Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da su izuwa can kololuwar sama ya kama tsala gudu yana keta giza gizai tamkar gudun taurariwa mai wutsiya A Dai dai wannan lokaci ne aljani Raugatul Aguwanu yaji dan motsi a cikin kunnensa har ya daga dan yatsansa guda zai cusa a cikin kunnen yaji an fara masa susa Page 149 zidane kd 180 TASKARNOVELS.COM.NG Dan karen dadi daya ji ne yasa ya fasa sanya dan yatsan nasa ya saki jikinsa cikin kwanciyar hankali ya cigaba da tsala gudu: A Wannna lokacin gimbiya Shalbirat ta kamu da tsananin farin ciki takama murmushi: Boka sadusa ya dubeya cikin mamaki yace ke kuwa mene ne ya saki farin ciki haka har kike ta murmushi da yake baki? Shalbirat tace gaba ai dolene na kasance a cikin farin ciki, tunda rabona da gannin fili haka ba a cikin keji ba yau shekara goma sha tara kenan: Da jin haka sai tausayi ya kama sadusa da Halyal har idanunsu suka ciko da kwallah: A cikin kunnen aljani Raugatul Aguwanu kuwa, Boka radiyan ya dubi Gimbiya Hursiya ya ce bari na karasa miki Labarin da dan uwanki sarki dujalu bai karasa miki ba hakan zai debe miki kewa kafin mu karasa bakin kogin bahar sufiya: Cikin tsananin mamaki Hursiya ta dubi boka Radiyan ba tare da ta iya furta masa komai ba: Boka Radinyan yayi murmushi yace kada ki yi mamaki akan lamarina domin na wucce dukkan tunaninki na san abinda baki sani ba zaki gasgata hakan idan kiyi la akari da abubuwan da suka faru 181 TASKARNOVELS.COM.NG tsakaninmu tunda haduwarmu kawo izuwa yanzu da muke cikin kunnen aljani Raugatul Aguwanu page 150 Gimbiya Hursiya ta gyada kai kawai cikin tana sauraron boka Radiyan Shi kuma ya cigaba da dora mata Labarin Kamar Haka : * * * MAZAN JIYA! (4) Kashi na sittin da biyar (65) ABDUL'AZIZ SANI MADAKINGINI (King ofAdventure Story) . LOKACIN da jarumi SHADDADU ya cigaba da tafiya bisa wannan tsuntsun tsafi, ga Mashin Galilul Haras daure a gadon bayansa kuma gashi a cikin gagarumar shigar Yaki, sai tsuntsun ya ci gaba da keta gizagizai a sararin samaniya ba kakkautawa. Sai 182 TASKARNOVELS.COM.NG da suka shafe sa'a biyar da rabi suna tafiya sannan tsuntsun ya sauko kasa-kasa da kansa, ashe wani babban Birni suka tunkaro a gabansu. Koda ya rage bai fi zira'i goma ba tsakaninsu da Birnin sai tsuntsun ya sauko kasa. Shadaddu ya sauko daga kan tsuntsun. Saukarsa ke da wuya sai tsuntsun ya rikide ya zama dan karami kuma ya tashi sama ya dira a kafadar Shaddadu. Faruwar hakan ke da wuya sai Shadaddu ya kunna kai izuwa kofar wannan Birni ba tare da shakkar komai ba. Da isarsa bakin kofar garin ya iske masu gadi wadansu Dakaru samudawan karti kimanin su arba in a tsaitsaye cikin shigar Yaki. Ko kallonsu Shadaddu bai yi ba ya nufi bakin kofar Garin wacce take a rufe. Su ma Dakarun sai suka yi kamar ba su ganshi ba, domin ko kallonsa ba su yi ba. Shi ma sai ya ki ya yi musu magana ya je ya kwankwasa kofar domin a bude masa duk da cewa ya ga daya daga cikin masu gadin a zaune daf da bakin kofar bisa wata kujera rike da katuwar Kuba. Shadaddu ya