Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
samu shiga cikin wepsite namu sai ya turo mana da littafin ta Email namu hausaebooks@gmail.com TASKAR AJALI 4 Littafi na hudu 4 Na Abdulaziz Sani m gini Ebook creat by Shuraih Usman Ebook publish by www.hausaebooks.cf Ebook din nan yazo maku ne daga shafin www.hausaebooks.cf Kuna ziyarci shafinmu don samun sababbin littatafai Ga duk wanda ke bukatar ebooks nashi ya samu shiga cikin wepsite namu sai ya turo mana da littafin ta Email namu hausaebooks@gmail.com L OKACIN da aka ruguntsume da Masifaffen Yaki tsakanin Sarila dasu Yazirina ya zamana cewa sun kasa mai da mata da martani sai kokarin kare kansu kawai sukeyi sai kare kan nasu ma ya gagara.Shi kuwa Boka Matawus da sauran dakarunsa na yaki sai suka zama yan kallo kawao suka tsaya suna ta kyalkyala dariyar farinciki.Shidai Boka Matawus hankalinsa dana dakarunsa ne ya kwanata suka cika da dimbin farin ciki tunda sun tabbatar da cewar sun fita daga tarkon Sarila gashi ya cika alkawarin dake tsakaninsu ya kawota inda su Yazirina suke.Lokacin da Sarila taga ta kuntata Yazirina da Aljani Lafwas sai ta shammace su ta daka tsalle sama ta gabza musu wawan naushi da kafafunta biyu akan fuskokinsu saboda karfin naushi saida kowannansu yayi katantanwa a tsaye sau uku suka kama layi zasu kife kasa,kawai sai Sarila ta sake gabzawa Aljani Lafwas mummunan naushi a ciki ya sunkuya ya furzar da gudan jini daga bakinsa sannan tasa takobinta ta fille masa kai ya badi kasa matacce ko shurawar kirki bai yi ba.Ita kuwa Yazirina data fadi kasa magashiyan sai Sarila tasa kafarta guda ta take kirjinta ta dubeta tace maza ki gaya mini inda taswirorin nan guda biyu suke ko yanzun nan kema na karasa kashe ki.Adaidai wannan lokaci tuni Mujahid ya fara zubar da hawaye bisa ganin halin da masoyiyarsa Yazirina ke ciki domin numfashinta ma sama sama yake fita ga jini na yoyo ta hanci da bakinta,kawai sai sukaji Yazirina ta bude baki cikin matukar karfin hali ta bushe da dariya.Lokaci guda kuma ta turbune fuskarta ta dubi Sarila tace ashe ma na cika wawiya mahaukaciya idan na gaya miki inda na boye wadannan taswirori guda biyu tunda nasan cewa koda na fada miki ko ban fada ba kashe ni zakiyi.Da jin wannan batu sai Sarila ta sake fusata ainun tace aiko baki gaya mini inda kika boye su ba sai mun gano wajen da karfin sihirin tsafi don haka idan ma kina da wata wasiya ta karshe ki fadi yanzun nan zan zare miki ruhin numfashinki.Yazirina ta sake bushewa da dariya a karo ba biyu tace wasiya ta kawai itace zan mutu da farin cikin sanin cewa na boye wadannan taswirori a inda babu wanda zai iya daukosu har abada bare ya iya zuwa kogon Taskar Ajali ya debo dukiyar mahaifina.Ba tsafi ba kome zakuyi kun rasa su kenan har abada kamar yadda nima na rasa su.Koda jin haka sai zuciyar Sarila ta kama tafarfasa kamar zata kone kuma nan danan idanunta suka kada sukayi jajur,kawai saita kwarara uban ihu mai tsananin firgitarwa ta daga takobinta sama ta kaiwa Yazirina mummunan sara da nufin ta tsinke mata kai!Tuni Mujahid ya kurma uban ihu ya fashe da matsanancin kuka,kawai sai gani akayi wata takobi ta kare saran da Sarila ta kawo,wanda ke ruke da takobin kuwa kamar daga sama aka jehoshi ya dira a gaban Sarila.Wani jarumi ne a cikin koren tufafi ya rufe