na Saidawa sai su awara a samu a ci a sha ruwa.
Duk da ina nuna komai ba komai ba ne ni kada'i nasan Halin da na ke kwana ina tashi, Kirjina suya ya ke yi ji na nake yi kamar ba ni da Sauran amfani,ammh in na Tuna Amma sai naga ina da amfani a wajen Amma bayan ni bata da kowa.
Salisu na raina, ba ni da in da zan samu labarinsa shiyasa na ke masa addu'an Allah ya bashi lafiya ya dawo da kafafunsa cikin koshin lafiya.
Habiba sai asabar da Lahadi take zama a gidan ranakun Sati kuma tana zuwa makarantar Boko da Safe, da yammah kuma taje islamiya, da Daddare kuma ta je makarantar Dare.
Shiyasa yawancin ayyukan gidan suna kaina, Daman kula da Amma ni na Daukeshi a wuyana da kaina ina Kafa kafa da lafiyarta fiye da tawa lafiyar.
Adda Rukayya sai sati uku da Faruwar abun ta zo gida tana ta yamutse yamutsen Fuska tazo ta sameni ina Dafa shinkafar yammah, tunda mun fara satin da ya shige lokacin da ta shigo ina kofar Dakin Amma ina gyaran shinkafa.
Sama da kasa ta kalleni ba ta tankani ba sai ni ce na yi mata mirmishi ina fadin"Adda Rukayya ke ce tafe?Sannu da zuwa."
A saman lebe ta amsani ta rab'ani ta shige ciki ina jinta Suna gaisawa da Amma. Shuru na dan wani lokaci kafin naji ta ta na fad'in"Amma ya mganr da muka yi? Tunda Fati ta fad'amin Shima Salisun ya saki Hasiyar"
Kai Tsaye Amma tace"Wata mgana kenan?
Yaya Rukayya tace"Mganar tafiyar Hasiya wajen Adda Hari mana. Amma shawarar nan ita ce Mafita haka ma Baban su Amna ya ce da na Fad'a masa."
https://chat.whatsapp.com/CPRnRPcAD5K8vEY91Ziz8V
+201123302418
Ban ji me Amma ta ce mata ba sai dai naji Muryan Adda Rukayya a harzuke tana fad'in"To shikenan Amma ni mafita daman na kawo ai shikenan"
Ban tsaya jin sauran mganganun ba na tashi daga wajen zuwa wajen ma zubar ruwa na wanke shinkafa, acikin raina ina ta kokarin karfafa kaina, sanda ta fito ina zuba shinkafan ne cikin Tukunya.
Tunda waken Dabam mu ke dafa shi,Haka ta wuce ni Fuu ko kallo ban isheta ba ni ce na bita da cewa "A sauka lafiya"
Ina mirmishin takaici, matan gidanmu suka bita da kallo tunda duk suna waje ana hada hadan d'ora na dare, Masu d'orawan kenan irin su Maman Boy sai zaman gulma da yi da mutane tana fita suka fara kuskus ana kallona ana mgana, komai za su Fad'a bazan damu ba tunda sai bango ya Tsage kadangare ke samun wajen shiga.
Sai da Ramatu ta leko ni Daga awo take tazo Dubani, a bakinta na ke jin Salisu an yi masa aikin an daure inda ya samu karayan Musbahu ya kirata ya ke Fad'amata kuma yadda ya ke Fad'a jikin Salisun da sauki tunda yana cin abinci sannan kuma yana mgana.
A raina na yi Hamdala a fili kuma nace"Allah ya kara masa lafiya"
Ramatu ta amsa da Ameen sai yammah ta tafi, Muna ta zencen haihuwanta tunda ta shiga wata na Tara, Har ina mata Fad'an ta daina Fita hakanan kada ta haihu a Hanya.
Muka yi wasa da Dariya na Saba Rakata har bakin Titi ta samu adaidaita ko mashin, ammh yau ban fita ba saboda ina kauce ma idanuwan mutane a kaina.
