Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sai Jarumi Darusi yayi caraf yace ai na ukun nasu shine mata ko ba haka bane?Yazirina ta murtuke fuska tayi shiru,Ita kuwa Sarila sai ta bushe da dariya tace ka tona mana asiri ai kamata yayi kayi shiru da bakinka amma yanzu da ka fadi zaka iya sawa wasu su tsorata damu suyi taka tsantsan kuma su ki baiwa mace yardarsu ko cikakkiyar SOYAYYAr su a garemu.Koda jin wannan batu sai Jarumi Darusi yayi murmushi yace ai kukan kurciya ma jawabi ne mai hankali ke ganewa,yana gama fadin hakan saiyaje ya kama dokinsa ya haye sannan ya dubesu su duka yace wata bakwai fa ba kwana bakwai ba ne saboda haka sai kuzo mu kama hanya domin himma bata ga rago ba.Gama fadin hakan keda wuya sai Darusi ya kada linzami dokinsa yayi gaba.Cikin sauri Sarila,Yazirina da Mujahid ma suka hau nasu dawakan suka bishi. Nima ganin sun hau dawakansu yasa na dakata nan. Suka hau nasu dawakan suka bishi.Mujahid sai ya zaburi nasa dokin da gudu ya riski Jarumi Darusi yace waishin me kake nufi ne da kukan kurciya jawabi ne mai hankali ke ganewa? Koda jin wannan tambaya sai Darusi yayi masa murmushi yace kada ka damu yakai Abokina da sannu zaka ga abinda wannan kalma take nufi da idanunka.Kawai sai Darusi yayi shiru bai kara cewa komai ba ya cigaba da tafiya.Duk wannan magana dasu Darusi sukeyi Sarila da Yazirina basuji ba domin suna bayansu da kimanin tazarar taku biyar sun jero bisa dawakansu suna tafe suna hira,inda Yazirina ta dubi Sarila kawai ta bushe da dariya,koda ganin haka sai Sarila ta dubeta a fusace tace menene kuma abin dariya a fuskata har da zaki kalleni ki kama kyakyatawa?Daji n wannan tambaya sai Yazirina ta nutsu tace ba wai wani abu na gani ba ya bani dariya a fuskarki kawai mamaki ne ya turnuke ni bisa ganin yadda wai yanzu ni dake muka jera muke tafiya har muna hira cikin kwanciyar hankali da nishadi alhalin mun kasance abokan gaba masu FARAUTAR RAYUWAr juna.Wai dama ashe akwai ranar da za'a sami wannan sulhu a tsakaninmu?Koda jin wannan batu sai itama Sarila ta bushe da dariya sannan tace ai wannan sulhun namu na dole ne saboda idan ba muyi shi ba dukkaninmu zamuyi asarar abinda muka fito nema.Ni babban ma abinda ya daure mi kai shine yanzu dai ga taswirori biyu a hannunki kuma ni ma ga tawa a jikina amma duk sun zama na banza domin tun dama ba da su zamuyi amfani ba.Kai lamarin wannan bakon jarumi akwai al'ajabi,to waishin ma ta yaya akayi yasan a inda kogon Taskar Ajali yake alhalin mahaifina ya boyeshi yadda babu mai iya gano shi face da wannan Taswirar guda uku?Koda jin haka sai Yazirina ta numfasa tace bakiyi mamakin irin tsananin jarumtakarsa ba sai mamakin yadda ya gano inda kogon Taskar Ajali yake?Ni bama wannan ba akwai abu guda da nake tsoro,wai shin bayan ya kaimu kogon taskar ajali idan kuma kikayi kokarin shammatarsa don ki kashe shi kika kasa fa?me kike tunanin zai biyo baya?Dajin wannan tambaya sai Sarila tayi murmushi tace ta yaya ma haka zata faru?Ai da ganin Jarumi Darusi mutum ne mai yarda da mika amana saboda haka bazai taba tunanin cewa zamu ci amanarsa ba.Yazirina tayi ajiyar zuciya tace to shike nan wannan abu dai mace ce da aiki ba'a san abin da zata haifa ba,akwai wani abu da nake tunani waishin bakya tunanin cewa manyan sarakuna suna nan sunyi mana kwanton bauna?Ke kin sani cewa ba zasu taba zuba mana ido ba kawai suna ji suna gani har mu mallaki wannan dukiya muzo mu mallaki komai nasu.A yanzu haka inaji a jikina cewa suna biye damu a cikin wannan tafiya ba tare da mun sani ba.Koda jin haka sai Sarila ta busje da dariya tace saboda me zaki damu kanki a kan abinda baikai