addini ne na karya, tsafin da
suke yarda da shi shirka ce kuma bata ne
mabayyani, domin Ubangijine wanda yafi
cancanta da a bauta ma wa, shine wanda ya
halicci sammai da kassai kuma shine ya halicci
mutum da aljan badan komai ba face su bauta
masa a doron kasa, amman sai wasunsu suka
bijire masa suka bautar waninsa suna aikata
kafirci da alfasha a bayan kasa. Lokacin da
Jarumi Hasnalu Ibn Bashriyya ya zo nan a
zancensa sai gimbiya Hursiyya ta cika da
tsananin mamaki fiye da koyaushe ta dubeshi
ta ce yanzu kai ta yaya zaka iya aiwatar da
abinda ya gagari mahaifinka? Koda jin wannan
tambaya sai Hasnalu yayi murmushi ttare da
cewa ai daman na fada maki tun farko ni da
245
TASKARNOVELS.COM.NG
ubangijina na dogara, tunda kika ga mahaifina
ya kasa jaddada addinin Allah a wannan
nahiyoyi naku to Allah ne bai nufeshi da dacewa
ba, amman ni ina sa ron dacewar. Hursiyya ta yi
shiru tana tunani gami da nazari al'amari a cikin
zuciyarta, daga can kuma ta dago kai ta dubeshi
ta ce yanzu yaya za a yi na gamsu cewar
wannan addini naka shine na gaskiya akan
namu, kuma ya za a yi nasan cewa Ubangijinka
shine mafifici akan dukkanin wani Ubangiji?
Hasnalu ya sake yin murmushi a karo na uku
sannan ya ce ai ni indai muna tare d ke, to da
sannu zaki gaskata hakan. Hursiyya tace ni
kuwa idan har na fahimci addininka shine na
gaskiya, to zan kaika inda zaka sa gaba daya
mutanen dake wannan nahiya su karbi
addininka kuma nayi maka alkawarin zan sa a
bincika labarin mahaifinka, idan ma yana raye
zan sa a nemoshi a duk inda yake. Koda jin
wannan batu sai Hasnalu ya cika da mamaki
gami fa murna ya dubi Hursiyya ya ce ke kuma
wace ce awannan nahiya da har kike tunanin
zaki iya yi mani wannan taimako? Hursiyya ta
kalleshi sannan ta yi murmushi kana daga
bisnai ta ce da shi suna na gimbiya Hursiyya,
246
TASKARNOVELS.COM.NG
kuma na kasance kanwa ga sarki Dujalu, sarkin
da gabadaya nahiyoyin nan babu kamarsa a
karfin tsafi, mulki, jarumtaka gami da arziki face
wani sarki d ake kira Maharaz. A yanzu haka
dakarun sarki Dujalu dana Maharaz suna can a
bakin wani teku da ake kira bahar sufiya suna ta
gabza yaki a tsakaninsu... Nan dai Hursiyya ta
zayyane wa jarumi Hasnalu dukkanin abinda ke
faruwa har da makasudin wannan yaki, wato
akan dauko kayan yakin mazan jiya saboda
kowanne sarki yana da burin mallakar kayan
yakin dan kawai ya samu damar mulkar
mutanen duniya gaba daya. Yayin da Hursiyya
ta gama baiwa Jarumi Hasnalu wannan labari,
sai ya cika da tsananin mamaki bis yadda
mutane suka yi imani da karya da tsafi, sannan
kuma sai ya kamu da farin ciki dan yana ganin
cewa ya samu hanyar da zai jaddada addinin
Allah a wannan nahiyoyi. Hursiyya ta dubi
Hasnalu cikin nutsuwa ta kare masa kallo sai
taga bai kasance wani katon mutum ba mai
kirar Sadaukai kuma gashi ya ce shi baya tsafi,
dan haka sai fara tunani a ranta cewar ta yaya
zai iya nuna wani abin jarumtaka wanda har zai
sa mutane su amince da shi su karbi addininsa,
247
TASKARNOVELS.COM.NG
tabbas indai zai je bakin tekun bahar sufiya ya
