zuwa kaduna saboda in an gama gini shi nan zan zauna, ko da Abba ya tuntua6e shi da wannan batun sai ya ce haka ne don haka ya saka shiriritar gama aikin nima haka na ke so, domin yanzun shi kan shi da zai ganni ba yabon kai ba yasan na fi karfin wulakanci daga shi har matarshi basa gabana na samu labarin an ce tana da ciki amma watan cikin hudu ya zube yanda nake ji gurin su Jamila tamkar zai yi kuka saboda zubewar cikin na ce su karata. Duk da matsatsin fiar da ya Umar ke ma Farida hakan bai hanata hulda da abokan shashancin ta ba,ta kan fake da zuwa gidan Yarta dake nan Abuja cikin ta ma cire shi tayi saboda yana bata matsala da abokan harkarta. Alhj Sambo shi ne ya hada ta da likitan da ya cire mata cikin. ********** cikin Yardar Ubangiji muka kammala karatunmu bayan kammala komai aka bamu kyautuka kowa ya kama gabanshi sai dai abn farin ciki ina daya daga cikin dalibai uku da makaranta ta za6a don daukar nauyinmu,muyi karatun Likita saboda hazakarmu in ka ji ana Asma'u to a kaduna ne Amma Abuja har gobe Queen suke kirana..... Sai da muka dawo gida na samu Momy zata biki jos danginta na bita muka tafi ansa bikin Hadiza da Shema'u Sai na Ya Usman da Aminiyata Rahma,Hadiza da na Ya Aliyu ne haka Shema'u yaron yayan Mamanta ne Sadik. Tun da biki ya matso ba mu da sukuni kawayena su Mina duk na gayyace sy kuma nasan za su zo. Biki ya yi biki kenan,na musu ankonmu duka don har da su cikin kawayen aana gobe daurin aure suka iso Mina tariga su isowa saboda tafi kusa,sannan Balkisu sanda Fatima shehu ta iso mun gama shirin tafiya lunchen ko hutawa bata yi ba ta yo wanka muka fito,muna ta shakiyancinmy da muka saba,Kowace direbansu ya kawo ta, don haka muka shiga motar su Mina muka shiga tunda shi direban su ya huta haka muka kayata gurin tamkar taurari gaba kin su Mina baya gajiya da fadin Queen duk in da na bi nan sauran mutune suka dauka Queen-Queen,duka amaran lunchen gurin daya muka hada tunda duk gida ne har angon shema'u tunda ya saba dama dasu ya Usman ni da Jamila mun dauki kwalayan abubuwan da zamu raba ma mutane muna kaiwa gurin ajiye wakafin mu sona rabawa,Anty Saluna ta kira ni nazo ta ce ina aurans Na ce wane aure kuma?Har ga Allah ni ina mantawa wai ni matar aure ce,Har mijin kanshi na manta da batunshi. Ta ce iye lallai Asma'u kin hadu shi yasa ko dan gyale ba ku saka ba,na ce share kin ji har zan tafi Anty Fatima ta ce kishiyarki ta ko zo? Na ce tazo bata zo ba ban sani ba,anty Aina'u ta ce na ganta gab da zamu zo nan na ce ita ta sani ni ina ruwana...... Guri ya yi guri,na rasa duk inda nayi jama'a kallona suke,ga mai wakar ya kama Asma'u Queen ban san da wanda ya sanar dashi sunana ba,Har da fadin Queen din Umar Soja marmari daga nesa,naja tsaki na ce bar hada ni da wani Soka,Jamila ta dauki kafadata ta ce dama tun dazun nake son in ce miki duk wanda ya kira ki zamu dau mataki kanshi,na ce jacan ki bani guri,yanzu nake tashena wannan Sojan ya min Tsufa,don haka duk wanda ya kira ni zuwa zanyi muka saka dariya ni da su,gashi dama muna da wata sara ni da su Mina,in munyi abin dariya mun dara sai muce wa ya dukanmu Jamila ta ce Allah ya shirye ku,Haka aka sha lunchen muka taso muna mota su Mina suka dame ni wai wanene Umar Soja? na ce don Allah ku bar zancan shi nima ban san shi ba,Fatima shehu ta ce ba wani ba ki so nw musan Saurayinki kawai Queen.Jamila zata yi Magana na toshe mata baki amma sai da ta ce musu