haka sai ya ga jini bai
daina
tsatstsafowa ba kuma har a sannan
Sarila bata
farfadowa ba.Al'amarin dayayi
matukar dugunzuma
hankalin Jarumi Darusi kenan ya kasa
zaune ko
tsaye ya rinka kai kawo yana tunanin
abinda ya
kamata yayi.Koda ganin haka sai
Mujahid ya dubi
Darusi a fusace yace saboda me mu
ba zaka zo ka
taimake mu ba alhalin kana ganin
cewa duk mu
biyun mun sami karaya a jikinmu
kuma jikinmu ya
bugu sosai ba zamu iya yiwa kanmu
komai
ba.Koda dai ka kamu da son Sarila ne
shi yasa ka
dimauce haka?Koda jin wannan batu
sai jarumi
Darusi ya fusata ainun ya dakawa
Mujahid tsawa
yana mai cewa baka da hankali ne ko
kuwa baka
ganin halin da take ciki ne?Duk ku
biyun kuna
cikin haiyacinku ita kuwa bamu san
ma halin da
take ciki ba,shin ka manta ne cewa
nayi alkawarin
zan ceci rayuwarku a duk sa'adda
kuka kasa ceton
kanku.Koda gama fadin haka sai
jarumi Darusi ya
koma kan Sarila ya tofa mata wata
addua'a akan
raunin,faruwar hakan keda wuya sai
jini ya daina
tsatstsafowa daga cikin raunin amma
kuma da
Darusi ya dubi yadda take sai
hankalinsa ya
dugunzuma ainun saboda ya fahimci
cewar jini mai
yawa ya zuba a jikinta.Mafi akasarin
mutanen da
suka rasa jini mai yawa haka a jikinsu
mutuwa
sukeyi kuma koda sun rayu sai an
basu kyakyawar
kulawa kuma sai sunyi jinya ta dan
lokaci sannan
zasu sami cikakkiyar lafiya gami da
kwarin
jiki.Jim!Kadan da tofawa Sarila
wannan addu'a
saita farfado daga dogon suman da
tayi tana mai
jan dogon numfashi gami da bude
idanu a hankali
da farko cikin dishi dishi taga jarumi
Darusi
tsugune a gabanta kuma fuskarsa a
rufe idanunsa
kadai ne a waje,sannu a hankai
idanun nata suka
washe amma sai taji kanta da sauran
gangar jikin
nata sunyi mata nauyi ainu ko motsin
kirki ba zata
iyayi ba.Da kyar ta juya da kan nata
ta dubi inda
Yazirina da Mujahid suke,kawai sai
taga kafar
Yazirina a karye har ta dan fara
kumbura shi kuma
Mujahid hannunsa ne a karye kuma
dukkaninsu
akwai alamun tsananin jigata a tare
dasu.Sarila ta
dago hannunta da kyar ta shafi raunin
nata koda ta
jishi a dinke har an shafa masa
magani sai ta dubi
Darusi tayi masa dan guntun
murmushi a karon
farko tunda suka hadu tace ina godiya
a gareka
bisa ceto rayuwata da kayi.Koda jin
haka sai
Darusi yace ki gafarceni lalura tasa na
taba jikinki
domin yi miki maganin.Sarila ta sake
yin
murmushi tace nayi farinciki daya
kasance
addininka bai hanaka taimako ba a
irin wannan
domin da tuni yanzu na dade da
zama
gawa.Darusi yayi murmushi yace ai
addinina yana
da adalci kuma baya son zalunci,na
sani cewa ba
zaki iyayin komai ba yanzu da kanki
don haka in
Allah ya yarda zan cigaba da
taimakonki har izuwa
lokacin da zaki sami lafiya.Yanzu
zanje na taimaki
sauran yan uwan naki.