kwankwasa kofar har sau uku, amma shiru ba a bude kofar ba. Kawai sai ya ji masu gadin sun kama yi masa dariya. Daya daga cikinsu ya dube shi ya ce, 183 TASKARNOVELS.COM.NG "Ya kai wannan sakaran bako, shin ba ka da da'a ne ko kuwa ba a koya maka ladabi ba ne a gidanku? Idan haka halayyarka take a can garinku to mu nan ba haka ba ne. Amma idan kai Kurma ne sai ka gaya mana". Kawai sai Shadaddu ya kalli mai maganar yai masa murmushi ba tare da ya maida masa da martanin maganar ba. Kawai sai ya ja da baya kadan ya daga ya daki kofar garin wacce ta kasance mai kauri da nauyin gaske ta zallar bakin karfe. Nan take kofar ta jijjige ta fada ciki. Al'amarin da yai matukar firgita Dakarun ke nan suka zazzare mnakamansu amma kuma suka kasa afka wa Shadaddu sakamakon ganin wannan gagarumar jarumtaka da ya yi. Shadaddu ya waigo ya dubi Dakarun ya yi musu murmushi a karo na biyu sannan ya juya ya shige izuwa cikin Birnin. Nan fa Dakarun nan suka kama duru-duru suka rasa abin da za su yi tsakanin su bi wannan bakon saurayi su yake shi ko kuma su kai rahotonsa izuwa ga Sarauniyarsu? Nan dai suka yanke shawarar daya daga cikinsu ya ruga izuwa fada ya kai labari. Nan take kuwa aka bi wannan shawara. Lokacin da Shadaddu ya kunna kai izuwa cikin 184 TASKARNOVELS.COM.NG wannan Birni sai ya zama abin kallo, duk inda ya ratsa sai ya ga mutane har fitowa suke daga cikin gidajensu suna binsa a baya, musamman mata domin dimaucewa suka rinka yi. Abin da yai matukar bai wa Shadaddu mamaki ke nan, domin shi bai ga abin kallo ba a tare da shi. Abin da Shadaddu bai fahimta ba shi ne tsananin kyawunsa da kwarjinihsa ne ya sa ake kallonsa. Koda ya ga kallon da ake yi masa ya yi yawa, kuma jama'a dada karuwa suke ana ta binsa sai ya juya ya kwarara uban ihu ya yi kamar zai zare Takobinsa. Nan fa jama'a suka tarwatse cikin firgita suka kama gudu. Kafin cikar dakika biyar babu kowa akan hanyar. Shadaddu yai dariya ya ce, "Ashe ma duk matsorata ne a garin. Kawai sai ya ci gaba da tafiya. Burinsa kawai shi ne ya ga kasuwa ko inda ake siyar da abinci domin yunwa ta fara damunsa ga shi bai taho da wani abinci ba a cikin jakar guzurinsa sai tarin Dirhami mai yawan gaske. Haka dai ya ci gaba da tafiya yana kutsawa ta cikin lunguna da sako-sako na Garin, amma kuma bai ga mutane sun daina kallonsa ba, sai dai ba sa biyo shi a baya sakamakon ganin rashin annuri akan fuskarsa, 185 TASKARNOVELS.COM.NG kai da gani ka san cewa mutane suna shakkarsa saboda ganin irin kirarsa ta manyan sadaukai. Yana cikin dube-dube ne ya hango wani gida wanda aka yi rubutu a jikin saman kofarsa kamar haka. 