Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
haka yasa nace ka bani kwai ni nasan me zance musu, na fada ina duban fuskarshi yace a'a sai naji tukunna,na sunkuyar da kai inawasa da yatsun hannuwana nace zance kwai ka sake ni ya jeho min tambaya da sauri kan wani dalili? Na dube shi nace ban ganeba, yace insuka ce kan wani dalili na sake kime zakice? nce zan ce ba komai yace kin taba ganin anyi saki babu fada? nace a'a zance nice na ce ka sake ni, yace to in sunce meyasa kika ce na sake ki me zaki ce? na ce zance sbd banason ka, yayi shiru sbd kalmar tana mishi zafi, yce toh shi kenan zanbaki yanzun, amma kin tanadi gurin zuwa? na dube shi cikin rashin fahimta, ya cigab kinmanta batun alhj da suka ce inkin kashe auranki ki nemi gidn uba? mama cewa tayi ko danginta kada kije bare alhj daya ce ya cireki daga cikin 'ya'yanshi. numfashina sai da ya nemi ya dauke sbd faduwar gaba na saka hannu na rike baki sam na ma manta yayi 'yar dariyar nasara, ni ko dan shirme sai nace to baga nan gidan ba? na cigaba ai dam na dade wurin momy ka manta? nan yamin kllon yarinta, yanzun ne ya gane wannn karamar yarinya ce, kuma cikin lkc kalilan zai mata wayo, ya jehomn min tambaya shekarunki nawa? na dube shi sannan nace 18 da wata 7 a zatona harda shekaru ake rubutawa cikin takardar sakin shi kam ashe wauta ta ce. ta saka shi tambayarta jin haka yayi murmushi laillai yarinta ya raya a ranshi, ya sake Ya sake cewa hakane na tuna anan gidan kike zama, sai dai kuma kina ganin za ki iya cigaba da zama da momy bayan kince baki son danta ina nufin ba zakiji kunya ba? nan take na gano kuskure na in har nasan kunya lallai ne nabar gidan nan to ina zani? zuciyata ta amsa min sai ki shiga duniya. na daga nace ba komai ka bani kawai zan tafi koma ina ne. da sauri ya dube ni, kina nufin zaki shiga duniya? nace eh, yace can cikin duniyar zaki samu ci da sha da gurin kwana da kayan ado da kuma uwa uba karatun da kike so? bari kiji in sana'a zaki kama shekara nawa zaki yi kafin ki samu registration, balle je batun skul fees, banda books, nan mana gano kurena, nayi shiru kawai yace inbaki ne? na dube shi to kai baza ka taimaka min ba? yayi driya sannan yace haba asmy cewa fa kikayi baki sona sannan kuma kice in taimaka miki? nace ai naga lkcn da baka sonama ka taimaka min na gama secondary, yace to wannan baki ganin lkcn kina da aurena a kanki? yanxun fa rabuwa zamuyi kin manta? na sake yin shiru yace to yanzun ya ya za'ayi? na dai kasa mgn dan naga gano bani da mafita, duk mun yi shiru gidn ma yayi tsit domn dama dre yayi Can yace ga mafita da sauri na dube shi in gaya miki zaki yarda,kuma zki yanda nace? na gyara zama me zai hna in dai zaka sakeni? yce zan sake ki mana, nace to ina jin ka yace zan biya miki kudin skul har ki gama zan dauki nauyin yi miki komaihar ki gama duk karatun da kike so, sannan kuma zan cika miki burinki na sake ki, in har kin yarda ki zauna dani ki haihu, kina haihuwa zan sake ki, kuma in cigaba dabiya miki kudin makaranta sannan zan gaya ma su abba cewa nine na sake ki don kainaba wai don kin min komi ba, na ce to in ban haihu bafa? yace nan da 2yrs sai na sake ki to karatunfa? yace daga mun koma abj zan nema miki jami'a ki fara inmun rabu sai ki tafi inama kika ce ? nace america inda su mina suka tafi yace ok, to me kika ce? nace to zanyi