darajar sauro ba a nauyi akan tafin hannunki,kin sani cewa inda sarakunan duniyar nan kaf gami da gaba dayan bokayen duniya da jaruma duniya zasu taru a nan domin su yake mu ni kadai zan iya kashe su a cikin kankanin lokaci.Koda jin haka sai Yazirina ta jinjina kanta tayi shiru bata kara cewa komai ba.Haka dai su Yazirina suka nausa cikin dajin sukayi ta tafiya basa tsayawa face idan jarumi Darusi zai gabatar da sallah ko kuma idan dayansu nason ya kawar da wata bukata wato dole a tsaya shi kuma duk inda mutum zai zagaya domin kawar da bukatar tasa sai an caje wajen an tabbatar da cewa babu wani abu mai cutarwa a wurin amma banda jarumi Darusi domin shi komai duhun waye da surkukinsa kawai kunna kai yake yi ciki yana karanta addu'ar neman tsari a cikin zuciyarsa.Muhaj id da Yazirina da Sarila kuwa suna matukar mamakin yadda jarumi Darusi keyin ganganci da rayuwarsa haka.Abinda basu sani ba shine ya dogara ne da ubangijinsa dari bisa dari yayi imani cewa zai kareshi daga dukkan abinki.Saida su jarumi Darusi suka share kwanaki uku suna ratsawa ta cikin mugayen dazuzzuka ba tare da sun hadu da wani mugun abu ba,abinda ya daurewa su Yazirina kai shine ganin yadda Darusi ya rinka kurdawa dasu ta cikin surkuku iri irin kuma kafin aje wani a sai ya gaya musu cewa za'a riski abin dake wajen,idan yace akwai tsauni a nan gaba tafiyar kimanin rabin sa'a na isa wurin kuwa sai suga tsaunin.Hatta girman tsaunin da yanayinsa saiya shaida musu hakama tsirrai ko fadama ko dutse ko kogi,Darusi yasan komai dake cikin dazuzzukan tamkar a rubuce suke cikin kwakwalwarsa.Al 'amarin da yayi matukar basu mamaki kenan.A ranar kwana na uku ne daf da faduwar rana suka iso wani wuri mai yanayi iri daban dana sauran dukkan dazuzzukan da suka wuce a baya.Wurin fili ne fetal cike da yashi tamkar sahara.Akwai tsirarun bishoyoyi a wajen a can gaba kuma kamar tazarar zara'i arba'in da biyar akwai wani katon dutse wanda kasansa kogo ne kuma gaba daya dutsen a lullube yake da bishiyoyi masu rassa da ganyaye don haka wajen yayi matukar duhu mutum bai isa ya hango abinda ke wajen ba ko cikin kogon dutsen dole sai mutum yabi ta gefen wannan kogon dutse sannan zai iya wucewa izuwa kan hanyar da zata kaishi daji na gaba.Kawai sai su Mujahid sukaga Jarumi Darusi yaja linzamin dokinsa ya tsaya sannan ya sauko daga kan dokin nasa,koda ganin haka sai duk su ukun suka ja linzamin dawakan nasu suka tsaitsaya.Mujah id ya dubi Darusi cikin alamun rashin fahimta yace me yasa ka tsaya anan?Darusi yace dalili na farko shine lokacin ibadata ya gabato,dalili na biyu kuma inason na baku dama ne kuyi duk irin shirin da kuke ganin zakuyi domin fuskantar bala'in dake cikin wancan kogon dutse domin baku isa ku iya wucewa ta gaban dutsen ba batare da kun fafata da abinda ke ciki ba.Koda jin wannan batu sai cikin Mujahid ya duri ruwa tsoro ya baibaye shi ya ce ka sani cewa ni ba jarumi bane don haka kada ka barni da karfina.Koda jin haka sai jarumi Darusi yayi murmushi yace ai babu wata kariya da zan baka a yanzu tunda ba kayi imani da ubangijina ba,kamar yadda na fada da farko ba zan taimaki dayanku ba face naga muraran zai rasa rayuwarsa.Kada ka manta da cewa kai shahararren barawo ne mai karfin sihirin tsafi daka gagari a kamaka a wannan nahiya saboda haka kayi amfani da karfin sihirin nake anan ka cece kanka.Koda gama fadin hakan sai Darusi ya dauki butar alwalarsa daga cikin jakar guzurinsa ta nufi gefe daya ya tsugunna domin yayi alwalar,Mujahid ya rugo gareshi ya durkusa daf dashi yace wace irin masiface a cikin wannan kogon dutsen?Darusi yace nifa kuna bani mamaki yaya ni da nake bako