Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
inka haihu sai ya tafi sun min allura,kuma sunce 3 xa-a min kudin in haihu inna haihu kuma amin 2 dama wai 5ce.ya umar ya saka ma ranshi dani,shine xaisa ya iya haqura dani dan gaka ya yanke shawaran barina kd.... [7:49PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----12 Yawancin masu ciki kan samu hk in aka harfu sai yatafi sunmin allura da dabara sun ce uku za ai min kafin inhaifu in na haihu kuma aimin 2 dama 5 ce ya umar ya saka ma ranshi wani sonta dani shine zai sa ya iya hakura dani don hk ya yanke shawarar baring kd inyi goyon ciki bayan na haihu sai ya sawwake min gidansu momy na cigaba da zama kafin cikin ya cika wata 9 kowa tausayamin yakeyi satin yaumar 4 sannan yazo yaci fada gun momy ya ce kiyi hkr tana raina yrny nan bana samun zamane shi yasa hkln shi ya tashi da ganin yanda na kumbura ciki yayi kato kowa cewa yake bai taba ganin ciki maigirma irin wannan ba sukan likitoci sunka hoto sun ce lfy ta lau hk ma cikina kuma watan cikin 8 bai isa haihuwa ba ya umar yaza kullum yana hanyar kd da abj dr ya ce indinga zaga gari hkn yakan tasani gaba mufita zagaye duk inda muka muce sai anmin sannu inko ina zaune ne hk zaita matsamin kafafu su dan saki yanaga min kalamai masu sanyaya rai inshallahu zaki haihu lfy kada ki damu kinji? Duk addu'a muke miki cikin sallolinmu kema kina yi? Me zaki ci? Hk zaita lallabina wani sa'in har tausayi ya ke bani. Cikin bacci naji kaman an tsungule na farka da kyar na sauko daka kangado ba nason nayi motsi mai karfi momy ta tashi bata samun bacci sosai bayan gida naji inaji don hk na shiga toilet amma yaki fitowa dg nan basai ciwo ya matsamin ba na fito na kafa kai jikin gado momy ta farka da sauri ta ce yayane asma'u ? Na ce bayana marata zan mutu momy ta ce kiyi salati da addu'a bari inyi waya usman yazo ko aliyu atare suka iso aliyu ya dauke mu nida momy usman kuma yaja su abba da anty dr na dubani ya ce haihuwa da saura yanzu ma nasoma nakuda domin ban bude ba jin hk yasa nasadakar mutuwa zanyi ban taba jin irin wannan ciwo ba don hk na sama raina tawa ta kare Shi kam yaumar tun dare jikinshi ya bashi kd babu lfy sbd mafarkai barkatai da yayi aranar tun asubahi yake kiran wayata amma shuru babu wanda ya dauka hankalin shi yatashi sosai yasan da tana kusa zata dauki wayar ko da masifa zatai mishi yakasa natsuwa sai kusan A zaton shi ni ce ya ce Asmy jamila ta ce ba ita bace ya ce tana ina? Ta ce em tana bayi don ance kada su gaya mishi ya dan ji sanyi har ya shirya fita kafin yakai ofis dinsu ya koma kira ta dauka ta ce bata kusa cikin tsawa ya ce ina taje? Nan ta dabure tarasa me zata ce can ta ce bari na nemota takashe wayar ya dubi direba ya ce yi paking a gefe nan ya nemi momy akashe ya nemi abba tana ringing ba'a dauka ba ya kira antynshi akashe duk lkcn su kam wayoyin su suma gida nan fa hkln shi yatashi zuciyar shi tagaya mishi asma'unshi tarasu nan take ya ce da direba sukama hanyar kd sun iso 11 gidan bakowa sai nafisa ya ce ina momy ? Ta ce na asibitin diamond ya ce shine don iskanci kika cemin asma'u tana bayi? Yana magana ne yana fita don hk bai ji amsa datake bashi ba sanda ya iso asibitin na jigata ba kowa guna sai likitoci yaumar