tunani za gobe, yce shike nan. tashi kije ki kwanta. sanda na shiga dakin momy tayi bacci ko kuma tana jina tayi shiru ne? oho na hau gado na kwanta shiru ina son yin tunani ne game da magarnar mu da ya umar , damuwata daya yanda zn jure zama dashi har na haihu, ko kuma in ban haihu ba yace 2yrs sai ya sake ni kuma yace zamn 2yrs xan mishi biyayya zan iya kuwa? Na sake juyawa naci gaba da tunanin in ba a wannan hanyar ba saidai in shiga duniya ga tsinuwar iyaye, hka nayi ta tunani har kusan asubahi, amma ban tuno wata hanya mai sauki ba, bayan na tashi saidai na yanke zan kara tuntubarshi da safe koda text ne inji ko zi taimaka min a zaman da zamuyi kada ya kusance ni? da wannan tunanin nayi bacci. shi ko ina fita yayi dariya sannn yace yaro dai yaro ne,ban da haka yaushe zata yarda da wannan mgn mai kama da tatsuniya, fes ya kwanta zuciyarshi tana shaida mishi ta same ta matsalar shi daya ce son da bata mishi, saidai yayi alkawarin shi umar faruk zai koya mata yanda zata so shi. da safe ina karyawa momy tace in ba da wuri zaku tafiba ki kwanta ki huta mana?na dube ta ban san sanda zamu tafin ba, amma na gaji jiya banyi barcin kirki ba, momy dama tasani shi yasa take son jin shin me ya hana ta barci, don duk tana jin motsnta da yawan jan tsakin da takeyi sai tace me ya hana ki bacci jiya? a shirme na da zan gaya matane sai wayata ta soma ruri na dauka muryan ya umar ta sauka cikin dodon kunnena, karki sanar da kowa halin da muke ciki,inason ya zama sirri nace to ni ma zaka ga text dina yace ina jira. Na dubi momy dake jiran bayani nace me ma kikace momy? tace cewa nayime yahanaki bacci jiya ko baki jin dadine? nace kaina ne ya danmin ciwo, sai na share mgnr, shi kam ya umar jikinshi ne yabashi xaniya fadama momy, shiyasa ya katseni kona ce yayi min kashedi. na fito wanka ina zaune bakin gadoina shafa mai nan na tuna da text din da zanma ya umar, na rubuta mishi cewa donAllh ya umar ina son kayimn wani taimako daya? in har zakamni toh xan amince da shawarar jiya , na tura mishi nan da nanko sai ga amsa ya turomin, sai na tura mishi cewa in har ka yarda zaka kyale ni ina nufin ba zaka kusance ni ba, na tura mishi sai gashi ya kirani kamar kada na dauka sbd nauyin mgnr takemin, amma sai na dure na dauka yace asmy kina jina?nace eh,yace ai wannan ba zai yiwu ba, taimkon da zaniya yimiki kenan, ki haihu min ni kuma inbiya miki skul in wanke ki gurn iyayenmu bayan na sake ki, kin yard ko a'a? yaci gaba da fadin ina lallaba ki ne kawai amma kin san matata kike addini ya bani dama ko da karfine in nuna gurin saduwa dake wato in kika ki kenan,na dai duba laifukan dana miki ne na baya shiyasa nakeson wanke kaina gurin ki, [7:40PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----6 Amma in kina son haka zan miki ya dan kausasa muryarshi,sannan yace ki zaba ko yanda nace ko kuma mu mukoma inta nuna karfina ina saduwa dake kuma ki samu cikin ki haihumin, sannanbaxan sake ki ba babu kuma karatun inma naga dama duk shekara sai kin haihu da yardar allah. .da sauri na ce don allah kayi hakuri na yarda a na farkon yace shi kenan,na zabga tagumi ina tunanin ta ina za'a fara?bayan na shrya,ya umar ya shigo yana sanye da kaki yace zai je ya dawo na zama cikin shiri ni kunyarshi ma nake ji tunda wannan zancen ya shiga tsakaninmu yana tafiya momy ta ciro