'GIDAN ABINCI'. Koda ganin wannan rubutu sai murna ta kama Shadaddu ya kunna kai izuwa cikin gidan. Yana shiga ya iske mutane da yawa a zazzaune bisa kujeru a karkashin tebura suna ta cin abinci kala-kala. Lokaci guda kowa ya dago kai ya kalle shi sannan aka kawar da kai aka ci gaba da cin abincin babu wanda ya sake dubansa. Al'amarin da ya daurewa Shadaddu kai shi ne gaba dayan mutanen da ke cikin gidan abincin maza ne, kuma karti majiya karli, ababan kwatance. Mace guda daya ce jal a cikin gidan, kuma ita ce mai bayar da abincin. A can gefe daya bisa wani dogon tebur mai dauke da tukwanen abinci kimanin guda goma. Shadaddu ya sake yin nazarin kartin da ke cikin gidan ya ga kowannensu yana da siffa irin ta mayaki duk da cewar babu makamai a jikinsu. Nan take jikin Shadaddu ya ba shi cewar akwai tuggun da ake son shirya masa amma sai ya basar ya nuna ba ya tunanin komai. Kai tsaye 186 TASKARNOVELS.COM.NG ya nufi inda mai bayar da abincin take. Da zuwa sai ya bude jakarsa ya dauko Dirhami goma ya ajiye a gabanta sannan ya nuna mata irin kalar abincin da yake so. Kawai sai ya ga ta kura masa idanu ko kiftawa ba ta yi har sai da ya doki tebur din da ke gabanta sannan ta dawo cikin hayyacinta. Ashe tsananin kyawunsa ne ya dimautata ta sandare kamar Gunki. Koda ya buga teburin ta dawo cikin haiyacintae ta ga ya ajiye ma ta kudi akan tebur sai ta gan nufinsa. Hannunta na karkarwa ta dauki cokali da faranti ta zuba masa abincin. Shadaddu ya karbi abincin ya je ya zauna akan wani tebur wanda babu kowa akai ya fara cin sbincia. Yana cikin cin abincin ne ya ga wadannan mutane da ke cikin gidan sun fara mimmikewa tsaye suna zaro makamai a jikin karkashin tebur din da suke zaune. Ko motsawa Shadaddu bai yi ba, da ma ta wutsiyar idanu ya kalle su, kawai sai ya cigaba da cin abincinsa. Koda wannan mace mai bayar da abinci ta ga an fara zaro makamai sai tavyi wuf! Ta ruga izuwa cikin wani ɗaki ta kullo kofa. A sannan ne aka rufo kofar shigowa gidan gabadaya. Hakan ba ta sa Shadaddu ya ji ko dar ba! Kawai sai ya ci gaba da cin abincinsa. 187 TASKARNOVELS.COM.NG Lokaci guda gaba dayan kartin suka afkawa Shadaddu da nufin su daddatsa shi. Cikin masifaffen bakin zafin nama Shadaddu ya zare tasa Takobin, ya yi wata irin katantanwa a tsakiyarsu ya tarwatsa su da karfin tsiya. Nan fa aka ruguntsume da Yaki, suka yi masa rubdugu suka rinka kai masa sara da suka ta ko ina. Shi kuma ya yi ta kare hare-harensu amma sai ya dinga mai da martani da bugu da naushi maimakon da makami. Nan fa ya rinka hada musu jini da majina, amma saboda naci da juriya irin na maza masu Jarumta ko sun fadi kasa sai ka ga sun mike zumbur! Sun ci gaba da kai masa munanan sara da suka, amma ba a samu wanda ya sami nasarar koda lakutar jikinsa ba. Shi kuwa Shadaddu sai ya nuna tsagwaron sadaukantaka da fifikon yaki, ya ki ya sari jikin dayansu da makami. Haka dai ya ci gaba da gabza musu naushi da musu bugu hannu da kafa har sai da ya bazar da gaba dayansu a kas, bayan an kakkarya tebura da kujerun da ke gidan, an lalata komai ya zamana cewa komai ya ragargaje. á Sai ga shi karti sama da mutum arba'in kwance kas sun yi lagalaga sun kasa tashi. A sannan ne wannan 188 TASKARNOVELS.COM.NG mace mai siyar da abincin da ta ji an daina kwarmazuwa ta bude dakin da ta shiga ta бuya ta fito da sauri ta ga Shadaddu ya dauki tulun giya ya kafa a bakinsa yana ta sha. Sai da ruwan giyar ya kare kaf sannan