fuskarsa da rawani idanunsa kadai ake gani.Koda haduwar takobin tasa data Sarila sai tartsayin wuta ya tashi gami da hayaki,babu shiri Sarila ta ja da baya tana mai gyara tsayuwarta kuma ta kura masa idanu suka fara kallon kallo.A wannan lokaci ne Yazirina ta mike tsaye da kyar ta tofar da jinin dake cikin bakinta ta koma bayan bakon jarumin ta tsaya.Shi kuwa Boka Matawus kasa motsawa yayi saboda kaduwa da mamaki domin a zatonsa duk duniya a halon yanzu babu wani jarumi dazai iya gangancin tarar Sarila gaba da gaba.Mujahid kuwa daya ga Yazirina bata mutu ba saiya bushe da dariyar farin ciki.Bayan anyi kallo tsakanin Sarila da bakon jarumin sai ta dubeshi ta daka masa tsawa tace kai kuma waye kuma daga ina ka fito har da zaka zo ka shiga fadan da bai shafeka ba?Maza ka baiyana kanka ko yanzun nan kaima ka sheka Barzahu.Kafin Sarila ta gama rufe bakinta tuni bakon Jarumin ya tari numfashinta yana mai cewa sunana Darusi Bin Sardus mai yaki da zalunci kuma mai kokarin tabbatar da gaskiya bisa karya.Burina shine haske ya mamaye dukkan duhu,mutane su farga su daina bautar gumakan banzan da shaidanun aljanu su koma bautar Sarki guda daya mahaliccin komai da kowa.Kuyi mini bayanin makasudin wannan yaki a tsakaninku domin nayi muku sulhu na baiwa mai gaskiya gaskiyarsa.Koda jin wannan batu sai Sarila ta bushe da dariyar mugunta lokaci guda kuma ta murtuke fuskarta ta dubi bakon jarumin a fusace tace baka isa kasan komai ba dangane da wannan rigima kuma tunda dama na fuskanci kazo mana ne da bakon addini to tabbas bani da makiyin daya fika saboda haka yanzun nan zan gama dakai sannan na gama da wannan shashashar dake bayanka.Sarila na gama fadin haka sai ta dako tsalle a sama daga inda yake ta kawowa bakon jarumin mummunan sara a kafadarsa da nufin ta tsargeshi gida biyu.Cikin bakin zafin nama na gaban kwatance sai gani akayi ya daga takobinsa ya kare saran,nanfa suka ruguntsume da azababben yaki cikin matukar jarumtaka da gwaninta ya zamana cewa suna kaiwa junansu hare hare.Ko dakika ashirin ba'ayi ba da fara wannan gumurzu Sarila ta fahimci cewar lallai yau ta gamu da gamonya domin kuwa kafin ta kaiwa bakon jarumin sara guda daya shi ya kai mata uku kuma zafin namansa ya ninka nata sosai.Nan danan ya fara kuntata mata domin sau uku yana kadar da takobin hannunta ya tsirata da tasa amma sai yaki kasheta ya kara bata dama ta dauki takobin tata su ci gaba da fafatawa.Da dai Sarila taga cewa tabbas ya fita iya yaki sai ta fara amfani da karfin sihirinta ta huro masa wata irin iska mai karfin gaske domin ta sure shi sama ta makashi da jikin wani dutse amma sai taga iskar ta kasa daukarsa ta juya izuwa kanta ta sureta ta makata a jikin wata bishiya.Sarila ta fado kasa tim!a lokacin dataji kamar- ™Abubakar Haleefah Physicist™ kashin bayanta ya karye amma bata daddara ba saita mike tsaye zumbur ta cigaba da watsawa bakon jarumin mugayen abubuwa,saidai kaga bishiyoyin dajin suna tunbukowa daga cikin kasa har jijiyoyinsu suna faduwa akan bakon jarumin.A lokaci guda sama da bishiya arba'in ne suke tahowa da gudu izuwa kansa zasu makeshi amma sai aga ya tashi sama ya bubbuge su sun ratattake sun zube kasa.Kai bama bishiyoyi ba har manyan duwatsu Sarila ta rinka watsa masa masu mugun kwari da nauyi amma sai gashi bakon jarumin yana