Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
aka shiga Emergeny da ita ba su fito ba sai daya da wani abu na Dare shima ta agogon asibitin na Fahimci haka. Mutumin suka yi ma bayani sannan shi naga ya na ta shi ya fita ashe  fita ya yi ya siyo mganguna da allurai a wani kwali suka amsa suka shiga ciki. Ni ko ina Tsaye jiri na ke gani ammh na kasa zama sai da naji ina barazanar zubewa yasa na samu kujera na zauna ina kara Fashewa da kuka. Bansan ya zo kusa da ni ba sai da naji Tattausan muryansa yana fad'in"Ki yi hakuri ki daina wannan kukan. mahaifiyarki na nan da Ranta bata Mutu ba." Da Sauri na Dago Fuskata muka Had'a ido Hudu da shi. Akwai haske a asibitin tunda akawai wuta da Farin kwai. Tar fuskata ta haska shima haka tashi. Kallona ya ke yi yana ganin Fari na da haske kamar wata zabiya ashe ma yarinya ce bai dauka haka ba. Ni kuma ba ma shi na ke kallo ba Tunani na da ya ce Amma na da ranta ba ta Mutu ba. Cikin Dashewar murya nace"Amma ba ta Mutu ba? Kai ya gyadamin kafin yace"In sha Allahu." Da Sauri nace"To ta na ina? Kai Tsaye yace"Ta na ciki sun ce jininta ne ya yi kasa sai low sugar ammh sun samu nasaran ceto numfashinta." Sai kawai na Rumgume hannuwana a kirjina ina fadin"Alhamdulillah.." Hawaye na Diga bisa zanin jikina. A jikina naji gir! Har sai da na tsorata sai daga baya na Fahinci wayace na daga zanina na Dauko wayar bawan Allah nan ne. Na mika masa lokacin shi kuma ya na kallon gefe na ya na Tsaye ya saka Hannayensa duka cikin Aljihun wandonsa. Cikin wani yanayi na ce"Bawan Allah." Kai Tsaye ya juyo sai na mika masa wayar ina Fad'in"Ga wayar ka ana kira." Bai karb'a ba sai da yace"Sunana Abubakar Sadiq. Ba bawan Allah ba." Da Sauri na kallesa jin sunan da ya ambata suna mai Daraja a wajena. Shi kuma bai Kara kallona ba sai kawai ya juya ya d'an yi nesa da ni ya na amsa wayarsa. *Wattpadian Family kuna da yawa masu karantawa, ammh kun rage comments da Vote* *Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.* *Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332. mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode* *Janafty* *TSAKA MAI WUYA..!* *Wattpad:Jamilaumar315* *Mallakar:Janafty* *Arewabook:Jamilaumarjanafty* https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk Ku zo ku yi sayayyarku tare da Yar Gidan Imam, inda za ku sami komai cikin sauki, tun daga kan kayan kicin, kayan yara,atamfofi da lesissika uwa uba da kayan gyaran jiki irin na manyan matan da suka San kan su,har counselling mu na yi yadda duk damuwar da ki ke ciki a game da aurenki da gyaran jikinki zaki samu solution. Ku dai ku shigo cikin wannan gidan na karamci kai tsaye domin more tagomashin da ke ciki. *14* Tahir ke kiransa ya na Dagawa yaji Muryan Tahir cikin Firgici yana fad'in"Sadiq ka na ina ne? Har daya saura na dare baka dawo ba? Wlh na zata ka dawo gida barci ne ya kwasheni sai farkawa na yi naga baka dawo ba." Sadiq ya shafa kansa da Hannunsa guda d'aya kafin yace"Eh ban dawo ba." Cikin Tashin Hankali a muryan Tahir yace"Sadiq ba ka dawo ba? To ka na ina ne? Kamar bazai yi mgana ba sai kuma dai