musu fa?
Sadiq yace"Ba karya na yi ba ni asalina dan Shinkafi ne tunda nan ne Tushena. Su Umma kuma ban san Dalili ba kai ma kasan ba kowa ya ke sanin hakikanin waye ni ba."
Daga haka ya wuce Tahir ya rike kugu ya na bin bayansa da kallo cikin mamaki. Haka kurun ya ke ji aransa Wani abu zai faru wanda ba Daidai ne ba shi fa mutanen ba su yi masa ba. Wasu kamar yan gudun Hijira ita kuma yarinya farinta ne baya so kamar wata Zabiya.
Bayansa ya bi ammh ba su kara tada mganar ba. Mashin suka samu zuwa gida kuma har suka kwanta Tahir bai kara yi ma Sadiq mgana ba sai dai ya na kallonsa ya na nazarinsa.
Yana fatan Allah yasa ba garin taimako Sadiq zai jajbo ma kansa Wahala ba.
Washegari kafin Sadiq ya tafi wajen aiki yaji yana jin cin Danwake kamar yadda aka saba da kansa yaje da karamar kularsa. Da datti ya ci karo tun kafin ya kirasa yazo da Sauri ya na Fad'in"Danwake zaka siya?
Ya gyada masa kai da Sauri Datti yace"Ba'a yi mai Danwaken mamanta ba ta da lafiya. Suna asibiti har yanzu ba su dawo ba."
Shuru ya yi ya na nazari kafin ya yi mirmishi ya Dafa kan Datti naira Dari ya zaro daga Aljihunsa ya bashi ya tafi ya na tsallen Murna.
Bai damu ba har ya juya zai tafi sai mganar yaron ta kara Dawo masa sai ya tsaya bayan ya juyo ya na kare ma gidan kallo kamar gidan kamar kuma ba nan ba ne.!
Domin kore mamaki ya ga Salihi na gara taya zai shiga gidan sai ya kwala masa kira sannan ya fitosa da Hannunsa. Saninsa ya na ba da kudi yasa Salihi ya zo da Sauri bakinsa washe yace"Ba'a Danwake yau."
Da Sauri yace"Na sani. Y
ya sunan mai yin danwaken?
Salihi yace"Adda Hasiya."
Sadiq ya maimaita"Hasiya."
Salihi yace"Eh mamanta ba ta da lafiya suna asibitin in ji mamanmu."
Sadiq ya cika da mamaki sai dai bai bari Salihi ya tafi haka ba shima darin ya ba shi ya tafi ya na ta murna.
Sadiq na tafiya a hanya ya na Mirmishi har da Dariya shi kad'ai.
"Hasiya mai danwake."
Tabdijam.
Daga alamunsu daman ba su da Hali Talakawa ne. Ammh ina mahaifin su? Me ya asalin su? Duk wad'anan amasoshin ba shi da mai amsa masa shi.
Ammh har ya koma dakin su yana Dariyan sunan Hasiya da ya maida mata da Hasiya mai Danwake.
*******
Sai da Amma tayi sati Cur sannan aka sallameta Lokacin ta samu sauki sosai ta na zuwa bayi da kanta. Sannan ta sallolinta a Tsaye ta samu karfin jiki.
Ba bu abunda zan ce ma Abubakar sai Godiya. Domin komai na laluran asibitin nan shi ya yi mana shi hatta kudin gado da sauran magungunan da aka sake rubutama Amma shi ya siya.
Sannan ya samo mana adaidaita ta Dauke damu da kayanmu har gida shi kuma yabi bayanmu a kan Babur.
Da farko ya ki shiga ciki sai da na matsa sannan ya shiga har daki ya Duka ya kara gaida Amma.
Amma ta rike hannuwansa ta na fadin"D'an nan ina ka samu kudade da ka yi ta mana wannan Hidimar?.
Kai tsaye yace"Amma ba na gaya miki ina Hidimar kasa ba? To ai gwammati na ba mu wasu kudi duk karshen wata."
Ina zai gayamusu Abba ne komai na shi tunda ya riga yace ba shi da iyaye shi maraya ne.