naushin duwatsun da hannayensa da kafafunsa suna farfashewa suna tarwatsewa tamkar da guduma ake bugunsu.Saboda tsananin mamakin wannan jarumta ta bakon jarumi Boka Matawus,Yazirina,Mujahid da wannan dakaru dubu na birnin yamein basu san sa'adda suka wangame bakunansu ba,idanunsu suka zazzaro kuma suka kame tamkar gumaka.Lokacin da Sarila taga ta jefawa bakon jarumin bishiyoyi da duwatsu domin ta hallakashi amma duk ya ragargajesu sai kuma ta watsa masa kibiyoyin tsafi masu dauke da mugun dafi sama da guda dubu a lokaci guda,kawai sai bakon jarumin yayi amfani da takobinsa yayi dan tsalle sama kadan ya harde kafafunsa ya tankwashe su tamkar a kan shimfida yake zaune kuma ya rufe idanunsa ya rinka karkade kibiyoyin tsafin suna zubewa kasa a kakkarye ko guda daya bata taba jikinsa ba kuma bata samu damar wucewa ba ta gabansa.Ita kanta Sarika saida ta razana bisa ganin wannan gagarumar jarumtakar da yayi ta dan ja da baya a tsorace a lokacin da kibiyoyin tsafin nata gaba daya suka gama zubewa kasa.A sannan ne jarumin ya diro kasa bisa kafafunsa har a sannan fuskarsa na rufe bai bude ta ba daga cikin rawani,kawai sai ya dubi Sarila cikin murmushi yace kin yakeni da makami bakiyi nasara ba,kin yakeni da sihirinki na tsafi ubangijina ya bani kariya,yanzu kuma menene sauran abin dogaron naki?Koda jin wannan tambaya sai Sarila tayi jifa da takobinta kuma ta gyara tsayuwarta tana mai dunkule hannayenta tace yanzu kuma zan jarraba tsagwaron karfin damtsw na akan naka.Koda jin haka sai Jarumi Darusi yayi murmushi yace ina mai shawartarki daki gaya mini matsalar dake tsakaninki da wadannan mutane da kuke yaki domin na sulhunta ku nayi tafiyata amma tabbas na zaki iya yin galaba ba a kaina ba.Sarila ta girgiza kanta tace ai sai an gwada sannan ake sanin na kwarai.Kafin Darusi ya kara cewa wani abu tuni Sarila ta dako tsalle daga inda take tsaye cikin shammace ta kawowa Darusi naushi a fuskarsa da kafarta guda.Cikin sa'a kuwa ta gabji bakinsa yayi baya taga taga kamar zai fadi amma saiya tsaya cak lokacin dayaji dan radadi a kan lebensa na kasa.Koda Darusi ya shafa leban nasa yaga jini saiya dubi Sarila yayi mata dan guntun murmushi kuma ya gyara tsayuwarsa ya yafito ta da hannu alamar cewa idan ta isa ta sake kawo masa hari.Kash!rashin sani yafi dare duhu,tabbas inda Sarila tasan abinda zai biyo baya da batayi gangancin sake kawowa Darusi hari ba domin koda ta sake dako tsalle a sama ta kawo masa wani wawan naushi da kafa sai a kaga yayi farat ya ruke kafartata da hannu daya take ya wulwulata a sama yayi mata hajijiya sannan ya makata a jikin wani dutse.Take hannunta na hagu ya karye ta fado kasa sumammiya ta baje.Faruwar hakan keda wuya sai jarumi Darusi ya dubi Boka Matawus da dakarunsa yace ku kuma fa zaku jarraba naku karfin ne a kaina?Dajin wannan tambaya sai Boka Matawus ya juya da sauri ya kama dokinsa ya haye ya juya da baya ya zabureshi da gudu,take suma dakarun nasa sukayi koyi dashi aka rufa masa baya.Adaidai wannan lokaci ne jarumi Darusi ya karasa inda Mujahid ke tsaye a daure cikin sarkar tsafi,koda Mujahid ya shafi sarkar saita zagwanye ta zama ruwa,cikin kaduwa Mujahid ya tsugunna kasa ya kama godiya amma ko kallonsa Darusi baiyi ba saiya juya ya dubi Yazirina yace maza kije ki duba hannun wannan jarumar