dauko takobin Saiful Lujara a karkashin takun
kowa ya gani to da ya tsaida yakin gabadaya
kuma dole ne a gaskata ubangijin nasa. Tana
cikin wannan tunani ne suka hango aljani
Radiyan ya taho da gudu dugul-dugul kamar zai
kife kasa saboda gajarta, har jarumi Hasnalu ya
zare takobinsa zai afka masa, sai Hursiyya ta
sha gabansa ta dube shi cikin murmushi tace
mayar da takobinka ai wannan abokin tafiyata
ne, in ba don shi ba da ban zo nan ba, har ma na
sadu da kai, nan take aljani Radiyan ya ja
Hursiyya gefe suka kama kuskus, ya dubeta
cikin alamun tsoro kamat ace ket ya fita da
gudu, jikinsa na tsuma yace shin kin tabbatar da
mutum ne wannan ba aljani ba? Hursiyya ta
kyalkkyale da dariya sannan ta ce na tabbar
mutum ne. Nan take ta kwashe labarin dukkan
abinda ya faru tsakaninta da jarumi Hasnalu ta
zayyane masa. Koda jin haka sai boka Radiyan
ya murtuke fuska ya dubeta cikin fushi ya ce
saboda me zaki gaskata zancen ma'abota
addinin Musulunci, mutanen da suka kasance
abokan gabarmu tun iyaye da kakanni, to ki sani
cewa bamu da makiya sama da wadannan
248
TASKARNOVELS.COM.NG
mutane, kuma duk abinda ya fada maki zancen
banza ne babu gaskiya a cikinsa, kada kyawun
wannan saurayi ya rudeki kizo ki aikata abinda
zaki jefamu a cikin danasani. Sa'ad da gimbiya
Hursiyya ta ji wannan batu sai ta yi ajiyar zuciya
kuma ta yi shiru tana tunani har izuwa tsawon
yan dakiku, sannan ta dubi ljani Radiyan tace
dole ne na jaraba wannan saurayi domin na
tabbatar da gaskiyarsa ko rashinta kafin na ki
bashi yarda ta, ai masu iya magama sunce
ranar wanka ba a boyon cibi, kuma sunce
sannu bata hana zuwa sai dai a dade ba a je ba,
kawai mu cigaba da wannan tafiya tare da shi
har mu kure karyarsa. Koda ta zo nan a
zancenta sai Hursiyya ta rabu da aljani Radiyan
taje gun Hasnalu ta dubeshi cikin murmushi ta
ce ni da abokin tafiyata mun amince mu tafi
tare da kai har ixuwa filin daga inda ake fafata
yaki, amman bisa sharadi guda, sharadin kuwa
shine dole ne kayi abubuwan al'ajabi guda uku
wadanda zasu nuna mana cewa ka cika jarumi,
kuma ubangijinka shine ubangijin gaskiya.
Sa'ad da jarumi Hasnalu ya ji wannan batu sai
yayi murmushi shima y ce nayi imani da
ubangijina dari bisa dari, dan haka nasan cewa
249
TASKARNOVELS.COM.NG
zai bani ikon hayewa wannna sharadi da kuka
gindaya mani, nima kuma bisa sharadin muddin
na yi wadannan abubuwa da kika shardanta
mani to zaki karbi addini na. Hursiyya ta yi
murmushi sannan t ce na amince zan karbi
addininka matukar kayi abubuwan dana
sharadanta maka, muje zuwa mahaukaci ya
hau kura. Koda ta zo nan a zancenta sai jarumi
Hasnalu ya mayar da takobinsa a cikin kubenta,
kuma ya nannade buzunsa ya sabashi a
bayansa ya daure sannan ya dubi aljani Radiyan
ya ce wace hanya zamu bi ta kaimu zuwa bakin
kogin na bahar sufiya inda ake yakin? Aljani
Radiyan yayi nuni da hannunsa izuwa yamma
yana mai cewa nan zamu bi. Nan take Hasnalu
ya wuce gaba yan mai karanta wasu Addu'o'i na
musamman a zuciyarsa, Hursiyya na biye fa shi
daf da daf, sannan sai aljani Radiyan a bayansu.