Itama sanin haka yasa ba ta damu ba Habiba na saka ta rakata har bakin Titi, tunda Ranar ba islamiyan yammah jumma'a ce.
Ba mu da matsalan abinci Tunda muna ci cikin sana'ar mu, dagani sai Habiba Amma ce ta kan bukace koko ma wani lokacin amm ni in na ci Danwake na da Safe sai wani Daren kuma inna ci sauran Shinkafan da na kan rage mana ni da Habiba, Amma koko na kan Damata da Daddare ta sha, da Safe kuma wani Lokacin Add Fati na kawo mata kayan tea. Bata cika sha ba, in dai ba duka Zan had'a mana mu sha ba.
Ranar asabar da Safe ina Hada had'ar kwabin Danwake sai ga kiran Adda Fati ta wayar Maman boy, sai da gabana ya fad'i da Maman boy ta kawomin sai dai Hankalina ya tashi da naji ta na Fad'amin Ramatu ce ta kirata taje asibiti tun jiya maranta ke ciwo to sun Riketa sun ce Haihuwa ne, tana asibitin Abu na Tudun wada naje na sameta. Ina jin haka na ruga Daki na Fad'a ma Amma cikin Sauri tace"Maza ki hanzarta ki je ki sameta. Allah Sarki Ramatu Allah ya raba lafiya"
Cikin Saurin na Sauya kaya ko wanka ban tsaya yi ba, Habiba na bar ma kwabin Danwaken tunda ta iya cikin kudin Ciniki na Dauki 1k na mota na Zurma hijabina har kasa mai ruwan kasa,Fuskata Fuskata kozai kozai haka na fita Maman boy har ta gama yee kuwa da mganar sai fad'i suke yi Allah Sarki Ramatu Allah ya Raba lafiya.
Sai ga shi har na kai bakin Titi ina ta Faman rufe fuskata da Hijabina, adaidaita na samu zuwa Pizzet, Dagachan na samu na Tudun wada,na sha wahala kafin na gano Ramatu. Haihuwa ce ammh sai zuwa Dare sukace sun dai riketa ne tunda Maran na Damunta nayi mata sannu ta amsani cikin yanayin ciwo.
key din gidanta ta bani tace na je na kwaso kayan haihuwan da ta had'a acikin karamin akwatinta,vsai zannuwa da zan Dauko mata. Sai Fulas da Filo da kayan tea duk ta ce na Dauko. Sauri Sauri ko na sake hawa mashin naje na Dauko mata komai da komai na iske Fulas din cike da ruwan zafi Daukowa kawai nayi, kayan tea din kuma a kitchen dinta na gani na kwaso su duka.
Tunda Nura kam ba abunda ya Rage Ramatu da shi.
Sanda na dawo naguda gadan gadan,ina asibitin Inna talatu tazo bata jima ba tatafi, tunda kannen Nura da mahafiyarsa sun zo duk muna tare da su,bRamatu ta sha wahala sosai Nura baya nan sun tafi aiki Abuja Hankalinsa duk ya tashi yana ta kiran kannensa a waya domin jin ko ta haihu? ba ita ta samu bud'e ido ba sai Dare misalin goma.
Ni Daman ban ma yi tunanin komawa gida ba,hankalina bai kwanta ba sai da Nurse ta fito tace Ramatu ta sauka an samu y'a mace sannan ni da kannen Nura muka saki Hamdala.
Cikin lokaci kalilan Labarin Haihuwar Ramatu ta yi Tambari ni dai ba waya a hannuna ammah na san Inna talatu ta Kira Adda Fati, ita kuma zata sanar da Amma ko ta wayar Maman Boy ne.
Ni nace ma Kannen Nura su tafi gida ni na kwana da Ramatu ,sai Daukan bby na ke yi farinciki ya cikani Yarinyar mai kyau da ita, gaskiya jarirai na da ban sha'awa Ramatu sai Faman dariya ta ke yimin, duk ta rame Lokaci d'aya lalle Haihuwa yakin mata.
