fama da Ciwan sanyi duk nacin sanyin ki hajiya kikai amfanin da maganin Mmn khairat saikin warke duk ko iya da d'ewarshi ajikinki..Domin k'arin bayani👉 WhatsApp no 07044450136, 08167453086
*06*
*Zaria*
Samaru_Tsamiya.
8:11am.
A cikin anguwan samaru Layin Tsamiya, Ire iren gidajen su na b'arayin wajen zaku ga akwai d'akuna a waje saboda anguwa ce ta yan makaranta, Makaranta kuma Babba a Africa wato ABU ZARIA.
Ko bayan makaranta akwai y'an kasuwa da masu huldar arziki da neman na kansu, iren iren gidajen wajen duk akwai dakunan a waje domin ba da Haya na maza matasan yan makaranta.
A irin hakane na hango wani gida mai Damdamali a kofar gidan har da Rumfa sai Dakunan waje jere a layi Guda biyar, Daga gefe har da makewayin su na lalura.
Gidan na marasa karfi ne ammh kuma bai lalace sosai ba, yanzu haka kila ma megidan ya rasu dakunan magada ne.
Dakunan duka suna Rufe ne,Sai guda d'aya na farko ne a bud'e har da Labule, Kai tsaye sai ga wani Dogon Saurayi ya fito Sanye da kayan yan Bautar kasa completed, a jikinsa Farar Riga da Green din wando,sai Falmaran din su Green sai Facin cap itama kalan green mai haske.
Kafarsa sanye da Booth din takalminsu mai ruwan goro. Bayansa goye da wata Bakar Jaka karama ta baya.
Dukawa ya yi yana kara tamke igiyan takalminsa duk da yana Duke ne ammh Dole za'a kirasa ingarman Namiji Tunda ya had'a tsawo da Fad'i na Budewar cikakkun maza.
Ya nan nan a duke Wani farin Saurayi ya sake Fitowa daga Dakin shima da irin shigar sak, Daga gani ni masu yi ma kasa Hidima ne ma'ana Corpers.
Kofar Dakin ya Rufe ya saka makullin yana kullewa lokaci d'aya yana fadi'n"Hala yau tafiyar kasa zaka yi?
Ya fad'a daidai Lokacin da ya gama kulle Dakin, Shima yana da jakar baya kalan kayansa wato green. Sai ya kara gyara zamanta a saman kafad'ansa na Hannun Dama Key din kuma sai ya zura a aljihun wandonsa.
Wanda ke duke kuma bai tankasa ba,Illah cigaba da tamke igiyoyin takalminsa da ya yi, na tsayen ya kara kallonsa lokaci d'aya ya duba Bakin agogon Fatan da ke hannunsa cikin Kosawa yace"Mallam mun fa makara. Ka tsaya sai faman tamke igiyoyin takalmi ka ke yi."
Sai a lokacin ya mike yana kara Dage wandonsa sama har ana ganin sawowin kafarsa mai cike da gargasa ga su nan duk sun kwanta. kai tsaye ya kai duban shi kan agogon Silban da ke hannunsa 8:20am na safe kuma ya kamata By now ya isa inda zashi.
Yana shirin mgana wayarsa da ke aljihun wandonsa ta Dauki Vibration alamun ana kiran shi,Hannu ya saka ya ciro wayar yana duba mai kiran duk da yasan Daga gida ne, Tunda itace wayarsa da kowa ya san layin. Babbar waya ta makaranta ce da aiki ba kowa ya san shi da ita ba.
Sunan UMMA da ya gani ne yasa ya yi kasake shi bai dauki wayar ba, shi kuma bai maidata aljihu ba.
Saurayin da ke bayansa ya yi Dage tunda ya fishi tsawo ya leka yana Fad'in"Waye ke kira?
Ko SULTANA ce?
Da sauri ya kauce bayan ya jimke a wayar a hannunsa yana sauke numfashi, Dariya na gefensa ya saka kafin yace"Yarinyar nan na bala'in ji da kai, tana kulawa dakai kai kuma ga shi ban ga kana kula da ita ba"
"Tahir..."