da tayi yaki dani ta karye ki gyara mata karayar.Koda jin wannan batu sai Yazirina ta dubi Darusi cikin matukar mamaki tace saboda me zaka ce naje na taimaki abokiyar gabata wacce takeson ta hallaka ni?Me yasa kai ba zaka taimaketa ba da kanka? Darusi yace mutum baya sani waye masoyinsa ko makiyinsa muddin zuciyarsa na son kowa,makiyinka baya daina kinka face ka taimake shi,dake da ita duk kuna cikin bata ne mabaiyani saboda haka inason na taimake kune na sanyaku a kan tafarki madaidaici.Watakila idan ta fardado daga suman da tayi zuciyarta tayi sanyi kuma ta cire duk abinda ke zuciyarta na mugunta a kanki saboda haka inason ki hanzarta yi mata magani kamar yadda na umarceki.Koda jin haka sai Yazirina ta dubi Mujahid shi kuma yayi mata inkiyar tabi umarnin.Yazirina ta karasa inda Sarila ke kwance takai hannunta domin ta duba hannun Sarila amma saita fasa ta waigo ta dubi Jarumi Darusi tace har yanzu baka bani amsar tambayata ta biyu ba,menene dalilin da yasa kai ba zaka gyara mata karayar ba da hannunka?Kuma menene yasa har yanzu kaki ka nuna mana fuskarka muga irin kamaninka?Lokacin da Jarumi Darusi yaji wadannan tambayoyi guda biyu sai yai dan guntun murmushi sannan yace ni a addinina haramun ne namiji ya taba jikin macen da bata kasance muharramarsa ba face bisa lalura,abinda yasa kuwa kiga naki baiyana fuskata a gareku shine ubangijina yayi mini wata baiwa wacce ke kawo matsala ga wasu jama'ar idan sun kalle ni,zaku iya ganin fuskata a wani lokacin anan gaba idan mun sake haduwa,maza ki gyara karayar hannun yar uwarki kafin hannun ya kumbura?Koda jin haka sai Yazirina ta duba hannun Sarila da sauri take kuwa taga ashe lallai karyewar tayi,cikin hanzari ta umarci Mujahid yaje ya saro yan kirare sannan ta gyara ™Abubakar Haleefah Physicist™ karayar aka shafawa hannun magani kuma aka daureshi da kararen.Gama hakan keda wuya sai Darusi ya karaso garesu ya tsugunna dag dasu ya karanta wata addu'a ya tofa a kan hannun Sarila sannan ya dubi Yazirina yace da izinin ubangiji na wannan karayar zata warke a cikin kwananki uku kacal kuma ba zata sake jin wani ciwo ba a hannun.Koda gama fadin hakan sai ya mike tsaye ya koma can gefe daya ya dauko wata sarewa ya busata sau daya.Faruwar hakan keda wiya sai ga wani Doki daga nesa ya taho da gudu har saida dokin yazo gaban Darusi sannan ya durkusa bisa guiwoyinsa,Darusi ya shafa kan dokin yace an gaisheka Haidimul Dini,kawai sai Darusi ya bude wata jakar guzuri dake kan dokin ya dauko butar alwalarsa ta duma gami da farin buzu ya koma gefe daya ya zauna ya kama yin alwala,bayan ya idar da alwalar sai ya hau kan farin buzun ya tayar da sallah,duk wannan abu daya faru wato Darusi yayi Yazirina da Mujahid sun kura masa idanu kawai suna kallonsa cikin matukar mamaki.Ita kuwa Sarila har wannan lokaci bata farfado ba.Lokacin da Darusi ya fara sallah ne Yazirina ta matso daf da Mujahid tace yanzu menene abinyi? Ga Sarila a sume har yanzu bata farfado ba shi kuma wannan bakon jarumi ya kama yin wata irin ibada wacce ni ban tana ganin irinta ba,ko waige bayayi bare ya kallemu yaga abinda mukeyi,baka zaton cewa zamanmu anan a haka yana da mugun hadari?Ina ganin cewa zaifi mana alheri mu gudu kafin Sarila ta farfado ta kashe mu sannan ta kwashe wadannan taswirori na jikina.Koda Yazirina