Amma ta shiga kwarara add'au tana ma iyayensa da suka rasu addu'a da samun salama.
Har sai da ta yi hawaye ganin haka yasa ya ce"Amma bakomai. Ki daina kuka."
Dole Amma ta yi shuru ta na ta saka masa albarka.
Da zai tafi ni na rakasa ina ganin Matan gidanmu kallo kamar zasu fad'i.
Sai da muka fito ya kalleni ya na Fad'in"Gidan ku kuna da yawa haka ne?
Kai tsaye nace"Gidan haya ne .mata goma sha uku ne aciki, Dogon gida kenan."
Sadiq ya jinjina kai kafin yace"Dogon gida kad'ai ake kiransa?
Na gyada masa kai ina fad'in"Eh."
Kai Tsaye ya na kallo na yace"ba'a cewa gidan su Hasiya mai Danwake."
Zaro ido na yi ina kallonsa shi kuma yana Dariya yace"Amma ta ji sauki a cigaba da yi ma na Danwaken mu"
Cikin mamaki nace"Ya aka yi kasan ina Danwake?
Kai Tsaye yace"Ina siya ne."
Cikin kura masa ido nace"Ka na siya?
Kai ya gyad'amin ya na mirmishi.
Kamar an tunamin na nuna sa ya na Fad'in"Kai ne daman me zuwa da kula da Dubu daya har ka ke barin min chanji."
Bai amsani ba sai da ya yi mirmishi da yasa na gane shi ne. Kallonsa na ke yi nima cikin jin dad'in kafin nace"ka ci sunan ka. Masu suna Abubakar Sadiq ma su tausayi ne da yakana ma su jinkai ne da Taimako."
Na fad'a kai na Tsaye ina kallonsa Idanuwana suna faman cika da kwallah da tuna wani bangare na Rayuwata.
Shi kuma sai ya tsaya ya na mamakin mganata cikin sigar tambaya yace"Kin san wani mai irin sunana ne?
Kai na gyad'a masa ina fadin"Sosai ma kuwa. Shima kamar ka ya ke ga Kirki ga Tausayi Fara'a sanin ya kamata yakana jin kai da Dattako. Duka ya na da shi shima."
Na fad'a hawaye sun cikamin kwarmin idanuwana ina son Abubakar ammh kaddara ta rabani da shi.
Kai tsaye yace"Saurayin ki ne?
Sai lokacin na dawo Tunanina da Sauri nace"A'a.."
Na kauda fuskata ganin yasa bai tsawaita mganar ba. Ya yi min sallama zai tafi nima kuma daman na kosa na koma gida an fara wucewa ana kallon mu.
Kuma nasan mamakin ganina da wani ake yi wasu har suna yi ma Abubakar kallon Tausayi.
Sun zata Saurayina ne.
Ko da na koma gida sai kuzarina ya Ragu bayi na shiga na ci kuka na kamar bazan daina. Ina kewar Abubakar kewa mai yawa sai dai ina yi masa Fatan alheri a duk inda ya samu kansa.
Tunda har Sadiq na son Danwake yasa na gayama Amma zan cigaba Saboda shi. Amma tace ko shi kad'ai sai a rika yi masa ya na zuwa ya karb'a ya Chanchanta.
Washegari kad'an na yi namu na gida da na shi ina ta Allah Allah yazo to bai dawo ba sai bayan kwana Biyu ya zo Duba Amma.
Amma da kanta ta fad'a masa na yi masa Danwake shekaranjiya bai zo ba.
Cikin natsuwarsa yace"wani uzuri ne ya hanani zuwa Amma."
Ni kuma da na fita rakashi da yi masa godiyan ruwa da maltina da kayan marmarin da ya kawo ma Amma sai yace kada na kara wahalar da kaina.
Na cigaba sa sana'ata in yana so zai aiko a siya mishi.
Lura da na yi bayason gaddama yasa na amsa masa da Toh.
Habiba na Tura kasuwa ta yi mana Cefane tunda da Adda Rukkaya ta zo gida kara Duba Amma dubu biyar ta bani Adda Fati kuma ta kawo mana kayan abimci. to da su na had'a aka siyo kayan Danwake.
