Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kowa zaman lafiya a gidan nan" Sadiq yace"Innani sai anjuma ko zamu iya cin wani abu. Sai da muka karya sannan Hajja ta bari muka kamo Hanya" Innani ta washe baki tace"Shiyasa na ke kaunar kakar Attahiru. Ta na kular min da kai kamar yadda na ke kula da kai, To ya kuka baro su? Attahiru ya wajen yan'uwa ka na chan Dauran? Tahir ya bata amsa da suna gaisheta lokaci daya da Tura mata ledan gabansa yana Fad'in"Hajja tace a kawo muku Innani. Ayar ciki tace taki ce" Innani ta ja ledan ta kara gyara zaman gilashin idanuwamta Lokaci daya tana Fadin"Kai naji dadi kamar tasan ina son wasa hakora na kwanakinan" Sadiq ya kalleta yana mamakinta matar da kullum cikin cin nama take da kayan dadi ammh tana Fad'in kwana Biyu bata wasa hakora ba. To ina ma taga hakoran? Ta na washe bakin yaga na Robanta das a bakinta suka kalli juna da Tahir suka saka Dariya. Sultana kunya yasa ta kasa zuwa Falon Abba ta fad'a musu dawowan Yaya Sadiq sai Siyama ce taje ta Fad'a. Umma ta mike da Sauri ta na Fadin"Auta na yazo ganin gida kenan" Haka ma Abba ya mike har jikinsa na Rawa Fadi ya ke yi"Mun yi mgana da shi jiya kuma bai ce min zai zo ganin mu ba. Ke Suwaiba a shirya ma Magajin gida abun karyawa." Siyama ta yi saurin cewa"Abba shi da Ya Tahir ne" Abba na bin bayan Umma yace"To daman duk in da kika ga Magajin gidan zaki ga Attahiru a wajen.. ki yi kokari Suwaiba kafin Innani ta fara fadan an barsu da yunwa." Mama ta ce"To Alhaji ammh mu je nima mu gaisa da su. Siyama zata yi ma Salima mgana zata ji da abun karyawan na su" Abba yace"A'a ba na son korafin Innani kinsan Halinta kije kawai ki yi abunda na saka ki" Mama bata da mafita illa juyawa zuwa Shashenta tana Danne abunda ke ranta. Tana shiga ta ga Sa'ima da Salima suna Hira afalo ganin yanayinta yasa suka hada baki wajen fadin"Mama lafiya? Sai ta saki Fuska kafin tace"Magajin gida ya zo. Kuje shashen Innani ku gaisa da shi kafin kakarku ta fara tsinan ku." Salima ta mike da Sauri tana Fadin"Bros ya zo? Kafin mama ta kara mgana ta fice a guje Sa'ima ta mike ta na gyara Lullubinta tace"Mama bari na je mu gaisa da kanina na yi kewarsa sosai." Mama ta murmisa tana fadin"Ki turomin Siyama ta taimakamin wajen hada musu abun kari" Sa'ima ta amsa ta na Ficewa. Tunda Mama ke da girki sannan Ranar asabar da Lahadi yan aikin su basa zuwa tunda yaran nan na gida kuma a Tsarinsu a karshen sati duk mai girki ita zata yi da kanta saboda Alhaji na gida. Ko da Sa'ima ta isa Shashen Innani ta iske Abba rike da Hannun Sadiq kamar wani zai kwace sa gefensa Umma kuma ce ya d'ora kansa saman kafadanta ya narke kamar yaro. Gabansa kuma su siyama ne da Salima sai su Afiya kowa sai mgana ya ke yi Salima fadi ta ke yi"Yaya Sadiq tun wata daya da ya wuce na yi chart dinka a wsop baka duba ni ba" Ta fad'a cikin shagwaba Siyama kuma fadi take yi"Yaya Sadiq mu ma a siya mana waya ni da Sultana" Sai dai aka fadi Sultana ya Daga kai yana kallonta tana gefen Innani ta Rakube kanta kasa kamar wata marainiya. Tahir ya kallah da ke kallonsa gira ya daga masa shi kuma ya balla masa Harara. Innani sai msifa ta ke yi"Haba don