Ranar asibitin ya cika da Mutane Dangin Nura, shima adaran ranar ya Dawo, Bakinsa har kunne ni kuma ina masa tsiyar angon karni yana kwasar Dariya,komai da zamu bukata Nura ya siyama na. Sannan abinci daga gidansu Nura ake kawo mana Tunda suna Wajen Danmagaji ne.
Ramatu tayi ta yi naje gida na yi wanka nace mata bazani ba sai ta kyaleni, Washegari sai ga su Inna talatu har da Adda Fati da Amma, bakina ya ki rufuwa ganin Har da Amma akazo.
Zuwa chan kuma sai ga mutaan gidanmu Maman boy ce Jagoran su. Sun jima sai yammah suka tafi Amma ta zo min da kaya kala Biyu da Hijabi tunda tasan gidan Ramatu zan wuce,vkamar ko ta sani a daran aka sallame mu muka koma gidanta,Sai bayan suna zata koma wajen Inna talatu ta yi jegonta.
Ramatu ba kawa ba ce a wajena yar'uwa ce shiyasa komai na yi mata ban Fad'i ba, kan jikina na ke Hidima da ita ko ruwan wankan ta Safe da yammah na Dauke ma Kannen Nura ni nake yi girki ne suke taikamin wani Lokacin, ammh har wankan Bby na iya sai dai Kanwar maman Nura ke zuwa da Safe ta yi mata wanka Ramatu kuma Amma ce yakamata ta zo ta yi mata to bata da lafiya sai aka Dauketa mata,wata abokiyar wasan Ramatu ke zuwa ta yi mata Safe da yammah.
Ni kuma na ji da yan wanke wanken kayan Ramatu da baby, Nura kam ya shirya ma Ramatu sunanta daidai karfinsa, Shinkafa aka Dafa da wake Jalop,har da zobo Ramatu ashe ta yi mana Dankin wata Atamfa Cinghamvi, iri d'aya sai dai na yi hawaye,ita na saka na ci suna ba ni da Dan kunne da Sarka nata ta bani na akwatinta da ya rage guda d'aya bata yi amfani da shi ba. Na fito tsab da ni nima ina walwalina ni ce kuma kan komai na abincin, Adda Fati tun Safe tazo nan ta kwana ita da kanwar Inna Talatu Rahane daga Soba tazo.
An yanka Raguna Guda Biyu Yarinya taci sunan mahaifiyar Nura, Khadija Ramatu tace zamu rika kiranta Noor haske.
Washegari su Adda fati suka yi soye aka raba naman gida uku kashi Daya na dangin Nura D'aya kuma na Nura da Ramatu,D'ayan kuma na danginta, duka Ramatu tace kashi d'ayan a kai ma Inma talatu ta ba wa wad'anda suka kamata cikin na su ta Dibarmin nawa, sai da ta kwana Goma ta koma sabon gari gaban Inna talatu sai na rakata har chan sannan na wuce gida da sha tara na arziki daga Ramatu da mijinta.
Atamfa ta bani tare da su manshafawa, kayan kwalliya takalmi Sabulan wanka da na wanki, Hijabai kala biyu sabbi,ta kuma had'amin da kayan abinci tace na kaima Amma tunda gida zata koma kuma daidai gwargwardo sun fi mu rufin asiri. Nura kuma Dubi biyar ya bani nayi ta godiya har ina kwallah da na koma na nuna Amma itama tace an kawo mata nama mai yawa da yajin jego har da Fallen zani da Omon wanki.
Amma ta kalleni bayan ta gama Daga kayan da na zo da su Habiba ta Dauki Hoda da Jan baki tana fadin"Adda Hasiya ni dai ina son kayan kwalliyar kin ji don Allah"
Ina mirmishi nace"Ke daman nace zan ba ma wa dauka Habi"
Ta fara tsallen Murna muna yi mata Dariya ni da Amma. Dubi biyar d'in da Nura ya ba ni na mikama Amma ina fadin"Amma sai mu kara a jarin shinkafa ko?