yace"Ina asibiti ne." A firgice Tahir yace"Asibiti? Innalillahi me ya faru da kai? Tahir ya fad'a gabansa na fad'i saboda Matukar Razana ya razana da rashin Dawowar Sadiq abunda bai taba Faruwa ba ne. firgicinsa kada wani abu ne ya samu Sadiq din ya shiga Uku. Sadiq yace"Eh ina asibiti ne nan cikin Samaru." Tahir yace"Baka da lafiya ne? Sai da ya juya ya kalleta ta na zaune ta had'e kai da gwiwa daga ganinta ta na son mahaifiyar nan nata shiyasa ta ke cikin Damuwa da kuka. Kafin ya yi ajiyar rai ya ce ma Tahir"ba ni  ne ba ni da lafiya ba Tahir." Tahir cikin kosawa yace"Ka na so ka kasheni da Zullumi ne Sadiq? Waye ba shi da lafiya.? Sadiq yace"Taimako na yi Tahir. Wata baiwar Allah ce." Tahir ya jinjina kai kafin yace"Zaka dawo ne? Shuru Sadiq ya yi Kara kallonta ya yi ita kad'ai ne bai kamata kuma ya tafi ya barta ita kadai ba. Ga ta karamar yarinya ba bu mataimaki a kusa da ita. Kai Tsaye ya ce"An ya? Ban tunanin haka." Tahir ya sauke ajiyar zuciya kafin yace"Wani asibiti ne? Sai na zo na same ka." Sadiq yace"Ka yi zaman ka Tahir lafiyata kalau fa." Tsaki Tahir ya ja kafin yace"Dilla ka Turomin sunan asibitin gani nan zuwa.." Daga haka ya kashe wayarsa. Sadiq ya Sauke wayar daga kunnensa shi kanshi bazai iya fad'an sunan asibitin ba. Sai da ya fita daga Haraban Asibitin ya ga sunan asibitin sannan ya Rubutama Tahir ya tura masa. Dawowa ya yi cikin asibitin ya isketa har ta yi barci ta d'ago kanta saman masagin kujerun da ke wajen domin zaman masu jinya. Daga gani a wahale take numfashin ma nata a wahale ya ke fita, kauda kansa ya yi ya na kallon gefe. Bayan ya zura duka hannuwansa a aljihun wandonsa yana nazarin wasu abubuwan. Kudad'en hannunsa gabadaya sun kare, Allah yasa ma ya na yawo da Atm dinsa da baisan yadda zai yi ba kudin bankinsa sun yi kasa akwai bukatar ya kira Abba ya sake Turo masa kudad'e. Jiya ba su yi mgana ba Shekaranjiya  ne ya kirasa da kansa saboda Matsalan Innani tsohuwar nan matsala ce mai zaman kanta a gidan Abba. Wai sultana babanta ke son taje shinkafi ta yi hutu tunda ta gama Jss3 zasu shiga Ss1 ita da Siyama. Umma ta shirya mata Tafiya Abba kuma daman bai da matsala, Ammh Innani naji ta fara Tsine ma Mahaifin Sultana ta na kawo Labaran da bata san Tushen su ba ballatana makamar su ba. Akan Sultana bazata je wajen Mahaifinta ba, ban da Innani da Shegen kafiya da Rikicin Tsufa ta ina zaki raba y'a da mahaifinta? Duk da Sultana yarinya ce tasan Mahaifinta kuma ta na son shi tare da Sauran yan'uwanta. Umma ta kirasa ta fad'a mai Abba ya ce Sultana ta zauna Tunda Innani ba ta so taje. Shi kuma sai ya kira wayar Innani ba ta shiga sai ya ce ma Umma ta kai ma Innani wayar zai mata mgana Umma tace ya Rufa mata asiri kada Innani ta ce ita ta kai kararta wajen Magajin gida. Dalilin haka yasa ya kira Abba ya ce in ya shiga wajen Innani ya kirasa zai yi mgana da ita. Innani dole ta yi shuru da bakinta Tunda ya ce mata Sultana zata tafi Shinkafi taga Babanta da yan'uwanta Dole Innani ta amsa, ammh kuma jiya sun yi mgana da Umma tana fad'a masa Innani ma ta shirya kayanta tace kafarta kafar Sultana kada shitu