ya wurgi da tulun ya fashe. Ko alamar buguwa bai yi ba ya dubi macen ya ce, "Ina cigiyar wata Jaruma mai suna ZIYA'UL HAK ko kin santa?" Cikin alamun tsoro matar ta dubi Shadaddu a lokacin da jikinta gabadaya ya kama tsuma ta ce "Ba mu taba jin ma mai irin wannan suna ba a garin nan ya kai wannan bakon saurayı ma'abocin kyau da jarumtaka. Wane ne kai, kuma daga ina ka fito?" Koda jin wannan tambaya sai Shadaddu ya yi mata wani guntun murmushi sannan ya ce, "Ni kaina ban san amsar tambayar da kika yi min ba!" Koda gama fadın haka sai ya sake bude jakar guzurinsa ya dauko dirhami ashirin ya mika mata ta karba sannan ya ce, yanzu Makwanci nake bukata . Matar ta yi murmushi ta ce, "Samari ka sami makwanci har ma da mai debe maka kewa. Shaddadu ya yi ma ta wata irin harara wacce ta sa zuciyarta ta buga da karfi, ya dube ta a fusace ya ce, "Ba na bukatar mace a kusa da ni". Cikin rawar jiki ta ja 189 TASKARNOVELS.COM.NG Shaddadu suka fice daga cikin wannan gida suka kunna kai izuwa cikin wani lungu. Ai kuwa suna shigewa wannan lungun sai ga Dakarun gidan Sarautar garin sama da mutum dari biyu sun shigo unguwar a guje rike da makamai suna neman Shaddadu domin tuni labari ya isa ga Sarauniyar garin cewa ga wani bakon Sadaukin saurayi can ya ɓalla kofar gari da karfin tsiya ya shigo kuma har ya fara barna a cikin gari. Bisa wannan dalili ne Sarauniyar ta taso Dakaru domin su zo su kamo wannan bakon Jarumi a mace ko a raye.. Lokacin da Dakarun Sarauniya suka je wannan gidan abinci suka iske wadannan karti arba'in a kwakkwance mashe-mashe sun sha duka kuma suka ga komai na gidan a ragargaje sai suka cika da mamakin yadda za a ce wai mutum daya ne ya yi wannan aiki. Nan dai suka shiga neman Shaddadu amma ko alamarsa babu. Da suka ga babu shi sai suka koma can fadar Sarauniyar tasu suka sanar da ita cewa ba su ga wannan bakon saurayi ba. Lokacin da Sarauniya ZUBAINA IBINI LAIYARA ta ji cewar ba a ga bakon saurayin ba sai ta bushe da dariya. Al'amarin da yai matukar bai wa kowa mamaki 190 TASKARNOVELS.COM.NG ke nan a fadar, aka zuba mata idanu kawai. Daga can kuma sai ta tsuke bakinta ta murtuke fuska ta ce, "Tabbas BABBAN GORO sai MAGOGIN KARFE. Hakika babu wanda zai iya tarar wannan bakon saurayi face ni. Da kai na zan yi shiri na tafi farautarsa a cikin garin nan. Na yi bincike a kansa na gano cewa yana da matukar karfin sihiri da jarumtaka, to amma duk abin da yake takama da shi ya zo gidansa. Tun da na hau kan karagar wannan mulki a wannan Birni namu na HADIYAS ba a taɓa samun wani tsagera da ya zo mini Birnina babu izini yakarya mini kofar gari kuma ya je gidan abinci ya yi wa Dakaruna dukan tsiya. Hakika idan na kama wannan bako sai na gana masa azaba mai radadi har izuwa lokaci mai tsawo sannan na yanke masa hukuncin kisa." Koda gama wannan jawabi sai Sarauniya Zubaina ta mike tsaye a fusace ta shige izuwa cikin gidan Sarautar, a sannan ne fada ta watse kowa ya tafi yana fadin albarkacin bakinsa. Wasu suna cewa, "Lallai wannan bako ya tabo