Amma ta ki karb'a Lokaci daya tana Fadin"A'a kudin ki ne, ki rike a hannun ki Hasiya"
Ban samu zarafin mgana ba mukaji Ana maraba a tsakar gida, kamar Muryan Adda hari na rika ji sai da Habiba ta fita sai ga ta ta shigo da Buhu a hannunta bakinta har kunne tana Fadin"Adda ce da Badd'o'
Amma ta washe baki tace"Harin ce da yamman ne? Maraba da Hari ta Jari"
Hakan ta kan Fad'a daman Saboda chan Gada kowa da haka ya san su,in aka ga Amma ace mata Jarin Hari, in kuma aka ga Inna sai ace mata Harin jari.
Adda Hari bakinta har kunne Saboda Murna ni kaina murna duk ta cikani Yarta autarta Badd'o kuwa haka ta nade jikin Amma ta na mata oyoyo da Gurbattacen Hausanta,Tunda su sun fi jin Fullanci hausan na su sai a hankali ko Amma da zama ne ya yi zama bakinta yaji Hausa, ammh duk da haka akwai fullanci a harshenta mu kam mukan ji iya sunayen abubuwa da baza'a rasa ba.
Amma ta kasa zaune ta kasa tsaye,Sai da suka yi sallah suka natsa Ruwan zafi na dafa musu suka sha Tea da Buredi sannan aka zauna saman Hira bayan Inna Hari ta kwance Buhun tsarabanta,su Daddawa ne sai Fura da Nono da manshanu,sai garin kuni da yawa,Amma nata godiya ina tayata Habiba da Baddo na gefe suna ta shan Hira.
Adda Hari bata sako mgamar aurena ba ko kad'an ba Duk da Amma ta kirata ta wayar Adda Fati ta fad'amata mutuwar aurena da Salisu. Daman tace tana tafe in ta samu dama sai da Safe ta yi ma Amma zencen Lokacin ina waje ina Hidimar danwake, Habiba da Baddo suna taimakamin da Zubawa suka yi mganganun su adaki da yar'uwanta sai da muka gama na koma Daki sannan Adda Hari ta kirani nazo gabanta na zauna Kaina ta Dafa kafin tace"Ki kwantar da Hankalin ki Hasiya. Babu wani farar kafar da kike da shi, sannan ke baki gaji Maita ba. Watarana sai labari haka Allah ya Tsara" na kalleta ina gyad'a mata kai Duk da tana cikin Rugga Adda tana da iliminta daidai gwargwardo.
Sun cigaba da mgana da Amma duk a kaina ni ko ina chan gefe ina gyara kayana, ina ji Amma na fad'ama Adda Hari mganganun Adda Rukayya.
Adda tayi Dariya kafin tace"Kyaleta Jari. duniya ce zata gayama Rukayya gaskiya. Mganar Hasiya kuma ni kin ki min ne Jari da Tuni ta na hannuna."
Amma tace"sai dai ki dauke mu gabad'aya"
Inna Hari na Dariya tace"Duk zan iya da ku kin sani. Tun yaushe na ke hakilon ki dawo wajena?
Amma ta kad'a kai kafin tace"Saboda yaran nan ne Hari"
Inna Hari tace"Yara suna ina? Fati na gidan mijinta Rukayya ma haka. Hasiya da Habiba ne kuma na ce dukkan ku zan iya rike ku jari zaman ki anan bai da wani amfani ga shi ba ki da ishashiyar Lafiya.
Hasiya ce kuma kinga ga irin jarabawarta in zaki amince duka sai mu tattara mu koma da ikon Allah Hasiya zata yi auranta achan ta kuma zauna lafiya"
Amma ta yi shuru ba ta yi mgana ba ni kuma saboda ba da ni ta ke mgana ba yasa ban saka musu baki ba. Ammh ni kaina zan so mu koma chan da Rayuwarmu kila Hankalin mu zai fi kwanciya.