ya cuta mata ya ganta marainiya. Shi ko kara bi ta kanta bai yi ba innani case ne mai zaman kanta a wannan gidan in ka toshe nan ne sai kaji ta kara balle wata kofar, yasan zuwa zatayi ta yi ta rashin Mutumci sannan ta hana yarinya sakewa a gidan Ubanta tare da sauran yan'uwanta. Ga shi ya lura Mahaifin Sultana Tsoron Innani ya ke ji in ta zaunar da shi ta na ta zage zage Har Allah ya isa ta sha masa ammh iyakarsa ya ba ta Hakuri ammh Tsohuwar nan har yau ba ta Saduda ba. Kila sai ranar da Ciwon Ajali ya kamata ba, ammh ki na Tafiyar da kyar ga makanta kice sai kin je, Haushi ma yaji yasa ya ce ma Umma ta barta taje din taci abunda zata ci achan. Fitowar Nurse shi ya katse masa Tunanin da ya lula. Ta na gayamasa jikin Amma da Sauki nan da zuwa anjuma zasu kawota dakin da zata Huta. Ni kam mafarki na yi naga su Adda Fati sun zo asibiti suna ta kuka sai na Farka a firgice ina kiran sunan Amma. Sai na hange shi yana mgana da ma'aikaciyar Jinya. Daidai lokacin da na mike baya na ya amsa na duka ina wash ita kuma Nurse din ta tafi,da Kyar na karisa gabansa ina dingishi kallonsa na ke yi da Kumburarun idanuwana Tun kafin na yi magana da Sauri yace"Ta na samu sauki. sun ce zuwa anjuma zasu dauko ta zuwa Dakin da zata Huta." Sai da yaji karfafan ajiyan zuciyan da na Sauke kafin hawaye su gangaromin ban damu da Sharewa ba na kallesa ba ni ya ke kallo ba na Fahimci ba shi da Dabi'an yawan kallo shi,cikin Shakkiyar muryata nace"Nagode sosai. Allah ya saka da Alheri Allah ya jikan magabata." A hankali ya amsa da Ameen kafin kai tsaye ya kalleni ya na fad'in"Ki je ki zauna naga kina dingishi ne" Da kai na amsa masa kafin na juya ina Tafiya sannu kafata ba takalmi sai lokacin ya lura da haka. Da wani irin kallo ya bi ni, kallon da ko Sultana da taso a cikin gidan su a gabansa bai taba mata irin shi ba. Kallo daga sama har kasa, Tabdijam ya dad'e ya na mamakin sirantarka Sultana sai yau da ya ga wannan yarinya ya san Sultana gwaiwa ce kafafunta ya kalla kanana sirara kamar na yara kanana. Ta ya mutum zai rika yawo ba takalmi kuma ta na mace? Macen ma acikin asibiti kafarsa ya kallah yaga takalminsa mai hanci ne sannan in ma ya bata bazata iya sakawa ba. Yana da Babban kafa da Tsawo da Tudu lamba arba'in ne ya ke sakawa. In ta saka takalminsa saboda Siranta bazata iya daga kafarta ba ma. Har taje ta zauna ya na kallonta ta gefen ido yana kiyasatawa a tunaninsa bazata wuce sa'ar Sultana ba. Yarinya karama a barta  da mara lafiya haka? Ina babansu da sauran yan'uwanta? Shi kadai ya ke ta wannan Tunanin a ranshi, ya na kallonta ta na ta share hawaye daga gabanta ya matsa saboda baya son kuka barin ma na mace Raunana masa zuciya ya ke yi saboda shi mai Tausayi ne. Kujerun da ke gefe chan da shigowa babban falon asibitin kusa da ma su ba da kati ya samu kujera ya zauna yana jin sanyi sanyi yasa ya saka hannayensa cikin Aljihun Jaket din da ke jikinsa. Ita ya ke kallo yaga ta kara Dunkulewa cikin zanin da ta yi mayafi da shi ta Dauki kafarta ta dora saman kujeran ta dunkule jikinta waje daya daga alamu itama ta na jin Sanyin da ya ke ji. Muryan