Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
anti kudi ta sai duk abin da ya dace, cikin farin ciki abba ya samai albarka. Abba yace dama nasan baxaka watsamin qasa a ido ba, yarinyar ma ta gida ce, asma'u ce yar gidan babanka alhj ahmad, gabanshi ya fadi da sauri ya dubi abba, abba ya ce yaya? ya umar yace a'a ina mamakin ta isa aure ne? abba yace qwararai shekara sha biyar ina laifi? takaici ya cika ya umar amma babu dama ya nuna, yace a'a babu laifi amma inaga gobe xan koma sad muna da training jibi. abba yace to kaje ku gana da matarka sannan abokanka su xama wakilanka anandin, yace shi kenan abba xan yi duka, daga nan dakin momy ya wuce ya sa mata rigima shifa baya san wannan yarinyar yar iska ce, momy tace kai na gari ne? yace Allah ya sani ni momy ina qoqarin kiyaye dokokin ubangijina, momy tace to kasa ma ranka ka auri mata ta qwarai, shiru yayi yana mamakin yanda su momy da abba basa kishin dansu. sunfa san halin yarinyar nan,amma sun nace,itama cewa tayi yaje ya gana dani sannan tace yasa abokanshi cikh kan ya tafi. ba ya iya ja da iyayanshi dan haka yace to momy, amma Allah yarinyar nan batada kunya. Ya umar yace kinsan fa ta taba watsamin ruwan datti? momy tace ai yarinya ce quruciya ke damunta, yace haka xanje ina fama da ita? tace ai xata daina ba xama tayi ba tunda taga daga kai sai ita, ya fita ranshi bace,kofar gida ya tsaya ya kira aminu, amininshi ne yace aminu ina jiranka nan kofan gidanmu, aminu yace captain umar kana kd kenan? yace eh dan allah kaxo ina cikin damuwa. kafin xuwan aminu sai ga ya aliyu yayi mamakin ganin ya umar dan ya kan kira shi ya sanar da shi xuwanshi, yace yaya yanxun kaxo? ya umar yace bari kaidai aliyu sai addu'a ba dadi ya kawo niba, amma shiga gun anty ka ce ta rbt abubuwan da ake so game da lefe da sauran abubuwa sai kaje ka cire kudi kuje kasuwa da anty, yace auran wa xa ayi? yace shiga kaji gun anty ko momy? aisha ta sameshi tsaye ta rusuna ta gaidashi sannan tace mama tace kaxo,yace to kice gani nan xuwa, tun dama shi dan dakin mama ne girma ne da kuma yawon aiki ya sa ya rage shiga gunta.ya shiga gefen mama ya nufa ya same ta xaune duk bata cikin walwala. Yayi sallama tace shigo faruk, ya umar ya shiga tare da fadin mama kina ciki? tace uhum ina ciki faruk, dama ina tunanin yanda zan ganka sai aina'u tace minute gka. waje shine nace Aisha ta kiramin kai, yace jiya nazo abba ne ya kira ni kan zancen aure, tace nima neman da nake ma kaa kenan , shawara zan baka kar ka amince da zancen auran nan, don yarinyar nan llaataccya ce, cikin mamaki ya dubi mama tace kana mamaki ne? nasan ba xan boye gaskiya ba in goyi bayan karya, ji nayi yana jin kunyar mama domin mace ce mai mutunci ba zai ya nuna bayason jininta a gabanta ba, domn ba zai manta lbrn da momy take bashiba takan ce haihuwrka kaawai nayi amma mama itace ta rene ka taci kashi da fitsarinka, lokacin bata haifi abubakar ba. haka sanda ta haifi abubakar din ma sai ta'aje shi ta dauke ka , shi kansa sanda ya taso yasan shi dan gidan mama ne sai shi ne ma yasa mata mama ya bita, tuna wannan da yayi shine yasa ya kara sadda kai kasa sannan yace mama ai yarinyar nan kanwata ce, kada ki damu mama tace kaima baza ka bani goyon baya ba? na sankaa faruk tund ka taso baka