mijinta ne,na ce kunha nayi kama da matar aure? Muna tsayawa kofar gidanmu Anty Salima ta miko min yaronta Muslim ta ce don Allah Asma'u ki kai danku gurin Momy,na ce yaron nan kato da shi yana tafiya ga surutu amma sai kuyi ta daukan shi? Ni dai ba zan dau ke ka ba sauka ka taka da kanka.Anty Aina'u ta ce dama ke ai ba ki san yara na ce ku ai yaranky sun cika kuya Anty Fatima ta ce kema in ki haifa kin rike naki na ce ba konai suka shige gidanmu mu kuma muka nufi gidan Abba da kawayena ina rike da muslim sam ban kula ba she su Ya Umar da ya Abubakr ne a gurin tare da wasu daban ban san su ba.Muslim ne naga ya kwance hannunshi ya ce ga Dadyna ya nufi gurin Ya Abubakar.Mina ta ce la ji yaro da wayi yasan Babanshi ko ba Babanshi ba ne?? Na ce Babanshi ne mana Bilkisu ta ce yayanki ne, Na ce shi ne Na farkonmu a dakin mu muka zo gota su yi nayi tamkar ban gansu su ba saboda ya Umar dake gurin sai naji su Mina suna gaishe su, har mun gota naji muryar ya Abubakar yana cewa kE Asma'u zo nan na juya na zo shi nake duba na ki kallo gurin Ya umar, na ce gani ya ce ke har yanzu..... Kanki bai dana hayaki ba ko? Na 6ata rai ya ce gaba kina kallonmu kin wani dauke kai sama sannan dubi shigarki babu ko dan gyale kin daura gwargwaro a kai gashi a waje tamkar ba matar aure ba ko?Na dubi sasheb ya Umar da gefen ido waya yake amma na kula da kallom da yake min da gefen ido, na wuce ban ce komai ba, Fatima Shehu ta ce wai da gaske kina da aure ne? Na ce don Allah muje ciki. Falon Momy na bar su na shiga dakin Anty Amarya dan na dan watsa ruwa kasancewar gidan bai cika kamar gidanmu ba,tun da nan gidan Maza ne wanka nake na tuno ya Umar da na ganshi yau in har ba zan manta ba yau shekara biyu da wata shida kenan rabona da na sa shi a idona. Ya Allah sam ban ji zuciyata tayi farin ciki da ganin shi ba,duk da cika da kyau da kwarjini da na lura ya kara,sannan ga kudi da ya zauna. Can waje kam ya Umar ya dubi Muslim sannan yasa hannu ya dauke shi tare da fadin zo nan big boy,yayi sha'awar yaron kwarai da gaske.Yanzu kam ya matsu yaga dan kanshi. Farida ya lura abin bai dame ta ba,in yayi la'akari da yanzun makarantar da ta koma tafi dauke mata hankali,ko dai zai............sai kuma yaja tsaki yayi shiru,yana son yin shawara da Anty shi ya dubi Abubakar ya ce bari na ga Antyna,Muslim ya ce zanje gurin Dadyna,ya Umar ya ce nima Dadynka ne ai ya ce a'a ga Dadyna nan Ya Umar ya mika shi suna dariya ya ce jeka gurin Babnka ya nufi cikin gidan ma ba mutune sosai kamar yanda ya zara ya shiga gefen Antynshi babu shamaki,ko ina shiga yake kai tsaye ya shige bedroom yana fadin ina Antyn tawa take? Ni kuma na fito daga ni sai wani dan tawul wanda iyakarshi cinyata,kallonaya tsya nayi wani abu ne yaji shi tub daga yatsun kafarshi har kanshi idunanshi sun kasa daukewa daga kaina. [2:07PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 1----18 Ganin yana min kallan qurilla na juya na koma toilet ya bini da kallo har na shige na kulle qofar. ahankali ya kulle ido ya sake bude su sannan ya jingina da bangon dakin a hankali ya furta ya salam.jikinshi babu qarfi ya fita xuwa falon anty ya xauna kan kujera wani abu yana mishi yawo aranshi yayi ajiyar xuciya tare da jingina bayanshi da kujerar,lkc guda ya kwantar da kanshi,yarinyan nan ce haka? daman haka qiranta take?wata xuciyar tace ko dai kaji sha'awanta ne?kafin ya samo amsa sai yaji maganan anty,ta dubeshi