Tahir yaji ya na Tambayan ma su ba da kati. Sai ya saka baki ya kira sunan shi ya juyo ya na kallonsa kafin ya yi mgana da su kila ya na fad'a musu ga wanda ya ke nema chan. Wajensa ya zo ya na fad'in"Ka ji ni shuru ko? Kasan dare ne na jima ban samu abun hawa ba." Sadiq ya matsa masa gefensa ya zauna ya na fadin"Ai sai da nace ka yi zaman ka ba sai ka zo ba." Tahir ya kallesa lokaci daya yana kara bin asibitin da kallo. Har bangaran Hasiya dake dunkule waje daya cikin Sigar Tambaya ya kalli Tahir kafin yace"wannan ce mara lafiyam? Ya fad'a ya na nuna Hasiya, Sadiq ya girgiza kai kafin yace"Mahaifiyarta ce.". Tahir ya jinjina kai kafin yace"Uhm Allah ya sauwake." Sadiq ya amsa da Ameen shuru na wani Lokacin Tahir ya gaji yace"Yanzu ina mara lafiyan? Sadiq yace"Ta na ciki sai anjuma zasu kawota dakin da zata huta suka ce." Tahir yace"To ai shikenan ma sai ka tashi mu tafi gida. Tunda ga yarta sai ta zauna da ita." Wani kallon baka da Hankali Sadiq ya yi ma Tahir kafin yace"Sai mu tafi mu barta ita kad'ai a asibitin nan? Baka ganin yarinya ce karama" Tahir ya ce"To mene? Ba taimakonsu kayi ka kawo su asibiti ka kuma biya musu komai to me ya rage Sadiq? Sanin Halin Tahir yasa ya yi masa Banza Tahir yace"Ba dai tunanin kwana a asibitin nan ka ke yi ba? Sadiq yace"Shiyasa nace maka ka yi zamanka ba sai ka zo ba." Tahir ya bude baki ya Rufe saboda mamaki kafin ya sake budewa ya na fadin"Nufinka anan zaka kwana Sadiq? Sadiq yace"Anan zamu kwana dai. In ma ka fita yanzu bazaka samu abun hawa ba." Takaici yasa Tahir ya kasa mgana Sadiq ya kallesa ya na Danne Dariya kafin yace"Allah yasa a mizani Tahir Yusuf Daura." Tahir ya kallesa cikin jin haushi takaici duk ya ishesa ya ma kasa mgana Saboda haushi. Sadiq ne fa sanda suna makaranta ya sha kwana da Dalibai in ba su da lafiya a Clinic din makaranta, ya na mamakin wata irin zuciyaa Allah ya ba ma Sadiq. Zuciyarsa ba irin ta kowa ba ne ya na da zuciyar Tausayi Imani da jinkai, zai yi maka wahala da Aljihunsa sannan ya taimake ka da karfinsa shi kam bazai iya wannan aikin ba. Bai kuma taba Fatan ya kwatanta ba ai aikin Allah suna da yawa. Shuru suka zauna kowa na saka abunda ya ke sakawa a ranshi Tahir ya gaji da latsa wayarsa bayansa ne har ya kage yasa ya kalli Sadiq kafin yace"To a ina zamu kwana? Sadiq bai kallesa ba yace"A bayana zaka kwana Tahir" Tahir ya hararesa kafin yace"Dole kace haka mana. Yanzu nufin ka anan kan wannan kujeran zamu kwana? Sadiq yace"Sai ka sauka kasa duka zabi ne" Tahir ya kule kamar ya yi kuka ya gyara zamansa kan kujeran yadda Wuyansa bazai samu matsala da Safe ba yace"Wlh baka kyautamin ba ina zaman zamana ka taso ni zan kwana cikin Takura. Wannan ko Sultana ce zata haihu sai haka" Sadiq na jinsa bai yi mgana ba sai da ya Murmusa. Tahir ya rigasa yin barci sai faman buge bugen sauro ya ke yi yana Tsaki shiko daman ba ya iya barci a asibiti ko ya ci wani abu ko ya sha wani abu. Ya dad'e bai yi barci ba har wajen uku na Dare sannan barci ya kwasheshi sama sai biyar da rabi ya farka shima Tafiya ya rika ji ashe Nurses suka fara Zirga zirga shi ya tada Tahir