wani galan cike da wani abu da naji tana kira tsumi tun farkon aurena da ya umar take dirka minshi sai dai in banzo garin kaduna ba ko hutun makaranta nazo lokacin sai ta bani nasha,niko uwar kwadayn zuma tabani na cewa yauwa momyna kamar kinsan nayi kewar wannan tsumin na ce yauwa momy na kai kamar knsan nayi kewar wannan tsumn na diddilo a kofi na soma sha A mota yana ta jana da fira na dake nan take yayi min tuni cewa har da fa biyayya cikin sharadin shi kuma dole ne in ya min magana na ba shi amsa,kuma na saki fuska,nace to a raina nace zanko iya?...Mun iske farida da kawayenta su lady na rigashi shiga ciki saboda ya tsaya gurin su joseph,su farida surutu yaci karfinsu dan haka basu ji shigowata ba.lady tana cewa ai ke naga sakarcinki yaushe zan samu miji kamar naki sannan in tona kaina,ki dubi yadda ya yarda dake,yana alfahari matarshi ustaziya,sannankina sha'aninki da abokan harka yadda ranki ke so,kudi suna shigo miki yadda ya kamata,sannan ki tsokani fada?dayar tace kyaleta lady,farida sakaryace kina zaton da zaki kashe auranki su haji jamilun auranki zasuyi?lady ta amshe da cewa yaushe zasu aureki duk kyanki sun fi son su auri kananan yara suna tsotse su,ba gamu ba sun yarda harka ta duniya ayi ta amma da kin yi musu zancen aure yanzun nan sai ku bata,Farida tace nima tunanin danayi kenan shi yasa na matsa na dawo., Domin alhaji sambo ya ce ynxn sunfi yayin hulda da matan aure,Lady tace sosai ma,baki ganin yanxun knfimu abokan harka farida ta ce hakane,dayar tace ina xaton kila wani sihirine 'yan iska ni zan gaya muku haka,domin watarana ni da wani wawa kum ma sanshi dan iskan ministan nan tsohon banza,lady ta ce ATY kike nufi ko?ta ce eh shi mana,har fa mun soma harka sai dan iskan kawalinshi ya yi mishi waya wai ga matar aure nan ya dagani ya bani dubu goma,na ce Allah bai isa ba bazan amshi ten ba shine ya ce to in jirashi..Ke a takaice gabana ya ba matar auran nan dubu dari da hamsin dana soma tsiya sai yace koni da ina da aure haka zai bani da na so insan dalili sai yace wannan wani sirri ne don haka kada na daga hankalinki kan wannan yarinyar,lady tace ki dae hada da kisisinar da muka gaya miki suka yi dariya suka tafa,ni dai kaina ne ya daure,shin harkar me farida ke yi?irin wacce kawayenta ke labari yanzun?sallamarya umar tare da rufe kofar da yayi da karfi ce tasa suka waigo,ya dubeni asmy yaya baki shiga ciki ba?ni dai kallon su farida nike yi lady ta zungureta da hannu nan da nan ta tashi ta nufi ya umar da sauri tana fadin sojana kun sha hanya ta dube ni shigo mana asma'u Ta amshi jakar hannunshi ya dube ni kije dakinki tafiya nike ina kallonsu,ya shafi gefen kumatunta tare da fadin i miss you,ya dubi sashen su lady ya ce yau su malama hafsa ne a gidan na mu? tace wlh munji shirmen da faridar taka taso tayine shi ne mu kazo don mata nasiha banda abin farida duka duniyar na wa take?ya ce a ton kuda ku ke waje ku za ku fita sanin me duniyar ke ciki,dayar ta ce tabbas mun gaya mata,su ka kalli juna su da farida naga sun kashe ido,tace nima ai nagane kurena kuma na bada hakuri ko sojana?dama shi ya dauki hanyar zuwa dakinshi daga can ne yake fadin hakane my farida,dama rigima ai ba halinki bane,ya shiga daki ta yi musu alamar tana zuwa da hannunta itama ta shige suka juyo dubansu gareni inda nike tsaye rike da kit dina..Suka