HALEEFAH A ABUBAKAR
Yanzu zanje na taimaki sauran yan uwan
naki.Koda gama fadin haka sai Jarumi Darusi ya mike tsaye ya tafi inda Yazirina ke kwance ya shiga gyara mata karayar dake kwaurin kafarta.Nan da nan cikin kankanin lokaci ya daure kafar da karare ya shafa mata wani magani na musamman sannan ita ma ya tofa mata addu'a daga nan sai kuma ya mike tsaye ya koma kan Mujahid yayi
masa duk irin taimakon da yayiwa Sarila da
Yazirina.Bayan ya gama yi masa komai tsaf sai ya dubeshi yace dazu kace naki na taimake ku na taimaki Sarila har kana cewa ko na kamu da sonta ne ko?To yanzu kuma me zaka ce tunda gashi
nayi muku duk irin taimakon da nayi mata kuma ka gane cewa na fara taimakonta ne saboda halin data shiga yafi naku hadari.Koda Darusi yazo nan a zancensa sai kunya ta kama Mujahid ya dan
sunkui da kansa kas yana sosa keya yace ka gafarceni yakai JARUMIN JARUMAI hakika zargina kawai yasa na fadi haka.Dajin haka sai Darusi ya mike tsaye daga gaban Mujahid ya juya masa baya sannan yace a addinina zargi haramunne koda ya zamana gaskiya don haka sai ka kiyaye.Darusi ya dubi Sarila,Yazirina sannan ya juya ya sake duban Mujahid yace duk ku ukun ba zaku iya cigaba da tafiya ba a cikin halon da kuke ciki yanzu.A kallah sai kunyi jinya ta kwanaki ashirin kunga kenan kwanakin tafiyarmu sun karu.Koda jin wannan batu sai hankalinsu Sarila,Yazirina da Muhajid ya dugunzuma ainun,Sarila ta dubi Darusi ta budi baki cikin matakuar karfin hali tace yakai wannan GWARZON JARUMI yanzu babu yadda za'ayi mu
cigaba da tafiyar nan a haka in yaso mu cigaba da jinyar jikinmu akan hanya.Ka sani cewa zamanmu a waje daya yana da matukar hadari saboda duk sa'adda ka gusa daga kusa damu masu farautarmu zasu iya baiyana su kashe mu domin su rabamu da taswirar zuwa kogon Taskar Ajali.Koda Sarila tazo nan a jawabinta sai Jarumi Darusi yayi
murmushi yace da izinin Allah babu abinda zai sameku a tsawon zaman da zamuyi,inaso ku tuna cewa a halin yanzu fa doki daya ne jal daya rage mana tunda Aljana Marwisa ta kashe naku
dawakan.Ta yaya zamu cigaba da tafiyar da doki daya kuma a cikin yanayin da kuke musamman ma Sarila wacce ko zama akan dokin ba zata iya ba,ko zata iya fara zama sai nan da cikar kwana bakwai kuma ko ta fara zama ba zata juri dadewar zaman ba a kan doki.Koda jin wannan batu sai duk su ukun suka jinjina kai alamar cewa sun gamsu da abinda ya fada amma sai Sarila ta kuma budar baki tace na amince muyi kwanaki bakwai muna jinya a nan.A ranar kwana na bakwai ni da Yazirina sai mu hau dokinka,Mujahid a matsayinsa na wanda ya karye a hannu zai iya taka kafarsa yayi tafiya kaima haka,idan kun gaji da tafiyar kafa zamu iya tsayawa ku huta sannan mu cigaba da tafiya
hankalinmu zaifi kwanciya idan ka amince da
wannan tsari dana zo maka dashi.Koda jin wannan batu sai Jarumi Darusi ya kawo gwauron numfashi ya ajiye sannan yace hakika wannan shawara da kika zo da ita zata yiwu to amma kuma akwai yan matsalolin da zamu iya fuskanta wadanda zasu zamo tamkar munyi gudun gara ne mun tarar da zago.Caraf sai Yazirina ta tari numfashinsa tace babu matsala zamu iya jurar duk irin matsalar da muke fuskanta.Dajin haka sai Darusi ya gyada kai yace shikenan tunda kun aminta da hakan,yanzu abu na farko da zamuyi shine mu dauke gawar