wanda ya tashi yana Faman soshe soshe da Taba wuya alamun dai kwanciyar ba ta yi masa Dad'i ba. Fuskar nan ta shi kamar Buredi saboda kumburi. Sadiq ya kallesa kafin yace"Mu tafi masallaci." Tahir ya mike yana fad'in"Wash baya na ya 'kage." Sadiq yace"Daman kai ai ba Namiji ba ne" Tahir yace"Dole kace haka tunda ka Halakani da kwanan asibiti. ni dai ina Fatan wannan zuciyar taimakon naka ya yi sanadiyar Shigan ka Aljanna Sadiq." Sadiq yace"Ameen tare da kai da ka ke taimakamin wajen kwanan asibiti." Ya fad'a ya na Dariya Tahir ya Tureshi yana Hararansa har zasu fita sai ya ja ya Tsaya ya juya ya na kallonta barci ta ke sosai abun mamaki a yadda ta kwanta ko motsawa ba ta yi ba ta na nan a yadda ta Dunkule. Tahir ya juya ya na kallon in da ya ke kallo kafin ya samu zarafin mgana yaga kawai ya fara tafiya har zuwa gabanta mamaki bai barsa ya yi mgana ya bi bayan shi yana Taba wuyansa da yaji ya sage. Sadiq kujeran ya duka ya na Dan Bubbugawa ya rasa da wani suna zai kirata Tunda bai san sunanta ba. Daman barcin nawa a cikin tsoro na ke yin shi mai cike da mafarkan Amma, shiyasa ina jin ana Buga gefena nayi zaraf na tashi. Kai na D'ago cikin Firgici Fes sai acikin idanuwansa na kallesa shima ya kalleni. Mikewa ya yi kafin yace"Armm ki tashi ki yi sallah." Kai na gyad'a masa kafin na Sauko da Siraran kafafuna a kasan Tayels din Asibitin kamar yadda na bi kafar tawa da kallo haka shima ya bi ta da kallo kafin yace" Kada ki yi yawo haka  ba  takalmi acikin asibiti" Cikin sanyin murya nace"ban zo da takalmin ba ne." Na fad'a daidai ina ta shi Tsaye kuguna ya amsa da bayana jikina ya yi tsami na cije baki ina kara Daidaita natsuwata tare da gyara Lullubin zanin jikina ko D'anwali ba bu a kaina Tarin suma na ko gyara babu shi ya saka kan nawa ya cika. Ba tare da Tunani ko shawara ba Sadiq ya cire takalmin kafarsa ya mika min ya na fadin"Zaki iya saka nawa? Yadda na dago kumbararun idanuwana na kallesa haka Tahir shima ya kallesa cikin mamaki da Al'ajabi lalle Sadiq kullum cikin yin abubuwan ban mamaki ya ke yi. Ni kuma na kasa mgana Alherin bawan Allah gareni mai girma na kalli Takalmin har ya ciresu ya Turomin gabana kafin nace"sun yi min yawa." Kai Tsaye yace"Ki saka hakanan in na fita sai na siya miki ko silifas ne.". Dago kaina nayi na kalleshi idanuwana cike da kwallah nace"Nagode sosai Allah ya jikan magabata." Bai amsa ba ni kuma sai na zura kafafuwana cikin takalmin ina Ruwan Sauro ko kwatan takalmin ban ci ba, Ina da Doguwar kafa sai dai ba kauri ne ina kallon kafata sai da dariya ta kamani cikin mirnishin nace"Kafata karamace ka ga ni ban ci ko Rabi ba." Sadiq ya jinjina kai kafin yace"Nagani." Sai alokacin da na kara Dagowa na kula da Tahir ya kafeni da ido ya na kallona cikin mamaki na kallesa na kuma kallon Sadiq ganin inda na ke kallo yasa ya juya ya na fadin"Abokina ne Tahir." Sai na jinjina kai cikin sanyin murya nace"Ina ina kwana." Tahir ya amsa da Lafiya lau. Ya na kara kallona daga sama har kasa. Hasken Fatata sai ya fara kashe masa ido ballatana ga hasken fararan kwai sai Fuskar ta yi wani 'Dau da ita. Sadiq yace