tsuliyar Dodo". Wasu kuma suna cewa, "Ai saukin wannan bako kawai ya samu ya sulale ya gudu daga garin saboda kowa ya san cewa Sarauniya 191 TASKARNOVELS.COM.NG Zubaina ta kasance BASADAUKIYA ta gaban kwatance, kuma hatsabibiyar Bokanya ce wadda babu kamarta a gabadayan Nahiyar. Al'amarin Jarumi Shaddadu kuwa, lokacin da wannan ma'aikaciyar gidan abinci ta ja shi suka shiga cikin wannan lungu, sai suka yi ta wuce gidaje har sai da suka je karshen lungun sannan ta shige da shi izuwa cikin wani gida. Sai da ta sa mukulli sannan ta bude gidan, suna shiga, ta mai da kofar ta rufe. A cikin wani dan karamin falo Shaddadu ya tsinci kansa mai dauke da daki guda daya jal, sai kuma bandaki. Saboda rashin yarda sai da Shadaddu ya leka cikin dakin da bandakin ya tabbatar da babu kowa a ciki sannan ya dawo ya zauna a falon. A sannan ne matar wadda shekarunta ba za su haura talatin da biyar ba, mai kyan diri da fuska ta dube shi ta yi dariya ta ce. "Kana zaton za a hada baki ne da ni a cuce ka? To ka sani cewa ni karuwa ce, kudi ne kawai a gabana. In dai za ka biya ni zan ci gaba da rufa maka asiri har izuwa lokacin da za ka bar garin nan". Kafin Shaddadu ya budi baki ya ce wani abu sai suka jiyo an shigo lungun da gudu kuma alamar mutane ne da yawa suka shigo.Cikin sauri 192 TASKARNOVELS.COM.NG matar ta mike tsaye ta ruga izuwa bakin taga ta yaye labule ta leka. Da sauri ta saki labulen kofar la ruga izuwa wajen Shaddadu a gigice ta ce, "Zo mu je na boye ka, Sarauniya ce da kanta ta fito nemanka". Shaddadu ya dubi matar cikin alamun matukar mamaki ya ce, "Akan me za ki бoye ni an gaya miki ni ina shakkar wani ne? Ki bari Sarauniyar taku ta shigo har nan ki ga yadda za mu wanye." Matar ta dubi Shaddadu kamar za ta yi kuka ta ce, "Ni dai ka rufa mini asiri idan Sarauniya ta zo ta ganka anan gidana kashe ni za ta yi". Koda jin haka sai jikin Shaddadu yai sanyi. Ba tare da gardama ba kuwa ya bi ta suka shige cikin wannan dakin barci nata da sauri. Suna shiga sai ya ga ta yaye dardumar dakin, ta daga wata kofar katako sai ga matattakala izuwa cikin gidan kasa. Matar ta dubi Shaddadu ta ce, "Shiga nan ka yi zamanka". Cikin sauri Shaddadu ya shige cikin gidan kasan, sannan ta mai da kofar ta rufe sanna dardumar. Faruwar hakan ke da wuya sai ta ji ana, bubbuga ma ta kofar gida. A guje ta je ta bude, Sarauniya Zubaina ta gani tsaye a gabanta cikin gagarumar shigar Yaki, ga wasu manyan Dakarunta su goma suna take mata 193 TASKARNOVELS.COM.NG baya. Zubaina ta dubi matar da kyau a cikin nutsuwa ta ce, "Ya ke YALDISA ina wannan bakon saurayi?" Yaldiṣa ta risina cikin girmamawa ta ce, "Ya Shugabata, rabo na da bakon saurayi tun da muka fito tare daga gidan abinci ya tambaye ni hanyar kasuwa na nuna masa anan muka rabu". Koda jin wannan batu sai Sarauniya Zubaina ta yi murmushi mai nuna alamun rashin yarda sannan ta hankade Yaldisa ta fadi gefe guda. Kai tsaye Zubaina da Dakarunta suka kunna kai izuwa cikin falon. Sarauniya Zubaina ta zauna akan kujera sannan ta umarci