ko gaisuwa baiyi da su momy ba ya ce musu ina nake? Suka nuna mashi dakin haihuwa sai ya shige dr ya ce yanlabe kayi hkr kajiramu waje ya ce madam nima kimin hkr naga matata ya nufo ni ya rungume ni sannu ya ke min tamkar shi nakudar take jira ta tashi gadan gadan amma haihuwa shuru likitoci sun ce dayan rana zan haihu amma har 2 shiru yaumar hkln shi yakai karshan tashi ya ce sumin aiki su cire adan in huta sun ce in ankai 4 ban haihu ba zasuyi min aiki ya fita don yo salla tunda sauran karfina har nakai bana iya koda nishi biyar dai dai anmin shirin aiki yan uwa sai addu'a wasu na kuka kada ma momy taji, A dakin tiyata wani sabon ciwo ya tashi wani uban nishi nayi sai ga yaro ya fito fit jim kadan sai ga sabon ciwo nan suka gane yan biyu ne suka taimakamin aka fito da ita nan suka fito da yaran don gyara dangi suyi matukar farin ciki da sauka lfy anshiya yara anata murnar ganinsu shi kam ya umar ni yake son gani dr ta ce kada yadamu ana kimtsa nine sun min allura sannan suka kaini dakin hutu bacci nake bansan irin hidimar da nake su ba sanda na farka tara tayi momy ce da ya umar ya taso da sauri sannu asmy kin tashi? Kallon shinake kurum a raina na ce badole kai min sannu ba tunda ka hada ni da aiki sai kuma naji dadi dana tuna yau ko gobe zamu rabu da shi ya ce momy a hada mata tea bari ta wanke bakinta shi yatadani na wanke bakina cikin wani kwanon silba sannan na dan sha tea kadan momy ta ce yarta baki ce ina abinda kika haifa ba? Shuru na mata araina ko fadi nake ina ruwana da abinda na haifa ya umar yaje gadon su yadauko daya ya ce kinga arzikin da Allah ya bamu asmy na kwanta naki kallon su da momy ta matsamin sai na ce ni ina ruwana dasu Shuru yayi yana kallona momy ta ce wanna karon zamuyi rigima dake asma'u suka fita fatima na ce yaya babu wani lallash ka bude mata wuta ba'a bada nono ke aka baki? Suka fita yazo gaban gado na ya zauna bakin gadon zcy shi tana har bawa yanzu ma bai san ta inda zai soma ba can ya tashi yaje ya dauko maccan ya zauna kusa dani ya ce asma'u ki hkr nasani duk komai laifina ne kada kiyima yaranki horo da laifin babansu ki bada nonon nan domin Allah ba don ni ba kinga ita macce tanada rauni na dube kasan baka mukayi dakaiba don hk bazan bada nona na ba yanzu ina takarda ta? Yayi ajiyar zcy kinsan zan baki tunda nina ce zan baki amma yanzu kisan zuyi ta jin haushin yan uwanmu zasu tsaneki na soma hawaye wannan karon na shirya na yarda in fuskanci ko wace irin matsala ce kai dai ka sallame ni yamike yana jijjiga yarinya sbd kukan da take yi yasa mata lebanshi abaki ya dan jijjigata sai tasoma bacci ya mannata akirjinshi sannan ya zauna bai san me zai ce mata ba yaje ya kwantar da ita sannan ya fita gurin dr yaje ya bashi bayani kan babies suna jin yunwa mamansu tana fushi ta hanasu nono dry likita yayi sannan ya rubuta kalar madaran da ta dace dasu ya ce koda tana basu nono ba dole ne ya ishe su ba dama sai an hada da madara yaje ya sayo ya kawo nan da nan aka dama masu suka soma sha shi kuma ya koma abj sbd bai sanar ba gashi suna cikin wasu bincike ne washe gari yayi lagos Nikam har sannan naki bada nono na, kwananmu uku aka sallame ni mukayi gidansu momy dama su abba basu sani ba haka nan momy ta hana a fada ma