Muryansa cikin Kaushi da asset din Zamfaranci acikinta ta katse Tahir da ke masa Tsiya. Rai ya bata kafin yace'Tahir me? Ba gaskiya na Fad'a ba. Ina fa lura da kai tun satin nan ta ke kiran ka da wayar Umma ba ka Dauka"
Mirmishi ya saki kafin ya juyo suna kallon juna. Fuskarsa Ma'abociyar Haiba da zati ta bayyana, Baki ne mai ruwan kalan haske doguwar Fuska garesa Dauke da Dogon Hanci da idanuwansa matsaikata. Yana da Zagayyen Saje da gemunsa baki Suluf Cikin Yanayin Mganarsa ta cikakkun maza yace"Au ashe? wa ya saka ka aiki a kaina?
Tahir yace"Sai an sakani? Kasan dai tare muke kwana nasan komai da ya Danganceka"
Kai ya jinjina masa kafin yace"Ka sani mana Tunda ka na sakamin Ido"
Ya fad'a yana hararansa Dariya ya yi lokaci d'aya ya Dafa kafad'ansa yana Fad'in"Na gaida Magajin gida"
Wani mugun kallo ya yi masa. Da yasa da Sauri ya Daga Hannunsa sama yana Fadin"Afuwan. SADIQ.. "
Kokarin maida hannunsa ya ke saman kafad'arsa ya yi saurin tureshi ya wuce gaba. Da gudu ya bi bayan shi yana Dariya. Duk da ya so kada Tahir ya yi masa shakiyancin Dafe nan sai da ya Dafa shi suna tafe suna Rangaji kamar wasu yara.
Suna tafe zuwa bakin Titi Tahir ya kallesu ganin Sadiq s ya fisa tsawo shi kansa wajen kafad'arsa ya ke. Yasa ya ce"Tabdijam. Gaskiya ka na da Tsawo kamar wani Samudu"
Kai tsaye Sadiq yace"Shi ne.."
Tahir ya yi shegiyar Dariyan sa da Sadiq ya tsana kafin yace"Kai ma ka sani kenan?
Kallon juna suka yi kafin Sadiq ya jinjina kai yana Fad'in"Ina maka Fatan samun lafiya Tahir yusuf Daura"
Tahir na Danne Dariyansa yace"Ba ni lafiya ne? Sadiq ya gyada masa kai kafin yace"Eh mana. ai ciwon ka ba shi da mgani saboda Dariya soso min Hauka ne"
Tahir ya dauke Dariyan sa ya na kallon Sadiq shi ko ya sha Mur ko kara kallon su bai yi ba,Tahir ya daga kafa ya bisa ganin ya yi gaba ya barshi sai da ya bari sun jera sannan yace"Nasan mganin ka. Innani zan gayamawa abunda kace a kaina. wato ina Hauka ko Sadiq?
Mirmishi ya saki mai tsada ammh bai yi mgana ba. Tahir ne ya cigaba da zuba mganarsa yana jinsa ammh ba kowacce mgana ya ke bashi amsa ba. Duk da shi ba miskili ba ne ammh mganarsa Ra'ayi ce akwai Lokacin da Ra'ayin hakan baya zuwa masa.
Suna tafe in sun ga gungun matasa Sadiq zai daga musu hannu ya yi musu sallama, in Dattijai ne kuma ya gaishe su da kwana bayan ya yi musu sallama. Tahir ma dolensa ya ke yi Tunda yasan Halin Sadiq suna yin gaba zai fara masa wa'azin yad'a sallama a tsakanin Mutane na tsaye ya gaida na zaune har ya Haddace wannan Mganar.
Suna tafe Rai rai har bakin Titi suna zuwa Tahir yaga Sadiq na kokarin sama musu adaidaita, da Sauri Tahir yace"Mu hau mashin mana. mun makara fa."
Ya fad'a yana kara Duba agogon Hannunsa Tara saura. Bai tanka sa ba sai da ya tsare musu adaidaita sannan ya kallesa lokaci d'aya yana Fadin"A daidaita zamu hau Tahir"
Tahir ya bata rai kafin yace"Haba don Allah. Kamar wasu mata? Mu hau mashin mana Sadiq"
Sadiq ya ja sa yana Fad'in"Adaidaita nace zamu shiga Tahir. Kuma da ka ke mganar Mata daman kai namiji ne?