Adda Hari sati tayi mana sannan ta koma, kafin ta koma na rakata gidan Inna talatu ta yi ma Ramatu barka da yar Dubunta tace a siyama Noor kwalli, Sannan har gidan Adda Fati mun je itama tazo ita da mijinta sun gaisheta Adda Rukayya ce bata zo ba kuma bata kira waya ba, sannan ba wanda ya damu da ita. Cikin Dubi biyar din da Nura ya ba ni na cira 1k na bama Baddo, Adda Fati ko 8k ta kawo ma Amma tace a bama Adda Hari tayi na Mota sannan ta siyama Baddo kayan kwalliya da Hijabi.
Adda Hari ta koma akan Amma tace in ta shirya zata kirata tace ita ba ta da matsala.
Sauran Dubu hudu kuwa saka na ba ma Kultumen gidanmu tunda sana'arta ne, ta sakama Noor Huluna guda hud'u masu kyau, da ta gama naje da kaina na kaimata duk da sai da ta yi min Fad'an me yasa na kashe kud'ina? Na harareta ina fadin"Bansani ba"
Dariya ta yi har kuma a ranta taji Dadi, shi alheri komai kankantar shi yana da dadi sosai.
Kwanci tashi babu wuya a wajen Ubangiji, Har Ramatu ta gama jegon arba'in ta koma gidan ni naje na yi mata kwana biyu na tayata gyaran gidan,sai da Nura ya dawo sannan na koma gida Amma jiki ya yi kyau tunda in ba na nan ita ke Danwake,da yammah kuma ta yi shinkafa da wake, Mganar komawar mu wajen Adda Hari kuma ta sha ruwa tunda har Haya naji Amma ta yi ma Adda Fati mganar sake biyan na shekara. Wannan D'akin dubu Talatin muke biya duk shekara.
Tunda naji haka sai na cire ma raina Sauyin muhalli na kuma san dalilin Amma na kada ace da gaske zargin da ke kaina Shiyasa muka bar gari, tana danne komai ne saboda ni.
Adda Rukayya sai bayan Tafiyar Adda Hari tazo ita da ya'yanta kuma ma aranar sai da ta kara yi ma Amma mganar nan dai Amma ta kalleta ido cikin ido kafin tace"Ke Rukayya ki fita idona. Na ce ki fita idona na rufe ina ruwan ki da Hasiya ko akan ki take? Kina ci da ita ne ko kuwa akwai abunda kika Dauke mata ne da kika Kwazzabi kan ki sai ta bar miki garin nan ne?
Sai Adda Rukayya ta Fara kame kame Ran Amma ya baci ta nuna mata kofar fita tana fadin"Daga yau sai yau in dai kin san mganar Hasiya zata kawo ki to na gode ki zauna gidan ki ba sai kin zo ba, da ke ko baki zamu cigaba da Rayuwa Rukayya shi ruwa cikin cokali ya isa mai Hankali wanka"
Sum sum ta yi ta kai ta fara ba ma Amma Hakuri ganin ranta ya baci yasa har ta jima agidan, ganin har da yaranta suka zo yasa na yi jallop din shinkafa da rana mai allayahu yaranta ta koya musu bakin Halinta ko cin abinci ba su yi sun raina.
Amma ko har ta tafi bata kara kallonta ba, Kunya taji ta zaro dubi biyu ajaka ta sauke Gaban Amma tana Fadin"Amma ku kara wlh Baban su Amna ne ba su yi albashi ba."
A ciki Amma ta amsa da cewa"Allah ya ba da lada"
Har ja ya'yanta suka fice Amma bata kalleta ba ni ce ma ma aiki Habiba ta siyoma yaran Biskit, a rene Adda Rukayya ta amsa ba ko Nagode ni kuma bai dameni ba saboda nasan Har Abada Adda Rukayya ba ta isa ta sauya jinin da ke Tsakanina da ita ba
Ashe taji Haushin mganar Amma ta taka har Gidan Adda Fati ta na Fad'amata tazo Amma ta rufeta da Fad'a sabo da ni. Sannan har su Anma ba ta ja ajiki ba ta na jin haushinta domin ta kawo mafita.