mama. Ran kwana hudu ya iso da kaya niki niki mota guda tamkar masu kayan tashi, duk na yara ne. Su rahama suka fita da su hadiza kowa baya jin dadi yanda yake ganina rai cunkus, bana cin abinci. Hadiza tace Allah yau sai na gaya wa mama, su anty aina'u. ma da gangan suka yi shiru har alhaji ma sai yaji. Rahma tace a'a ya umar ne yace likitocin sun ce kada a matsa mata fa! Hadiza tace ba dai ya son ya matsa mata amma na taba ganin mai jego ba cin abinci kuma ba zata ba yara nono ba sai shegen bakin rai? Ni kam dama na kosa su fita tunda naji zuwan ya umar yau kama sai ya sallame ni, ya zauna bayan ya dauko yarinyar. Bansan me yasa yafi daukar yarinyar ba, maman 'yan biyu na same ki lafiya? Banza nayi mishi yace yarinyar nan tana kama dake sosai, shi ya sa nafi sonta. Na harare shi, wannan ba damuwa ta bace ni yanzu damuwata ka sake ni, ban ma kaina adalci ba in har naci gaba da zama da kai. Duk sanda na dube ka ina tuna wuyar da ka bani tare da bakaken maganganun da kasha gayamin amma in ka sake ni zan yafe maka kuma raina ya huce. Ya tsugunnan gabana yanzun to wa zai shayar min da yarana? Wai zai kula min dasu? Nayi murmushi sannan nace ka manta da faridarka? Wacce ta iya yiwa yara tarbiya kuma 'yar masu tarbiya? Ya zauna kasa, ban da magana a yau amma kiyi hakuri. Nace na daina yarda kana min wayo da yawa, gashi ka samu yaran da kake muradi, san...sallamar mama ce ta katse ni, ina take mara hankalin yarinyar, dan ubanki ba a bada nono ni na baki nawa? Ta shigo bata 'yar ta bata nono ko in tsine mata yanzun nan. Ko kuma ki biyani nawa. Don kin sha wuya su suka dora miki? Ba Allah ne ya doro miki ba? Gani nan tun daga haihuwarki na samu hawan jini amma ban hana ki nono ba sai ke? Kuka na saka su momy suna ta ba mama hakuri tace ba fa zata tafi ba sai na basu nono. Ta dubi ya umar tace kai kuma faruk baka gaggaura mata mari? Yarinya mara jin magana. Ya umar yasa ta cinyata, momy ta ciro nonon ina kuka aka sa mata. Nan ko ta kama sai sha tace, shima yana bacci ya umar don mugunta sai da ya taso shi shima suka saka mishi nono ya hau sha, ranar nayi kuka har da ciwon kai. Da dare ya umar ya shigo na dan dube shi wallahi duk ya rame. Ya ce me da me kike so game da suna gobe zan koma jibi zamu zo da my farida saboda tana dubai yau zata dawo, na dube shi ina ruwana da suna? Ni fa babban sunana ka sallame ni. Yace zan sallame ki amma ki bari ayi suna mana! Nace ran suna? Yace da dare ba. Nace shi kenan yace to ki saki ranki ki dinga cin abinci kina basu nono, na ce nifa ba zan iya ba da nonon nan ba. Ya ce ke da su daya ne a raina kinji asmy? Yanda yayi maganar cikin muryar tausayi don haka sai ya bani tausayi. Ya umar ya kashe kudi da sunan nan tamkar a kasa yake hako su. Ni kallonshi ma nake yi. Akwati saiti daya yayi min guda biyar, zannuwa talatin da shida ga key din mota ta academy 'yar mai kyau sabon sanfur ga hajji da umara sannan ga takardun gidan shi na nan kaduna, yace na wane halak malak ko bayan ranshi ko ba ma tare nawa ne. Alhaji da mama fada suka kama yi wai duk iskancin da nake yi har ya birge shi ya min kyauta haka? Abba da momy cewa suka yi babu ruwanku wannan tsakanin miji da mata ne. Haka yasa ni jin tausayin ya umar nasan yana yi ne