Dakarunta da su caje ko ina na gidan. Lokacin da Yaldisa ta taso ta zo gaban Zubaina ta durkusa tana mai sunkui da kanta kas ba tare da ta nuna wata alama ta tsoro ba ko rashin gaskiya. Zubaina ta sake duban Yaldisa ta yi murmushi a karo na biyu sannan ta ce, "Ya ke Yaldisa yau shekara bakwai ke nan kina aiki a karkashina. Na san dukkan halayenki, ke karuwa ce wadda in dai za ta sami kudi babu abin da ba za ta iya yi ba. Ki gaya mini gaskiya tun kafin lokaci ya kure miki. Idan na gano cewa kina da hannu akan ɓoye wannan bako daga baya, kin san halina, ba sani ba sabo. Ban san 194 TASKARNOVELS.COM.NG tausayi ba kuma ban san hakuri ba, kashe ki zan yi kawai". Yaldisa ta dago kai ta dubi Zubaina ta ce, Ya Shugabata tsawon shekaru bakwan da nake aiki a tare da ke ban taba yi miki karya ba, wannan ya isa ki aminta da ni. Zubaina ta jinjina kai gami da ajiyar zuciya ta ce, tabbas abin da kika fada gaskiya ne, amma ai a wajenki kudi su ne gaba da komai. Ni na abbatar da cewa za ki iya siyar da iyayenki ma muddin za ki sami kudi. Gama fadin hakan ke da wuya sai ga Dakarun Zubaina sun dawo gabanta. Shugabansu wanda ake kira SADAR ya risina ce, "Ranki ya daɗe, babu kowa a cikin gidan nan". Koda jin haka sai Zubaina ta mike tsaye ta nufi bakin kofa, Dakarun nata na biye da ita. Har ta sa kafarta guda a waje sai ta juyo ta dubi Yaldisa ta ce. "A ko yaushe za mu iya kawo ziyarar bazato, Kar ki manta hukuncin kisa ne a kanki idan na kama ki da laifin boye mai laifi". Gama fadin hakan ke da wuya sai Sarauniya Zubaina da Dakarunta suka fice daga cikin gidan. Yaldisa ta mai da Rofar ta rufe sannan ta jingina bayanta a jikin kofar tana mai yin doguwar ajiyar numfashi cikin tsananin tsoro. Ba ta matsa daga inda take tsaye a jikin Rofar ba sai bayan 195 TASKARNOVELS.COM.NG lokaci mai tsawo bayan ta tabbar da cewa su Sarauniya Zubaina ba sa kusa sannan ta nufi dakin barcin nata. Tana shiga sai ta iske Shaddadu a kwance akan gadonta har ma ya kama barci abinsa tamkar ba shi aka zo nema ba. Cikin fushi ta girgiza gadon, Shaddadu ya mike zaune ya dube ta cikin mamaki ya ce, "Lafiya za ki katse mini barcina alhalin a cikin gajiyar tafiya nake?" Koda jin haka sai Yaldisa ta sake fusata ta ce, "Au! Kai ta barci ma kake ba ta raina ba? To tsaya ka ji, ga kudinka da ka ba ni, ba zan iya siyar da rayuwata ba a kan dirhami ashirin kacal da ka ba ni". Koda jin haka sai Shaddadu ya yi murmushi, nan take ya janyo jakar guzurinsa ya bude ya sake debo dirhami ashirin ya mikawa Yaldisa ya ce, ga wannan ki kara. Ni dai ki kyale ni na yi barcina. Yaldisa ta tankwaɓe hannun Shaddadu dinaren ya zube kasa ta yı masa tsawa ta ce, "Ran nawa zan siyar maka akan dinare arba'in? Ka ga ni ba na bukatar kudinka kawai ka tashi ka bar mini gida don ba za ka janyo mini hukuncin kisa ba a banza". Maimakon Shaddadu ya yi fishi sai ya yi dariya kuma ya dauko kullin dinarensa gabadaya ya cilla wa Yaldisa ta cafe ya ce. 196 TASKARNOVELS.COM.NG "Gashi nan gabadayan abin da na mallaka ke nan in kin so