wannan Aljana mu kaita can nesa mu kone ta yadda warinta ba zai dame mu ba koya dami
sauran halittun dake cikin dajin nan.Bayan nan kuma sai mu shiga cikin wannan kogon dutse na wannan Aljana mu caje shi mu tabbatar da cewar babu wani mugun abu a cikinsa domin mu zauna acikinsa.Koda jin wannan batu sai Sarila tace to yanzu in banda abinka ta yaya mu da muke a
nakasce zamu iya tayaka wannan aiki?Darusi yayi murmushi yace ai dama ba cewa nayi sai kunsa hannu ba a cikin wannan aiki,kawai dai ina sanar daku ne yadda ya kamata ayi.Gama fadin hakan keda wuya sai Darusi yaje ya dauko wata doguwar igiya a cikin jakar guzurinsa wacce matafiya ke amfani da ita wajen hawa duwatsu da tsaunika masu tsawo ya hada gawarwakin dawakan a waje guda gami da gawar Aljana Marwisa ya daure su tamau kawai sai ya kama igiyar da hannu daya yaja gawarwakin duka a kas ya nufi wani bangaren daban na dajin.Yana cikin tafiya ne ya tsaya cak kawai sai ya dawo da baya ya baro mushen
gawarwakin acan gaba yazo gaban su Sarila ya tofa wata addu'a sannan ya dube su yace kada dayanku ya kuskura ya ketare nan inda kuke.Koda gama fadin hakan saiya juya yaje ya cigaba dajan mushen su kuwa su Mujahid sai suka bishi da
kallo kawai cikin tsananin mamaki har saida ya kauce,ba komai ne ya basu mamaki ba face ganin irin tsananin KARFIN DAMTSEn sa sun sami cewa inda zasu taru duk su ukun ma ba zasu iya jan gawarwakin ba uku a kasa saidai da karfin sihirin tsafi amma gashi Darusi ya hada har dama gawar Aljana Marwisa wacce nauyinta ita kadai ya ninka na doki guda sau uku.Nanfa sukayi ta Al'ajabi suna tattaunawa akan al'amarin inda Yazirina ta dubi Mujahid tace kai waishin anya kuwa Darusi mutum be kamar mu dinnan?Koda jin wannan tambaya sai Mujahid ya bushe da dariya yace tabbas Darusi mutum ne kamar mu yana ci yana sha kuma
yanayi duk irin bukatar da mukeyi,idan yaji ciwo jini na fita a jikinsa,idan ciwo ya kama shi sai yayi jinya,to menene bambancinmu dashi?Bambanci
shine yana da baiwa ta matukar karfin
damtse,Addininsa ba irin namu bane,yana da
matukar hakuri gami da jurewa wahala komai
tsananinta domin cika burinsa,ban taba haduwa da mutumin daya burgeni ba kamarsa.Koda Mujahid yazo nan a zancensa sai Sarila da Yazirina suka kamu da tsananin mamakinsa.
5 hours ago
Abubakar Haleefah Physicist
Yazirina ta dubeshi tace idan har Darusi yana
burgeka hakan na nufin cewa zaka iya yin imani da addininsa haka ne?Mujahid yayi murmushi yace wannan tambaya ba akaina ni kadai take ba,tana kanmu duk mu ukun nan nina tabbatar da cewa
kuma Darusi yana burgeku.Koda kuwa kun tsane shi a cikin zukatanku amma na sani cewa da
sannu za kuji kuna sonsa kafin mu kare wannan tafiya.Akwai abu guda dazai faru yasa dukkaninmu muyi amanna dashi.Koda jin wannan batu sai
Sarila da Yazirina suka dubi Mujahid,cikin mamaki Sarila ta budi baki da kyar tace menene wannan abu dazai faru wanda zai sa na kaunaci wannan shashashan jarumi?Ka sani cewa na tsaneshi
kamar yadda na tsani mutuwa ta duk da cewa ya cece rayuwata ni kawai inayin wannan tafiya ne tare dashi bisa larura saboda yana da matukar amfani a garemu.Sa'adda Mujahid yaji wannan