Yana mgana ya na Tura Tahir cikin adaidaita shima ya bi bayansa lokaci d'aya yana fadin"Ni kwangila za ka sauke ni. Shi kuma"
"Pizzet zan sauka mallam"
Tahir ya katse shi da Sauri yana kunkuni,;Sadiq sai da ya yi dariya kafin yace"Mallam mu je"
Mai adaidaita yaja suka Fara tafiya Tahir ya sha kuni, yaki mgana ballatana Dariya sai ma ya fiddo wayarsa yana Famam dannawa shi kuma Sadiq na kallon Hanya.
Sun kawo Bakin ABU aka tsaida shi wata mace ta shiga. Tahir ya matsa kusa da Sadiq ya na Hararansa cikin kunkuni ya yi tsaki. Sadiq na jinsa bai yi mgana ba yana dai ta mirmishi kafin su isa in da Sadiq zai sauka an dauka an ijiye yafi sau biyar Ran Tahir ya baci sai masifa ya ke wai yana Duba agogo wai ya makara Saboda Sadiq ya tankasa su yi tsiyar a hanya sai kuma bai kulasa ba har ya sauka, ana sauke shi ya ba da kudin gabadaya bayan ya fito da Wallet dinsa. Ta baya ya dawo ya Dafa kafadan Tahir ya na Fad'in"Abokina sai mun had'u ko?
Da Sauri Tahir ya fizge kafad'ansa yana Fad'in"Mu je don Allah mutane sun makara ka tsaya kana ta share share a kan hanya."
Mai adaidaita ya tada Napep dinsa yana fadin'"Bawan Allah adaidaita ta haya ce in da baka san share share sai ka dauki Drop. Kare da kud'insa ya sha lahaula.".
Sadiq sai da ya yi dariya har Fararan Hakoran sa suka bayyana a waje. Daganan titi ya tsallaka zuwa Ofishin Road Safety. Chan ya ke C.D.S. dinsa shi kuma Tahir Fada zai je a secateria za su had'u da yan team din su dagachan zasu wuce in da suke na su C.D.S. d'insu kuma rana d'aya su ke yi duk Ranar Talata.
Sai bayan La'asar ya baro wajen yunwa ya ke ji,cikinsa har wani kara ya ke yi, Yau furan da ya ke siya ya sha ya siya yaji nonon da karni ya kyutar da shi. Matar da ta ke kawo nonon bafullatana ne to ba ta zo ba yau sai wata ce ta kawo kamar Nononta ba pure ba wani iri ya yi masa baki da ya bata masa Yanayin bakinsa.
Ba shi da matsalan siyan duk abunda ya gani yaji yana sha'awa. Bayan nan ya siyi zogala aka kwad'an ta masa shima yaji Bakinsa ba Dad'i ya kira almajiri ya ba shi. Sai rogo da gyada ne ya siya bayan ya kamo hanya. In dai ya zo ranar shi ya ke ba da sallar Azahar da La'asar a wajen in bai zo ba kuma wanda ya saba jan su sallah sai ya ba su.
Adaidaita ya sake tara har samaru ya kuma gangaro da kafarsa har inda suka kama domin zaman bautar kasar su a garin Zariya. Yasan Tahir ya dawo tunda yasan ba sa Dad'ewa. Tura Dakin ya yi yaji a rufe bai damu ba ya na da key a hannunsa. Kuma yasan ya rufe ne ta ciki tunda aka taba musu sata suke kulle dakin su ko da suna ciki. Ya na ko budewa sai ga shi ya shiga yaga Tahir kwance share share akan katifa kamar ya mutu daga shi sai gajerun wando, ga kayan da ya cire nan watse a kasa takalminsa har da agogo jakarsa ga wata bakar leda nan a kasa itama ana ta muhallin.
Sadiq yq bi sa da kallon Takaici. Tsallake kayan ya yi zuwa chan kurya ya zauna gefen katifar,Tahir cikin barci ya mulmula ya maka ma Sadiq kafarsa, shi ko cikin fusata ya juyo ya Hauresa da Kafarsa shima bayan ya mike. Tahir ya kara juyawa zai koma Barci Sadiq ya sa takalminsa ya taka masa kafa yana Fad'in"Dilla ta shi mallam. Yanzu haka ko sallah baka yi ba ka kwanta kamar wani gawa"
Tahir ya bude ido dishi dishi yana kallon Sadiq kafin ya yi mika ya mike zaune tare da Hamma haaaaa..!