Har ta na fad'in"Fati nima fa ina son Hasiya ai kanwatace kamar yadda ta ke kanwarki. Bana jin dadin zarge zargen da ke kanta ne, ni wlh ina mata Fatan Rayuwa mai kyau in ta koma gaban Adda Hari"
Adda Fati dai ta bata baki, ammh ta rike Amma ta ki kula ya'yanta Saboda ni,ita kuma tana so na ne ta nemar min mafita da Adda tazo tana gayama Amma,vkyafci ta yi kafin tace"Fati bar ni da Rukkyya Mutuniyar wofi ce. Ta zabi miji da danginsa da mutanen Duniya akan uwarta da danginta. Ba inda zamu koma tunda ba mu gagara lallaba rayuwarmu anan ba Fati. Adda ba shi gareta ba karfin Hali ne bazan kwashi jiki na koma na D'orata mata nauyi ita da ya'yanta ba. Sannan bazan bar Hasiya ta koma ba tunda nan aka Haifeta akwai nakasu in har na ce ta koma chan da zama"
Da haka Amma ta kashe mganar komawata wajen Adda, da Addan ta kira ce mata kawai ta yi"Adda zan zo dai na miki kwana biyu gabadayanmu in Habi ta yi Hutun makaranta in sha Allahu" Adda bata damu ba tace tana jiran mu duk sanda muka zo.
Tundaga Lokacin Adda Rukayya ba ta kara ma Amma mganar ba ko ta zo gidan sai ta koya ma kanta kame bakinta.
Ni ko na kama mutumcin kaina Daga gaisuwa ba na shige mata Hankalina na kan sana'ar da muke ci da kanmu da Rufin asirin mu, tare da Kula da Amma cikin wattani uku duk abubuwanan suka faru sai abunda ya Faru na aurena da Salisu ya lafa tunda har ina Fita Diban ruwa ko zuwa kasuwa ko chemist siyo mgani. Ba fargaba tunda daman abun na Lokaci d'aya ne yana wucewa shikenan kamar komai bai Faru ba.
A bakin Mutanen gidanmu naji Salisu ya dawo gida an saka masa karafa a kafafunsa na Dori da Karafan asibiti guda biyu ya ke tafiya.
Ammh duk bayan wata daya suna komawa sannan ana masa Dressing a gida.
Ni dai nawa yi masa fatan alheri da Fatan samun waraka komai tsakanina da shi ya jima da karewa kamar bai faru ba.
Na kuma tabbata daga kan Salisu kila na gama aure tunda yanzu dai ko daga nesa wani ya zo da sunan aure na, zuwa daya zai yi bazai kara Dawowa ba tunda za'a karanta masa komai a kaina har da karin gishiri da maggi.
Nasan kaddara ce ko in ce Jarabawata ce haka.
Ammh ban taba Tunanin Wata Kaddaran zata sake bibiyata nan kusa ba.
Bani kuma da masaniyar zanen kaddara ta na kusa da ni ban sani ba.
Slm ina maiso taga tayi kiba jikinta yayi kyau tazama yar lukuta 😘ina maiso taga nono yacika yayi kyau ina maiso taga duwawu yafito kinzama cikakiyar mace ❤️ina maza da basacin abinci ina maza masuso suyi kiba ina yara da basuda kiba ina mai farin cikin sanar daku *ZUMAR K'IBA*, zumace wadda take saka k'iba cikin kwana 7 da yardar Allah *ZUMAR K'IBA* zumace mai inganchi wadda aka had'ata da magun-gunan gargajiya Masu kyau da da tasiri ajikin d'an Adam,hajiya indai kina fama da rama d'an gwada shan zumar mu kisha mamaki indai kika sha zuma sai kin chanza..,Ina masu fama da Ciwan sanyi duk nacin sanyin ki hajiya kikai amfanin da maganin Mmn khairat saikin warke duk ko iya da d'ewarshi ajikinki..Domin k'arin bayani👉 WhatsApp no 07044450136, 08167453086
*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
*Janafty*
*TSAKA MAI WUYA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk
Ku zo ku yi sayayyarku tare da Yar Gidan Imam, inda za ku sami komai cikin sauki, tun daga kan kayan kicin, kayan yara,atamfofi da lesissika uwa uba da kayan gyaran jiki irin na manyan matan da suka San kan su,har counselling mu na yi yadda duk damuwar da ki ke ciki a game da aurenki da gyaran jikinki zaki samu solution. Ku dai ku shigo cikin wannan gidan na karamci kai tsaye domin more tagomashin da ke ciki.