a cikin wannan nahiya taku ace na fiku sanin sirrin dazuzzukanku,ka tuna fa cewa ba wani nisa mu kayi ba a cikin wannan tafiya daga cikin birninku tafiyar kwana uku kacal ce.A matsayinka na gawurtaccen barawo ya kamata ace kasan komai dake cikin dazuzzukan da suka kewaye ku.Mujahid yace ai ni ba dan fashi bane,ba mai buya a cikin daji a cikin gari nake satata inda ya gagari barayin daji shiga.Koda jin haka sai jarumi Darusi yayi shiru yaci gaba da alwalarsa.Koda yazo zaiyi shafar fuska saiya juyawa su Mujahid baya ya wanke fuskar tasa sannan ya hattama alwalar tasa ya dauko buzunsa ya tayarda sallah.Adaidai wannan lokaci ne Sarila ta yafito Mujahid da hannu yazo garesu,ita da Yazirina,Tayi masa wani irin kallo cikin murmushi mai dauke da alamar tambaya(?)ta bude baki da nufin tayi masa magana amma sai Yazirina tayi wuf ta sha gabanta saboda kishi ne ya turnuke ta ta dubeta tace bana son naga wata alaka na kulluwa tsakaninki da Mujahid.Koda jin haka sai Sarila ta bushe da dariya tace saboda Mujahid mijinki ne ko kuwa saboda ya kasance dan uwanki ne? Yazirina tace babu daya cikin biyu kawai saboda ban yarda dake bane domin a ko yaushe zaki iya yaudararmu ki cutar da dayanmu.Sarila tayi murmushi tace ba gaskiya kika fada ba kishi ne kawai ya turnuke ki saboda kina ganin cewa nima ina son sa ko?Dajin haka sai kunya ta kama Yazirina ta dan kau da kai ita kuwa Sarila sai ta cigaba da bayani tana mai cewa kada ki damu ni a rayuwata soyayya da aure basu zame mini dole ba ina iya kawar dasu daga raina nan take. Hmm Nine Jarumi DarusiIna iya kawar dasu daga cikin raina nan take.Kai Mujahid waishin me kake tattaunawa ne kai da Darusi wannan shine kadai abinda nake son na tambaye shi,koda jin haka sai Yazirina ta dan saki ranta tayi guntun murmushi.Mujahid yace ya gaya mini cewa muyi shirin tunkarar masifar dake cikin wancan kogon dutse dake gabanmu kuma dana tambayeshi ko wace irin masifa ce sai yace dani wai zamu ganta da idanunmu.Koda jin wannan batu sai Sarila ta bushe da dariyar mugunta tace yanzu akan haka ne naga duk ka wani firgice,to koma dai kai bazaka iya yin komai ba ai ka sani cewa ni da Yazirina ba zamu taba barin wani abu ya cutar da kai ba.Gama fadin hakan keda wuya sai suka ga Jarumi Darusi ya idar da sallarsa ya shafa addu'a.Nan take ya mike tsaye da sauri ya nannade buzunsa ya sanya shi cikin jakar guzurinsa ya hau dokinsa ya dubi su Sarila ya ce kuzo mu cigaba da tafiya.Kafin dayansu yayi wani yunkuri tuni Darusi ya kada linzamin dokinsa kuma ya zare takobinsa ya nufi inda wannan kogon dutse yake yana karanta wata addu'a ta musamman a cikin ransa,ita kuwa Sarila sai ta bishi da kallo cikin harara ta daka tsaki tace nifa na tsani wannan mutumin.Baya magana sosai kamar kurma baya yi mana bayanin komai ya barmu a cikin duhu sannan kuma yaki yarda muga fuskarsa nidai ina kyautata zaton cewa shi mummuna ne na kwarai shi yasa baya son muga fuskarsa.Tana gama fadin hakan sai tayi sauri ta kama dokinta ta dane kuma itama ta zare takobinta tabi bayan Darusi.Take Yazirina ta rufa mata baya,Mujahid ne na karshe kuma kana kallonsa zaka gane cewa a tsorace yake domin akwai alamun firgici akan fuskarsa.Lokacin daya rage saura baifi taku goma ba tsakanin kafafun dokin Darusi da wannan kogon dutse sai ya rage saurin tafiyar dokin nasa kuma ya kura idanunsa sosai akan kofar kogon dutsen,suma su Sarila sai sukayi koyi dashi,saida Darusi ya dan gifta kofar kogon dutsen kadan sannan wata katuwar macijiya mai KAWUNA SABA'IN DA DAYA ta jeho kawunan nata gaba daya waje daga cikin kogon dutsen,amma sai kawunan suka tsaya cak kuma suka kurawa Jarumi