Sadiq ya ji haushi cikin kufuluwa yace"Ka tashi daga barci ba Salati ba kiran sunan Allah. Sannan ka yi hamma ba Alhamdulillah ka bud'e baki kamar wani sakarai yanzu ko yara sun san in sun tashi daga barci su kira sunan Allah. Sannan sun san in sun yi Hamma su Rufe baki"
Tahir ya bisa da kallo da Shanyayyun idanuwansa da alamun barci bai ishe shi ba.
Sadiq ya shure kayansa da kafarsa yana Fad'in"Kai dai mugun kazami ne Tahir. Miye haka?
Tahir ya mike yana mika lokaci d'aya yana Fadin"Kar ka isheni fa. Na dawo a gajiya me ka ke tunanin zan iya tsinana ma kaina?
Sadiq ya kalli Tahir cikin takaici ya ma kasa mgana illah kad'a kai kawai da ya yi yana fad'in"Biyar saura ka je ka yi sallah Mallam"
Ba musu Tahir ya ja wandonsa ya zura ya saka wata karamar riga da ya Dauko saman akwatinsa,:sannan ya fice Daga Dakin bayan ya zuba ruwa a buta .
Sadiq ya bishi da kallon Haushi. Ba ya iya zama da kaya a watse a daki shi Mutum ne da ke son kimtsi. Karshenta shi ya kare da tattara ma Tahir kayansa ya ninke masa ya Bude akwatinsa ya saka masa. Sannan ya fito masa da karamin wando da Riga na shan iska. Yasan waye Tahir da Hauka wajen dauko kaya sai ya kara watsar da wasu kayan kuma bazai maida ba ko ya yi mgana kunnen uwar shegu ya ke yi da shi. Bakinsa har tsini ya ke yi saboda mgana ammh in dai akan Tahir ne a banza ne.
Shima kayan jikinsa ya cire ya shanyasu saman Hanger saboda su sha iska, Akwatina uku ne a Dakin Biyu na Sadiq d'aya na Tahir ne shima karamin ciki ya Bud'e ya Dauko Jallabiya ya saka Mai ruwan kasa. Ya zura ya kuma kai komai nasa a muhallinsa Dakin Tsaf kamar na mata,komai yana muhallinsa.
Gefe katifarsu ce Babba na kwanciya Sai wajen kayansu, Kayan kwalliya na maza sannan sai wani Dirowa kasa kuma inda suke jera takalmansu. Daga gefe kuma Gas din girki. Sai kayan abinci da kayan girki. Sai botikan wanka guda Biyu sai babban roba in da suke Tara Ruwa. Daga kusurwa kuma ga karamin Fridge din su tunda suna zuwa da miya ko wani abun da zai lalace shiyasa suke da Fridge din.
Kafin Tahir ya shigo har ya gyara gadon ya share Dakin. Sai da ya gama Hiran sa da Matasan da ke gefen dakinsu suna waje suna wanki sannan ya shigo ya ta da Sallah.
Sadiq na zaune a gefe yana kallon shi har ya Idar ya mike yana ninnike Darduman Lokaci d'aya yana fad'in"Sultana dai ta huta in dai ta bangaran gyaran Daki ne"
Yana jinsa ya yi masa banza sai ma ya jaho Ledan Rogonsa ya Dauko ya Bude ya fara ci. Gefensa Tahir ya zauna yana leka ledan gabansa kafin yace"me ka ke ci ne?Rogo da aya?
Tab! A ci lafiya"
Tashi ya yi ya bude fridge ya Dauko bakin Coke dinsa guda d'aya da ya siyo da zai dawo ya saka a Fridge ne Tunaninsa za'a kawo wuta kuma yau suna jin Halin na su.
Gefen Sadiq ya kara komawa ya zauna ya jawo ledansa da Sadiq ya ijiye masa nan gefen Littafansa tunda kowa bangaran da yake kwanciya yana ajiyan littafansa masu muhimmanci.
Cake ne babba aciki ya fito da shi yana ci yana korawa da lemu gefe d'aya kuma yana Faman chart ta wayarsa.