kalleni suka tabe baki,na tura kofa na shige,Lady ta dubi dayar tace kinsan allah Sara inda nice farida tuni zanyi waje da shegiya,ba boka ba malam tsabar kissa bare ga shaidar dakamin ita kuma ga mummunan tambarin daka kamata ai sharri kala-kala zan dinga hada mata,Sara ta ce ke bari irin yarannan sune ake ce ma dan hakin daka raina sai kiga yarinyar ta kere ta,amma tana da hanyar da zata ma yarinyar korar kare.... Farida ta dubi sojanta don allah ka ba Asma'u hakuri dan yanzun kunyar yarinyar nake ji bai dace ina babba in dinga zubar da mutuncina ba,ya dube ta cikin farin ciki ka da ki damu,dama yana da kyau mutum in ya yi abun da bai dace ba,in an fahimtar dashi ya fahimta sannan ya nuna yayi kuskure,ta ce hakane nima banyi amfani da hadisin nan ba, Farida ta dubi sojanta dan Allah kaba asma'u haquri dan yanxu kunyar yarinyar nake ji bai dace ina babba in dinga xubar da mutuncina ba,ya dubeta cikin farin ciki kada ki damu, dama yana da kyau mutum in yayi abu da bai dace ba, in an fahimtar dashi ya fahimta sannan ya nuna yayi kuskure, tace haka ne nima ban yi amfani da hadisi nan ba, wanda ya hore mu da soma dan uwanmu abin da muke soma kanmu, kishi ya hanani ganin gsky amma insha Allah daga yau na daina xan yi koyi da irin kishin da matan manzon Allah sukayi.da sauri ya juyo ya rungume ta tare da fadin shi yasa kullum nake qara sanki my farida, kuma ina san ko ba kece kika haifa min yara ba xan baki su ki musu tarbiya ta qwarai, tace na gode. bari inje muyi sallama dasu hafsat gida xasu je, ya jawo dirowa ya ciro kudi ya miqa mata gashi ka basu, haka ake san abota da mutanan qwarai,gasu cikin shiga ta mutunch, ta isa gunsu tana dry suma suka soma dryr tace shegiya ni ,sukace me ya faru yar iska mai fuska 2 Ta koro musu komai suna ta dry,sara tace har yana cewa munyi shiga ta mutunci bai san saida na koyi yanda xan saka hijabin nan ba? lady tace ni xafi ma ne duk ya dame ni muna fita daga barikin nan xan cire shi,ta miqa muru kudin ga shi kinsha sigari, sara tace gara mu ke fa shegiya me juye giya a kwalbar cocacola tace naji ku tashi ku fitar min a gida,ta raka su suna mata tsiya itama tana musu.ina cikin juyayin me xaije yaxo ne a cikin wannan xaman da xanyi danake mishi laqabi da xaman waqafi. bayan sallar isha'i, xaune nake na hada tagumi wayata ta soma rngng, na duba na hadda ce no ya umar amma ban haddace tawa ba, na dauka yace asmy ki fito ga munan a dining nace na qoshi fa, yace ki fito kawai kinsan kina cikin sharadi ne, na fito jiki ba qwari na ajiye hijabina,riga ce da wando na kamfala rigan kamar ta maxa aka dinkata iya cinya wandan kuma fela na kama gashina da dan kwalin sbd ni ban cika san daura dankwali ba Zamanta kenan nima na iso gun ya nuna min kujera xauna na xauna kusa da farida,ta xuba mishi tuwon shinkafa miyar ogun, ga nama manya ta xuba mashi farfesun kaji, ita kuma farar taliya ta xuba da miyar kayan kayan lambu,sannan ta saka soyayyan naman kaji ta dubeni da fara'a me xan xuba miki qanwata? nace a qoshe fa nake ni,tace me kika ce? shuru na mata shi ko sai ya cika kofi da fresh milk ya miqo min da strw na xuqa, yace kinga irin nata nan, kinsan ita ba komai take ci ba,dama dai dan wake ne a yanka mishi qwai.da sauri na dube shi a raina nace waya gaya mishi? ban gama mamaki ba naji yace kinsan ko farida yarinyan