dan gidana,yayi dan murmushi ya ce ina kuka jene? tace munje kai abincin biko mana,yace kai mata kun cika bidia,yanxu tsakanin gidannan dana baba alhj har akwai wani biko ne ko bai kone ma kika ce? tayi dry tace hakama mama tace,yaja murmushi yace ina farida ne? tace aini tunda muka gaisa tace min xataje gurhn wata qawanta gashi har magariba bata dawo ba, ya ja tsaki yace tasan inta fadamin baxan barta ba shine watan ta tafi?yace anty matsaloli sunyi yawa dama ina san mu xauna.... Ya dubi agogo ga lkcn sallah yayi bari ayi isha'I cewar anty daidai nan nazo na wuce su ya dube ni sannan ya dubi anty yace yarinyar nan ta samu daurin gindi wurin momy ko gaeshe ni batayi ba . anty tace harda kai dangidana , da ace tana gidanka dole ta gaishe ka . yace bari naa dawo. mukam gidansu rahma muka nufa inda za'aje a kwashe mu xuwa zuwa gidan kanwar momy da take u/dosa , dan can xa'aa sa lalle. lkcn da ya umar ya samu xama da antynshi ya dube ta kin san anty meke damuna? na farko kamar yanda kika sani inason yara kin sani anty sannan naa 2 farida tunda ta koma makranta bataso ina mata xancen haihuwa , ga shegen yawo, look at, lkc yanxu kusan 9 bata dawo ba haka in taje makaranta bata dawowa akan lkc ga matsalar abinci saidai muci na kuku ga yawan zuwa yola suna yau suna gobe biki na gaji. anty tayi shiru a ranta tana nazarin me xatace dashi in kuma ta fad xai yarda? amma duk da haka sai tayi kuru tace umar yace naaaam tace mexai hana ka dauki matar ka asma'u ?ya dube ta da sauri tace kwrai, tana da kyau tana da diri inda bata da kunya yanxun tana dashi hakanan bata duk halayen ta daka santa dasu duk ta daina koh masifa dama sai an tabo ta, snnan zata iya haihuwa, shiru yayi yana nazarin maganar anty, ta sake dubanshi sannan kuma xakasha fama da momy . shiru yayi yana tunanin maganar anty , yasan tabbs shi bayason yarinyar saidai zata iya haihuwa amma ya zai cema momy Ya dubi anty me zance wa momy? gaskiya don son yarinyar nan banayi na tsane ta saedae don son haihuwa , xan nemi komenta ko nace zan tafi da ita saidai momy ce matsalar. dan na kula yanxun ban cikin yan harkokinta kuma duk akan yarinyar ne. anty tace ta baya xaka biyo wato wurin abba, kafin yayi magana farida ta shigo da sallama, tare da fadin anty kin ganni sai yanxun koh? ganin soja yasa tayi tsit tasan tayi laifi tun xuwan su ta kama gabanta ta zauna ta fadin danAllh kayi hkr sojana na kir wayar ka taki shiga ya dubi agogo 9 daidai sannan ya dube ta ina kikaje? kafin ta bashi amsa wayar ta tafara ruri, ta duba ta ganin ahj sambo ne yasa gabanta ya fadi, ta dauka cikin tsorofuskarta daure tace lfy? yace na kiraki ne naji kin kai gida lfy? tace eh yace kin manta pant dinki anan , tsaki taja sannan tace sai anjim, ya kwshe da dariya ta kashe wayar, yarda duk ta tsargi kanta yasa ya umar tunanin batada gaskiya, yace ina kikaje nace? nan ta soma shiryo karya , wlh wta 'yar set dinmu ce a skul dama nan suke da mijinta ke aiki can shi ne ya samar mata skul dinmu , jiya na kirata nace mun zo kd. Shine tace itama tana kdsai tamin kwatance naje. yaja tsaki yace wa kika tambaya ya baki izini ? tace yi hkr , bai kuma magana ba ya dubi anty xan tafi masaukina , don masaukin gidan nan xai cika yau.farida ta tashi bari naje ya daga mata hannu alamar kada ta bishi sannan yace inaso na samu rest of mind, ba tare da ya jira komai ba ya tafi , anty tace meyasa xkiyi gngancin nn kinsan