don in zauna dashi in daina maganar saki to ni bana son shi haka nan bana son 'ya'yanshi. Farida ma tayi hidina sosai, dangi sunyi hidima da mu. Akayi suna yara suka ci momu da abba, kowa ya wadatu da kayan suna. Rago biyu shanu bibbiyu haka ya umar ya yanka. Daren ranar na jira shi dan ganin takarda bai zo ba har sai da nayi bacci. Ya shigo yaran yaje ya tsuguna gabansu yayi musu adduo'I sannan ya sunbace su, yazo kusa dani ya sunbaci kumatuna sanna ya aje min wata 'yar farar takarda kusa dani, sammako yayi don haka bamu hadu ba, ni kam ban ma ga takardar ba sai da ina karyawa naga takarda na dauka da sauri ina dubawa. Cewa yayi: “ki min afuwa ba zan iya sakin ki ba saboda son da nake miki, ki zabi wani horo mai tsanani wanda kike ganin yafi kowanne horo wahala ki min shi, na yarda in dai zaki janye batun saki. Sannan ki taimaka ki kula mini da yarana domin ki tuna ko ba aure na san zaki iya kula min da yarana don zumunci. Kina da hakuri, ki kara hakurin na gode”. Tsaki naja sannan na yaga takardar, nace ba zan iya zama da kai ba in ko ka ki wallahi zaka ga wulakanci ganin idonka. Haka mukayi ta yin wankan jegon nan yara kam ko kallonsu bana yi, nono kuma sai momy ta tsaya a kaina sannan zan basu, in ko ba ta nan in dage ince sun sha. Satinmu uku ya umar yazo dubamu sanda shigo suna ta kuka ni ko ina kallon filn dina, kuma ina jinsu dama ko suna kuka sai dai wani ya dauke su ya basu ruwa, har mamakin su momy keyi wai ko da labari basu taba jin labarin shashashar uwa uwa irina ba, kashe TV yayi sannan yayi bedroom, ya dauko su yana duba na ranshi bace. Ban san irin qin da kike min ba asma'u, ko baki sona ai kya so 'ya'yanki. Na dube shi in dai ba zaka sake ni ba toh baka soma ganin takaici ba ya umar. Yayi shiru can yace toh bata nono shi kuma sai in bashi madara, nace bani dashi. Na mika na fita. Innalillahi wa inna ilaihir raji'un kurum yake ambata a zuciyarshi. Haka ya basu ruwa da madara, gashi ba aikin shi bane duk ya bata jikinshi. Sai ga nafisa ta dawo daga makaranta, nan ta taimaka mishi ni kam ina tsakar gida. Haka muka yi arba'in ko yawon arba'in bamuyi ba su abba suka ce maza in shirya zasu kira mijina a waya mu tarkata mu koma tunda iskancin da nake ma yaran kenan. Inje in ma zan kashe su ne in kashe su. Da na sa ma momy kuka sai tace kada in mata kuka itama tafi son yaran a kaina don haka bazata iya kallon cin fuskar da nake yi ma yaran kuma jikokin da tafi so duk cikin jikokinta, haka na hakura saboda dama gurinta kadai nake ganin fuska yanzu kan yaran nan har rahma tsiya mukeyi da ita. Waya abba yayi ma ya umar kan cewa yazo ya kwashe mu yace toh amma ba cikin wannan satin ba, saboda farida bata da lafiya yanzu ma asibiti zaije kaita. Abba yace assha, me ya same ta? Yace wallahi ciwon ciki haka ta kwana abba yace Allah ya sawake mata. Farida tana ta murkususu tamkar zata mutu, likitoci suna ta bincike kanta, ya umar tare da wasu abokanshi suna ta kai kawo a kofar da aka rubuta emergency. Kusan awa daya likitocin suka yi ta fita daya bayan daya, duk wanda ya umar ya tunkara sai yace yana zuwa. Daga karshe babban likitan ya fito ya dubi sy ya umar yace wanene mijinta? Cikin fargaba ko ta mutu ne ya umar yace nine. Likitan yace biyo ni