tazo nan a zancentsa sai Mujahid ya girgiza kai alamar cewa bai yarda da shawarar ba da tazo da ita don haka saiya dubeta yace yanzu idan muka gudu ina zamuje?Babu inda zamu iya zuwa face gidan yar uwarki Muznaira kuma kinsan laifin da mukayi mata mun sace kambunta na tsafi kuma gashi an kashe shugaban dakarunta Aljani Lafwas a sanadiyyar mu,babu wanda zai iya karemu face wannan bakon jarumi.Duk inda muka shiga sai Sarila ta kure mana gudu ta kashe mu kuma ta dauke wannan taswirar taje ta cika burinta.Ni ina ganin cewa zaifi kyau mu jira jarumi Darusi ya gama ibadar tasa mu sanar dashi gaskiyar duk al'amarin dangane da Taskar Ajali da dimbin dukiyar dake cikinta wadda a kanta ne yanzu kowa hankalinsa ya raja'a domin yaga ya mallaketa.Koda Mujahid yazo nan a zancensa sai Yazirina ta daka masa harara tace amma dai bansan cewa baka da basira ba sai yau,Kai wane irin wawa ne zaka sanar da irin wannan gawurtaccen jarumi mai tsananin karfin sihiri sirrin wannan dukiya ta mahaifina,ai yana jin komai shike nan ya sami tsuntsu daga sama gasashshe.Abinda nakeso dakai shine mu lallaba shi mu yaudare shi mu numa kamar muna sha'awar wannan addinin nasa.Kai idan ta kama mu karbi addinin nasa ma sai mu karba har ya rakamu izuwa can kogon taskar Ajali,ina da tabbatar da cewar zai iya karemu daga dukkan sharrin dake cikin dajin kuma kaga zai bamu kariya daga sharrin Sarila har hannunmu yakai kan wannan dukiya,kawai sai mu shammaceshi mu kashe shi.Yayin da Yazirina tazo nan a jawabinta sai Mujahid yaja dogon numfashi gami da ajiyar zuciya sannan yace a rayuwata nayi karya sau ba adadi nayi yaudara da cin amana yafi sau dubu ba tare da shakkar komai ba amma wannan karon ina tsaoron nayi karya ko yaudara ga wannan bakon jarumi,gaskiya ni zan karbi addininsa bisa gaskiya kuma bazan yaudareshi ba amma idan ke kina ganin zaki iya tofa ban hanaki ba.A iya rayuwata ban taba ganin matsafin dayayi irin gagarumar jarumtakar da yayi ba a yau,lallai jikina ya bani cewa shi ba matsafi bane kuma lallai wannan gagarumar jarumtakar tazo masa ne daga karfin da yafi karfin tsafi.Koda jin wannan batu sai jikin Yazirina yayi sanyi tayi shiru batace komai ba daga can kuma saita cakumo kwalar rigar Mujahid tace ka sani dai cewa wannan dukiya dake Taskar Ajali tawace nice kadai na cancanci na gajeta saboda haka ban yarda ka sanar da wannan jarumi inda take ba koda kuwa zaka sanar dashi komai.Mujahid ya gyada kai yace to shikenan nayi miki alkawari bazan sanar dashi ba to amma kuma idan ba'a sanar dashi ba ta yaya zai rakaki can din har ya kareki daga sharrin abubuwan dake kan hanyar da kuma sharrin Sarila wacce ita ma na tabbatar da cewar ba zata taba janye manufarta ba akan mallakar wannan dukiya ta Taskar Ajali?Koda jin wannan tambaya sai Yazirina tace kada ka damu ai hanyar kashe makahon kare ba wuya gareta ba ni nasan abinda zanyi kawai ka zuba mini idanu.Gama fadin hakan keda wuya sai Sarila ta farfado daga dogon suman da tayi,koda ta bude idanunta ta tsinci kanta kwance a kas a gefe daya ga hannunta na dama a daure cikin karare alamar cewa ta kuma ga Yazirina da Mujahid a can gefe daya sun kura maya idanu.Jarumi Darusi kuma na zaune bisa buzu kusa dasu ya idar sa Sallah yana shafa addua'a sai takaici ya turnuketa ta kamu da tsananin bakin