Nan fa suk cigaba da kutsawa cikin sarkakiya,
duhuwoyi, koramu d kwazazzabai, haka suka
cigaba da tafiya tamkar ba zasu daina ba, wani
lokacin sukan jiyo kukan manyan dabbobin daji
acn nesa da su, wani lokacin ma sai suji tamkar
a gabansu dabbobin suke kuka, amman wani
iko na Allah har sai da suka shafe rabin sa'a sun
250
TASKARNOVELS.COM.NG
tafiyar basu yi arba da muguwar dabba ko guda
daya ba, banda kukan dabbobima sukan jiyo
gurnani irin na dodanni da aljanu wanda hakan
yasa aljani Radiyan da Hursiyya suka tsorata
ainun jikinsu ya kama tsuma, amman sai suk ga
shi jarumi Hasnalu ko gezau beyi ba, kawai sai
cigaba yake ma da tafiyarsa tamkar a cikin gari
yake ba a daji ba. Kwatsam sai kawai suka ga
sun shigo cikin wani wuri mai wani irin yanayi na
ban tsoro, wajen yana dauke da wasu irin
dogayen bishiyu masu tarin dogayen jijiyoyi da
suka zubo kasa tun daga sama, sannan akwai
ruwan wata korama a wajen da ke kwararowa
daga kan duwatsu, bugu da kari kuma sai suka
ga bishiyoyin ayaba da yawa a wajen kuma g shi
an tsittsinki ayabar, anci wata an kuma zubar da
wata a kasa gata nan a ko'ina birjit. Koda suka
yi arba da wannan wuri sai jarumi Hasnalu ya
tsaya cak, kum ya juyo yayi w su Hursiyya da
suma su tsaya kuma suyi shiru. Nan take kuwa
suka bi umarninsa, Hasnalu ya zaro takobinsa
daga cikin kubenta a hankali dan kada aji sautin
zaretan, sannan ya fara kallon gabas da
yamma, kudu da arewa yana nazarin hanyar da
ya kamata su bi, domin su cigaba da tafiya,
251
TASKARNOVELS.COM.NG
amman sai yaga hanya daya ce jal dole ne sai
sunbi ta wani katon kogon dutse mai duhun
gaske. Nan fa Hasnalu ya ji a jikinsa cewa lallai
baza a rasa wani mugun abu ba a cikin kogon,
kuma gashi duhune dundum a ciki, suna shiga
abinda ke ciki zai iya cutar da su ba tare da sun
ganshi ba, nan fa Hasnalu ya fara tunanin
dabarar da zai yi yasa duk abinda ke cikin kogon
ya fito waje ayi gaba da gaba. Nan take kuwa
dabara ta fado masa ya daga kansa sama yana
mai wangame bakinsa ya kwala kabbara da
karfi, aikuwa take dajin ya kama amsa kuwwa,
duk wani abu dake wannan daji sai da ya razana
tsuntsaye suka kama tashi sama suna sauya
sheka, dabbobin dake wannan daji suka kama
fitowa suna karo da masu kokarin shiga saboda
rudewar da suk yi, aikuwa a sannan ne suka ji
cikin wannan kogon dutsen ya rude da wani irin
gurnani mai yawa da karfin gaske, al'amarin da
yayi matukar razana aljani Radiyan da Hursiyya
kenan, kafin kiftawar ido sun ruga da baya
izuwa cikin duhuwar bishiyoyi suna masu leken
jarumi Hasnalu domin suga abinda zai faru
gareshi. Shikuwa Hasnalu sai ya kara rike
takobinsa da hannu biyu yana mai gyara
252
TASKARNOVELS.COM.NG
tsayuwarsa alokacin da wannan mugun
gurnanin yake dada karuwa, gami da wani irin
takun sawaye tamkar giwaye ne ke shirin fitowa
daga cikin kogon dutsen wanda har sai da ya