*05*
*GUSAU_ZAMFARA.*
_Area:Tudun wada_
*Lahadi, 10:40am*
"Wai wani shegen ne ke min burutun a shashe na da Safiyar Allah nan?
Ta fad'a cikin kufula da takaicin yadda aka maida ita banza tana ta mgana ita kad'ai.
Kokarin mikewa take daga zaunen da take lokaci d'aya tana Laluban sandar ta, tana cigaba da fad'in"Ko wani d'an jakar uba ne ya bari na fito mu ga juna yau sai na Deb'e masa albarka"
Ta samu mikewa kan kafafunta, ta kuma samu nasaran ganin Sandarta ta karfe a gefenta sai dai kamar akwai sauran rina akaba, tunda sai faman lalube take yi kamar ganinta na da rauni.
Garin lalubenta ne hannunta ya kai kan wani bakin gilashi ta dauko shi tana fad'in'"kaji rashin tabbas na Abun nasara yanzu gilashi na fuskata na nemesa na rasa. Mtswww aikin banza da wofi"
Bum! Taji kamar an fad'o dakin nata a rashin sukuni a zafafe ta saka gilashin nata cikin Masifarta da tun tana matashiyarta ya zame jiki har tsufanta tace"Nace wai waye zai zo ya Dameni da burumtu ne? To ko waye in bai yi mgana ba Allah ya tsinee..."
"Innani ni ce".
A kafad'a da wata sanyayyiyar murya mai cike da yarinta da kuruciya. Wacce aka kira da Innani ta d'ago kanta a masifan ce tana yamutsa Tace"Ke ce wa? Baki da suna ne? Ina na ke iya gane muryoyin yaran gidan Sulaimanu, ku rika wani make murya kamar wasu ya'yan gyare"
Ta fad'a lokaci d'aya ta na kara gyara zaman gilashin da ke fuskarta sosai ya cika mata fuska kir kuma ta sauke ganinta kan yar yarinyar dake gabanta sanye da Hijabi mai ruwan kasa. Kanta na kasa tana wasa da yatsun hannunta.
"Sultana ce. Sultana ce Innani"
Baki Innani ta washe kafin tace"Au ki ce Sulsana ce ta wajen Salamatu ko nace Matar MAGAJIN GIDA. uwargida Sarautar mata a gidan Abubakar Saddiqu alkawarin Allah sai ya cika da yardan Allah, ya ki nan yar nan taho ki zauna kusa da ni"
Ta fad'a tana ya fito ta da Hannu. Jikinta kamar ba karfi ko na ce wacce ta tashi matsananciyar jinya ta karisa gefen Innani ta zauna. Innani ta gyara zama tana fad'in"Ke kam ki rika kama jikin ki mana Sulsana. Ayi mace kamar wahainiya saboda rashin kuzari"
Ita dai kanzil bata kara ce mata ba, kanta na kasa tana wasa da yatsun hannayentaa. Innani ta kara kallonta cikin nazarinta kafin tace"Daman kece kika zo kina min bare bare a sasana? Tsiyana da ke wauta ko rashin wayau ne ma zan ce ni Dije? Ayi yarinya sai shegen tsoron mutane. Allah dai ya yaye miki kin ji ko"
Wannan karon ne ta murmusa ammah ba tayi mgana ba, ganin haka yasa Innani ta washe wawulan bakinta da babu Hakora ko d'aya duka sun gama barewa, Daman na Roba take makalawa in zata ci abinci abubuwa masu tauri kuwa sai dai ta saka wuka ta yi gutsi gutsi da shi,
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 24