na samu wata Nurse in tambayeta in da zanyi sallah. Sai na amsa masa suka fice suka barni kamar yadda yace haka nayi d'in wata Nurse na tambaya ta nuna min bayi na shiga na kama ruwa na yo alwala. Duk da ba na sallah gwara na wanke jikina da kafafuwana da suka yi min tsami. Dawowa na yi na zauna in da na tashi Amma na ke son gani kamar sun sani sai ga shi wata nurse tazo tace na biyota da Sauri na tashi na bita zuwa wani Daki akwai gadaje uku ne adakin Guda d'aya akwai mutum Ashe Amma ce har an kawota dakin da zata Huta. Ba ta dai Tashi ba ta na barci na karisa kusa da ita ina kiran sunanta jikina ya na rawa Nurse din da ta kawoni tace"Alluran barci na tare da ita saboda ta samu hutu. Jininta ya yi kasa ne sannan akwai low sugar" Bayanin da mutumin nan ya yi min kenan au Abubakar Sadiq yace sunan sa daman ma su suna Abubakar masu Tsausayi ne da jinkai. Nurse tace min na zauna ammh kada na yi hayaniya ko Surutu. Na gyada mata kai har zata fita ta dawo ta na fad'in"Ina yayanki da kuka zo jiya tare? Kallonta na yi cikin mamaki kafin na Tuna wanda ta ke mgana da Sauri nace"Sun ta fi masallaci." Sai ta gyada kai ta fice. Farar kujeran da ke wajen na ja na zauna ina kallon Amma cikin Dare daya ta rame ta Fita Hayyacinta ruwan da aka saka mata na rika lekawa naga yana tafiya ita kuma sai barci ta ke yi cikin sukuni da salama. Shuru ba su dawo ba har gari ya waye sai na fara Tunanin ko sun tafi ne,sai chan sai ga su sun shigo again wannan Nurse din ta kawo su dakin. Suna shigowa na mike ina kallonsu yana rike da Leda baka a hannunsa shi abokin ya na daga baya kamar bai da son mutane. Ni ya mikama ledar na saka hannu na karb'a lokaci daya ya na fadin"Ashe sun bata daki" Kai na gyad'a masa batare da nayi mgana ba. Cikin natsuwarsa da lura ya na dashi Tun jiya yace"Waina ne sai ruwan zafi ki samu ki sha tun jiya baki ci wani abu ba." Kai na gyad'a masa kafin nace"Nagode sosai Allah ya saka da Alheri." Bai amsa ba sai ma ya karisa gaban Amma ya na kallonta kafin yace"Allah ya bata lafiya." Na amsa da Ameen. Tahir daga chan baya yace"Zamu makara fa Sadiq." Jin haka yasa ya kalleni sai kuma ya Duka ya cire silifas din kafarsa da ya siya a waje ya mikamin ya na fadin"Saka wannan shi zai fi yi miki daidai." Da Sauri na cire na kafata na saka Silifas din, lokaci daya ina fadin"Sannu da kokari nagode.". Ya jinjina kai kafin yace"Zamu tafi. In da wani abu ki kirani kin ji ko? Ina so nace masa ba ni da waya ballatana ma lambarsa. Ban samu damar mgana ba Abokinsa ya kara fad'in"Sadiq." Da Sauri ya juya ya na Fadi'n"Mu je Tahir sai mun dawo." Kokarin Biyosu na yi har wajen Dakin da Sauri ya juyo ya na fadin"Ki koma ciki." Ya fad'a ya na kallona sai na kasa masa gaddama cikin ladabi nace"To." Na juya na koma sai da yaga shigata sannan ya wuce ya bi bayan Tahir. Har suka samun abun hawa ba wanda ya yi mgana sai da suka kusa Sauka sannan Tahir yace"Wai yarinyar nan wani irin fari gareta? Albinion ce.? Sadiq ya yi kamar bai jisa ba sai da ya kara maimaitawa sannan yace"Ina zan sani Tahir. Me yasa baka tambayeta ba? Tahir ya tabe baki kafin yace"Ina