fara haifar da yar karamar girgizar kasa. Sai dai
hakan bai sa jarumi Hasnalu ya razana ba ko
kuma yayi yunkurin ja da baya ba, kwatsam sai
ga rundunar wasu burirrika manya manya masu
tsananin tsawo da kaurin gaske gami da
tsananin muni, su dai wadannan burirrikan
adadinsu ya kai kusan dari, suna da zara-zaran
farata a hannunsu, masu kaifi da tsini kamar
wukake, duk da cewar jarumi Hasnalu yana da
dakakkiyar zuciya amman sai da zuciyarshi tayi
rawa yayi tunanin cewa lallai fa yau ya gamu da
gamonsa. Al'amarin su Hursiyya da aljani
Radiyan kuwa lokacin da suka hango wadannan
burirrika a take suka firgice suka kwanta a kas
cikin duhuwar ciyawa, kuma suka dauke
numfashinsu tamkar marasa rai. Lokacin da
wadannan munanan burirrikan sukaga
biladama guda daya jal a gabansu yana rike da
makami, sannan babu alamar tsoro a tare da
shi sai suma suka tsaya cak suna kallonshi cike
da tsantsar mamaki, ba wani abu ne yasa suke
253
TASKARNOVELS.COM.NG
mamaki ba face shine kadai mutum na farko
daya taba yin arba da su ba tare da ya sume ko
kuma ya haukace ba. Nan fa aka fara kallon
kallo tsakanin burirrikan da jarumi Hasnalu har
izuwa tsawon yan dakiku, a duk sa'ad da yayi
arba da jajayen idanun burirrikan masu ban
tsoro da tsananin ja tamkar an gasa dan bida a
cikin wuta sai yaji kamar jiri na dibarsa. Nan
take Hasnalu ya fara karanto addu'o'i na neman
tsari domin ya fuskanci cewar burirrikan suna
da kofi a tare da su. Sannu a hankali burirrikan
suka fara rarrabuwa suna yiwa Hasnalu
kawanya, shi kuwa sai ya cigaba da tsayuwa a
inda yake ba tare da ya motsa ba, kawai kuma
sai ya rufe idanunsa tare da daga takobinsa
sama sosai tsininta na kallon sararin samaniya.
Al'amarin da ya dan tsorata burirrikan kenan
yasa suka kasa afka masa farat daya, suka rinka
kusantarsa da kadan kadan. Hursiyya da aljani
Radiyan dake boye suna ganin dukkanin abinda
ke faruwa, kawai sai suka sake cika da dumbin
mamaki musamman ganin dakewar zuciya irin
ta jarumi Hasnalu, kuma suka cigaba da zuba
ido dan suga irin gumurzun da xai yi tsakaninsa
da wadannan birirrikan. Kamar hadin baki sai
254
TASKARNOVELS.COM.NG
kawai birirrikan suka yunkura gaba dayansu tare
da afka masa a lokacin guda da nufin suyi
gutsu-gutsun da sassan jikinsa kowa ya ja
rabonsa, aikuwa sai suka kaiwa isk sara da suka
domin kuwa tuni Hasnalu ya daka tsalle sama
tamkar daga cikin baka aka harba shi, kafin su
dga kawunasu sama yayi alkafira a saman
kawunasu ya dawo kasa hannunsa na rike da
takobinsa, a sannan ne ya shiga gididdiba su
yana sare masu kawuna, koda ya dira kasa
kuwa sai ya cigaba da daukar rayukansu cikin
bakin zafin nama irin wanda dan adam bai taba
gani ba, yana saransu da sukansu yana hadawa
da kabbara, sai dai kaga sassan jikin birirrikan
na shawagi a sama ko kuma kaga hanjin cikinsu
na bullutsowa waje suna faduwa kasa matattu.