Darusi idanu aka fara kallon kallo tsakaninta dashi.Sarila,Yazirina da Mujahid kuwa koda sukayi arba da wannan maciya mai tsananin girma da munin fuskoki guda saba'in da daya sai suka firgita ainun domin ko a labarai basu taba jin labarin irin wannan macijiya ba.Duk da tsananin jarumtakar Sarila da Yazirina basu san sa'adda suka ja linzamin dawakansu ba sukaji kamar su ruga da baya,shi kuwa Mujahid jikinsa ne gaba daya ya kama karkarwa yayi wuf ya matsa kambunsa na tsafi domin ya bace amma sai sihirin tsafin nasa yaki yayi aiki.Al'amarin da yayi matukar kara razana shi kenan ya saddakar da cewa lallai yai dai kam ranar AJALINsa ce.Saida Jarumi Darusi ya wuce gaban wannan macijiya har ya bata yar tazara suna kallon kallo ita bata kawo masa wano hari ba shima kuma baiyi wani yunkurin ba na kai mata hari.Hakika masu iya magana sunyi gaskiya da suka ce BABBAN GORO sai MAGOGIN KARFE.Tsakanin wannan Macijiya da Jarumi Darusi KAR TA SAN KAR ne domin a wancan karon sunyi bakin gumurzu tasha bakar wahala a wajensa shima ya wahala amma shi ya sami damar hallaka bai kasheta ba ita kuwa kasa hallakashi tayi.A yanzu tana ganinsa ta shaidashi don haka ne taki cutar dashi.A wannan lokaci a akwai tabon raunikan da Darusi yayi mata a sassan jikinta sunfi guda dari,shi kuwa rauni daya ne tayi masa da kaifin hakorin bakinta guda a lokacin data kawo masa wani mugun sara ya goce cikin bakin zafin nama.A wannan lokaci da farko saida suka shafe sama da sa'a guda tana kawo masa duka da jelunanta kuma tana kawo masa sara da cizo da bakunanta duka yana gocewa cikin bakin zafin nama yana kadesu da hannayensa da takobinsa da kuma kafafunsa.Darusi yana wannan jarumtaka ne da zallan karfin damtsensa da kuma zafin namansa,ita kanta wannan muguwar macijiyar tayi matukar mamakin Darusi saboda wannan ne karo na farko data hadu da wani mahaluki daya gagareta kashewa a cikin dakika biyu walau MUTUM KO ALJAN ko kuma dabba,shi kawai Darusi ransa ne ya baci da yaga KAIFI DA TSINI basa tasiri a jikin wannan macijiya domin duk sa'adda ya sareta koya soka mata takobinsa sai yaga jikin nata ko kwarzanewa bayayi saidai tarwatsin wuta ya tashi amma kuma naushin da yake gabzawa macijiyar akan fuskokinta da hannayensa da kafafunsa suna dimautata domin ji take kamar dutse yake maka mata.Nan da nan yasa idanunta suka rinka kumbura fatar gefen idanuwanta ya rinka durar ruwa kafin shedewar sa'a guda macijiyar ta jigata ainun ta fara wani irin nishi na wahala.Babu shiri macijiyar taja da baya tana haki kamar ranta zai fita suka sake kurawa juna idanu a lokacin da Darusi ya gyara tsayuwarsa kuma ya ruke takobinsa da hannayensa biyu ya fara karanta wata addu'a ta musamman a cikin zuciyarsa.Ita kuwa macijiyar saita fara tattaro dukkan dafin dake cikin cikinta izuwa hakoranta kuma ta dago gaba dayan kawunan nata sama kawai so take ta kawowa sassan jikin Darusi sara da dukkan kawunan nata a lokaci guda.Cikin shammace gami da amfani da dukkan zafin namanta sai macijiyar ta kawowa Darusi sara da kawunan nata kawai sai gani tayi Darusi ya daka tsalle sama da baya tamkar wani tsuntsu ne ya sureshi kawunan nata suka doki kasa gaba dayansu,take kasar wajen ta daddare wata bakar mugunyar kumfa ta jike kasar wajen tamkar bakin shuni aka zuba har wani irin tururin zafi ya rinka tashi a wajen,ba komai ne ba wannan face masifar fitar dafin macijiyar.Shi kansa Darusi daya kalli wajen da Macijiyar ta sara da bakunan nata bai san sa'adda ™Abubakar Haleefah Physicist™ ya yiwa Allah godiya ba a cikin ransa saboda ya tabbatar da cewar inda jikinsa bakunan macijiyar ya sara da tuni tasa ta kare.Koda