da mugun hali ita fa? ga rshin kunya a gunta kwani fatima tace min har ruwa ta watsa maka? yace ai wannan ya wuce mama kada ki damu, yanxu ina take dama dan ita nazo in hada ta da abokaina,ni muna da training jibi gobe znbi jirgin safe ne, Shiru mama tayi harga Allah bata so haka ba, don tasan ko itace ce abubakar zai auro mai irin halin asma'u baza ta yarda ba, kudi ya zube mata sannan ya fita, tace ai ni daka barsu faruk tunda momyn ka ta hana ka yarda da batuna, yana fita yaga aminu yazo sun gaisa sama sama sannan ya shiga rattafama aminu halin da yake ciki saidai bai sanar dashi yawon da asma'u keyiba, ya dai ce mishi bata da kunya, kuma yarinya ce karama. amma ko me kenan su hadu da dare. bayan sunyi sallama yace ta shiga gidan alhaji ta kiramai mara kunyar gidan yana fadin haka tasan asma'u ce, don haka saita wuce. a dakin hajiya a same ni muna kallon tashar MBC2 tace asma'u ya umar yana kira na dafa kirji [1:39PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Biyu1-----10 Nayi shiru hjiya tace naje bansan me kiran ke nufi ba, don haka yanda nake haka na fita hijabi kadai na saka sanda naje yana waya da faridanshi ne don naji yana cewakada ki damu farida ki sama ranki wannan auran dashi bababu duk daya ne zan kuma kira ki ya dan jima yana bata baki kafin daga baya sukayi sallama, ni dai ko a jikina tunda ban sn me ake ciki ba, yamin rin kallon dana tsana, tamkar yaga kashi, yace ke karama jeki canza kaya ba zaki shigar minute mota da datti ba, ban fahimce shi ba, don haka nace ni ban gane ba, yace ai ba zaki gane ba ya shiga gidansu nima na wuce gida, har naje daknmu na kwanta sai kuma nayi wani tunani kadanayi laifi ni 'yar sarkin laifi don haka sai naje na samu mama, nace ya umar yacena canja kaya na same shi, ni kuma ban gane nufin shi ba, harara ta sakar min sannan tace ai da wanda zakuje party ne baza ki zo ki gayanba,jin haka yasa na fita. shadda na saka riga da siket green , na saci hijabin hadiza na saka,saboda yafi nawatunda ni duk cikn hijabaina babu dogo. dga cikin zauran gidan mu ina kallonshi yana waya, a raina nace Allah mutumin nan mugu ne ,jibi yanda yake wani shan kamshi yana waya ma kenan shiyasa na tsane shina tsaya a kofar gidanmu ,yana gamawa ya dube ni cikin hada rai a raina nace donka ganni da kananan kaya ai ba wani ka gnni ba, na isa gurin yana kokarin bude mota ya shiga, sai ga abba ya fadada murmushi ganinmu tare yace sai ina haka umar? yace zan kaita ne abba ta gwada wasu takalma , abba yace to Allah ya shi muku albarka , gabana ya fadi na dai durkusa na gaida abba ya amsa sannan ya isa gurin motarshi ni kam kaina ya daure da yawa, ya umar ya shiga motarshi nima na kama gaban xan shiga yace karki yarda ki shigo min nan ni sa'an ki ne shiga baya, na shiga na zauna, Allah ba don ina tunanin kada na koma gida inyi laifi ba, Allah bazan bishi ba, don dai ni a gidan mu bani da 'yanci yin abu komai kankartar sa, shi kenan nayi laifi, don kuturun wulakanci muna cikin tafiya sai cemin nayi maza in saukar mishi daga kan seat in tsugunna kada agan mu tare sunan shi ya baci, raina yayi mugun baci har kwalla suka soma zubomin haka na tsugunna gurin aje kafa. Bansan ina muke tafya ba saidai naji ya kira farida, suna hirar soyayya, a raina nace har