Koda birirrikan suka ga Hasnalu yayi masu
mummunar barna kuma ga shi a tsakiyatsu
amman sun kasa koda warzanar jikinsa sai suka
fusata ainun kuma suka haukace suka rinka
jijjigo bishiyoyi daga karkashin kasa suna masu
kai masa duka ta ko ina, a hakan ne daya daga
cikinsu ya samu nasarar kwada masa bishiya a
kirji, saboda karfin dukan sai da Hasnalu yayi
sama bayansa ya gwaru da jikin wata bishiya
255
TASKARNOVELS.COM.NG
take yayi aman jini, kuma tsinin reshen bishiyar
ya sokeshi a gefen hakarkarinsa na hadu, nan fa
Hasnalu ya kwala kabbara a lokacin da ya
subuto sakamakon tsananin zafi da zugin da ya
ji, a matukar galabaice ya fado kasa aikuwa sai
birirrikan suka yo masa ca domin su cinye
namansa danye, a lokacin ne hankalin gimbiya
Hursiyya ya dugunzuma ainun bisa mamaki sai
kawai ta ji hawaye ya subuto mata dan ganin
Hasnalu zai hallaka. Ba zato ba tsammani sai
kawai taga Hasnalu ya mike tsaye zumbur ya na
mai cigaba da yakar burirrikan yana gididdibasu
da takobinsa yana mai cigaba da yin kabbara, a
wannan lokacin ma sai karfinsa gami da zafin
namansa ya ninku fiye da na baya duk kuw da
cewar har wannan lokacin jini na zuba a
hakarkarinsa inda wannan reshe ya sokeshi.
Wohoho! Nan fa kasuwar daukar rai ta bude,
duk inda jarumi Hasnalu yasa gabansa sai dai
kaga birirrikan na zubewa kasa matattu, lokacin
da wuya tai wuya sai birirrikan suka ga cewar
Hasnalu ya kusa karar da su saboda haka sai
suka fara ja da baya dan su tsira da rayukansu
amman sai jarumi Hasnalu ya rinka kure masu
gudu yana rafkesu, sai ga shi girman birirrikan
256
TASKARNOVELS.COM.NG
gami da karfinsu duk si ya zama na banza,
daman ance in kaji ana ki gudu to fa sa gudu ne
bai zo ba. Nan dai Hasnalu ya cigaba da saran
birirrikan sun masu ihu gami da kururuwa suna
kum faduwa kasa mattatu a haka dai sai da ya
karar da su gaba dayansu, ya zamana cewa ko
daya bai tsira da rayuwarsa ba. A sannan ne jiri
ya kashe shi ya fadi kasa sumamme, ai kuwa sai
gimbiya Hursiyya ta yi wuf ta fito daga inda take
boye ta ruga da gudu izuwa kan Hasnalu, shima
aljani Radiyan sai ya fito daga maboyarsu yana
waige-waige cikin alamun tsananin tsoro dan
gani yake kamar akwai sauran wadannan
birirrikan a boye a wajen. A lokacin ne kuma
jarumi Hasnalu ya farfado daga dogon suman
da yayi, ko da ya farfado sai ya tsinci kansa bisa
cinyar Hursiyya idanunta cike da kwalla, a
firgice ya mike zaune zumbur yana mak kallonta
cikin mamaki sannan ya dubi raunin dake
hakarkarinsa, yaga an samasa magani kuma an
daure wajen da kyallen rigarta. Koda Hursiyya
taga Hasnalu ya mike tsaye sai ta kamu da
tsananin farin ciki ta dubeshi cikin murmushi
mai taushi ta ce godiya ta tabbata ga
ubangijinka wanda ya baka nasara da sa'a akan
257
TASKARNOVELS.COM.NG
wadannan mugayen burirrika. Kada jin wannan
batu sai jarumi Hasnalu yaji gabadaya tsigar
jikinsa ta tashi, nan take a karon farko ya ji a
rayuwarsa wata ya mace ta burgeshi saboda
dalilai guda biyu; dalili na farko kuwa shine
ganin kwalla a cikin idanun Hursiyya a lokacin
daya farfado daga dogon sumar d yayi wanda
hakan ya tabbatar masa da cewa tana cikin