nan ba girkin kowa take ciba,domin ko ita ta hada abinta in bai mata ba xubarwa take yi ta dora wani,na saki baki ina san tuno wanda ya gaya mashi, to waye domin ba kowa sannan shi bayanan. na kalle shi yayi min murmushi yaci gaba da cin abincinshi, yanxu kuma ya s6a bani tsoro domin ina xaton qila yana da aljanu,domin haka ranan da mukaje ganin rabon gidan nan yace jim da gun wasanni sbd ni. Dan yaga akwai ni da san xuwa jim,nasan ko su joseph basu san ina xuwa gun nan ba, inko sun sani waya gaya masa na girki...ya ketse ni,tunanin me kikeyi kisha mana, in kuma kinfi san ki xuba xuma da madasa to kije ki dibo na tsura mishi ido, ya dake tamkas ba shi yayi maganar ba. jiki babu qarfi na dauki strw na soma shan madara, araina nace allah abin tsoro ya umar abin tsoro, sai kace mai gani har hanji, ina jinsu na soma hamma, yace bacci ko asmy? na daga kai yace tashi kije ki kwanta, farida tace ya dace a sa mata ko da gado ne kadai a dakin,yacf nima nayi wannan naxarin,ni dai kallan su nakeyi, araina nace ke kika sani da munafincinki, na kwanta na toma bacci naji turo qofar shi yaxo ya tsugunna gabana ya shafi gefen kumatuna sannan yace asmy saida safe, ya fita yaja min qofa,washe gari da kamar sha biyu shi baza na dan tun safe yayi tafiya sai gnbe yai dawo, haka ya gaya min lkcn dana fito wanka da safen sanda yaxo yimin sallama,wasu mutane suka shigo su biyu sun sami farida tana shirin fita. Joseph ne yace yawwa madam ga baqi nan xasu miki bayani, ruka sanar da ita cewa oga yace suxo su duba dakin amarya, ta nuna musu sannan tace suje,sun shigo suka min sannu sannan sukayi ta yan gwaje gwaje suka tafi, washe gari sai ga su sun dawo da kaya niqi niqi fita nayi na basu gu suka yo waje da kayan dakin suka shiga shirya dakin. kusan 3hrs sannan suka tafi.da sauri na shiga dakin domin daga yanda nake ina kallansu sunata aikin shirya dakin, tsayawa nayi galala ina kallan yanda aka kafa gadan. mamakin da nake ban ga sun shigo da kayan gado ba, da kwalaye na gansu amma sai gashi sun tashi gado da wordrop,mirror ga labulaye masu shegen kyau suka dora min katifata suka shimfida gado,gsky dakin yayi min kyau, na fito na kwashe kayana na xubasu cikin sabuwar wordrop. misalin qarfe hudu da rabi na idar da sallan la'asar ina xaune kan sallayar qara kallan dakin nake yi, araina kuma ina naxarin kudin kayan nan ko xai kai nawa?wayata ta soma ringing watona momy ce sai naga no din ya umar ce, Gabana ya fadi domin kwana dayan nan da baya nan ji nake tamkar an cire min qaya na dauki wayan nasa a kunnena bance qala ba shine yace hello, nace ina jinka, yace ina hanya a kiyasina nanda xuwa 7 xan iso da fatan baki manta cewa yau kece da miji ba?gabana yayi mugun faduwa,nace ni ce da miji fa kace? yace yes kwana 2 2 xaku dunga yi keda my farida, kada ki manta cikin sharadi kike tare da bin doka duk abinda nace maki to yaune doka xata fara aiki ,kuma dama na gaya maki ko shekara daya kikayi kina bin doka rana daya kika karya to fa wannan shekaran ta xube sai kin kuma wata shekara biyun, ke ko gobe shekara biyun xata cika kika saba sai kin sake wata 2. tamkar xan fashe da kuka domin har hawaye ya wanke min fuka,nace kai ya umar wlh ba kace haka ba fa,Allah ko ranar da muka yi maganar a kd bakace haka ba fa, tamkar xai kwashe da dry yace to na manta ne yanxun gashi nan na