Allah ku bar min jika ya Huta daga Dawowarsa kun fara damunsa da Korafe korafe." Sa'ima ta yi mirmishi sannan ta yi sallama Falon Innani Tunda ba wanda yasan da Tsayuwarta.. Tana shigowa Sadiq ya mike yana Fadin"Ya Sa'im" Kai tsaye ya mike ya Nufeta suka Rumgume juna cikin Farin ciki ta shafa kan shi tana Fad'in"Dan kanin mu min yi kewarka" Yana Dariya yace"Bakwa kai min ziyara Shiyasa" Ya fad'a cikin Shagwaba da Sauri tace"Kada ka damu zamu rika zuwa..Sannu da hanya Tahir sai tare da Sadiq muke ganinka ko? Tahir na mirmishi suka gaisa ta na masa Tsiyan baya zumunci sai da Sadiq ko. Umma da Abba bakinsu ya ki Rufuwa duk wani walwalan gidan Alhaji Sulaiman yana tafiya ne tare da Farincikin Abubakar Sadiq. Dakyar ya kwaci kansa zuwa Shashensa shi da Tahir suka yi wanka sannan suka kwanta su huta. Tahir na kwance saman makeken gadon Sadiq a cikin Bedroom dinsa. ya na kuma kare ma Dakin kallo ba bu abunda babu na more rayuwa. kaya ga su nan kala kala takalma shurfa ne guda kamar wadrope,Shi bai ga abunda Sadiq ya nema ya rasa ba abunda ma bai nema ba ya samu. Har cikin Bedroom dinsa akwai karamin Tibin bango bayan faskekiyar plasma da ke falo, Sadiq gajiya tasa ya fara barci shi kuma ya kasa sai kawai ya tashi ya koma falo ya yi flat saman Daya daga cikin kujerun Falon Sadiq bayan ya kunna kallo remot a hannunsa yana Sarrafa tashoshi. Iskar A.c na kala shi sanye yake da karamin wando da riga mara Hannu kayan Sadiq ne sabbi yana ma Tunanin bai Taba saka su ba. Yana nan kwance Siyama da Sultana suka shigo da basket cike da kayan karyawan su. Suka masa sannu da  hutawa suka fita. Tarbiyan gidan su Sadiq mai kyau ce duk da sun taso cikin gata. Ko da Sadiq ya ke yayansu ba'a ba su daman su shigo shashen kai tsaye ba. yanzu ma sai da ya ba su izini sannan ba su zauna ba suna kawo abunda aka aikosu su ke tafiyarsu, gwarama yayenshi su Yaya Surayya su kan shigo su zauna ayi ta Hira. Tahir dai ya mike ya jawo kwandon gabansa Ferfesub kayan ciki ne, Sai Ruwan Zafi soyayyan kwai da buredi sai Ferfesun kaza yana Turiri. Shi ya zuba ya ci har ya na Dankwale da Buredi bayan ya gama ya sha lemun kankana mai sanyi. Ya koma ya kwanta ya na Hamdala. Tun yana kallo sama sama har barci ya kwashe shi wayarsa ba chaji ne sai ya sakata chaji cikin Bedroom din Sadiq. Ba su suka tashi ba sai Azahar. Shima din Sadiq ne ya tashe shi sun makara sai jam'i suka yi a daki. Suna cikin sallar a ka sake kawo musu wani kwandon abincin na safe ya Tadda na rana kenan. Sadiq ne kadai ya ci Jallop din shinkafa Tahir ya ce sai anjuma. Ashe suna barci ba su sani ba Innani ta saka Sultana ta yi ta kiran mata yan'uwan Sadiq ta na fadin kowacce tazo Magajin gida ya zo. Ko da suka sauya kaya suka isa Shashen Innani cike da ya'ya da Jikoki daman sun kosa su gansa Innani ta Hana su zuwa Shashensa tace yana barci kada adamar mata jikanta. Suna shigowa Dakin Innani ya Dau Sowan ga Bros. Har da Abba da Umma da Mama yau Shashen Innani suke tunda daman in dai Sadiq na gida wajen zamansa Shashen Innani ne. In yaje shaahen Umma sai domin kebewa ta uwa da Abunda ta Haifa, shashen Mama kuma yana shiga su gaisa su yi hira da