macijiyar taga jarumi Darusi ya tsallake wannan mugun hari data kawo mai sai ta firgita da al'amarinsa ta dubeshi ta bude bakinta na tsakiya guda daya tace yakai wannan hatsabibin bil'adama kai kuwa waye bokanka a cikin wannan duniya?Da wane irin tsafi kake yin aiki kuma wanene ya baka horon yaki? Koda Darusi yaji macijiyar ta bude baki tayi wannan magana sai ya gane cewa ba dabba bace lallai aljana ce ta rikide izuwa wannan siffa don haka saiya dubeta a fusace yace yake wannan shaidaniyar aljana ke kuma menene dalilinki na rikida izuwa wannan mummunar siffa kuma akan wane dalili kike kokarin hallaka ni?Sai kin bani amsar tambayata sannan nima zan baki amsar tambayar da kikayi min.Koda jin haka sai macijiyar ta bushe da wata mahaukaciyar dariya mai kama da saukar kwarankwatsa wacce babu dadin ji sannan tace yaro kabar hanin munyi gumurzu har na tsawon wannan lokaci ban sami nasarar hallaka kaba,to ka sani cewa shirina babbane yanzun nan kuma zan nuna maka hakan domin ni MURUCIN KAN DUTSE ce ban fito ba saida na shirya. Turkashi sai Mu hadu a Littafi Taskar Ajali Na Biyar (5) domin jin cigaban wannan kasaitaccen kayataccen labari. DONE FOR TODAY. SAI KUMA NEXT TIME. HALEEFAH A ABUBAKARTASKAR AJALI 4 Littafi na hudu 4 Na Abdulaziz Sani m gini Ebook creat by Shuraih Usman Ebook publish by www.hausaebooks.cf Ebook din nan yazo maku ne daga shafin www.hausaebooks.cf Kuna ziyarci shafinmu don samun sababbin littatafai Ga duk wanda ke bukatar ebooks nashi ya samu shiga cikin wepsite namu sai ya turo mana da littafin ta Email namu hausaebooks@gmail.com TASKAR AJALI 5 Littafi na biyar 5 Na Abdulaziz Sani m gini Ebook creat by Shuraih Usman Ebook publish by www.hausaebooks.cf Ebook din nan yazo maku ne daga shafin www.hausaebooks.cf Kuna ziyarci shafinmu don samun sababbin littatafai Ga duk wanda ke bukatar ebooks nashi ya samu shiga cikin wepsite namu sai ya turo mana da littafin ta Email namu hausaebooks@gmail.com K afin Darusi ya budi baki yace wani abu sai Macijiyar ta dako tsalle daga inda take ta kawo masa mugun hari irin na dazu a karo na biyu,maimakon Darusi ya dala tsalle da baya sai yayi gaba a sama ya dira akan tsakiyar kan macijiyar ya hau kawunanta da jelunanta da sara,ai kuwa sai gashi yana daddatsa su jini na tsartuwa da feshi,babu shiri macijiyar ta rinka kurma uban ihu da kyar ta samu tayi dungure da jikinta a kasa tayi wurgi da Darusi can gefe daya kawai sai ta rikide izuwa ainihin siffatar ta Aljana.Tunda Darusi yake ratsa manyan dazuzzuka a rayuwarsa bai taba yin arba da Aljana mai tsananin girma da muni ba kamar wannan Aljanar.Siffart a kala biyu ce ta Aljanu da dodanniya,da yawan mutane idan sukayi arba da ita a cikin wannan siffa take suke faduwa kasa matattu,yan uwanta ne Aljanu suke zautuwa ko kuma su kamu da matsananciyar rashin lafiya.Kai faratan hannayenta da kafafunta ma wadanda suka kasance zara zara kuma cako cako ba kyan gani sun isa su firgita mahaluki.Koda Jarumi Darusi ya dubi Aljanar yaga yadda yayi mata raunika a jikinta kaca kaca,jini na ta zuba kuma tana numfashi sama sama kamar ranta zai fita sai yaji ya kamu da tausayinta duk da cewa taso tayi masa KISAN GILLAH.Aljanar ta budi baki da kyar d wannan kai dake tsakiyar gangar jikinta tace yakai wannan gawurtaccen jarumi kayi mini rai kada ka kashe ni yanzun nan zan amsa maka tambayar da kayi mini.Da farko dai ni sunana Marwisa Bintu Hazmir,na kasance shugabar hadiman Bokan daya kirkiri Kogon Taskar Ajali,ina rikida ne izuwa wannan halitta ta macijiya domin na yaki duk mahalukin da yake da niyar zuwa kogon Taskar Ajali na kashe shi koda kuwa zaije ne ba da