mijinki bayason yawo? tace soja ya cika kishi ne anty, anty tace ai duk namijin da baya kishn iyalinshi jaki ne, saidai na wani yafi wani, nan suka kwanta tna tunanin yanda xata shawo kanshi dan tasan sojan bai iya fushi ba.kwance yake rigingine fuskar shi tana kallon sillntunaninshiyana kan yarnyar ,ganinta yake cikin slow tana tafiya lkcn da suka wuce da kawayenta , sannan tazo mashi rai sanda ya ganta daure da towel santla santalar cinyoyinta da kogunta ya tuna, nan zuciyarshi ta raya kwarai xata hafa mishi yara, saidai yasan xai fuskanci matsala wurin momy , ga yarinyar fa? Ranar daurin aure gidajan kam da jama'a Mu dai wannan lkcn muna gidan su Rahma Muna ta shirya yanda zamu gabatar da walima anjima bayan dauren aure.Lkcn daurin aure ya karato na ce kuzo muje gida muyo wanka kunga in gidan ya dinke da jama'a ba zamu samu gurin shiga ba,abokana ya Usman suka zo suka kawo mana drnks wanda zamu yi amfani da su gurin walima. Na ce su sauke mu gida,suka debe mu wajan har ya soma cika da mutane,gasu Ya umar da abokanshi irin su Al-Amin,da sauran su,ban da su ya Abubakar ga sunan.Muka sakko daga mota tun kan mu shiga cikin gida Mina ta dame ni da tambaya don Allah wancan yayanku ne? Mai sanye da farin boyl din can? Na dubi gurin ya Umar take magana amma sai nayi tamkar ban gane shi ba na ce wa kenan? Bilkisu ta ce wanda jiyan nan muka ganshi cikin kakin Soja, na ce sunanshi ya Umar shi ne babban yaron Momy, Fatinma shehu ta ce suna kama gaskiya,yana da kyau gayen na ce wane kyau anan? Bilkisu da Mina har suna hada baki gurin cewa ko ke ya fiki kyau Queen duk da kina mace, Na ce Allah ya kyauta,MINA ta ce yana da mata? Na ce kilama tana nan cikin gidan nan suka dage kan in tana ciki don Allah na nuna musu ita.... Tun daga nesa na hango dakin Momy fal da mutane haka falonta, haka muka ja birki kofar Anty falon ta da mutane ba su da yawa ban tsaya dubansu ba na ce ku zo nan dama kayanku na ciki.Bedroom din Anty muka shige,duk muka zube mata kan gado,na ce bari na debo mana waina ko tuwo? Suka ce wainar dai na dibo na shigo saina ga ashe harda Faridan ya Umar a cikin na zauna a falon Anty. Na shiga ina cewa kai 'yan iksa ga to matar da kuka ce in nuna maku Bilkisu ta ce matar Sojan nan? Na ce eh wata fara, duk suka tashi da gudu.Suka je suna lekenta. Suka dawo suna fadin tana da kyau gaskiya na ta6e ba ki na ce suyi ta kyansu,Fatima Shehu ta ce Amma dai ba mamnku daya ba? Nan na ce musu,nifa canne gidanmu,maman can gidan ce Mamana,ba Momy ba, yanda muke dasu yasa na basu labarin na amma ban sanar dasu yanada akayi auranmu ba na dai ce ba ma son juna aka hada mu,sun sha mamaki sannan suna ta min korafin me yasa bana sonshi dan Allah in yarda Mina cewa tayi wlh ban da ke da kike tsakani da sai na ce ina sonshi na ce ki ce mana,aini ba fa zan zauna da shi ba,ina samun wanda na ke so wlh dole ya bani sakina, Nan dai muka ci muka sha muka yi ta shakiyancin mu,sai dai kiji muna ihu muna cewa waya kwashe da dariya don ko a school in muna sama mutum iddo ya bani damu...... Wayar anty dake kan mirror ta soma kuka na duka naga ansa dan gidana nace a raina ya umar ne na aje hak yayi ta kira su mina suka ce na dauka nace a'a sojn nan ne suka ce na dai dauka don Allah tunda ta tana can cikn mutane , ina dauka ya soma fadin antyn, cikin masifa nace ba ita. bace tace to ko wcece tce frida tazo, na kshe wyar sannan nce ina ruwana

Chapter 7 of 16