office. Bayan likitan mai suna dacta bashir M ya bashi hannu sun gaisa yace matsalar matarka nake son shaida maka. Ya umar ya gyara zama. Dacto ya bar rubutun da yake yi yasa gindin biron akan habarshi. Kasan matarka tana shan giya? Ya umar ya mike da sauri, dr kace me ne? Kasan me kake fada kuwa? Dr yace calm down my friend. Da yawa matanmu suna irin wadannan dabiun. Ya umar ya katse shi to ni matata bata shan komai sai da coke ina zaton baka san aikinka ba. Ya fita yana masifa ya isko su aminu in da ya bar su. Yace kunji wannan wawan likitan wai farida tana shan giya, kuzo ku taimaka min in canza mata wani asibiti. Likitan yayi kokarin fahimtar da ya umar amma abin ya faskara dan yayi fushi sosai. Aminu da sali kam basu ji wani mamaki ba, domin sun jima suna zargin farida dan dai basu da shaida ne, amma sun taba ganinta da wani alhaji a wani guest house amma sai ta nuna musu wai matar mutumin ce kawarat kuma tare suke da ita ta shiga ciki ne. Su kuma sun san wannan mutumin mane min mata ne. Alhaji jamilu kenan. [7:51PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----13 Special hospital suka kai ta, a can ma sun ce suna zaton tana shan giya. Yace shi fa sam matarshi bata shan ko maltina sai dai coke. Sunce ko ma dai menene take sha to ta daina don ya soma lalata mata huhu da hanta. Sun cigaba da kula da ita bayan yayi waya mamanta tazo daga yola tana kula da ita. Suna nan su momy mota daya sukayi sukaje dubata har tana cewa ina yaranta? A ranar ne momy sukayi maganar dawowarmu ni da yara. Ya umar yace don Allah momy ta samo wata dattijuwa wadda zata dinga kula mishi da yara saboda ni makaranta. Momy tace ko ba makaranta asma'u bata son yaran nan ya ce tana son su momy kunya take ji. Kallonshi kawai momy tayi sannan tayi murmushi domin yanzu baya son laifin asmau. Haka akayi momy hajjo ta samo mana daga gombe mace mai son yara da tsafta tun a kaduna ta soma kula dasu, iyakata in ta matsa min in basu nono sau daya a rana. Ina jin nauyin hajjo musamman da take ce min anty. Banaso amma tace sunan babbar yayarsu gare ni don haka ba zata iya kiran sunana ba. Satin farida biyu aka sallame ta. Yazo ranar sati zai kwana mu wuce sundau, niko in da nake ma bai nema ba ya kwashi yaranshi masu hakuri inji momy tare da nafisa suka fita. Tun dare na soma shirin kayana kamar yanda momy tace inyi. Ban sallami kowa ba saboda na kula kowa haushina yake ji gidan mu kawai na shiga mukayi sallama. Mama tace dama ina so in gaya miki yarannan amana ce Allah ya baki kuma ranar gobe kiyama zai tambaye ki yanda kika bi dasu. Don haka kije ke da Allah in kin cuce su. A mota ya umar yamu da hajjo dasu sayyid da sayyida shine sunan da muke kiran yaran su anty aina'u ne suka samusu sbd sunan momy da abba ne nima zanshiga baya hajjo ta ce keko anty me zai kawo ki nan ga mijinki gaba? Ya ce a to gaya mata dai hajjo. Na koma gaba nazauna banida walwala har muka kai abj dakina na farko nan naga amaida dakin hajjo wani daki na kusa dana shi wai shine nawa kenan nida farida mun sakashi tsakiya lallai yana nufin zama zanyi Da dare ya shigo muna zaune da hajjo tana cin abinci ya ce intagama inje in nuna mata dakinta nima nakosa mu kebe sbd ina son takardata ko ta halin yaya ne. Na