na tausaya miki ko wacece wannan faridar baki san shi bane shiyas, aini dan auri y umar gara na mutu b mji, can naji ya kira doctor hassan yana fada mishi gashi nan zuwa koda mottar ta tsaya ina nn inda nake nafi minti 30 kafin naji an bude min kofar motr yace fto daa Allah I ni wannan sai na kaita wurin car wsh, ni dai na fito kafafuna duk sunyi tsaami yace wuce muje sai kace ya Allah tasha wani zunbulelen hijabi, fir'auna a zuci musa a baki, ban dai tanka ba yayi gaba na bishi a rana nace to wanene aka kwantar a nan asibitin,, dan naga an rubuta (dirman hospital). office din da muka zauna ba kowa, can lkitan ya shigo wani dan dogo fari, yace ku shigo? ya umar yace eh gatanan ya nuna ni ina zaune can gefe likitan ya dubeni ya jima yana kallona tamkar mai nazari, har dai na gaji na mishi kallo da yake nufn kallon fa? yako gane sai yace captain umar kanwar nan taka ta cika tsiwa, ya umar cikin daurewar fuska yacekayi abin da muka zo y , ai da'a tsiwa ta tsaya da sauk, na dubi ya umar abin shi ya soma isata, ya ballo min harara na sunkuyar da ka, in ya hade rannan tamkar zaki nake ganinshi. likita yace to ina zuwa nidai sauraron abin da za'ayi , fita likitan yayi bai dade ba ya dawo dauke da allura da sauran tarkace, ya tsaya kana kawo hannunki? ni uwar tsoron allura don da amin allura gara na mutu da ciwona, haka nakan fadi in bani da lfy, ance muje asibiti amma yau gashi dan kuturun wulakanci lfy ta lau an sako ni a mota gurn sa kafa za'a min allura, tsawa ya umar ya min ki ba da hannu akace, nace to ni me za'a min ? kai tsaye ya umar yace gwajin kanjamau, na mike tsye da sauri saboda sai naji kamar nima a nan za'a sa min ciwon. ya umar ya kuma daka min tsawa ina zaki? na soma kuma ni bani da koma ban karasa ba naji saukar mari, tuni na nutsu. likitan yace bi ta a sannu , ya kama hannuna yasa allura ya cako jinina, suka fa tare suka barni ina ta faman kuka, a raina nace kila ma sbd ya tsaneni ne shine zai kala min sharrin cuta,kusa awa daya ya umar ya fara shigowa yace in naji kin fada ma wani inda mukazo, Allah sai kin gane kuranki, ni dai ban tanka ba sanda likitan yazo ya umar yana waya, don haka ya shiga 'yan rubuce rubuce bayan ya gama lkitan yace captain munyi gwaje gwaje kamar yanda kace bamu samu cuta ko daya ba,wato captan yarinyar tana da lfy sosai, a wannan zamanin damuke ciki samun yarinya ko ince a dari da kyar a samu goma, don haka bata da kanjamau kuma bata da sauran kananan ciwuka. y umar ya harare ni, wuce ki zauna inda kika zauna dazun, Allah ya taimake ki ya jima sannan ya fito ina da gangan yayi ta wani shegen gudu sai bigewa nakeyi da kujeru, naji mun tsaya sannan fa ya leko yace in fitar masa daga mota, daknmu na shige na kwanta kan gado na darsawa a raina bani da babbanmakiyi nan duniya kamarya umar ina ruwanshi dani don bin diddigi zai kaini gwajin kanjamau? a fili nace Allah ya isa. sam koda wasa ban sani wai ana shirin aurena bane , har sauran kwana hudu amma duk 'yan gdanmu da yaran sun sani sai dai ance kar su gayamin, don kar mu gudu da suraj , basu san yau rabona da suraj din ba tun ranar partyn nan. yau dinnan rahma tazo muna hira ina bata lbrn musanyar jakar da mukay da samir ban gama bamukaji sallama, ni dama ina daga ciki gurin da muke