Kannensa Shashen Abba kuma yana shiga in mganata sirri ta had'a su ko yana son ayi wani abun. Hajiya Surayya ce ta fara tasowa itace babba a dakin Hajiya Umma. Cikin Annuri tace"Autan Umma ya zama Saurayi" Tafada tana Dariya. sadiq sai mirmishi ya ke yi ya nufi yan'uwansa. Surraya ce da Sadiya,Sajida,da Sa'adatu. Subai'atu da Saddiqa ba'a garin Gusai suke aure ba. Sai bangaran Dakin Umma Sa'ima Sakeena,Shahida na Umra Saliha ta raka mijinta Seminar a lagos. Tsakiyarsu ya zauna suka yayyameshi suna sa kawai ke tashi. Tahir kuma na gefe shima cikin Farinciki suka karbeshi suka gaisa a Mutumce da Tambayan mutanen gida. Sai ya juya suka gaisa da Mama, Umma da Abba daman sun gaisa tun dazu, Innani ko na gefe sai Taunar ayarta take yi da ance Innani mu ji ayan sai ta fara masifa tana Fadin"Ba zan bada ba. Ba wacce ta siyo ta kawomin. Sai kakar Yaron  nan Attahiru saboda haka ba Shegiyar da zata ci wlh" Sadiq ya kalleta kafin yace"Innani ba na hanaki zage zagen nan ba" Da Sauri Innani tace"yi hakuri Magajin gida raina ne ya baci. Haba duk abunda yaran nan suka ganni da shi sai sun yi kokarin rabani da shi.. nima D'an nawa ba arzikin garesa ba Rufin asiri ne kowace ta na da Miji taje mijinta ya siyamata mana" Kai tsaye ya juya yana kallon yan'uwansa kafin yace"To kun ji. Kada wacce ta kara rokar Innani abunta. Kowacce ta na da miji ya siyamata itama d'an nata da ke siyamata ba shi da wani kudi sai Rufin asirin Allah" Innani na Dariya da Hakoranta tace"Allah ya tsaremin kai Jikana." Dariya aka saka gabadaya Falon na Diraman Innani an samu dai bata Fashe da kuka ba ko ta yi tsine tsinen da ta saba ba. *Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.* *Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.* *SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode* *Janafty* *TSAKA MAI WUYA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Mallakar:Janafty* *Arewabook:Jamilaumarjanafty* https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk Ku zo ku yi sayayyarku tare da Yar Gidan Imam, inda za ku sami komai cikin sauki, tun daga kan kayan kicin, kayan yara,atamfofi da lesissika uwa uba da kayan gyaran jiki irin na manyan matan da suka San kan su,har counselling mu na yi yadda duk damuwar da ki ke ciki a game da aurenki da gyaran jikinki zaki samu solution. Ku dai ku shigo cikin wannan gidan na karamci kai tsaye domin more tagomashin da ke ciki. *09* Kowa kokarinsa ya faranta ma Sadiq rai, maganganu kawai ke tashi kowa kokarinsa ya fad'i bukatunsa Sadiq ya cika masa. Ga Abba zaune ammh kowa ya tashi sai dai yace Yaya Sadiq ina son abu kaza. Ina son a chanzamin kaza don Allah. Salima cikin Shagwaba ta ke fad'in"Bros wayata duk ta tsufa don Allah a sauya min wata." Ta karishe fad'a cikin Shagwaba. Siyama ko gefen hannunsa na hagu ta makale kamar wata yarinya fuskar nan a tabe kamar zatayi kuka tace"Ya Sadiq mu ko wayar ba mu da shi. A siya mana ni da Sultana" Dariya ya yi yana shafa kanta kafin yace"ba yanzu kuka ka gama Jsce ba? Ku bari in kun shiga SS1 sai a siya muku ko? Nakwa nakwa ta yi da Fuska ganin haka sai ya ja kumatunta yana Fadin"Haba Autan mu Smile