batu na Sarila sai ya gyada kai yace ba zan gaya miki abinda zakiyi ki kaunaci Jarumi Darusi
ba,anan gaba kuma ina mai shawartarki daki boye kiyayyarki a gareshi kuma kiyi kokari ki saisaita zuciyarki a kan kinsa saboda tsananta KIYAYYA ko SOYAYYA abu ne mai hadari a rayuwa saboda
makiyi kan iya zama masoyi kuma masoui kan iya zama makiyi.Koda Gama fadin hakan sai Mujahid ya mike tsaye yaje inda dokin Darusi yake ya dauko battar ruwa ya bude ya kurba sau biyu
sannan ya juya ya dubi Yazirina cikin murmushi yace kina da bukatar ruwan ne?Yazirina tayi
murmushi tace ina bukata mana.Mujahid ya nufi inda Yazirina ke zauna domin ya bata ruwa tasha amma sai Sarila ta kira sunansa tace ni laifin me nayi maka da bzakayi mini tayin ruwan ba?Ka sani cewa ko don doguwar tafiyar da muka sha kafin muzo nan da kuma bakin gumurzun da muka sha
da Aljana Marwisa dole ne kowannenmu yaji
kishirwa,idan kuma son da kake yiwa Yazirina yafi wanda kakeyi yi min ne saika fara bata ruwan tasha na gani.Koda jin wannan batu sai mamaki ya turnuke Mujahid ya kasa gane abinda take
nufi,shidai ya sani cewa tsakanin ita da Yazirina babu wacce ya furtawa KALMAR SO a fili amma
kuma ya fuskanci cewar kowaccensu tana sonsa amma a badini cikin zuciyarsa hankalinsa yafi karkata izuwa kan YAZIRINA saboda yana
matukartsoron Sarila bisa ganin irin tsantsar rashin imaninta da yadda ta mauar da rayukan bil'adama tamkar na kiyashi.Mujahid ya tsaya yana duru duru ya rasa wacce zai kaiwa battar ruwan yayin da yake ruke da battar da lafiyayyen hannunsa,daya hannun nasa kuwa Sa'adda Darusi ya gyara masa karayar ya rataye shi bisa wuyansa da wani farin
kyalle mai kwari.Mujahid na cikin wannan hali ne suka jiyo sukuwar dawakai da yawa an durfafo bakin wannan kogon dutse daga can nesa.Nan
take duk su ukun suka dimauce hankalinsu ya
DUGUNZUMA ainu Mujahid ya rasa abinda ya
kamata yayi har ya yunkura zai ruga izuwa gaba ya barsu Yazirina a wajen sai Yazirina ta daka masa tsawa ta dubeshi da idanunta da suka ciko da kwallah tace Kai!Mujahid ashe dama zaka iya guduwa ka barni yayin da kaga masifa?Ni a tunani na kana sona kamar yadda na kamu da tsananin sonka na zaci cewa zaka iya sallama rayuwarka domin ceto tawa tamkar yadda zan iya sallama tawa don taka.To ka sani cewa tsayuwarka anan ne kadai zaisa ka tsira da rayuwarka amma idan kayi taku daya gaba mutuwa zakayi tunda Jarumi Darusi ya gargademu akan hakan,idan ka manta ne yanzu na tuna maka kaga kenan na ceci
rayuwarka.Yanzu nike binka bashi a rayuwa ba zan sake yarda da kai ba har abada face ka biyani wannan bashi da nake ninka wato ka ceci
rayuwata.Koda jin wannan batu sai Sarila taji wani irin mugun KISHI ya turnuketa har ta bude baki zata ce wani abu saiga rundunar mayaka ta iso daf da bakin kogon dutsen.A kalla mayakan sun kai su Dubu Dari Hudu kuma dukkaninsu a cikin
gagarumar shigar yaki suke dauke da muggan
MAKAMAN YAKI a gabansu mutum hudu ne mafiya
kwarjini.KALLO DAYA zakayi musu ka gane cewa SARAKAI ne saboda yanayin shigarsu da kuma