ciki ba don komai ba sai saboda yaune karo na farko da'a ka sami jarumin daya samu lagonta tundaga ranar data fara gumurzu da mazaje.Nan take kwallar takaici ta ciko a cikin idanunta ta yunkura ta mike tsaye da kyar ta tako kafafunta tazo gaban jarumi Darusi,kawai sai ta sake yunkurawa da nufin ta dokeshi da kafarta amma sai taji kafar tata ta sage wani irin mugun zugi ya shigeta bata san sa'adda ta kwalla ihu ba ta fadi kasa. Bata san sa'adda ta kwalla ihu ba ta fadi kasa.Al'amarin da yayi matukar baiwa su Mujahid mamaki kenan,shi kuwa Jarumi Darusi bai ma san abinda takeyi ba har saida ya gama shafa addua'arsa sannan ya juyo.Koda yaga Sarila ta farfado harma ta zo kusa dashi sai ya dubeta yace to yake wannan babbar jaruma shin kece zaki fara yi mini bayanim abindake tsakaninku da wadancan abokan fadan naki ko kuwa sune zasu fara.Ni yanzu alkali ne kawai a tsakaninku mai son yi muku sulhu.Koda jin wannan batu sai Sarila ta dubi Darusi cikin irin murmushi wanda yafi kama dana yaudara tace tsakanin ni dasu duk wanda ya fara bayani daya ne babu laifi kawai dai abinda na sani shine dole ne ko ni ko su a sami wanda zaiyi maka karya alhalin kuwa na fuskanci cewa kai baka karya kuma baka son muyi karya.Darusi ya gyada kai yace tabbas abinda kika fada gaskiya ne kuma nayi matukar jin dadin bayanin naki to amma ki sani cewa su alkalai Allah ya basu ilmi na fahimtar gaskiya da akasinta da izinin ubangijina daga bayananku zangane wanda ya fadi gaskiya da wanda yayi mini karya don haka yanzu zan fara sauraron naki bayanin saiki fara.Sarila tayi gyaran murya tace Da ni da waccan duk a hannun Boka Guda muka taso ni tsintata yayi ya raineni ita kuwa 'yarsa ce ta cikinsa,kafin mutuwarsa ya adana wata dukiya mai tsananin yawan da babu kamarta a cikin wannan duniya a wani boyayyan wuri kuma ya zana taswira ta zuwa wannan wuri har guda uku kuma dole sai an hada wadannan taswriro guda uku a waje guda sannan taswirar zatayi aiki.Taswirar ta farko ya zanata ne a kan gadon bayana barima ka gani.Koda fadin haka sai sarila ta yunkura zata cire rigarta amma sai Darusi yayi sauri ya rike hannunta ba tare daya tanka ba yace a'a dakata ba sai na gani ba cigaba da bayaninki.Sarila tayi murmushi tace ragowar taswirorin guda biyu akan fatar dabba ya rubuta su kuma yanzu haka suna hannun yar uwan nan tawa Yazirina ta boye su,dani da ita da dukkan manyan sarakunan duniya bamu da burin da yafi muje inda wannan dukiya take mu mallaketa saboda duk wanda ya mallaketa tamkar ya mallaki duniyar nan ne kaf,bisa wannan dalili ne take so ta kashe ni ta kwafe taswirar dake zane bisa gadon bayana ni kuma nakeson na kasheta na kwashe taswirorin dake hannunta,na gama nawa jawabin saika saurari nata sannan kayi mana hukunci bisa adalci amma kafin nan inason na roki wata alfarma guda daya a wajenka.Alfarmar kuwa itace bayan kayi mana shari'a kafin mu rabu inason ka bude fuskarka domin naga kamannin jarumin daya fini karfin damtse,iya yaki da karfin sihiri saboda har abada bazan taba mancewa dakai ba kuma sa na zana fuskarka da kirar jikinka na ajiye a cikin kundin tarihin rayuwata.Lokacin da Sarila tazo nan a zancenta sai jarumi Darusi yace bazan iya baiyana fuskata ba ga kowa a wannan nahiya taku face na kammala abinda ya kawo ni.Koda gama fadin hakan saiya