Amma na da kwana biyar da Dawowa gida na cigaba da sana'armu ta Danwake ranar farko da ya aiko sai nace a maida masa da kudinsa. Ya ki karba yace a dawomin da shi sai na saka Hijabi na fita da kaina nace masa don Allah ya bar kudinsa.
Kai tsaye yace"Hasiya duk sanda zan aiko siyan danwake ki karbi kudi nace."
Yadda ya yi mganar ne yasa ban isa na yi gaddama ba a muryansa ya na da wani abun da in ya ce abu baka iya masa gaddama.
Ya rage yawan shigowa Duba Amma bai wuce a sati sau daya ba.
Sai dai in ya aiko siyan Danwake sai yace"a gaida masa Hasiya mai Danwake"
In ko bai aiko ba ranar haka zan wuni cewa ma Amma''Yau fa bai zo ba Amma ko lafiya?
Sai Amma tace ya na lafiya kila wani abu ne ya tsaidasa.
Ina jinsa a raina kamar wani yayana Ban ko iya kiran sunansa sai dai nace shi.
Habiba ko Hamma ta ke kiransa Sosai muka saba da shi.
Matan gidanmu har sun fara Tsegumi tunda Kaltume har tareni tayi da tambayan shine Sabon Surukin na su?.
Kai Tsaye nace mata"A'a wannan Dan'uwan mu ne"
Daganan na kashe bakin munafukai ammh nasan ana nan ana lura da ni ana jiran aji wata mgana ne a tare shi da Labarina.
Bai taba tambayanta komai game dani ba, sai dai ya taba cewa"ina baban ku? Nace masa ya rasu da Dadewa."
Sai yace"ina dangin mahaifin na ku?
Sai nace masa suna nan. Daganan bai kara min wata tambaya ba, sai dai suna Hira da Amma har sunan gidanmu ta fad'a masa na Anguwan Kona.
Sannan in suna Hira ta kan fad'a masa ita bafullatanan Gadan mallam mamman ce, aure ya kawota zariya.
Sannan mu mun dauka da gaske Abubakar maraya ne ba shi da kowa.
Ina jin dadi in nagansa ya zo ina jinsa kusa da zuciyata.
Ban san me yasa na Damu da shi Fiye da kaina ba.
Bansan wata irin kaddara ce ke shinshina a tare da Mutumin da ban Dade'da sanin sa ba.
Kaddarace mai girma Hasiya.
Girman kaddaran da zata iya sanadiyar shigan ku Tsaka mai wuya.
.*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
Albishirinku ya yan'uwana An-Nisa! Ina wacce ta dade tana amfani da Sabaya amma bata ganin aikinsa duk kuwa irin shan da take masa ? To share hawayenki tamu Sabayar ingantacce ne wanda muka sake bakin aljihu muka zuzzuba kayan gyaran jiki wanda bana cutarwa ba infact shi wannan hadin 2 in 1 ne…. Hadin SABAAYA da ADUMULMULA, in kina fama da matsalar zubewar Nono to wannan had'i naki ne, in kinaso ki cicciko fatarki tayi kyau ki koma tamkar ‘yar yarinya to ki riki wannan hadi namu… Aikinsa bai tsaya iya nan ba hatta da kara lafiyar garkuwar jiki yanayi da kuma kara ni'ima…kowa na iya shansa, matan aure, Masu shayarwa in kin kusa yaye, 'yan mata, babba da yaro, maza da mata kowa na iya amfani da wannan hadi namu…. Muna maraba da mai siyan daya ko sari.
Abangare guda kuma muna had'a magani ingantacce na ciwon sanyi da yaki jin magani, in aka daure ana amfani dashi ana dacewa bi'izinillahi ta'ala, kai hatta da maganin hawan jini da diabetes duk muna saidawa kuma ana dacewa in sha Allah.