ruwana da ita  wai a ina ka had'u da su? Na ganta ne kamar buzayen nijar masu gudun hijara." Sadiq ya yi mirmishi kafin yace"Bansani ba fa Tahir nima jiya na fara ganinta." Daganan ya fara ba shi labarin yadda ya Had'u da Hasiiya jiya.. Ya karishe da fad'in"Ni ko sunanta ban sani ba jiya na fara ganinta." Tahir ya rike baki kafin yace"Sadiq anya ba gamo ka yi ba? Sadiq bai bashi amsa ba sai da suka Sauka sun fara takawa sannan Sadiq ya ba shi amsa da cewa"Nima na yi tunanin haka da farko, sai daga baya na gane mutane ne" Dariya suka saka gabadayansu. Tahir yace"Ni dai ina fatan kada garin wannan Shegen son taimakon nan naka watarana ka kai kanka da kanka a saida ka." Sadiq yace"To Ameen"  yana mirmishi, Koda suka isa Dakin su Takwas saura a gurguje Tahir ya kunna musu gas ya dora Ruwan zafi, Shi kuma Sadiq ya saka a kettlo tunda akwai wutar nepa. Saboda suna Sauri Tea suka sha Tahir sai Kunkunin ya ke yi Sadiq ya ja masa kwanan wahala ga shi yanzu maimakon ya huta zai kara fita kuma. Sadiq dai bai tankasa ba Tahir ya rigasa fita shi ne karshe ya kulle dakin na su saboda ya makara yasa  ya hau mashin Saboda ya isa akan Lokaci. Ko achan wajen aiki yarinyar na yawon fad'o masa arai. Sai biyu ya taso daga wajen da ya ke Hidimar kasa. Saboda yanayin da ya kwana aciki yasa bai tuna da Danwake ba. Ko da ya dawo ya iske Tahir na ta sharan barci zafi ya ke ji yasa ya Dibi Ruwan sanyi ya yi wanka ya Sauya kaya ya iske Tahir ya Dafa Farar shinkafa shi Tahir da kifin gwangwani yaci ya rasa me ya ke had'a Tahir da cin kifi. Shi kuma sai ya Dumama miyar da Umma ta yi musu akwai saura ya ci da Naman sa. Sai da ya koshi sannan shima ya bi lafiyan gado ya kwanta sai la'asar ya tashi ya Bugi Tahir ya na fad'in"Sai ka tashi an yi la'asar." Tahir yace"ni ka kyaleni bayan duk kai ka kai ni in da nagaji." Sadiq bai kulasa ba ya tashi ya fita waje ya kama ruwa ya yi alwala ya tafi masallaci Tahir sai ana Tahiyar karshe ya shigo masallacin Da suka idar shi ya tsaya addu''a Har Tahir ya gama na shi Sallar suka fita tare. A hanya Sadiq ya kalli Tahir ya na Fadin'"Sai yanzu na tuna. Dazu nace ma yarinyar nan ta kirani in suna bukatar wani abu ammh Kasan me? Tahir yace"Sai ka Fad'a.? Sadiq yace"Ban ko karbi lambar wayarta ba. Itama ban bata nawa ba." Tahir ya kallesa kafin yace"Allah yasa ma ta na da wayar." Sai Sadiq ya yi shuru kafin yace"Kuma fa domin ni dai ban ganta da waya ba. Ko kuma zai iya yuyuwa rudewa yasa ba ta zo da ita ba." Tahir ya jisa ammh bai tankasa ba. Suna komawa yaga  Sadiq na shiri har da saka manya kaya cikin mamaki yace"Ba dai asibitin zaka koma ba? Sadiq yace"Eh ai tare zamu koma? Da Sauri Tahir yace"Wlh tallahi ba in da zani. Kai dai da ka siyan ma kanka Allah ya kiyaye Hanya." Sadiq yace"Ameen addu'ar da ka yi ma ta wadatar." Shigan manyan mutane ya yi har da Hulansa kube mai kyau zanen aikin jikin Shaddarsa mai ruwan madara ya yi ma Tahir sallama ya fice. A hanya ya kira Abba ya ce ya na son kudi Abba yace to zai turo masa. Kai Tsaye yace"Abba wasu bayin Allah ne ke bukatar taimako na lafiya shi ne na ke

Chapter 16 of 24