niyar dauko dukiyar maigidana ba.Maigidana ya ajiye kuma babu wanda ya isa ya tsallake sharrina face yana dauke da wadansu taswirori guda uku masu nuni izuwa hanyar da zata isa can kogon na Taskar Ajali.Mai gidanan nawa kafin ya bar duniya ya shaida mini cewa ya boye wannan dukiya ne domin yarsa ta cikinsa ta mallaki komai da kowa dake cikin wannan duniya kuma ko itace tazo nan gabana ba tare da taswirori uku ba kasheta zanyi haka kuma idan tazo da taswira biyu babu ta ukun kasheta zanyi wannan shine umarnin da mahaifinta ya bani kuma a kansa nake daga nan har mutuwa ta,bisa binciken da yayu babu wanda ya isa ya hada wadannan taswirori guda uku face ya cancanci ya mulki wannan duniya.Abinda ya kasa ganowa shine shin yar tasa ta cancani ta mulki duniyar?Lokacin da Aljana Marwisa tazo nan a batunta sai Jarumi Darusi ya tari numfashinta yana mai daka mata tsawa yace dake da bokan naki duk kuna kan bata mabaiyani,MULKI da ARZIKI duk Allah ke bada su.Mai gidanki bai isa ya iya hana wani ba MUTUWA da RAYUWA duk wanda yayi nufi zuwa kogon taskar ajali face idan kwanansa ya kare,nazo ne wannan nahiya taku domin na nuna muku cewa addinin da kukeyi na bautar gumaka da sauran abubuwa da kuma imani da tsafi da kukeyi duk karya ne kuma bata ne mabaiyani,ke a kanki yanzu kinga misali tunda gashi kin kasa hanani wucewa izuwa kogon taskar ajali,gaba daya sarakunan dake wannan nahiya taku sunyi imani da cewa duk wanda ya mallaki wannan dukiya ta mai gidanki sai yafi kowa karfin arziki kuma saiya mulki duniya gaba dayanta kuma wai a ko ina sai anyi fari da talauci a karsa ne kadai ba za'ayi annoba ba.To ni na karyata wannan tsafi kuma sai na tabbatar muku da hakan bazan kashe ki ba yanzu amma zan koma da baya naje na nemo wadanda ke dauke da wadannan taswirori guda uku nayi musu rakiya izuwa can kogon taskar ajali amma sai bayan naje can kogon naga duk irin masifun da mai gidanki ya zuba akan hanya don hana shiga kogon,idan kin gama jinyar jikinki kin warke in yaso ki sake tarata a dawowata ko kuma idan na dawo karo na biyu.Koda gama fadin hakan sai jarumi Darusi ya juya ya cigaba da tafiya abinsa ya nufi hanyar da zata kaishi can kogon na taskar ajali ko sau daya bai sake juyowa ba ya dubi Aljana Marwisa har ya kule a cikin dajin lokacin data bishi da kallo kawai tana mamakinsa.Saida Aljana Marwisa ta shafe wata shida da kwana ashirin da daya tana jinyar raunikan da Jarumi Darusi yayi mata sannan ta warke amma tabon raunikan basu bace ba a jikinta.A ranar dataji karfin jikinta Jarumi Darusi ya dawo daga can kogon taskar ajali kuma yazo giftawa ta gaban kogon dutsen da take cikin nutsuwa da takama ba tare da shakkar komai ba.Yana isowa kofar kogon dutsen yayi arba da aljana Marwisa tsaya a cikin siffarta ta macijiya amma ko kallonsa batayi ba sai ta koma cikin kogon dutsen ta kulle,shi kuwa ya wuce abinsa,wannan shine abinda ya faru a baya tsawon watanni takwas da suka shude tsakanin wannan muguwar macijiya da jarumi Darusi.Lokacin da Jarumi Darusi yaga ya wuce ta gaban Macijiya Marwisa lami lafiya saiya dubi Su Sarila ya yafito su da hannu yana mai yi musu nuni dasu tawo su wuce ta gaban macijiyar.Koda ganin haka sai Sarila,Yazirina da Mujahid suka dubi junansu dukkaninsu sai suka noke aka rasa wanda zai fara shiga gaba.Al'amarin daya fusata jarumi Darusi kenan ya daka musu tsawa yace yanzu a hakane kuke tunanin cewa zaku iya zuwa har can kogon taskar ajali alhalin gashi tun a matakin farko kun razana da abinda baifi somin tabi ba a cikin tsaro dake kan hanya.Idan har kun karaya da dukkan jarumtakarku da karfin sihirin tsafin naku kunyi imani cewa