Atuntubemu tanan whatsApp or call 📞 07065481260.. Don Allah don annabi in kin san ba siya zakiyi ba kar kizo ki bata mana lokaci da tambayoyi please kayayyakinmu original 💯ne babu algus
*Janafty*
*TSAKA MAI WUYA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
_Masu bukatar a tallata musu Hajojojinsu cikin Farashi Saukakakke 09069067488_
*16*
*GUSAU.*
Dakyar Innani ta bari Sultana ta yi sati daya a gidan mahaifinta tare da yan'uwanta.
Dafe ta yi ta kasa ta tsare yarinya taje domin ganawa da mahaifinta sannan ta samu zama da yan'uwanta, Ammh innani ba ta bari ba, ta na tare da Sultana kafa kafa kamar wacce za'a yi ma wani abun cutarwa.
Daga matan har shi kan shi Shitun ba su da mafita sun fi kowa sanin Halin Innani don ta fito ta tara su ta tsine musu to abu ba ne da zai zama mai wahala awajenta ba.
Hakanan suka rika Hakuri da ita ammh abu kad'an sai ta yi Allah ya isa akan Bakincikinsa da na matansa ya kashe mata Hauwa kulu akwai Hisabi Tsakaninsu Ranar gobe kiyama.
Sannan ta hana Shitu ya gana da yarsa da ya saka a ka kirata zai ga Innani tare da ita kafa kafa. Sai masifa ta ke yi ta na fad'in uban me zai kuma gayamata? Ba ta son iskanci da neman mgana da munafunci.
Dole Shitu ya kama kansa ya na ji ya na gani Sultana ta koma batare da mgana ta tsakanin Uba da yarsa ta shiga Tsakaninsu ba.
Sannan ranar da zasu koma Gusai Abba ya Turo Direba ya Dauke su Mallam Shitu iya karfinsa ya yi ma Innani da Sultana Hidima ammh sai Innani ta rika fad'in" Dama baka wahalar da kanka ba Shitu. komai da ka sani Sulaimanu na yi ma yarinyar nan babu abunda ta nema ta rasa, Sulaimanu da ka ke gani kudi garesa shiyasa ba mu rasa komai ba."
Ammh ta na jin kannen Sultana na fad'in zasu zo suyi mata Hutu wani Lokacin in suka samu Hutun makaranta karaf Innani ko tace"A'a ku yi zaman ku, wannan ai dora ma mai kokari wahala ne. wato kun ji nace Sulaimanu na da kudi shine za'a zo kwada'yi ko? To shima ba shi da komai Rufin asirin Allah ne ina ma laifi an Dauke muku wani Laluran? Wannan yarinyar Sulsana ko bante ubanku bai taba siya mata ba Sulaimanu ne da Salamatu. Allah dai ya biya su da Aljannah"
Shitu da Matansa da suka amsa da Ameen Innani dai ta rika masifan kada su so zl sulaimanu ba shi da komai sai Rufin asirin Allah.
Ammh tace su bari Bad'i in an tsaida lokacin bikin Magajin gida da Sulsana sai su zo.
Ba wanda yasan da labarin yanzu za'ayi auran Sadiq da Sultana ammh zuwan Innani Shinkafi labari ya bazu a kunnen kowa.
Har gidan su Baba Sammani da ta je duk haka ta rika ce musu bikin Magajin gida da Sulsana bad'i in sha Allahu. Shitu ma daki ta saka shi ta na fad'a mai cewa gwara ya fara Tanadi tun yanzu Sulaimanu dai ya yi masa na Allah ya yi masa na Annabi. In kuma ba na Shed'an ya ke jira ba sai ya nemi kudin aurar da yarsa Ina za su iya? Tunda shi Ubanta ya na raye? Daman ya mutu ne sai su Dauki na Musulunci su yi."
Shitu dai mamaki ya kamasa ya san da mganar auran Abubakar da Sultana ammh bai san da mganar nan kusa ba. Suna yawan mgana da Abubakar yaro ne mai hankali natsuwa da sanin yakamata wanda ko Alhaji Sulaiman ba su cika mgana da shi kamar yadda suke yawan mgana da Sadiq ba.