kai ta ta ce don Allah ki lura da yaran sbd dare koda zasu tashi kibasu ruwa na ce bamai hanani bacci na gwarama ki kauso su nan ta ce to andebo su mun samu yau mar yana gyara musu kwanciya hajjo ta ce dama nazone in tafi tasu ya ce barsu nan hajjo nan zasu na kwana insuyi wayo sai sukoma hannun ki ta ce to sai da safen ku tafita nashiga na zauna kan kujerar madubi ya dube ni kin watsa ruwa? Na ce ance maka nayi datti ne? Ya ce a'a na ce ba damuwar ka bane yanzu yaya maganar mu ? Ya ce aike kin cika hanzarine ina son insake ki akwai abubuwan da nake dubawa ne shiyasa kinga yanzu matsalar ki yarannan sbd su kowa haushin ki ya ke ji hakan bayamin dadi don hk nake son ki daure kishayar dasu na shekara daya sai in sallame ki hkl kwance yanzu amshi wannan ya mika mani wani dogon file wannan ki adana na yaranki ne kowannansu yanada hannun jari tare da acct din su na bude musu don care dubu dari bibbiyu nace ai kabar su gurinka ko kuma kaba farida tunda dama ita zaka basu ya ce ke nace ki adana na ce bazan amsa ba zanyi magana ya pls na amsa shi kuma ya fita wai yana zuwa gama shirin bacci na saka rigar bacci na kwanta na ba yara baya ina addu'a ya shigo ina shafawa ya zauna kusa dani shi shirin bacci yayo gajeren wando da rigar bacci mai budadden gaba na dubi kirjinshi gashine kirjin yana sa jin wani yanayi don hk na kauda kaina ya ce sufa bakiyi musa addu'a ba ban tanka shi ba nayi kwanciyata yayi musu addu'a ya kwanta bayana jikinshi ya jawoni na ce menene wannan hk? Kasan dai yanzu babu wannan a tsakanin mu ko? Ya ce dama ai shekara 2 na ce yasoma shafata to yau kadai kimin taimako na matsune na ce ka matsu da me wai baga matarka nan ba? Ya ce ai itama babu lfy na ce gaskiya ni yamanna bakinshi cikin nawa na soma mutsu mutsu amma tuni yasan hanyoyi janye hkln diya macce tuni na manta da batun ki maka lulu duniyar ma'aurata sai da komai ya natsu sannan naso jin haushin kaina na tashi na shiga wanka shima hk yana yana fitowa ya haukan sallaya yashiga kaim ubanjigi kukan shi ina bacci cikin dare sayyid ya tashi kuka ya saka babanshi ya dauko shi kusa dani ya zauna ahkl ya ciro nono ya mika mashi cikin bacci naji ana shamina nono na tashi da sauri yasoma shafamin kai yi hkr kinji kadan zai sha na ce shine har da sata? Yayi dry basata ba srry pls Muna zaune cikin sabon dakin nawa hajjo tana ba sayyid madara ya umar ya shigo cike da murna ya ce sannu hajjo suna shan madara sosai ta ce suna sha ai yaran nada hkr ya ce sun gado mamansu ne ya dan dube ni itama uwar tasu akwai hkr na kau da kai gefe ya ce kuzo ku gaida farida sbd ta kwanta asibiti hajjo ta ce to ta dube ni taso muje anty natashi muka shiga dakinta tana kwance tana waya ganinmu yasa ta dauko dogon lbr na ce da hajjo zomuje ta ce a'a bari tagama hk na hkr sai da tagama mun gaisheta ta amsa cike da isa ta dubi sayyida dake hannun hajjo ta ce wakike da suna ? Zo nan hajjo ta mika mata tare dafadin ga sayyida nan ni dai nafita na barsu ciki Kai ya umar akwai shegen wayo, haka yake min wayo shi ya same ni sannan su sha nono. Da rana ne ma ba na basu, yace ma hajjo ko basu sha da rana ba kada ta damu, suna sha da dare. Ko ran da baya dakina sai sun sha yake zuwa ya kwanta. In ko yayi tafiya ne bana