juya ya fuskanci Yazirina yace to kinji bayanin yar uwar taki yanzu kuma kece zakiyi naki bayanin kin kuma amince da duk abinda yar uwar taki ta fada gaskiya ne babu gyara,ba sai kince komai ba kawai zan zartar da hukunci nane.Caraf sai Yazirina tace a'a abinda ta fada akwai karya da yawa a cikinsa da ita da manyan sarakunan duniya suna son su mallaki wannan dukiya ne saboda kawai su ci gaba da zalunci a doron kasa,ni kuwa wannan dukiya tawace gado nane zan mallaketa ne don amfanin kaina ni kadai.Koda jin haka sai Jarumi Darusi yace ai kema ba adala bace kin zama azzaluma kamarsu,duk dan adam din da yake son dukiya mai tsananin yawa irin wannan don amfanin kansa shi kadai bazai taba zama mai tausayi dajin kai ba.Waishin abin tambaya anan shine shi kansa mahaifin naki ta yaya ya tara wannan dumbin dukiya?Koda jin wannan tambaya sai jikin Yazirina yayi sanyi ainun tayi shiru ta kasa cewa komai.Jarumi Darusi yayi gyaran murya sannan yace shari'ar da zanyi muku itace daga yau na hana yaki a tsakaninku tunda a kan taswirar zuwa kogon taskar ajali kukeyi.Indai kogon Taskar Ajali kukeson zuwa ni nasan hanyar da za'a bi aje can din kuma ina mai tabbatar muku da cewa na shiga har cikinsa kuma na fito da raye cikin koshin lafiya ba tare da wani abu ya taba lafiyata ba.Koda jin wannan batu sai Sarila,Yazirina da Mujahid suka zazzaro idanu suka kurawa Darusi idanu cikin alamar rashin yarda.Koda hanin haka sai Mujahid yayi murmushi yace na fuskanci cewa baku yarda da wannan labarin dana baku ba tunda kuna mamakin cewa na sgiga cikin kogon taskar Ajali na fito a raye.To me yasa bakuyi mamakin irin abubuwan danayi ba na jarumtaka da al'ajabi a gabanku ya zamana cewa sihirin tsafinku ya kasa tasiri a kaina?To ku sani ni ubangijina ne yake bani taimako da kariya a kan dukkan al'amarina ni ba dukiya ce a gabana ba ko mulki abinda yake gabana kawai shine ubangijina da addinina,kuyi mini alkawari cewa zaku karbi Addinina idan na raka ku har cikin kogon Taskar Ajali kuka sami wannan dukiya.Koda jin wannan tambaya sai Sarila da Yazirina suka kalli junansu sannan suka kallo Mujahid aka rasa wanda zaice wani abu.Darusi yace idan kun yarda da hakan akwai sharadi guda daya,sharadin kuwa shine zaku ceci kanku da karfin damtsenku,iya yakinku da karfin sihirinku,bazan taimake ku ba face naga zaku rasa rayuwarku ko dukiyarku.Koda jin wannan batu sai Sarila ta numfasa tace bari muyi shawara tukunna tana gama fadin hakan saita mike tsaye ta karasa inda Yazirina da Mujahid suke ta jasu izuwa gefe daya.Sarila ta dubi Yazirina tace yaya kike gani shin kin yarda da tayin da Darusi yayi mana?Idan kin yarda akwai matsala daya, matsalar kuwa itace idan har muka karbi Addinin Darusi tofa zamu mallaki wannan dukiya ne kawai amma ba zamu sami sihirin dake jikinta ba na mallakar duniya gaba dayanta,saboda tsafi da addinin Darusi basa haduwa a waje guda.Koda jin wannan batu sai hankalin Yazirina ya DUGUNZUMA tace to menene amfanin duk wahalar da mahaifina yasha kenan wajen tara mini wannan dukiya da sihirceta,yayi ne domin na sami daukakar da tafi ta kowa a duniya bana bakin ciki kema ki amfani wannan dukiya tunda baki san kowa ba a duniya face mahaifina,shine uwa da uba a gareki to amma ta yaya zamu ci gajiyar wannan gagarumin aiki da mahaifina yayi