sallah kan sallayan ma nake. rahma tana daga bakin kofa tana kallon waje sanaj tace ka! akwatunan wanene wannan? waye zaiy aure a gidanku? nace nan gidan kuwa? tace ga akwatuna gud 6 rabin dozin? na mike na leka na koma na zauna hadi da tabe baki nace oho ,kila nasu anty aina ne kinsan ni yanxun a gidan nan agola ma ya fini daraka, komai sai dai inga anayi bana sani.rahma tace ba haka bane Allah suna sonki, sunf son suga kin canza ne nnace ba wani so dai ai sha'ani tsan ce kawai tunda in dan kaya ne tun yaushe na daina sawa? amma ko da safen nan sai da ya usama ya rarrankwashe ni sai kace nayi mishi wni laif, wai fa don kawai munyi karo, tace ni kin tuna min sai ga ya usman a gidanmu jiya wai yazo mu gaisa ,ni sai naga tuntuni kamar zaice yana sona nace tab ai wlh ki ka yarda kika auri ya usman shi kenan ni da ke danba zanje gidanshi ba, tace kai don Allag sbd me? nace allai ashe sonshi kikeyi? tace bai dace ba? naja tsaki. canja min lbr ni yan gidannan saida na kalle su kawai. rahma tace har mamaki kike bani, yayama za'a ce 'yan gidanku sanan su tsane ki ko ka kuma suki ki? nace duk abin da akemin a gidan nan haka ke miki a gidanku? kafin ta bani amsa Aisha tayi sallama muka amsa , tace anty asma'u kije inji wani mutum. nace kn san shi? tace a'a nayi shiru can nace ba suraj bane? tace a'a nace jeki. ce wanene? jim kadan ta dawoyace sako zai baki na mike rahma zo muje tace sai kin dwo nace don Allah ke da zo muje ta mike muka fita. yana tsaye jikn gidanmu sanye da jeans da shirt ban gane shi ba amma saimuka karasa, muka gaishe shinace kine kake nema na? yace eh sai na ke gann kamar na sansh, yace kn sann? nay dan murmushi sannan nace eh to na dai ganinna taba ganinka yace ok to n abokin captan ne nace wanene kuma cptan yace umr,nay wani bala'in hada rai, yanzu na gane shi shine wanda na watsa ma ya umar ruwa suna tare,cikinmasifa nace to lfy malam? yace kwantar da hankalin ki , sunana Al-amin nazo ne nagana da kawayanki don musan shirunku da abubuwan da zakuy,naja tsakinace kayi kuskure don ban gane nufinka ba, zo muje rahma nayi gaba. yace da rahma, zo ke ,tace Asma'u zo kiji nayi tafiyata, yace ke kawarta ce? rahma taceeh yace maganan bikinta kinsan angon baya nan. shine nazo naji bukatunku, kan rahma ya daure tace auran asma'u dawa to? yace da ya umar baki sani ba? rahma tace itama banyi zaton ta sani ba, yace shi kenan yanxu kije ku rubuto abubuwan da kuke bukata, tace anyaba kuskure bane? malam ina ga ba asma'un gidan nan bace, yace zan dai dawo anjiman. ni kam ina shiga cikin gdan naci karo da su anty amaryar gidan su ya umar ita da wa'yansu mata sai naji tace yauwa gama amaryar nan, ta nuna ni na kalle su cikin rashn fahimta, su kam sai kallona suke suna fadin tubarakallah masha Allah, gata yarnyar 'yar karama zai more aure,na wuce ni fa abubuwan da suke faruwa 'yan kwanakinnan suna daure min kai. na shiga cikn dakin umma na jiyo hayaniyarsu ina isa naga duk daukacin 'yn gidanmu ne illa mama. kadai ce bata gurin. [1:41PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: uska Biyu1----11 Duk suna kallon kayan a akwatina shiga ina fadin kayan wanene? duk suka duben, umma tace kayan ki ne shigo ki gani. na dafa kirji naceni? tace kwarai. anty aina'u tace wasa ake dake