Ya na da tabbacin Innani ta zauna ta Tsara mganarta. Shiyasa a lokacin ya kalli Innani ya na fad'in"Ammah Innani Alhaji Ya fad'amin sai Sultana ta gama makaranta za'ayi bikin Lokacin shima Abubakar din ya gama karatunsa har ya kama aiki."
Ai sai Innani ta Zabga masa Dakuwa kafin tace"Allah ya tsine ma karatun albarka. Ka ji min ja'iran ci da lalacewa irin ta Shitu? A na mganar sunnar ma'aiki ka na mganar karatun Bokon tusa da tsiya? Maza ka yi istigifari domin ka yi sabo wajen Ubangiji."
Shitu dai ya ga abun mamaki ta wani bangaren kuma bai yi mamaki ba Tun kuluwa na raye sun sha zuwa Innani ta saka su a gaba ta yi masa wankan Tsarki. Wani lokacin tun Safe ta ke musu Dirar mikiya ka yi mgana ta tattara Tsinuwan bakinta a kanka shiyasa da yasan halinta sai yaci mganin zama da ita. Haka sauran matan masa ma tunda ba yau suka san Innani ba.
Haka suna mota da zasu koma Innani sai faman ciye ciye ta ke yi. ta na cewa su Hassu ba su da kirki sai ga shi ita ba ta kai musu komai ba ammh duk abunda suka bata sai da ta amsa. Aya ko ta yi tiya uku Wacce Innani ta zo da shi. Tsohuwar nan yar bala'i ce ba ta da hakora ammh sai Uban kwad'ayi da son abun duniya. Innani fa har goriba da rake ta ke sha, Wuka ta ke samu ta yi ta kankarewa ta na afawa a baki da hakoranta na Roba ta ke Taunawa.
Yanzu ma Aya ta ke ci sai faman mayau mayau ta ke da baki Direba ya fara Gudu Innani ta fara salati ta na Ihun ya rage gudu. Kuma ba fa gudu ya ke yi ba. Innani ta rika masifa har ta na kukan sai ta gayama Sulaimanu zai kashe masa uwa.
Sai Direba ya juyo ya na fad'in"Innani ba fa gudu na ke yi ba. a tamanin fa na ke tafiya."
Innani ta dake ta karfi tace"Allah ya Tsine ma maka kai da tamanin din. ni zaka raina ma wayau? In ni ba tsohuwar ka bace ka raina ni ai ka Daraja Furfuran tsohon ka ko?
Ya na jin haka bai kara mgana ba Sultana da ke ta kuka tun tahowarsa ta kallah cikin kufuluwa tace"Ke kuma kukan Uban me ki ke yi?
Sultana ta kalli Innani cikin Takaicinta kafin tace a hankali"Sati uku Fa Umma ta ce zan yi Innani.."
Innani sai ta saki baki ta na kallonta cikin mamaki kafin ta Dungure mata kai lokaci daya ta na fadin"Ta fi chan mara wayau ni gata na yi miki baki sani ba. Shitu da ki ke gani mugun bawa ne, da matan nan nasa ina barin ki cikin su sai kuma abunda Allah ya yi." Sai ta fara kuka ta na fad'in ke kad'ai kuluwa ta mutu ta barmin ta ina zan bari a nakasa min ke."
Bakinciki suka Hana Sultana mgana.
Ko da ta ke da kananun Shekaru ta san Ubanta ta kuma san yan'uwanta kuma ta na son su da kaunar su ba tun yau ba tasan Innani ba ta kaunar Abbanta ta sha zaginsa a gabanta tun bata damuwa har ta kai ga yanzu abun na yi mata ciwo.
Har suka iso Gusai Innani sai mugun Mgana ta ke fad'i akan Shitu har da tsohon Labarin aura auren da ya kara Saboda Kuluwa bata Haihu ba. Sultana kunnenta ta toshe ba ta son ji.
Saboda in dai Hadda ce ta rika gama haddace wad'anan Labaran.
Ko su kan su Umma sun sha mamakin ganin dawowarsu Sati d'aya kacal.
Da Umma ta yi mgana Innani ta harzuka tace"To uban me zamu tsaya yi!? Ina laifi ma an yi zumunci."