basu, komai ma bana musu. Hajjo ce wankansu, wankinsu, cinsu da shan ruwansu. Farida kan dauke su amma da ta samu sauki fa ba sauran zama sai yawo. Yau ma da take zaune cikin supermarket dinta kallon matashin yaron takeyi wanda yake cikin yaran da ke kula da gurin ta, jin sha'awar yaron ya shiga ranta sosai, don yau kam za ta neme shine. Sssss ta mishi alamun kiran 'yan gayu, ya juyo ta kira shi da hannu. Yazo cikin girmamawa ya dan rusuna tace ka iya jan mota? Yace na iya madam. Tace to zaka kai ni gidan kawata. Yace toh. Suka fita bayan ta ma mai kula da yaran bayani cikin mota take tambayar shi shi dan ina ne? Yace shi dan taraba ne. Tayi ta nuna mishi hanya har suka isa maitama gidan su aminiyarta lady. Ta shiga suna ta lido ita da saurayinta, ta kira lady gefe wani yaro ne da na jima ina jin shi a raina, so nake inji irin nashi kwazon. Lady ta saka dariya yaushe kika tashi ciwo, amma kin koma jarabarki. Toh kin gaya mishi? Tace a'a, lady tace toh ni dai zamu bar muku gidan. Ta shigo da yaron, ba ta bata lokaci ba gurin nuna mishi nufinta, saurayin mai tashen balaga sai wanda Allah Ya tsare. Take ya yarda da nufinta kuma ta yaba ba laifi, sai dai bai kai mijinta ba. Haka tace a cikin ranta. Allah ka tsare mu da sharrin zuciya. Cikin haka muka samu 'yan watanni kamar hudu, yara sunyi kwari gwanin sha'awa inji mutane. Suna zama kowa ya gansu sai ya kara dubansu. Tuni na cigaba da karatuna. Ya umar yace ya kusan soma hutunshi in shirya zai dinga koya min mota. Nayi murna don ina sha'awar tuka mota sai dai ban nuna mishi ba. Tafiya ta same shi ta gaggawa kuma sati uku zasuyi a can kara benin. Don haka yana ta bar mana amanar yara, nace kai ma kasan ban da lokacin yaranka. Ya bar su ga farida da hajjo sannan ashe ya hada computer shi yana son ta ringa dauko mishi yaranshi kafin ya dawo. Bayan tafiyarshi na lura da wani abu, farida tana son yaran ne na ganin idon babansu. Tunda ya tafi bata kula su. Ni ko bai dame ni ba. Ko hajjo ma ta kula, don haka ta min magana. Nace su suka sani, tace koda yake kema uwarsu kin ki su bare ita da ta gansu a sama taka? Allah ya shirye ki. Na taba ganin inda ake son uba amma ba a son yara? Na dube ta nifa bana son shi hajjo, tace tafi can 'yar nema, yarinta ko da nake tsohuwar da kike kina son mijinki. Naki salon son ne haka. Na dafa kirji. Allah hajjo ba sonshi nake yi ba. Tace ai sai kiyi. Na jima cikin daki ina mamaki, yaya kawai ta min fassara wai ina son shi, yaya ma son yake? Na taba son suraj amma bana jin zan tuna yadda so yake, me yasa hajjo tace ina son mijina? Naga bana mishi magana, ban mishi dariya amma tace ina son shi. Gidan aminu muka je yau ni da hajjo, tace zata bini don ta gaji da zaman gidan. Aisha matar salis nan muka same su tare da aminan aminu. Mun sha yini in da muka sha hira soasai, sai biyar muka bar wuse wato unguwar su amina. Mun dan shiga kasuwa sannan muka yo gida. A falo na ga dankwalin lace din farida. Na wuce shi, hajjo ma ta shigo dauke da 'yar daya a baya daya a kafada suka yi dakinta. Ina bude kofa na ga sun fito daga nata dakin ita da wani saurayi, da ganina sai duk suka rude. Ta soma mishi magana kace ma anty aminan zanzo kaji ko? Allah Ya kiyaye hanya. Cikin in

Chapter 14 of 16