da za'ayi miki karya? nace to wa zan aura? shema'u cikin doki tace kinji dadinki yaya umar fa soja kai dama nce? ya umar fa kika ce ? fatma tace ki godema Allah kike wani ya umar,nace na shiga 3 ni asma'u , na mutu. fatima tace shegiya a irin wannan halinnaki ma ya rufa miki asiri da gudu na nufi daknmama tanakrga kudi na shiga a firgice nace mama wa ni za'ama aure da da yaya umar? don Allah mama banason shi ki taimake ni, tsawa ta daka minute yi min shiru har kna wani baki son shi an gaya miki shima sonki yke? to bari kji rokonshi akayi ya aure ki dan ma kada kije kina daga mishi hanci ki dube shi da kyauba ajinki bane. mamkn mama ya cikani,nasha zata a zuciya nake magana ashe ba hka bane, nace anya mama ku ne ku ka haife ni? saukar mari naji tare da fadn , tsinto ki mukayi, da gudu na fita dama ni uwar kwakwazo gashi ta same ni gurin ido , ihu na saka ba kukan mar ba sai na kin auran nan yau kam na kara yarda ba'a kaunata,ba'a sona na shiga 3!! haka nake fada da gudu 'yan gidan suka fito daga falon umma, hajiya da umma suka kama ni. Rahma ce me tambayataa rude menene asma'u? asma'u meya faru? umma tace kinji halinki aike asma'u sai kwakwazon tsiya baza ki fadi magana ba, cikin kuka nace don Allah umma ku taimako banason ya umar mugu ne Allah gara k kashe ni da kanku, anty aina'u tace dubi yar iskar yarnyar nan zai rufa mikiasiri da wannan mugun halin naki ya aura amma har kike fadin baki son shi ban sanlokacin dana ke meyasa baki aura ba za'abani, don ba'a sona ....duka suka rufeni dashi ita daant aina'u da anti fatima , da kyar su hjy da umma suka kwace ni, sunamusu fadan meyasa zasu duke ni na kufce nayi waje da gudu zan fita mama tana cewa kada ki fita gidannan,kcibis mukayi da yaya usman,nabi ta gefenshi zan shara da gudu ya damko ni. gidan uban wa zakije haka sa kace mahaukaciya?nace da dai ku barni in tafi, ya wurgoni cikin gda, mama da kanta ta dauki ice ta shiga muka min . rahma ta rungume ni tana kuka, mama tace matsa ko kema inmaka miki, su hjy suka shiga ssai kuka nake . hjy tace kin ja ma kanki duka a banza, cikin kuka nace ba'a sona hjy wlh an tsane ni. hajya tace ba tsana bace ke ba abin alfahari bane a gurnki? nace haba hjy wane alfahari? dubi yanda aka bar su anti aina'u sukayi ta karatunsu, sai ni ce za'a ma aure kuma maimakon aban wani sai a ban ya umar , wlh nasan kashe ni zayayi. Hjy tace wanene mugun?Umar din?Ban bata amsa ba na ci gaba da kukana.Rahma ma kukan take tana bani hkr,kafin wani lkc zazza6i ya rufe ni fuskata ta kumbura.Rahma ta ce bari taje gida ta sanar ma Momynta,ni dai ina kudundune ban san ma lkc ya yi nisa ba,ashe hr dare yayi. Muryar Momyn gidn Abba na jiyo wato Maman su Ya Umar,ta shigo suna cin abnci a barandarta da su Umma,na ji tana cewa Hjy Saude dk naji abn d ku kai ma Asma'u dan cin zalin a bi yarinyar da lalama abu ya faskara,sai ku taru kuna shigarta sai ka ce jaka?Umma ta ce to ai a gaisa tukunna ko? Momy ta ce ba ita na zo ba, Mama ta ce kina take sani ne yarinyar nan Umar sa'anta ne? Ai shi aka cuta ga mugun hali yayi biyayya ya hkr shi ne ita da zai rufamawa asiri zata ban da she shi ana kallonta? Momy taja tsaki yanzun ina Asma'un take? Hjy ta ce tana can dakin a nan Momy ta same ni ina ta rawar sanyi ga fuska suntum. Da