ababan dogaronku ba zasu iya tserar daku ba to ku karbi addinia mana.Na rantse da girman ubangijina indai kuka karbi addinina yazu take zan kaiku kogon taskar ajali a cikin abinda bai wuce rabin sa'a ba kuma ubangijina zai ™Abubakar Haleefah Physicist™ kareku daga sharrin duk masifun dake hanya.Koda jin wannan batu sai hankalin su Sarila ya dugunzuma ainun kuma jikinsu ya kama bari take sukaji dukkan tsoro yakau daga cikin zukatansu,kawai sai Sarila ta fara sakarwa dokinta linzami tayi gaba sannan Yazirina ta take mata baya shi kuma Mujahid ya bita.Kaico!!!Ma i rabon shan duka sai ya sha shi domin ita kazar wahala indai aka yankata tofa dole ne a figeta,Koda Aljana Marwisa taga su Sarila sun durfafota zasu wuce ta gabanta sai ta kame cak tamkar gunki ta dauke numfashinya a zatonsu Sarila yadda jarumi Darusi ya wuce lafiya kalau haka suma zasu wuce.Yazirina ce kadai zuciyarta bata amince mata da hakan ba don haka hannunta na dama na kan kufen takobinta kuma idanunta na kan kawunan macijiyar guda saba'in da daya da kuma dukkan jelunan nata ko kiftawa batayi.Saida su Sarila suka iso daf da gaban Marwisa saura kiris su dan gota ta sai ta yunkura cikin bakin zafin nama ta kawo musu mugun sara da kawunanta uku,cikin tsananin zafin nama Yazirina ta daka tsalle sama ta kade kan macijiyar daya kawo mata hari da takobinta kuma ta take kafafunta a sama ta doki Sarila da Mujahid suka fado daga kan dawakansu,ai kuwa sai bakunan macijiyar biyu suka sari gadon bayan dawakan Biyu na Sarila da Mujahid.Take hakoran macijiyar suka datse gangar jikin dawakan biyu tamkar da adda aka saresu kuma dafin macijiyar yasa jinin jikinsu ya daskare sukayi bakin kirin tamkar a cikin wuta aka babbaka su nan take.Ai kuwa sai dokin Yazirina ma ya firgita ainun ya ruga izuwa cikin daji da gudu yana haniniyar doki.Cikin tsananin firgici Yazirina,Sarila da Mujahid suka mike tsaye zumbur a tare suka kama ja da baya baya tamkar su ruga da gudu amma babu damar hakan saboda ita ma macijiyar tunkararsu tayi tana shawagi da kawunanta da jelunanta a samansu.Ko yaya dayansu yace zaiyi yunkurin gudu sun san cewa kawai jefa masa bakinta zata yi guda ta lankwameshi ko kuma ta cafko shi da jelarta guda ta maka shi,ba shiri Sarila da Mujahid ma suka zare nasu takubban kuma suka cigaba da ja da baya macijiyar na biye dasu tamkar mai kaya ya taso barawo akan gaba.Koda Macijiyar taga Sarila sun kusan izuwa inda Jarumi Darusi ke tsaye sai ta zubo musu kawunanta gaba daya ta rinka kawo musu sara,nanfa aka kacame da azababben yaki ya zamana cewa suna kade hare haren nata da takubbansu da dukkan zafin namasu da iya yakinsu.Babban abinda ya dugunzuma hankalinsu shine duk sa'adda takubabban nasu ya hadu da jikin kawunan macijiyar saidai suji kara kal!na tashi tamkar karfe da karfe ne suka hadu gami da tarwatsin wuta kuma ko kwarzanewa jikin kawunan macijiyar bayayi.Duk sa'adda kuma suka kaucewa harin kawunan macijiyar tofa duk abinda bakunan macijiyar ya sara walau bishiyoyi ko duwatsu take suke ragargajewa su farfashe kai kace a cikin turmi aka dake su.Al'amarin da yai matukar dugunzuma hankalinsu kenan musamman da suka gane cewa ko alamar gajiya babu a tare da macijiyar su kuwa nan da nan jikinsu ya fara amsawa.Lokacin da macijiyar taga jaruman uku suna .atukar kokarin kare kansu daga hare harenta sai ta kara da jeho musu jelunanta ta tinka kawo musu duk dasu ta ko ina tana neman ta galabaiyar dasu.Koda ganin haka Sai Sarila tayi girgiza ta zama guda arba'in kuma kowace sarila da takobi a hannunta tana kare hare haren macijiyar tana maida martani.Duk da cewar takubban Sarila ta tsafi guda