ki kyale ni na kwana. Na yi miki alkawarin babu abin da zai taɓa lafiyarki koda asirinki ya tonu, kuma gobe da safe zan bar miki gidanki". Koda gama fadin hakan sai Shaddadu ya koma ya kwanta akan gadon yana mai juya mata baya. Kafin cikar dakika dari da ashirin ya fara munshari. Al'amarin da yai matukar bai wa Yaldisa mamaki ke nan kuma ya ba ta dariya. Nan dai ta sunkuya ta tsince ragowar wannan dinaren da ya zube kasa ta zuba a cikin kullin wanda aka ba ta ta boye, sannan ta je ta ci gaba da dan aiyukanta na gida. Har dare ya yi Shaddadu bai farka daga barci ba. Lokacin da Yaldisa ta ji ta soma jin barci har ma tana gyangyadi daga zaune sai hankalinta ya tashi domin dama can tsoro ne ya hanata zuwa ta kwanta, saboda tana ganin cewa a kodayaushe Dakarun Sarauniya Zubaina za su iya kawo ziyarar bazato. Da dai ta ga tana jin barcin sosai sai ta mike tsaye ta nufi cikin dakin barcin. Tana shiga ta ga har a sannan Shaddadu barci yake yi. Koda ta kura masa idanu ta dube shi sama da kasa ta ga irin tsananin kyawun fuskarsa da kyawun surar 197 TASKARNOVELS.COM.NG jikinsa, sai nan take ta ji ta kamu da tsananin sha'awarsa. Sai a sannan ne ta gane cewa ashe da can tsoro ne ya sa ta kasa yi masa kallon nutsuwa bare ta san cewa kyakkyawa ne. Nan dai Yaldisa ta kautar da tsoro ta cire tufafin jikinta ta sanya na barci sannan ta kwanta a bayan Shaddadu. Koda ta kai hannu ta tabo Shaddadu sai ya mike zumbur! A fusace ya dube ta ya daka mata tsawa da karfi. Yaldisa ta razana ainun har sai da hantar cikinta ta kada. Shaddadu ya ce. "Na gaya miki ba na bukatar mace a kusa da ni. Ki sauka daga kan gadon nan tunda dai biyanki na yi kudin komai a gidan nan". Cikin alamun tsananin mamaki Yaldisa ta sauka daga kan gadon ta dauki matashin kai guda daya ta dawo falo ta kwanta a kasa. Nan fa Yaldisa ta ci gaba da mamakin wannan bakon saurayi har barci ya sace ta ba ta sani ba. SHADDADU FA YANA DA GASKIYA. DOMIN KOMAI TUMBATSAR SADAUKI MATUKAR YA HADA SHAGALA DA MACE SAI AN YI NASARA A KANSA. SADAUKI HANTARU IZINA A GARE MU. Lokacin da gari ya waye sai Yaldisa ta ji ana tashinta daga barci. Koda ta farka ta bude idanuntasai ta yi arba da wata mace 198 TASKARNOVELS.COM.NG tsohuwa tukuf! Zaune gabanta. Cikin alamun tsananin tsoro ta mike zumbur! Ta koma jikin bango ta takure jikinta tana mai kallon tsohuwar a firgice ta ce, "Wace ce ke kuma yaya aka yi kika shigo gidan nan? Shin kin samu wani ban da ni a cikin gidan nan ne?" Koda jin wannan tambaya sai tsohuwar ta bushe da dariya, nan take ta rikide ta zama Shaddadu. Mamaki ya sake kama Yaldisa ta ce, "Ashe ma kai ne? Mene ne dalilin da ya sa ka rikide izuwa siffar wannan tsohuwa". Shaddadu ya yi ďan guntun murmushi a gare ta sannan ya ce, "Ai jiya bayan kin yi barci ya yin dà dare ya raba sai na tashi na rikide izuwa siffar wannan tsohuwa na ci gaba da barcina. Faruwar hakan ke da wuya kuwa sai ga wadansu hadimai na Sarauniyarku sun shigo cikin gidan nan da karfin sihirin tsafi, suka kama bincike. Koda suka shigo