mana. Za'a siya muku waya wannan cewar Magajin gida ne" Jin haka yasa ta saki mirmishi ta juya tana kallon Sultana kafin tace"Sultana kin ji mu ma mun kusa zama manyan yara su Yaya Salima a daina mana wukalamci kan waya.". Ta fad'a tana nuna ta da baki Salima ta zaburo ta na fad'in"Ni sa'arku ce da kike gasa da ni? Yaya Sadiq ya kalleta kafin yace"Salima.." Ta kallesa sai ya girgiza mata kai. Ta gefen idanuwansa Sultana ya ke kallo da har lokacin ko Tarinta bai ji ba. Yarinyar nan ta na da aiki. Innani na jin su bakam kawai tayi bata kara mgana ba. Umma kuma da Mama suke taba Hira Abba kuma an kira wayarsa ya fita. Tahir na gefe ya na duba wayarsa ammh kacokan hankalinsa na kan Sadiq da yan'uwansa da irin kauna da Gatan da suke nuna masa a ransa yana jin Dama ace Dama ace, Dama ace Shine Sadiq da Duniya ta jima da Shaida wannan gatan da ya ke da shi. Big sis  Hajiya Surayya ta kalli kaninsu kafin tace"Autan Umma sati na sama Muhsin zai dawo" Kallonta ya yi yana nazarin waye kuma Muhsin ganin haka yasa tace"kanin mijina mana da na so ku tafi waje karatu tare." Sai alokacin ya tuna da shi cikin Mirmishi yace"Oh Allah Sarki. Sai yanzu ya gama karatun na shi? Hajiya Surayya tace"Eh ammh zai koma ya samu kwarewa kan bangaran da ya karanta. Da yanzu ka tafi da muna nan muna shirya maka kyakyawan Tarba Shalelenmu" Kamar bazai yi mgana ba sai kuma ya yi mirmishi kafin yace"Big sis. Sunaanshi Muhsin ni kuma sunana Abubakar Sadiq. Ba zai zama Dole Ra'ayina ya zama na shi Ra'ayin ba. Shima ba lalle nawa Ra'ayin ya zama iri d'aya da na shi ba. Shi kanin mijin ki ne ni kuma kanin ki ne akwai bambamci Tsakanina da shi." Sa'ima ce ta yi karaf tace"To gaskiya in zaka yi masters dinka waje zaka fita ka zabi duk kasar da kake so kaji? Sadiq ya kalleta kafin yace"Yaya Sa'ima.". Da sauri tace"A'a mun gaji da ganinka kana gararanba a tsakanin Zariya da gusai kamar wani mara gata.". Sadiya tace"Kuma Alhalin ina Tunanin kaf set din su ba wanda ya kai shi gatan ba". Shahida ma ta saka bakinta gabadayansu suka yi masa caa da zencen zaman da ya ke yi a zariya. Sajida tace"Ni abun haushin ma haya fa ya ke mganar ya kama a chan wani gida suna zaune. In da ya yarda ba sai Abba ya siya masa gida achan ya zauna ba." Sakeena ta karbe da Fadin"Autan Umma mu dai ka dawo gida don Allah wlh muna kewarka ka bar garin nan sam ni Hankalina bai kwanta da zaman ka achan ba." Hannayensa ya Hard'e a kirji yana kallonsu yana faman mirmishi. Salima ta karishe mganar da cewa"Big bros kawayen mu duka yayyensu a kasar waje su ke karatu ni in suka Tambayeni rasa ma me zan fad'a musu na ke yi" Ta fad'a kamar zatayi kuka Dariya ya yi har Fararan Hakoransa na bayyana kafin yace"sai kice mu su a zariya ya yi karatu kuma yana chan yana Hidimar kasa." Salima ta Zaro ido kafin tace"Bros..". Kai ya gyada mata alamun eh hakane sai ta jime fuska ta yi mgana su Sakina suka saka Dariya. Tahir na gefe ya tsoma baki karo na Farko kafin yace"Sai ma kunga ire iren abincin da ya ke ciki.." Tahir bai tsaya ba ya shiga ba su labarin irin cimar Sadiq ke yi a zariya harda Danwaken da ya ke siya yana Tafiya da shi wajen aiki. Gabadayansu