Daganan ta kama bakinta Mama ko tak bata ce ba Tunda taga yar gaban goshi Umma ta samu rabonta ta tabbata ta yi mgana sai Innani ta Taso mata.
Da Abba ya dawo bai ko yi mgana ba. Shi fa Ra'ayin Innani ne na sa Ra'ayin Magajin gida ne kawai cewarsa da Ra'ayinsa ke kan na Innani.
Innani bata yi mganar bikin Magajin gida da Sultana da ta gama bazawa a Shinkafi ba. Ta bari ne sai ta samu zama da Sulaimanu kawai ta gayamasa bad'i ta ke son ayi auran nan ta matsu ta ga ya'yan Magajin gida hakanan
Umma ta fara ji tunda Matar Baba Sammani Madiha ta kirata ta ke tambayan ya su Innani su ka koma gida? Daganan kuma sai ta ke tambayan Umma ashe biki kuma ya zo.
Cikin mamaki Umma tace bikin wa? Madiha tace na Magajin gida da Sultana mana, nan ta kwashe mganar Innani ta fad'aa mata Umma tace to bata san da mganar ba ammh za ta yi ma Abba mgana in ma da bikin za su fad'a musu.
To shima Abba Shitu ya kirasa ya masa zencen yace masa sai ya koma gida sun yi mgana da Innani Tukunna.
Sai a kayi sa'a Umma ke da Turaka ranar sai ta samu lokacin Tambayansa ko sun yi mgana da Innani? Abba yace a'a. Me ya faru? Sai da ta gayamasa ne shima yace sun yi mgana da Shitu.
Umma ta yi shuru kafin tace"Abban Siyama ka na ganin in muka ce Auran nan ya taso ba mu yi gaggawa ba? Sannan ba mu ji Ra'ayin Auta akan mganar ba."
Abba yace"Kada ki damu. Abunda Innani ta ke so shi za'ayi Salamatu. Innani ta tsufa a kwai rikicin Tsufa tare da ita gwara na samu na Rabu lafiya da ita."
Umma ta jinjina kai kafin tace"Duk na san da wannan. Ammh ta ya ya za su yi aure Sultana karamar yarinya ce. sannan Auta bautar kasa ya ke yanzu bai ko kama aikinsa a hannu ba. Sannan bamu san Wani Tsari ya ke da shi nan gaba ba. ni na dauka sai ta gama makaranta shima kafin lokaci ya san in da ya kama Abban Siyama."
Abba ya yi mirmishi kafin yace"Nima haka na so da farko. ammh ya zan yi da Innani salamatu?
Umma sai ta yi shuru ammh tasan in su ba su isa ba. Wanda ya isan zai ji kuma zai dakatar da ita, Shiyasa ta bar mganar.
Washegari da Safe gabadayansu a Shashen Innani suka karya daman Haka suke yi ranar aikin Umma. Salima ce kad'ai ke zuwa makaranta ita Direba ya dauka Sultana kuma da Siyama SS1 zasu shiga Tukunnah.
Bayan sun gama Sultana da Siyama suka kwashe komai suka fita suka bar iyayen na su su zanta.
Innani tun safiyar Allah sai Bare naman kaza take sala sala ta na ci Kai Tsohuwar nan akwai rikici a lamarinta.
Gabadaya a gabanta suka Durkushe Umma da Abba sai Mama achan gefe. Abba ne ya fara kora mata jawabin kiran Shitu Innani ta saki naman kazan hannunta ta na salati har da tafa Hannu ga gilashinta da ya kusa cika mata Fuska ta na fadin"Na shige su ni Dije? Ashe Shitu Annamimi ne ban sani ba? ni zai yi ma makirci da Tuggu?
Umma tace"Subhanallah Innani ba Makirci ba ne ya kira ne yaji tabbaci."
Innani tace"Tabbacin Uban me? Zan masa karya ne shi Sulaimanun ina ce ba ni ce uwarsa ba?
Umma tace"ke ce Innani har mu ma ke ce mahaifiyar mu ba mu da kamar ki."