kayan yakin nasu irin na sarakai.Uku daga cikin sarakan fitattu ne a nahiyar,daya kuwa bakon sarki ne daga wata nahiyar daban kuma duk ya fiso
girman kwarjini gami da kira irin ta manyan
SADAUKAI.Da kira irin ta Manyan Sadaukai.Da
isowar wannan
runduna sai suka ja linzamin
dawakansu sukayi
cirko cirko suka kurawa su Yazirina
idanu yayin da
kurar dawakan su ta fara lafawa,bayan
kurar ta lafa
sai bakon sarkin ya dubi Sarila da
Yazirina ya
bushe da mahaukaciyar dariyar
mugunta sannan
ya murtuke fuskarsa tamkar an aiko
masa da
sakon mutuwa yace yanzu gashi a
karon banza
mun sami tsuntsu daga sama
gasasshe,kun gama
yakar junanku kunyi hadin kan dole domin kuje ku
malli dukiyar dake can taskar Ajali
amma ga iya
inda gudunku ya kare ba tare da mun
sha wahalar
komai ba zamu kashe ku mu dauke
taswirorin
dake tare daku tunda abin dogaron
naku Jarumi
Darusi baya nan bare ya baku
kariya.Ku sani cewa
nine Sarki Damshan na birnin
Damashkar a halin
nine shugaban sarakuna uku na
nahiyarku dake
tare dani domin sunyi muba'aya a
gareni,ina mai
tabbatar muku da cewa duk duniya
babu wani
matsafi daya kaini karfin sihirin
tsafi,nasan komai
akan dukiyar taskar ajali kuma duk
abinda ya faru
tsakaninku da wannan bakon jarumi
na gani a
cikin madubin tsafina,yanzu kuna da
zabi biyu ko
dai kuyi mubaya'a a gareni ku bani
wadannan
taswirori guda uku cikin ruwan sanyi
ko kuma na
kashe ku na kwace taswirorin da
karfin tsiya.Koda
Sarki Damshan yazo nan a zancensa
sai kawai yaji
Sarila ta bushe da dariya cikin
tsananin karfin hali
duk da cewa a kwance take tana jin
matsanancin
zafi da zugi a jikinta.Dafa can sai ta
karkato da
kanta da kyar ta dubi sarki Damshan
ya budi baki
tace yakai wannan sarki kayi sani
cewa kamar
yadda wannan duniya take da fadi
haka ma abin
cikinta yake da yawan gaske.Komai
sammakonka
wani a tafe ya kwana,komai nisan gari
akwai wani
a gabansa,idan ka gane abinda nake nufi kome
kake takama dashi sai an sami wanda
ya fika bisa
ganin yadda aka raine ni a cikin
tsumin tsafi kuma
aka bani gagarumin horon yaki dazai
iya fafatawa
dani ba ya kaini kas,amma dana hadu
da wannan
bakon jarumi sai na raina kaina
alhalin da ina
ganin kamar zan iya aza gammo a
kaina nayi
dakon duniyar gaba daya.Kamar
yadda ka bamu
zafi guda biyu nima yanzu na baka
zabi biyun
kodai ku gudu kaida mukarrabanka
domin ku ceci
rayuwarku kafin jarumi Darusi ya
dawo nan ko
kuma ku jarraba karbar wadannan
taswiroro guda
uku daga hannunmu wanda hakan
bazai taba
yiyuwa ba.Koda jin wannan batu sai
Sarki
Damnashi ya fusata ainun take
zuciyarsa ta kama
tafarfasa kamar zata kone kawai sai
ya dubi
dakarun dake bayansa yace kuyi musu
ruwan
kibiyoyi.Nan take dakarun suka
zazzaro kibiyoyi
suka dana akan baka kowa ya tabe
bakan nasa ya
saki harbi.Wohoho!Ha kika abin
al'ajabi baya
karewa a cikin wannan dubiya,koda
dubunnan
dakarun suka harbo kibiyoyin su sai
kibiyoyin suka
tsaya cak a gaban su Yazirina a sama
su basu
cake su ba kuma basu fadi kasa
ba.Koda ganin
haka sai Sarki Damnash ya fara
amfani da karfin
sihirinsa da hannayensa ya rinka
motsa kibiyoyin
domin suje su cake su Sarila amma sai kibiyoyin
suka jiyo da baya da gudu tamkar
sannan aka
harbo su daga cikin bakan suka je
suka cake gaba