cikin dakin barcinki sai suka ga tsohuwa akan gadonki tana shara barci har da munshari, sai suka juya suka fice daga gidan gabadaya. Wannan shi ne dalilin da ya sa na sauya kamannina don kada a zo a gan ni na shafa miki kashin kaji. Sa'adda Shaddadu ya zo nan a zancensa sai Yaldisa ta cika da tsananin mamaki da murna. Shaddadu 199 TASKARNOVELS.COM.NG ya dube ta ya ce, to ni yanzu nan zan tafi neman abin da ya kawo ni garin nan don haka sai dai na yi miki bankwana. Yana gama fadin hakan sai ya koma cikin dakin da yai barci ya dauko Mashinsa na GALILUL HARAS wanda ya rataye shi a jikin bango sannan ya dauko karamin Tsuntsun nan nasa na tsafi ya dora shi akan kafadarsa. Koda ya fito falo Yaldisa ta yi arba da Mashin da kuma wannan Tsuntsu sai ta dube shi cikin mamaki ta ce, "Yaushe kuma ka sami wanna Mashin da wannan Tsuntsun? Ni dai a sanina jiya ba ka tare da su". Koda jin wannan tambaya sai Shaddadu ya yi murmushi ya ce, "Ai babu mai ikon ganin wadannan abubuwa nawa face da amincewata." Yana gama fadin hakan sai ya sake rikidewa ya zama wannan tsohuwa wacce saboda tsananin tsufa sai da ta rankwafa ta yi doro. Shi ma Mashin Galilul Haras sai ya rikide ya zama sanda. Tsohuwar ta dogara sandar ta nufi bakin kofa za ta fita, sai Yaldisa ta ruga ta sha gabanta ta ce, "Haba ya kai bako, yaya za ka kwana a gidana na ba ka abinci kuma na ba ka makwanci duk da dai siya ka yi amma za ka tafi ban san koda sunanka ba? Ka yi sani cewa ina da wadansu 'yan tambayoyi 200 TASKARNOVELS.COM.NG guda uku rak a gare ka wadanda na ke son amsarsu kafin mu rabu.Tambayata ta farko ita ce, Mene ne dalilin da ya sa kake neman wata Jaruma mai suna ZIYA'UL HAK? Tambaya ta biyu, ina son na sani idan kai namiji ne cikakke, ko kuwa ba ka da lafiya? Tun da na fara karuwanci ban taba haduwa da namijin da bai yi sha'awata ba sai kai saboda kyawuna da kyawun surata. Tambaya ta uku ita ce, Yaushe za ka bar wannan garin namu?" Sa'adda Shaddadu ya ji wadannan tambayoyi sai ya yi murmushi mai taushi ga Yaldisa ya ce, Game da tambayarki ta farko, amsarta ita ce, ina neman Jaruma Ziya'ul Hak ne saboda ta kásance babbar abokiyar gabata a duniya, muddin zan yi arba da ita sai na hallaka ta. Amsar tambayarki ta biyu kuwa, ni namiji ne cikakke mai lafiya, amma mahaifiyata ta cire mini sha'awar 'ya mace da karfin sihiri, kuma ta hore ni da kaidinku tun ina karami don haka, a rayuwata babu abinda na tsana kuma nake tsoro sama da mata. Game da amsar tambayarki ta karshe ita ce ba zan bar wannan gari naku ba har sai na tabbatar da cewa abokiyar gabata Jaruma Ziya'ul Hak ba ta 201 TASKARNOVELS.COM.NG cikinsa. Na barki lafiya sai watarana idan da rabon mu sake saduwa. Koda gama fadin hakan sai tsohuwar ta je ta bude kofa ta fice daga cikin gidan. Ita kuwa Yaldisa sai ta ji ta kamu da tsananin damuwa da bakin ciki tamkar wacce ta rabu da wani dan uwata shakikinta kuma rabuwa ta har abada wacce ba za a sake saduwa ba. Kawai sai Yaldisa ta ji idanunta sun ciko da kwalla har hawaye

Chapter 8 of 18