fada miki.dan haka sai ki shirya mun tebur in kuku ya gama in kuma nima xa amin madara da xuma dinne to sai na iso ko? See Translation [7:41PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----7 Shiru nayi shi kuma ya katse wayar,kuka na saka na farko ga rashn son da nake ma ya umar ga kuma fargaban yadda zamu kwana gado daya,na mike ina 'yan gungunai shi ya umar dinnan ya cika wayo,bayan ba haka muka yi da shi ba zai ce wani in na karya doka sai na sake daga farko,haka nan jiki babu karfi na kira Rahma,ta san komai yadda muke ciki da ya umar cikin kuka nake gaya mata dariya ta shiga yi min domin ganinta hakan da ya umar ya yi shne dai dai,nace haka ma zaki ce?Tace to ni bnga abn ki agun ya umar ba,na ce Rahma ni nasan irn wuya tare da bakaken maganganun da na sha gurin ya umar,ta ce wannan kina lbrn abnda ya wuce ne,na ce gunki ko?don ni gare ni bai wuce ba,knsan Allah? bana son ya umar bana kaunarshi,wlh don dole nake ganinshi,ta ce lallai kina da aiki Asma'u.A haka ne zaki cinye shekara biyu kina biyayya?na ce shne nake tunani gashi ya ce ko na fi shekara indai na saba na rana daya to na rusa wancan shekarar na baya,ta kwashe da driya ta ce ai dama hakane dokar,Allah ya ba da sa'ar cin jarabawa,na kula harda iskanci take min dan haka sai na kashe wayar,na idar da sallar isha'i na shiga kicin kuku ya gama komai na soma jidowa ina kawowa dining...Ya Umar ya yi sallama fuskarshi cike da fara'a,na amsa zan tafi kicin ya ce asmy ba ki ganni bane?na ce sannu da zuwa,bai amsa ba ya iso guri na ya ce haka ki kaga my farida tana min?tana amsar abn da ke hannuna bayan ta rungumeni yayi kasa da murya tana kaini daki ta min wanka.da sauri na kalleshi sannan na sunkuyar da kaina ya ce kada fa ki manta kina bin doka ne. Na dube shi nace zan dai karbi jakar kawo amma gaskiya ni fa ba zan iya yi maka wanka ba. yace to rungume ni fa? kin dai san b zan miki afuwr abu 2 ba,na rasa yanda zanyi domin niba ma bazan iya rungume shi bane, zan iya amma rashin son da nake mishi ne yasa ba zan iya rungume shi ba,sai naji ya manna ni da jiknshi, yay kiss a kumatu na amshi jakar shi, sannan nayi hanyr dakinshi, yace rana ta farko dana shiga dakinshi. dakin ya tsari fiye da yadda zuciyata take rayamin a da, ina kokarin fitowa ne suka shigo shi da farida tana rungume dashi,na fita naa basu guri ko kusa banji haushi ba, domin sai kana son mutum ne sannan zakali kishinsa. sai da nayi sallar isha'I sannan na fito,na dai yi wanka ammabanyi wata kwalliya ba domn banason yayi sha'awata , doguwar riga na saka jallabiya baka na daura dankwalin rigar a kaina na fito,tuni sun so kan dinning din. ina zuwa kafinna zauna nasoma zuba mishi abinci kamar yanda naga farida ta mishi jiya, Yace good sauran ki zuba ma my faridada dan yatsina baki,no ki bar shi kawai zansa da kaina, ni kam fargaba ya hana ni cin komai duk da sha'awar kus-kus din ya bani fresh milk din dake kan dinnin dinshi na janyo na zuba cikin kofi na soma sha. ya umar ya kallo farida yace yrnyr nan 'yar madara ce, ta taba baki batace komai ba, na kula taji haushin yanda ya umar ke min ni kam data san haushin da shi kanshi yake bani da bata damu kanta ba. an gama cin abinci na tashi na shige dakina jim kadan ya shigo kai tsaye ya zauna bakin gado ya dubeni, kinyi shafa'I da wuturi? nace eh yace kije kiyo alwala muyi