dayan dakarun da suka harbo su da
farko.Nan take
gaba dayan dakarun suka fado kasa
matattu daga
kan dawakansu.Sai sarakunan uku
suka firgita
ainun suka dimauce nan take suka
kada linzamin
dawakansu suka juya da baya da
gudu suka
runtuma izuwa cikin daji suna yiwa
dawakansu
kaimi domin su tsira da rayuwarsu
suka bar sarki
Damnash shi kadai a tsaye zuciyarsa a
kekashe ko
alamar tsoro babu akan fuskarsa duk
da ganin
abinda ya faru,fuskarsa ce kawai ta
cigaba da
yatsinewa zuciyarsa na cigaba da
tafarfasa kamar
zata kone.Adaidai wannan lokaci ne
suka hango
Jarumi Darusi ya durfafo su a guje
yana ruke da
takobinsa tsirara,ba komai ne yasa
Darusi ya zare
takobinsa ba ya rugo da gudu face
hango dubban
daruruwan dawakai daga can nesa
amma koda ya
matsa kusa sai yaga ashe gaba daya
mahayan
dawakan sun zube kasa matattu saura
mutum daya
jal a tsaye a wajen sai ya daina gudu
kuma ya
mayar da takobinsa cikin
kufenta.Koda ganin haka
sai Sarki Damnash ya saulo daga kan
dokinsa ya
rike kugu yana mai fuskantar jarumi
Darusi yana
jiran isowarsa.Da isowar Jarumi Darusi
ya zamana
cewa tazarar dake tsakaninsu da sarki Damnash
bata wuce taku biyar ba sai ya tsaya
cak suka
kurawa junansu idanu.Kawai sai sarki
Damnash ya
bushe da dariya bayan yayiwa Darusi
kallon raini
da wulakanci,lokac i guda kuma saiya
murtuke
fuskarsa yace yakai wannan wawan
jarumi kayi
sani cewa bakin rijiya ba wajen wasan
yaro bane.A
halin yanzu duk fadin duniya babu
wani jarumi
daya fini KARFIN DAMTSE,iya yaki da
kuma karfin
sihirin tsafi,idan ka isa kazo mu fafata
da zallan
karfin damtsenmu da iya yakinmu.Na
rantse da
girman iyayena bazanyi amfani da
karfin sihirin
tsafi na ba kai ma ka rantse da
girman iyayenka
cewa ba zaka yi amfani da karfin
sihirinka ba
yanzun nan cikin dakiku kadan zan
kashe ka.Na
rushe burinka na son yada addininka
a wannan
nahiya gaba daya sannan na kashe
wadancan
matan na dauke taswirorin dake
hannunsu guda
uku naje na mallaki taskar ajaki na
zamo SARKITa gaban kwatance.Tunda Darusi yake karo da mazaje bai taba haduwa da zarton jarumi mai zafin nama,karfin sara da nauyi ba tamkar sarki
Damnash domin suna fara yin wannan gumurzu ne ya gane cewa lallai yaufa ya gamu da
gamonsa,amma saboda karfin imaninsa da dogaro da Allah ko kadan zuciyarsa bata karaya
ba.Sarila,Yazirina da Mujahid kuwa ko da sukaga irin salon yakin sarki Damnash kuma sukaga
yadda yake neman kuntatawa jarumi Darusi sai hankalinsu ya dugunzuma ainun suka fara tunanin cewa lallai wannan takadirin sarki zai iya samun nasara akan jarumi Darusi kuma da zarar ya gama dashi suma tasu ta kare.Nanfa zuciyoyinsu suka karaya suka kamu da tsananin bakin ciki gami da
karayar zuciya suka fara tunanin cewa dukkan burinsu na duniya ya rushe.Babban abinda ya
daga musu hankali shine koda aka sami kusan
rabin sa'a anayin wannan bakin gumurzun sai ya zamana cewa da kyar jarumi Darusi ke iya kare hare haren sarki Damnash kuma ko kadan baya iya mayar masa da martani saboda ya fara gajiya,shi kuwa sarki Damnash kamar ma a sannan ya fara gumurzun.Anan cikin haka ne sarki Damnash ya shammaci Jarumi Darusi ya daka tsalle sama ya kawo masa wani wawan sara a kafada.Darusi yayi amfani da hannayensa biyu ruke da takobi ya kare saran amma saboda karfin saran da nauyinsa saida kaifin takobin ya dira akan kafadar tasa ya yanke shi.Take jini yayi tsartuwa,Darusi bai san sa'adda ya kwala kabbara ba sakamakon tsananin zafin zogin da yaji amma sai shima ya yunkura cikin shammace ya daka tsalle sama ta gabzawa