suka Bude baki suna kallon Sadiq shi kuma ko ajikinsa. Tahir yace"Abun haushin ma masu saida abubuwan ba su da Tsafta wani abun ma baisan da ga ina aka Sarrafashi ya siya yana ci ba. Ko ni ba na irin Rayuwar da Sadiq ya ke yi kamar wanda ya fito daga Daji." Sadiq ya kallesa kafin yaace"Daman daga ina na fito.? Surayya ta kalli Sadiq kafin tace"Why Autan Umma? Nan fa suka taso masa suna ta mganan gaskiya gwara ya dawo gida ya yi Bautar kasarsa. Su ka gama mganganunsu bai tankan su ba sai daga karshe Umma ta shigar masa ta na Fadin"Ku kyalemin Auta ya yi irin Rayuwar da ya ke so haba. ai ba kauce ma Hanya ya yi ba Ra'ayi ne kowa da irin na shi" Sai Lokacin Sadiq ya yi mgana cikin Halin ko in kula yace"Yauwa Umma Fad'a musu ba mai zab'amin abunda zan ci, cikina ne rayuwata ne ok.! Sannan in kun ga na baro Garin Zariya na gama abunda ya kaini ne sai ko in mutuwa." Kawai sai ji akayi Innani ta fashe da kuka Tana fadin"Allah ya tsine ma duk wanda ke jifan jikina da kalmar mutuwa. Sulaimanu ba shi da wani magaji yau in magajin gida ya mutu ina zamu saka kanmu.? Allah dai ya tsine ma duk mai yi masa fatan Mutuwa akansa wlh." Ta karishe fad'a lokaci daya kukan nata ya Dauke ai sai falon ya dau shuru kada wata ta tofa Innani ta Sauke mata Tsine tsinen da ke bakinta. Sai Dakyar Sadiq ya lallabata ta yi shuru ta hakura, Shima tunda ya ce bazai bari ba suka kyaleshi sanin Halinsa na kafiya da Shegen girmama Ra'ayinsa saman na kowa. Hira suka cigaba da yi na zumunci sallar la'asar kadai ya ta da su kafin nan sun yi masa bakin me zasu kawo masa? Kowacce na masa magiyan ya kawo mata ziyara kafin ya tafi tare da Tambayanshi me dame me dame zasu had'a masa in zai koma? Kai tsaye yace"Kowa ya san abunda na fiso ko? Salima ta yi tsalle tace"Nama." Suka saka Dariya gabadaya su san Sadiq kamar kura ya ke wajen cin Nama. Innani ce ta fattakesu da Masifarta fad'i ta ke yi"Kai dilla kowacce ta ja ya'yanta ta tafi gidan mijinta kun zo kun cikama D'ana gida zaku cinyemasa dan abunda ya tara to shima ba shi da komai Rufin asirin Allah ne" Surayya tace"Innani ke fa ki rika kiran mu kina fadi'n mu zo ga magajin gida yazo sannan yanzu kuma munzo, kina korarmu" Innani tace"fisabilillah an yi na mutumci da arziki. Ba sai ku tattara ya'yan ku ku tafi ba? To billahillazi in ma bazaku tafi ba ku fice min daga Shashena kun isheni yarinyar nan Sulsana na so ta kebe da magajin gida kun bi kun kankane, ku fa wani Lokacin girma ne kawai ammh ba ku da wayau kwata kwata ba ku san ya kamata ba" Ta fad'a ko ajikinta ta na kara ma zaman gilashinta zama a idanuwanta. Sultana da ke gefenta ta Dago a tsorace ta kalleta baki Bude tace"Innani.." Innani ta juyo a masifan ce ta na Fad'in"Innani me? Don ubanki ai ba karya na yi miki ba? In ba mgana kike son yi da shi ba uban kike min a baya kamar wata yarinya? Ko ni ce uwarki? Ba ga salamatu chan ba meyasa baki je kin nanike ta ba. ni tashi daga baya na tsufa haba fisabillahi ai na yi wahala da ya'yana ya isa haka wani shegen jika ya yi ta kansa ni ma ta kaina nake yi." Ga dariya ba Halin ka yi Dariya Salima ta saki dariyanta ganin yadda Sultana ta yi kamar kazar da aka