talatin da tara basa iya yiwa macijiayr illa saidai karfin saran nasu ya zama lugudan duka a gareta.Nan take macijiyar ta fusata ainun ita ma tayi girgiza kawunanta suka kara girma suka ninka da sau uku haka ma jelunan nata kuma ko ina a jikinta yayi mugun santsi,babu shiri duk su ukun suka dimauce damar data samu kenan ta mammake su da jelunanta.Saril a,Yazirina da Mujahid suka yi sama suka gwaru a jikin kogon dutsen take kan Sarila ya tsage ta fado kasa sumammiya,Mujah id ya karye a hannu ita kuma Yazirina ta karye a kafa kuma duk su biyun suka fado kasa a matukar galabaice suna numfarfashi ko kyakyawan motsi babu wanda yayi a cikinsu batare su sami damar iya tashi.Nan take Aljana Marwis ta nufo kansu su ukun cikin matukar farinciki da mugun nufi domin tayi musu KISAN GILLA.Ba zato ba tsammani sai kawai taga Jarumi Darusi ya dako tsalle ya dira a gabanta ruke da takobinsa.Cikin razana Marwisa taja da baya sannan ta rikide izuwa ainihin siffarta ta dubi Darusi cikin alamun tsananin tsoro da kaduwa tace saboda me zaka hanani kashe su alhalin ina kan aiki nane na cika umarnin maigidana?Koda jin haka sai Jarumi Darusi ya daka mata tsawa yace saboda me zaka salwantar da sauran kwanakin rayuwarki a banza kina cika umarnin matacce wanda yanzu haka ya dade da rubewa a cikin karkashin kasa?Ki sani cewa dake da mai gidan naki duk kuna kan bata ne mabaiyani,ina mai umartarki daki ajiye wannan tsohon addinin naku na tsafi ki karbi addinin gaskiya wato addinin musulunci in ba haka ba kuwa yanzun nan zan kasheki na kawo karshen zaluncin ki a cikin wannan daji.Koda Darusi yazo nan a zancensa sai Aljana Marwisa ta takarkare ta bushe da dariyar mugunta lokaci guda kuma saita murtuke fuskarta ta dubi Darusi a fusace tace kabar ganin inajin tsoronka kayi zaton zaka iya rabani da addinin iyaye na da kakannina,akan na bar gadon gidanmu gwara na rasa rayuwata,kawai kayi addininka nima nayi nawa.Kafin Marwisa ta gama rufe bakinta tuni Darusi ya tari numfashinta yana mai daka mata tsawa a karo na biyu yace wannan sulju ba zai taba yiyuwa ba tunda nasan cewa har abada ba zaki daina wannan zalunci ba,idan na barki na baki dama ki fada mini hukuncin da kika yanke na ™Abubakar Haleefah Physicist™ karshe zaki karbi addinin gaskiya ko kuwa kin zabi ki mutu ne?Koda jin wannan tambaya sai Marwisa tace waishin wanda ya mutu zai dawo ne,ra'ayina bazai taba sauyawa ba ina nan akan addinina...Kafi n Marwisa ta gama fadin abinda ke bakinta tuni jarumi Darusi ya dako tsalle cikin bakin zafin nama da shammace ya soka mata takobinsa a makoshinta.Take takobin ta faso bayan wuyanta ta durkushe kasa bisa guiwoyinta yayin da jini ke kwaranyowa kasa bisa kirjinta ta kame kamar gunki domin tuni an zare ranta ta zama gawa.Koda ganin wannan al'amari sai Mujahid da Yazirina suka kamu da tsananin al'ajabi duk da cewar suna cikin mugun yanayi saida suka yunkura da kyar suka mike tsaye suka kurawa gawar Marwisa idanu suna mamakin yadda kayi Darusi yayi mata wannan kisa na farat daya.Duk wannan abu dake faruwa Sarila bata farfado ba daga suman da tayi,koda hankalin Darusi yakai kanta kuma ya dubi halin da Yazirina da Mujahid ke ciki ya tabbatar da cewar ba zasu iya bata wani taimako ba saiya dimauce bai san sa'adda ya ruga da gudu izuwa kanta Sarila ba ya tallafo kanta ya dubi raunin wanda baiyu zurfi ba sosai a saman kunnenta na hagu amma kuma bai daina zubar da jini ba.Cikin hanzari ya mike tsaye ya ruga inda dokinsa yake ya dauko jakar guzurinsa ya budeta ya fiddo zare da allurar dinke rauni ya kama dinke mata rauni sannan ya shafa wani magani akan raunin duk da

Chapter 7 of 14