sallar ma'aurata, da sauri na dube shi yace ko ba ki shirya shiga skul ba? nace na shirya mana yauwa sai ki dinga cewa to kawai duk abin da na saka ki matsawar bai saba ma addinin musulunci ba, shiru nayi sannan naje nayo alwala munyi sallah ya jma yana addu'oi sannan ya dube ni, Allah yasa yau ma ki samu cikin kinga kin huta kenan ko? idanuna sukayi rau-rau nace to muryata ma rawa take yi duk da boye dariyar da yake yi saida ya dan dara, a raina nace mugu ba dole ka min dariya ba, ya zauna bakin gado yana kara kallon dakin ya dube ni gaskya marhaba sun iya tsara guri, Dakin yayi kyau sosai ko? nace um, sbd jin shi kawai nake ni duk cikin fargaba nake. ya dan sha mur sannan yace bki fa zaki rinka budewa kina min mgn nace to, amma cikin raina fadi nake Allah ya shiga tsakanina da kai mugu, yace taso na tashi yace zo nan, naje jikina sai kyarma yake, yace wannan rawar jikin fa kamar kinga dodo? na dai yi shiru yace cire kayanki, a tsorace nakalle shi na soma kuka yayi kini -kini da rai menene na kuka abin nanba dole zabi na baki kika yarda in kinga ba za ki iya ba to na baki saki ki kije ki kare kanki gurin su alhj sannan kudina ya huta na jami'a dinki. gashi dakyar ma na samu form din, jin har an samo min form yasa na soma cire su, nasoma yarfa hannu irin yanda mutum ko ince yara ke yin suna jin tsoro ina kuka ya taso ya rungume ni ke kin cika tsoro , ba wata wahala zan baki ba in dai kin saki jikinki kai na matukar tsorata hakan yasa shi kwatar dani a jikinshi yana lallashi na har na dan nutsu ganin bai komai ba sai 'yan wasanni da yayi ta min haka muka kwana washe gari ya nuna min formdina har ya cika yace in dai ina bin yanda yace nan da satin da zami shiga zan soma zuwa skul, nace to nan ma ya rungume ni Tare da min 'yan wasanni shi dai ke kidan shi yake rawarshi. yau ma kamar jiya cewa yayi kadamana saka koma bayan da zanyi dolenayi yarda yace wasanni yakedani son ranshi danaji zai wuce gona da iri sai in saka kuka daya koma gurin farida,ranar ni na samu ishasshen bacci sbd fargaba daya na gunana kasa bacci,ke cikn kwana 2 har ramanayi banacin abinci ko yaushe cikin tagumi da tunani wannan karon daya kara dawowa guna cewa yayi duk abin daya min nimasai na mishi tafannin wasa bani da yanda zanyi dole ina mishi ina hawaye, wi don rashin imani irin na ya umar sai cewa yayi hakan yana burge shi domin ina yin kyu da kuka haka har kusan sati 2, sai dana saki jiki kan cewa ya barni sai yace shirya zaije kd yaga yanda marhaba suka tsara gidan nan da kaya ko ya yi kwana daya zaiyi sbd jibi zasu yi tafiya da faridarshi, kuma kila suyi sati 2 kofi da murna ta nace o ka barni can mana saikun dawo? yace to amma bri dai na gani inna samu yanda nakeso sai in barki din nan na shirya muka tafi.murna momy tayi da ganina ballantana yanda taga da ya umar yace kazo zanyi da sauri ga zatan ta yanzxn na som son shi ne n ko kan Sharadi nake duk dayace sai randana bada kai zan soma zuwa skul, ya di gamamin komai kuma sun bani lecture din da nakeso. da dare ina dakn anty saikumanace bar na shiga gurin su mama banje ba, amma an kaimusu tsaraba, anty tace kije ku gaisa, shi dan gidaba ai ya shiga dazu ko da dai yace min kila nan zai barki nace don Allah kisamin baki anty ni abj nan ma bana sonta dama yabarni tace zan mishi mgn amma kemaki dinga

Chapter 11 of 16