Tsoma a ruwan zafi da Innani ta Tureta. Innani ta ji tashin Dariya ta Daga Sandar ta tana fadin"Wata shegiyar ce ina mgana ta na min Dariya? Salima ta Rufe baki tana zaro ido aka yi shuru ba wanda ya tanka ta Surayya taje ta dago Sultana da har ta fara hawaye ta riko hannunta tana Fadin"Karki damu da Innani an juma sai tayi cigiyarki.." Innani taji an yi banza da ita ana ta mgana sai kawai ta karkace baki kafin tace"Ko wacece ta yi dariya nan Allah ya tsine.." "Innani.." Sadiq ya katseta da karfi jin Muryansa yasa ta yi shuru ta kama Jan hanci kamar zatayi kuka ta na Fad'in"yaran nan na sulaimanu na arzikin dai duk sun kare yanzu duk diyan banza ne" Sadiq ya bude muryansa ya na Fad'in"Innani wlh in na fita daga Shashen nan har na koma bazan kara dawowa ba. Sau na wa zan hanaki tsine tsine nan? Ki na ta aibata jikokin ki da kanki..? Sai Innani ta kasa mgana, jin ya yi shuru yasa ta dago ta na kallonsa kafin tace"Ka yi hakuri magajin gida Raina ne ya baci. Ka yi hakuri in ka gujeni ina zan saka raina ni Dije ba ni da kowa sai kai anan duniya nan" Kai Tsaye yace"Ba ki na da D'a ba. ga Abba nan mu ba kin gama tsine ma na ba? Da sauri Innani tace"Wlh ban tsine muku ba. Dukkan ku ya'yan nan Allah ya yi muku albarka ya tsare gabanku da bayanku ya kare min ku. Allah ya shirya muku zuru'an ku gabadaya." Sadiq ya yi mirmishi ya karisa gaban innani ya zauna ya Rungumota yana Fadin"Ameen Ameen Innani na." Suma Sauran da Ameen suka amsa saboda Sadiq an samu Innani na ta zabga musu addu'o'i kafin su fita daga Shashenta dukkansu sai da suka sauke mata kudade Inanni na Hawaye tana fadin"Kai duka ya'yan Sulaimanu yan albarka ne. Allah dai ya yi muku albarka ya kare ku da Sharrin makiya.     Ke sulsana ina kike ki kirgamin kudin nan muga nawa na samu? Surraya tace"Innani wata Sulsanan? Wacce kika ture kika kora.? Innani tace"Kaji sharri da karya abakin manya ni Dije yaushe na Taba Sulsana? Kai Saddiqu maza kaje ka tahomin da Matarka nan" Ba shi da mafita illah yace mata toh ficewa suka yi suka barta da Siyama itama din Innani sai fad'a take yi tana Fadin'Uban wa yace ki zauna min afalo? Ni fa Sulsana nace magajin gida ya kirata so na ke yi su samu kebewa tunda dai nan da wata Shekaran zan ce Sulaimanu ya yi musu aure nagaji da ganin wannan watsewar aciikin gidan D'ana yara sai rashin kunya da Rashin Tarbiya gwara kowwcce tayi ta kanta shima d'ana ya yi ta kansa" Siyama dai karshenta Fattakanta Innani ta yi ta fito tana fadin"Ga shi nan kici falon gabadaya. In ma kin kara ganin kafata." Innani ta Daga sandarta tana Fadin"In kika kara Dawowa sai na ci Ubanki. Lallataciyar yarinya mara tarbiya kawai. Kai Suwaiba dai bata iya Haihuwa ba duk ya'yanta ne suka batamin zuru'ar d'ana." Kowacce shashen uwarta ta shige kafin mangriba Sakina da Shahida suka hau motocin su suka tafi,bayan mangariba kuma Surayya da Sa'ima da Sadiya ma suka tafi da cewa gobe Zai ga Sakon su. Shi daman ya na waje tare da Mallam Tajudden suna karatun Bukhari da Musulim, Mallam Tajuddeen malami ne sosai mahaddaci masanin Hadisa shiyasa Sadiq in dai yana gida baya wasa da daukan karatu a wajensa. Tahir na cikin Shashensa