Damnash duka da kafarsa a fuska.Saboda karfin dukan saida Damnash yayi katantanwa a tsaye sau biyu amma saiya tsaya cak ba tare daya fadi ba saboda tsananin jarumtaka.Koda Damnashi yaji danshi a kan lebensa ya shafa yafa ashe jini ya fito sakamakon bugun da Darusi yayi masa sai ya
kamu da tsananin takaici ya kurma uban ihu a karo na biyu sannan ya dubi Jarumi Darusi yace kaine Jarumi na farko daya taba samun nasarar fitar da jini a jikina,tabbas daga yau ba zaka sake samin irin wannan damar ba kuma yanzu take zan
maishe dakai tarihin da ko a labari ba za'a sake tunowa dakai ba.Darusi yace ni kuma yanzun nan da izinin ubangijina zan bar maka shaidar da saidai a binneka da ita a kabarinka kamar yadda za'a binne tarihin daukakarka da
jarumtakarka.Kafin Darusi ya gama fadin abin dake bakinsa tuni Sarki Damnash ya fara ja da
baya.Koda ganin haka sai shima Jarumi Darusi ya fara ja da bayan yana kirga takun da Damnash keyi har saida kowannensu ya kurawa abokin gwamin idanu suna tunani da nazari akan abinda zasuyi su sami nasarar hallaka juna.Duk wannan abu dake faruwa Mujahid,Sarila da Yazirina sun zuba idanu suna kallo cikin tsananin tsoro da fargaba.Kamar hadin baki sai Jarumi Darusi da sarki Damnash suka daga takubbansu sama a lokaci guda kuma suka rugo da gudu izuwa kan juna.Koda ya rage saura taku uku kacal su hadu sai kowannensu ya daka tsalle sama ya kaiwa dan uwansa mugun
hari.A tare suka diro kasa suna masu juyawa juna baya amma sai su Muhajid sukaga Darusi da Sarki Damnash sun kame cak kamar gumaka
kowannensu akwai jini a jikin takobinsa amma
kuma a sasssan jikinsu ba'a ga digon jini ba.Tsawon yan dakiku kimanin goma suna tsaye a kame kawai kuma sai akaga hannun sarki
Damnash na hagu ya tsinke ya fadi kasa jini ya kama zuba daga cikin dungulmin hannu amma
saboda tsananin juriya da jarumtaka sai sarki Damnash ya sunkuya ya dauki yankakken hannun nasa ya kura masa idanu yana mai tsananin
mamaki da takaicin yadda akayi jarumi Darusi ya sami nasarar sare masa hannu.Shi kuwa Jarumi Darusi sai gani akayi ya dafe gefan cikinsa
bangaren dama jini na zuba kuma ya durkushe
kasa bisa guiwoyinsa amma saiya yunkura cikin jarumta ya mike tsaye yaje inda dokinsa yake yana layi kamar zai sake faduwa,a haka ya bude jakar guzurinsa ya dauko zare da allura ya kama dinke raunin dake gefen cikin nasa da kansa.Har ya kammala dinke raunin Sarki Damnash na tsaye
ruke da yankakken hannunsa yana kallon hannun yana dukan kansa tamkar mahaukaci sabon
kamuwa.Kuma yana cizon lebensa saboda
tsananin takaici da bakin ciki.Daga can kuma saiya takarkare ya kwarara uban ihu,ihun nasa ya cika dajin gaba daya da amsa kuwwa ya firgita duk wani abu mai rai dake cikinsa.
Mu Hadu A ''Taskar Ajali' Littafi Na Shida(6) domin jin cigaban wannan kasaitaccen kayataccen labari.