sauri ta fita ta samu Ya Ali ta ce ya dauko motar Abba muje asibiti bn san asibitin da muka je ba na dai ji ana gungura ni akan gado,allurar da bana so yau kam na sha ta,Likitan ya ce zamu kwana don dan karamin ruwa , sannan da safe in ga Likitan ido Momy ce Ta kwana a guna duk d Momy ta aiko masu Mama cewa anbani gado,sai Mama ta ce ai ta bani mana ba ta zo ba. Da safe Anti Amarya suka zo da Abba,ya yi fada kamar me? Su Umma d Hjy sun same shi yana fadan ya ce shi ne sai a samu yarinya ai mata irin wannan duka sai ka ce jaka? Ai zanga Alhj Ahmad din zuwa yamma Likitan ya Sallame mu muka nufo gida, tun a hanya na ce Ma Momy ni fa wlh ba zan koma gidanmu ba,ta ce ai nima ba zan kai ki gidan Abba muka wuce dakin Momy muka shiga na kwanta akan gadonta tasa Anti Salima ta dafa min wake da hanta na danci. Da dare ta kira Ya Umar a waya landline ta ce bn d lfy mun kwanta a asibiti, ya ce Allah ya sawwak'e yanzu ina ina ne? ta ce gani sai na amsa nasa a junne Momy ta fita tana Murmushi ina dauka ya ce ai ni sun min dai-dai,Sun ma miki kadan sai ma kin yarda kin shigo hannuna.. Tun jiya na samu lbrn lugudan da aka miki, ki shirya zaman uk'uba,ya kashe wayar,na koma na kwanta kuka na saka,san da Momy ta shigo ta same ni ina kukan ta zauna ta dago ni me ya faru ne? Gaya min me ya ce miki? Cikin kuka na ce Momy don Allah ki taimaka min a fasa Auran nan,Wlh Yaya Umar ba ya kaunata don Allah Momyna,rumgume ni tayi tana fadin "kwantar da hnklnki Asma'u in har naga abn ba mai yiwuwa ba ne ba zan bari ba, ke ko anyi naga da kwara zan san yanda zan yi a kai,na ce Momy Yaya Umar ba shiri muke yi ba,ta ce ki bar ni da shi bana son kina mgnr kada ki kara cewa komai ba na so kowa yana cewa ba ki da kunya.kiyi shiru duk abin d aka ce ki ce to kin ji?Na ce to.Tunda muka yi haka da Momy bn kuma mgn ba,sai kuka. Rayuea kenan,yau ni Asma'u ni ce zan auri Ya Umar mutumin da na tsana ya tsane ni,Rahma da wasu kawayena sune Momy ta sa su samu abokanshi lis din komai,ita ce in bar su ai raba mugu da makami ibada ne,sun shirya Sister day saiwalima don ni da don ta ne ni da sun bar shi. Ana gobe da daurin aure a kayi sister day din,kin yin wanka ma na yi sai da Momy ta sa baki ta ce in yi wankan tunda shi ba ya garin ma,,,, [1:42PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1----12 Dakyar dai momy ta lallabani nayi wanka ba don raina ya so ba, na danyi kwalliya amma raina a dagule yake, haka dai ake abubwan amma ina cikin damuwa a wajen sister day gaba daya hankalina yayi gida kawai dan sarari nake nema na samu mai machine ya kaini gida, Rahma ce take ta lallaba ni akan nayi hakuri har a tashi, sai da aka kusa tashi sanna Al-Ameen yazo shida wasu abokansu, bayan mun gaisa Rahma ce ta ce Munyi fushi sai yanzun hr an gama suka ce haba dai ta ce Allah munan ni gida zamu je ya dube ni to Amaryammu ya gaji ya?Na sakar mishi harara ya dubi sauran abokan ya ce kunga amarya tayi fushi ko ya matso kusa dani ya ce kada ki damu ya kara yin kasa da Murya, don Allah ba don ni ba kada ki bari wadannan abokan namu su gane halin da ake ciki.sbd basu san me yake faruwa ba.Hakan yasa na da daure na ce ina yininku?Suka ce lfy Amarya yaya jiki? Na ce da sauki Al-Amin ya gabatr dani Abdulmalik,Hasim,Sani,Sale