Sadiq bai ci rogon da yawa ba yaji ya Chusemai ciki sai kawai ya Ture ya kalli Tahir yana fad'in"Ka ci."
Tahir yace"A'a Arammah kai dai kaci ni nagode"
Sadiq ya yamutsa Fuska kafin yace"Ya cushemin ciki ne."
Tahir ya kallesa a karkace kafin yace"Ka ma ci sa'a a irin yameyamen da ka ke yi ma cikinka baka fara ciwon Tsakuwar ciki ba"
Sadiq ya kallesa kafin yace'"Fatan da ka ke yi min kenan?
Tahir ya Daga lemun hannunsa da Cake yana fad'in"Afuwan"
Daganan ya cigaba da shan lemunsa yana had'awa da Cake
Status ya ke kallo an saka wakar Turanci har yana bi. Sadiq ya koma ya kishingid'a yana Fad'in"Ka dafa mana abinci"
Tahir ya yi masa banza sai da ya kara maimaitawa sannan yace"Wani abinci kuma? Baka ci rogon ka ba. Ni kuma kaga iya wannan ni da wani abu sai gobe in muna raye"
Sadiq ya yi kasake yana kallonsa yasan rashin Mutumcin Tahir saboda yasan girki na da D'aya daga cikin abunda ke ba shi Wahala baya ma kwantatanwa Tahir din ke musu abinci.
Shiyasa wani Lokacin bai juran wulankancin Tahir ya ke fita ya samu wani abu yaci. Tahir kuma kamar da gayya sai yaga Dama ya ke d'ora abinci ko ya yi ta abubuwa ya na bata Lokacin barin ma in yaga ya yi mgana ko ya Lura yana jin yunwa.
Yadda ya Fahimci Tahir ya so ya wulakanta ne yasa ya mike ya saka Dogon wando ya Dauki kudi cikin Wallet dinsa ya fice. Yana ji Tahir na Fad'in"Me zamu Dafa?
Ko amsa shi bai yi ba ya zura Takalminsa masu taushi ya fita,Sallama ya yi ma matasan da ke waje yan makaranta ne su. Ganganrawa ya yi cikin Layin Tsamiya in da yake siyan awara. Yaje da kansa ya siyo aka saka masa yaji da kabeji har da albasa Dabam sun san shi Custumer din su ne Sosai Sadiq yasan muhimmancin awara. Sadiq ba bu abunda ba ya ci shi mutum ne kamar Social kamar kuma ba Social ba. Rayuwarsa Sannu sannu ya ke binta yadda ya Dauki al'amuransa sai ya baka mamaki a irin matsayinsa na Rayuwa. Ababen duniya masu dadi da kawatuwa ba su dameshi ba ya fi son na Mutanen da suka Dauki Rayuwa a sannu.
Duk wani abu na gargajiya Sadiq na Cinsa su ne cimarsa ma tun zamanin suna Hostel a Cikin Abu zariya. Tunda daga shi Tahir nan suka samu Shedar Degree din su na Farko. Ko da ya koma Daki Tahir na zaune in da ya barshi da waya a hannunsa ammh ya gama shan lemunsa da Cake dinsa ya kuma watsar da ledojar da goran anan bai kwashe ba. Ko mgana Sadiq bai masa ba ya tattara dattin ya fita waje ya watsa cikin Abun shara.
Yazo ya Dauko Filet karami ya juye awaransa da yajinsa tana tashin Tiriri ya samu gefe ya shimfid'a Darduma ya zauna. Daman ya wanko Hannunsa da ya fita waje ya yi bismillah ya fara cin awaransa Hankalinsa kwance.
Tahir na kallonsa Jefi Jefi shuru dakin ya Dauka na wasu mintina kafin Tahir ya kauda shurun da cewa"Jb na gaisheka."
Sadiq ya jinjina kai bai yi mgana ba sai da ya cinye awaran bakinsa. Sannan yace"kun had'u ne?
Tahir ya ce"A ina? a Chart muka yi mgana da shi."