mana idan har zamu karbi addinin wannan bakon jarumi?Koda Yazirina tazo nan a zancenta sai Sarila ta dubi Mujahid tace kai meye shawarka?Mujahid yace ai ni tuntuni na nuna muku ra'ayina akan wannan bakon jarumi daga yanzu zuwa ko yaushe zan iya karbar addinin nasa.Koda jin haka sai Sarila ta murtuke fuskarta ta dakawa Mujahid harara tace kai ba abokin shawarar mu bane bamu wuri nayi shawara da yar uwata.Cikin sanyi jiki Mujahid ya tafi ya barsu.Tafiyarsa keda wuya sai Sarila ta dubi Yazirina tace zamu jefi tsuntsu biyu ne da hoge daya,zamuje Taskar Ajali da taimakonsa kuma zamu yaudareshi a matsayin zamu karbi addinin nasa,da zarar mun isa can din saimu shammace shi mu kashe shi kinga kenan ba zamu bar aikin baba ya tafi a banza ba.Duk da newa nice gaba dake a shekaru nayi miki alkawarin cewa indai muka sami wannan nasara zan zama karama kece babba kuma zan zamo mai biyayya a gareki.Koda Sarila tazo nan a zancenta sai Yazirina tayi shiru tana tunani da nazari har izuwa tsawon yan dakiku sannan ta dago kai ta dubi Sarila tace na amince da hakan amma bisa sharadi guda,sharadin kuwa shine ni ba zan sa hannu akan batun kashe wannan bakon jarumin ba ba bar miki komai a hannunki.Sarila najin haka sai ta kamu da tsananin farinciki tace na yarda da hakan.Nan take su biyun suka dunguma sukaje wajen jarumi Darusi Sarila ta dubeshi tace mun yarda zamu karbi addininka muddin ka kaimu Taskar Ajali.Koda jin haka sai Shima Jarumi Darusi ya kamu da matukar farinciki kuma ya amince akan su ci gaba da yin wannan tafiya gaba daya tare.Ba tare da bata wani lokaci ba kowa ya shiga shirin tafiya,saida kowa ya kammala tsaf sannan Sarila ta dubi Jarumi Darusi tace tunda kai ne kasan hanya sai ka wuce gaba kayi mana jagora amma inaso ka gaya mana yanzu daga nan zuwa can kogon taskar ajali tafiyar kwana na wace?Koda jin wannan tambaya sai Jarumi Darusi yayi murmushi yace ai ba batune na kwana nawa ba saidai kice na wata nawa ne,a kalla sai mun shafe wata bakwai muna tafiya ta cikin mugayen dazuzzuka,manyan birane kuwa guda uku ne a gabanmu kuma a kowane birni akwai wata mummunar masifar data addabesu,dama na kudurce a raina cewa zan taimakesu basai na dawo saboda dama nasan cewa burina bazai taba cika ba a wannan nahiyar face nazo na riske ku.Koda Jarumi Darusi yazo nan a zancensa sai hankalin Sarila,Yazirina da Mujahid ya dugunzuma ainun ba don komai ba sai bisa jin doguwar tafiyar dake gabansu har ta kimanin tsawon watanni bakwai da irin masifun da zasu fuskanta a kan hanyar tasu,uwa uba kuma sai batun garuruwa ukun da sukaji cewar dole sai sunbi ta cikinsu kuma akwai bala'in da yake damun garuruwan uku wadanda jarumi Darusi keson magance su.Cikin alamun tsananin damuwa Yazirina ta dubi Mujahid tace kai ni fa na fara sarewa wai shin ma menene tabbacinmu cewar zamu tsira da rayukanmu a cikin wannan tafiya,lallai kowa yaci zomo yaci gudu kuma babu wani abu da mutum zai samu a saukake a cikin wannan duniya ba tare daya sha wuya ba,ni kam sai yanzu na gane cewa mahaifina ya yanka mana KAZAR WAHALA wacce gata ta zame mana dole mu figeta.Hakika duk wanda bai damu da abubuwa uku ba a cikin duniya daya gama morewa,abu na farko shine mulki,sai Dukiya,sai kuma na ukunsu wanda ba sai na fada ba.Koda Yazirina tazo nan a zancenta

Chapter 6 of 14