sai Muhammad, na ce sannuku suka ce yauwa.Al-Amin ya ce me yasa zaki hau mashin?Rahma ta ce kasan bata jin dadi shi ne take so taje ta kwanta. ya ce to shiga mota mu kai ku,na ce ku bar shi ai kuma naga kun cika motar,ya ce bari wasu su sauka haka dai dole muka shiga. Muna isa bn jira komai ba na shige gidan Abba, na bar su suna mgn d Rah,a.Momy tana ta kiciniyar shigar ma d baki wadanda suka iso yanzn nan da abinci sai ta ganni tayi turus yaya dai 'yar gidan Momy? Na ce kaina ne ke ciwo gajiri,ta ce tofa,ina zuwa ta shiga da abinci dakinta ta fito,ta kira Anti Amarya ta ce bani makullin dakin Soja (Haka take kiranshi) ta ce Momy me za ki yi a dakin?Momy ta ce kwanciya matarshi zata yi ni dakina cike ke ma haka,Kin san kuma ba hayaniya take so ba,Ni ina cn ban son ma kome akeyi ba sai dai naga Momy ta bude kofa ta ce zo ki shiga 'yar Momy,ni dai bn ma san dakinshi ba ne tunda ni dai wayona ban san shi ba,daga baya nake ganinshi gwanin Kamshi na leka bedroom din naga ashe hr d Kofa ina zaton kofar ita ce ta 6ulla waje kusa d ta Ya Aliyu,na kwanta kn duguwar kujera idanuna fes suka sauka kan hotonashi sanye cikin kaki,na tsura ma fuskarshi ido yanayin hoton ya burhe ni hannunshi yana gefen kanshi alamar sarawa,na sani Ya Umar yana da kyau sai dai bana son shine na rumste ido ina tunanin zamn doya da manja da zanyi. Na tuna jiya jin wasu kawayena suna min murna nayi dacen mijin nunawa sa'a,sai wata ta ce ai bana sonshi,nan suka cika da mmk. Samira ta ce ke ko me yasa ba ki san shi gashi mai kyau gashi Soja mai mukamn Captain Samun irin su locky ne ke da ba kya gurin in kin tanka to na tanka,ina jin Rahma Momy tana cewa ina nan dakin,muna nan kwance muna hira jife-jife hr magrib tayi munyi sallah hr da Isha'i ai bacci ma ya soma dauka na sai kawai naji ana fesa min nono (wato salalle)ya Allah bakin ciki kamar me? Na saki kuka Momy ce ta zo ta hana,ta ce su fitar mata a gida nan ta lallashe ni bata so in wannan kukan nawa samin jikina ya tashi,tana dakin naji Abba ya kira ta tana fitowa naji yana ce mata nayi waya da Umar dole yazo daurin auranshi gobe in ma zai zi ne ya koma shi ya sani amma lallai ina son ya zo cikin jin dadi Momy ta ce hakan yayi in baya yazo ya tafi da matarshi,kwana nayi babu bacci addu'ata daya ita ce Allah ya dauki raina kafin gari ya waye a daura min aure da ya Umar,da safe zazza6i na tashi nayi kuka na gaji.rayuwa kenan. Misalin goma naji ana ga Ya Umar tamkar in bar gidan haka naji nan akayi ta shigowa da abubuwan tsaraba,su katan katan na drinks tun daga kan ruwa C way,hr zuwa kalolin Juice hakan ya faranta ran Momy da Abba hr Momy take tambayarshi ya sanar a gurin aikin nashi? Ya ce wlh Al-Amin ne ya dinga tura ma abokan mu da message ta waya,wadanda yasan Number dinsu,ta ce ai Aminu yaron yana kokari ko nan yana ta hidima da ita da kawayenta.ya mike yana cewa Anti Fa? ta ce tana can tana fama da baki 'yan Bauchi d Gombe duk sun zo ya ce bari in rage zafin nan ya dan tsaya ganin dakinshi a bude kamar kar ya shiga sai dai ya auno kai. lkcn ina kwance,Rahma d Jamila kanwarshi suna kallo.Ya tsaya yana kallonmu,ya ce kai waya ce ku bude min daki hr d kunna min TV? Cikin in ina Jamila ta ce Momy ce ta ce mu zo nan ta kashe TV ta mike Rahma

Chapter 4 of 16