Daganan Sadiq bai kara magana ba sai da Yaji cikinsa ya kusa cika, sannan ya mike ya isa ga Fridge ya Bude ya Dauko Ruwan gora guda d'aya yana juyowa yaga Tahir gaban a waransa ya Dauka yana Fad'in"A ina ka siya awaran nan? Allah ya sa ba wajen kazaman masu awaran nan na bakin Titi ba ne?
Sadiq ya tsaya kyam yana kallon Tahir bai samu masa mgana ba illah ya Duka ya ja Filet din awaransa yana Fad'in"Ko ma nan ne ina ruwan ka?
Baka ce ka koshi ba?
Tahir yace"kamshinta ne ya yi min Dadi. Mu ji Allah ya sa da Dad'i"
Sadiq ya Daure fuska kafin yace"Kasan Allah? Bazaka ci ba."
Tahir ya yi dariya ya tura na Hannunsa baki ya tauna yana lumshe ido Kafin yace"Kai..Wow. da'di k'aramin don Allah"
Sadiq ya ce" ka fita ka siya in ka matsu"
Tahir yace"Ga shi ka siyo mana. kasan Allah? Nima sai na ci"
Tahir ya mike Sadiq ya mike suka Fara kokuwan awara Tahir na sai ya ce Sadiq na bazai ci ba.
Suka Fara Zagayen Dakin da gudu Tahir na Bin Sadiq a baya. Daman so ya ke ya gajiyar da Sadiq din ya yi fushi ya ba shi awaran ahakan ce ta Faru daga karshe ya dungura masa Filet din yana Fadin"Tahir.."
Da Sauri Tahir ya katse shi da Fadin'"Nagode Abubakar Sadiq Sulaiman Shinkafi."
Karamin tsaki yaja ya koma saman katifa ya kwanta ya juya ma Tahir baya. Yana jinsa yana Fad'in"Awaran nan ta yi dadi a ina ka siya hala?
Yasan bazai tankasa ba shiyasa yace" ina Tunanin me yasa aka haife ka a zamfara ba'a shinkafi ba? Kafi dacewa da gayun kauyen nan abokina."
Da Sauri Sadiq ya juyo yana Fuskantar Tahir cikin mirmishi yace"Da Sauki tunda ba'a Daura za'a Haifeni ba."
Tahir ya fashe da Shegiyar Dariyarsa. Sai kuma me? Kawai sai ya shake ya fara Tari Sadiq ya yi kwafa kafin yace"Tahir Allah ya kara"
Tahir idanuwansa Jajir ya Dago yana Fadin"Ruwa Sadiq. Ruwa.."
Sai da yaga Tahir ya ji jiki sannan ya mike ya Dauko masa ruwa ya mika masa ya bude ya kwankwad'a kusan Rabi, sannan ya koma ya kwanta a kasan cafet din dakin yana maida Nunfashi cikin azaba. Shakewar yaji ba ta da kyau ko kadan Tahir har ya Fita Hayyacinsa
Yana jin Mirmishin Sadiq yana Fad'in"Nan gaba ka koyi ladabin cin abin Tahir."
A wahale Tahir ya ce"To ya Alarramma Abubakar Sadiq."
Sadiq yace"Ba gatse ba ne Sunana kenan"
*******
Yanzu kam ba abunda zance ma Allah sai godiya, Rayuwa ta yi mana kyau da inganci, Ciniki mu ke yi sosai na kan sana'o'in mu, musamman ma Danwake na Safen nan shinkafa da wake ne cinikin sai a hankali.
Sai muka dawo da yin Danwake tare da Daffafen wake, Sai man kuli da manja duk wanda ka ke so a saka maka.
Matasa sun gane ma Danwaken da yan makaranta sosai a ke siya. Ayyukan sai suka maidani mai yawan Aiki ya kasance na kan jima ban Tuna Tarin kaddarorin Rayuwata ba. naa kan manta cewa Rayuwata ta na cikin Tsaka mai wuya ne.
Amma jikinta ya yi kyau bata kara ko Zazzabi ba, ni ne karfin duka ayyukan Habiba Saboda makaranta, Sai dai ta na taimakamin in tana gida sannan ita kan Shiga kasuwa in bukatar haka ta taso, duk da ina Fita ammh ba kasafai ba na tsame kaina da shiga Cikin mutane saboda Gudun gori da Habaici.