TASKAR AJALI 5
Littafi na biyar 5
Na Abdulaziz Sani m gini
Ebook creat by Shuraih Usman
Ebook publish by www.hausaebooks.cf
Ebook din nan yazo maku ne daga shafin www.hausaebooks.cf Kuna ziyarci shafinmu don samun sababbin littatafai
Ga duk wanda ke bukatar ebooks nashi ya samu shiga cikin wepsite namu sai ya turo mana da littafin ta Email namu hausaebooks@gmail.com
TASKAR AJALI
Littafi na Shida 6
Littafin Abdulaziz Sani m gini
Ebook creat by Shuraih Usman
Ebook publish by www.hausaebooks.cf
Ebook din nan yazo maku ne daga shafin www.hausaebooks.cf
Kuna ziyartar shafinmu don samun sababbin littatafai
Ga duk wanda ke bukatar ebooks nashi ya samu shiga cikin wepsite namu sai ya turo mana da littafin ta Email namu hausaebooks@gmail.com
Sannu a hankali kuma sai ihun nasa ya rikide ya
koma kuka,idanunsa na zubar da hawaye shabe
shabe,adaidai wannan lokaci ne Jarumi Darusi ya
karanta wata addu'a ya tofa akan raunin da sarki
Damnash yayi masa sannan ya mike tsaye daga
durkusan da yayi bisa guiwoyinsa ya goge jini
Damnashi dake jikin takobinsa a kasa cikin yashi
sannan ya mayar da takobin cikin kufenta ya daga
kai ya dubi sarki Damnash yace,tabbas ka cika
Gwarzon Mayaki kuma gawurtaccen jarumi da
bazan taba mantawa da biwarka ta jarumta
ba,amma ka tafi da yankakken hannunka izuwa
birninka idan tsafinka zai iya dinke maka hannun
ya koma daidai kamar yadda yake da to sai yayi
idan kuma bazai iya ba to lallai da dungulmin
hannu guda za'a binneka cikin kabarinka kamar
yadda nayi alkawari,kaga kenan na dakusar da
dukkan daukakar ka da kuma shahararka ta
jarumtaka a yanzu cikin kankanin lokaci bisa
taimakon ubangijina.Koda gama fadin hakan sai
Jarumi Darusi ya karasa inda Sarila ke kwance a
kas ya sunkuya ya dauketa ya goyata a bayansa
sannan ya dubi Yazirina da Mujahid yace ku tashi
mu shiga cikin kogon dutsen nan mu kwanta
domin dukkaninmu muna bukatar muyi jinya amma
wancan sarkin mai yankakken hannu a yanzu ya
fimu bukatar agajin gaggawa indai yana son ya
rayu dole ne ya gaggauta tsayar da jinin dake
zuba a dungulminsa.Koda gama fadin hakan sai
Darusi ya juya ya kunna kai izuwa cikin kogon
dutsen goye da Sarila ba tare da tsoron komai ba
duk da cewa kuwa basu caje kogon dutsen ba sun
tabbatar da lafiyarsa.Cikin hanzari Yazirina da
Mujahid suka yunkura cikin matukar karfin hali
suka mike tsaye suka ruke kafadun junansu suka
taka Yazirina na dingisa kafa suka bi Darusi a baya
izuwa cikin kogon dutsen suka kule.Sai bayan
kulewar tasu ne sarki Damnash yaji ya fara jin jiri
kuma ya kama yin layi daga tsaye saboda jininsa
dake zuba nan take ya sake kurma ihu wanda yafi
na farko kara da tsoratarwa sannan yayi sauri ya
yagi kasan rigarsa ya daure dungulmin hannun
nasa ya nannadeshi don tsaida jini,kawai sai ya
ruga izuwa kan dokinsa yai tsalle daya ya haye
kan dokin ya zunguri cikin dokin da
kafafunsa,dokin ya zabureshi da gudu da
baya,lafiyayyen hannunsa na ruke da yankakken
kuma ya cigaba da kwarar ihu tamkar wanda ake
sara a sannan.Kamar yadda Jarumi Darusi ya fada
haka al'amarin ya kasance wato saida suka shafe
kwanaki bakwai a cikin wannan kogon dutse suna
jinyar jikinsu amma a cikin kwanaki biyu rak raunin
Jarumi Darusi ya warke sumul tamkar ma bai taba
yi saidai tabo wajen kawai.A tsawon kwanakin
bakwai Darusi ne ke ta fama yin hidima ga Sarila
domin shi ke bata abinci da baki har ta koshi
sannan ya goge mata maikon bakin,idan zata
kawar da wata bukata sai ya bata wuri ta kawar da
bukatar idan ta gama zata kwala masa kira ya
dawo ya dauketa ya sake goyata ya mayar da ita
cikin kogon dutsen.Abinda baya yi mata kawai
shine sauyin tufafin jikinta wannan Yazirina ce keyi
mata duk da cewa ita ma tana da karaya a
kafarta.Mujahid da Yazirina sunyi matukar mamaki
bisa ganin yadda Jarumi Darusi ya rinka dawainiya
da Sarila tamkar yar uwarsa ta jini,alhalin ita ko
kadan bata sonsa a cikin zuciyarta.Duk tsawon
wannan lokaci babu wanda yaga fuskar Jarumi
Darusi a cikinsu bare yaga irin kamanninsa ko
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 14