Sai Innani ta ji sanyi ta Sassauta Murya ta na fad'in"To shi ne shi ya ke Tunanin na yi masa karya ko? To ba karya ba ne da gaske ne Bad'i na ke son a yi auran magajin gida da Sultana."
Falon na Innani ya Dauki Shuru Umma ta kalli Abba ta na masa inkiyar ya yi mgana.
Sai ya muskuta ya na fad'in"Innani..Dama.."
Innani ta Dakatar da shi da Fad'in"Sulaimanu nace bad'i uwar haka naga Yarinyar nan Sulsana a dakin magajin gida ba na son wata mgana."
Da Sauri yace"Shikenan Innani yadda kika ce haka za'a yi."
Umma ta kallesa shi kuma sai ya kasa kallonta. Mama ta matsonta mata mgana a Hankali" Umman su ki yi mgana mana."
Karaf ko Innani ta gani ta balla mata Harara ta na fadin"wata gulmar kuma ki ke gayamata? Kin ga Suwaiba ki Fita idona kafin na ci miki Mutumci."
Da Sauri Mama tace"A'a Innani ina ce mata ne ta tambayeki wani wata ne za'a saka na bikin?
Innani ta kura mata ido kafin ta tabe baki tace"ke dai kika sani."
Daga haka ta cigaba da zare sala salan kazanta ta na tura a baki ta na ci.
Umma taga gwara ta yi mgana kafin komai ya zo ya kwabe.
Sai ta gyara zama ta na fadin"Innani.."
A Fusace tace"Mi ye wai ku ke ta kiran Sunana.?
Umma tace"Daman naga kin sauya ra'ayi ne. ni dai nasan a baya mun gama sai Sultana ta gama makaranta lokacin ta kai shekara sha takwas shima Auta ya gama bautar kasarsa har kila ma ya fara aiki kafin mganan auran na su ya taso."
Innani ta rika ballama Umma Harara ta na tabe baki kafin tace"Suwaiba ce ta kitsa miki ki ce min haka ko Salamatu?
Mama ta zaro ido ta na kallon Umma ita kuma da Sauri tace"Wlh a'a. innani."
Innani kamar bazatayi mgana ba Abba ta kallah kafin tace"Baka gayama matanka Umarnina na gaba da Umarnin kowa ba ne?
Da Sauri yace"Haba sun sani Innani. Su san Umarnin ki shine nawa Umarnin."
Kai ta gyad'a kafin tace"To ashe sun sani ke salamatu ban san me ya shiga kanki ba ki ke biyema Suwaiba da Munafuncinta ba, Ki yi ma murna magajin gida zai yi aure ko kema zaki ga jokokin ki."
Umma tace"Innani jikoki nawa garemu a gidan nan?
Kai Tsaye Innani tace"Ban gan su baa"
Mama ta yi karaf tace"Innani ba ki gan su ba? Kaf ya'yaan mu duk sun haiyyafa. Suma ai jokokin ki ne.".
Innani ta Daka mata tsawa ta na fadin"Ke ne zaki wani gayamin ya'yan ku sun haiyayyafa ce miki na yi ban san sun haihun ba ne? Ba na son tsirfa da Tsugudidi Suwaiba ba na so na gaya miki.
Sai Mama ta koma gefe ta na fad'in"Allah ya baki hakuri Innani."
A fusace tace"Ameen in da gaske kike yi."
Sai falon ya Dauki Shuru Umma na Tsoron sake mgana a taso mata Abba kuma na zaune kanzil bai kara cewa ba.
Ganin Umma ta yi shuru yasa Innani ta kalleta ta na saussauta Murya ta ce"Kwantar da Hankalin ki salamatu. Nasan sauran ya'yan ku sun haihu ammh su din ya'yan su ba jikokin sulaimamu ba ne halas malak . Duk tsiya suna da wani gidan kakanin na su magajin gida fa? Har abada ya'yan su shi da Sulsana ba su da kamar gidan nan. Duk duniya mu ne na su ba su kuma da kamar mu kuma jokokin ya'ya mata na gidan wasu
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 18 Chapter of 24