Ko acikin gidanmu ban tsira ba haka ko yan'uwan su suka zo a fito ana nuna ni ana mgana kasa kasa. To menene sabo a abunda suke Fad'a kaina duk abunda zasu fad'a an riga su Fad'an sa.
Yau ni kadai ke ta aikace aikace ne, Habiba bata nan tana gidan Adda Fati tun jiya. Ita ta kira tace Habiban ta zo bata jin dadi suna ta Fama da zazabi ita da yara.
Sau tari Mutanan gidanmu na yawan Fad'in ina ba su mamaki. a yanayin jikina kamar bazan yi kuzari ba ammh kuma ni macece mai zafin Nama ko aiki ne mai wuyan Ban fara ba, da na fara shikenan cikin Lokaci kad'an zan gama shi. Amma ta na yawan fad'amin cewa yanayina yanayin Adda Hari ce itama mace ce mai zafin Nama da komai cikin Hanzari da Kazar kazar.
Sai goma na Safe na gama Saka Danwake kuma ya kare duka bayan na gama ana ta aikowa na ce babu,Bayan na gama kankanta abubuwan da na bata na kawowa Daki na kawo na wankewa na wanke,Sannan na shiga daki na samu Amma na Sallar Walha.
Zama nayi gefen katifarta na Bude kwanon shan da ke cike da koko, ni da Dama mata da Safe, na saka karamin kofin da ta gama sha na zuba na koma gefe ina sha tas na shanye tunda ba tsami bazai min matsala ba.
Daidai Lokacin Amma ta Idar da addu'anta ta Dago tana kallona kafin tace"Ki kara mana in bai isheki ba"
Kai na girgiza mata kafin nace"ya isheni Amma kwarnafi na ke gudu. Don ma naji ba shi da Tsami ne na sha da yawa"
Amma ta jinjina kai kafin tace"To ai baki ci komai ba Hasiya?
Cikin Tabbatarwa nace"Na ci wake da mai da yaji Amma"
Amma ta kuramin ido kafin tace"Kin tabbatar? Kin san kina da lulura kuma ki rika wasa da cikin ki"
Dariya na yi kafin nace"Amma kada ki damu a koshe na ke"
Bata kara mgana ba ta fara jan Casbahan da ke hannunta ni kuma na isa ga jakar da nake tara kudin ciniki na Dauko na zube su a tsakar Dakin ina Kirgawa bakina har kunne na ce ma Amma Danwaken ana samu da shi Sosai.
Amma ta gyada kai kafin tace"Sai mu godema Allah"
Sai da na gama kirga kudin na ware na wanda za'a je kasuwa ina cewa"Amma garin Danwaken mu ya kare ga Habi bata nan"
Amma tace"Ki je da kanki mana. Tunda baki da tabbacin yau zata dawo kada ki jirata kuma gobe babu garin a hannu."
Da shawaran Amma na yi amfani sai da nayi wanka sannan na yi shirin Fita. Tunda Amma tace sai anjuma zatayi wanka ni na fara yi tunda fita zan yi, Hijabina na saka har kasa akwai Nikab na Habiba ne shi na ara na saka bana son a samu wata matsala ne.
Amma na gefe tana kallona har na Soke yar wata jaka mai igiya ta Habiba ce na ara saboda saka kudi nayi ma Amma sallama tayi min fatan Dawowa lafiya na fita.
A tsakar gida na ci karo da Maman Boy da maman salihi nasan sun yi da ni Saboda naga suna nunani da baki ban damu ba na fice ina Fad'in"Zan shiga kasuwa"
Da Sauri Maman Boy ta mike tana Fadin"Tsaya Hasiya. Daman ina son Citta da kunafari nawa sun kare"
Dole na Tsaya,Ammh Maman boy sai da tayi min taron mutane sako wajen na mata biyar suka hadamin ga shi kuci kuci hakanan na karb'a bani da Mafita.
Har na kai bakin Titi ba bu wanda yaa ganeni bakina alaikum na shiga kasuwa wajen masu had'a garin Danwake naje na fad'i iya adadin za'a hadamin sai na shiga cikin kasuwa na siyo wayan murhu da gawayi.
Sai na siyo wake da mangyad'a da Borkonu sai kayan maggi
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 7 Chapter of 24