yana fama da waya bai ma gayyacesa ba sanin Halinsa. Suna karatu karnukan Abba suna Damunsu da Haushi Sadiq ya kalli Mallam Tajudden kafin yace"Abba bai rage karnukan ba ko? Mallam Tajudden yace"an fita da wad'anda ka sani wad'anan manya ne guda biyu aka kawo su kwanaki." Shuru ya yi bai yi mgana ba ba domin Hujjar Abba ba. Da bazai bari ya ijiye karunuka a cikin gida ba. Sai da aka kira sallar Isha'i sannan suka Rufe karatun alwala suka Daura suka fita zuwa masallaci nan kusa da su. Bayan sun dawone suka yi musabaha tare da sallama Mallam Tajudden ya shige muhallinsa shi ma Sadiq ya koma shashensa. Ya na shiga ya ga Tahir rashe rashe kan kujera ga basket din abinci nan a gabansa ya ci duk ya watse komai. Kuma ya kure karan Tv kuma alokaci daya yana amfani da waya.. Sanye Sadiq ya ke da Jallabiya Mai ruwan kasa da Hula. Hannunsa kuma littafin bukhari da Musulim ne a Hannunsa. Yana shigowa kallo daya ya yi ma Tahir ya Dauke kanshi kafin ya cigaba da Tafiya zuwa Bedroom dinsa. Kamar daga Sama yaji Tahir na Fad'in"Alarammah barka da Dawowa." Sadiq ya juyo kafin yace"Yauwa. Ka yi sallah? Tahir yace"Wace sallar? Kai Tsaye Sadiq yace"Isha'i.." Sai Tahir ya zaro ido kafin yace"Wai kana nufin har an yi isha'i.? Sadiq ya yi karamin tsaki kafin yace"Ana ta jiran ka Tahir kaji ana ta jiran ka. Ka na da rauni wajen ibada ammh wajen Shagalan duniya baka da wannan Raunin Tahir ka gyara ka gyara Rayuwarka." Tahir ya yi dariya kafin yace"Ka na ba ni mamaki ko da yaushe sai ka na mganar na gyara Rayuwata?. Shin rayuwata ba ta  akan hanya ne ko ya ya? Sadiq haushi yasa bai kara mgana ba ya Juya ciki ya na ji Tahir na Fadin"Naji yanzu zan ta shi nayi shikenan". Shi dai Shigewarsa ciki ya yi ya adana Littafinsa a muhallinsa. Wanka ya shiga bayan ya fito ne Tahir ya shigo ya shiga ya yi alwala sama sama ya yi sallar tasa kamar yadda ya Saba ya fita ya koma Falo kan waya kai kawai ya girgiza Tahir sai Allah kawai. Riga da wando ya saka Fari da baki yana son ganin Abba Kafin ya kwanta akwai mganar da ya ke so su yi. Falo ya fito kujeran da ke fuskantar Tahir ya jawo basket din gabansa. Pepe kitchen din da akayi domin sa ya ci duk da Tahir ya ci ammh ko Rabi bai ci ba naman kawai ya ci ya kora da lemu ya yi hamdala. kayan da Tahir ya bata duk shi ya tattara ya ijiyeshi nan gefe yasan su siyama zasu zo su dauka. Sai alokacin ya Dauki wayarsa ya na Dubawa. shi waya ya Dauketa kawai a kira ka kira Mutum ba shi da Juriyan Chart gwara ma karanta labaran abunda ke Faruwa. Ammh Tahir har mamaki ya ke ba shi baya gajiya Tahir na daga cikin mutanen da waya ta ke hanasu koomai ciki har da cikakkiyar Ibada ta shiga ransu da ta sanya suka Shagala. "JB na gaishe ka.." Tahir ya fad'a Hankalinsa na kan wayarsa. Sadiq ya Dago ya na kallon sa cikin mamaki yace"JB..? Tahir yace"Yes yanzu ma haka da shi muke chart na fad'a masa muna Gusai.  Shine ya ke mganar bamu tab'a kai masa ziyara kano ba." Karamin Tsaki Sadiq ya yi kafin yace"Haka kawai sai mu bar abunda ke gabanmu mu kai masa ziyara Tahir? Tahir ya kalli Sadiq kafin yace"Yes ofcourse. Abokin mu ne fa Sadiq. Ba bu illah domin mun kai

Chapter 10 of 24