tsananin damuwa bisa halin d ya shiga, dalili na
biyu shine tunda ya shigo wannan nahiyoyi
tsawon shekara guda da rabi ya ratsa ta cikin
birane da garuruwa amman bai taba haduwa da
wanda yayi yabo ga ubangijinsa ba face gimbiya
Hursiyya kawai sai Hasnalu yaji kaunar Hursiyya
ta shigeshi farat daya, abinda ko a mafarki bai
taba faruwa a kansa ba. Cikin murmushi
Hasnalu ya dubi Hursiyya ya ce madalla da
wannan yar sarki wacce ta ceto rayuwata,
hakika bna an irin godiyar da zanyi maki ba,
domin n lura da irin jinin d ya zuba a jikina mai
yawa ne, kuma inba dan kin tsaidashi ba da
wata kila yanzu na dade da mutuwa. Koda jin
haka sai itama ta maida mashi da martanin
murmushi ta ce ai asarar irinka guda daya a
cikin al'umma gwara ayi asarar gari guda. Da
258
TASKARNOVELS.COM.NG
farko dai kaga kai kyakkyawa ne irin wanda sai
an tara kyawawa dubu ba'a samu kamarka ba,
kai gwarzo ne a cikin jarumai mai jarumtakar da
sai an tona, domin na fahimci cewar ko dan
uwana sarki dujalu iyakar jarumtakar da zai iya
kenan, ga dukkan alamu ma sai k fishi tunda kai
ka dogara ne da zallar karfinka baka tsafi. Ya kai
wannan jarumi kayi sani cewa kaine saurayi na
farko daya taba burgeni a rayuwata, kuma in
banda dan uwana sarkk Dujalu babu wani
namiji da jikina ya hadu da nasa, ni kaina nayi
matukar mamaki bis yadda aka yi har naji na
aminta da kai tamkar ka kasance dan uwana na
jini. Duk wannan hira da su Hasnalu ke yi aljani
Radiyan na zaune a gefe daya a bayansu, yana
mai kallonsu da sauraronsu amman zuciyarsa
sai faman tafarfasa take tamkar zata kone,
saboda ya fahimci cewar da sannu jarumi
Hasnalu zai ja ra'ayin gimbiya ta karbi
addininsa, kuma akwai alamun cewa zasu iya
fadawa cikin tarkon soyayya. Nan fa hankalin
aljani Radiyan ya dugunzuma ainun ya fara
tunanin hanyar da zai bi ya lalata wannan alaka
tasu, ko kuma ya dauke Hursiyya su bace wa
jarumi Hasnalu. Hasnalu ya dubi gimbiya
259
TASKARNOVELS.COM.NG
Hursiyya ya ce yake wannan yar sarki kiyi sani
cewa nima kece mace ta farko da jikinta ya taba
haduwa da nawa, wanda yin hakan haramun ne
a addinina kasancewarki ba muharramata ba,
babu wani dan adam ko aljan daya taba ceton
rayuwata sai ke, a gaba daya nahiyoyin dake
nan kece mutum ta farko da tayi yabo ga
ubangijina. Yanzu dai abinda nake so ki sani
shine duk wannan gagarumar jarumtaka da
kikaga nayi har na samu nasarar kashe
wadannan birirrikan ba wai tsagwaron karfin
damtsena bane ko dabarata ba face taimako
daga ubangijina. Shin yanzu kin gamsu cewa
ubangijina shine na gaskiya ko kuwa har sai na
cika sharadi nayi abubuwa al'ajabi guda uku
kamar yadda kika bukata a baya? Sa'ad da
gimbiya Hursiyya ta ji wannan tambaya sai ta
juya da baya ta dubi aljani Radiyan shi kuma sai
yayi mata nuni da idanunsa kar ta ce ta gamsu.
Hursiyya ta juyo ta fusknaci Hasnalu cikin
murmushi tace da shi mu bi dai a sannu a
hankali har ka cika ragowar sharadin. Koda jin
haka sai Hasnalu yayi murmushi sannan yace
yake gimbiya ki kasance mai ra'ayin kanki ba
wai ra'ayin wani ba, kuma ki tabbatr kinyi aiki da
260
TASKARNOVELS.COM.NG
gaskiya ba da son zuciya ba, yanzu sai ki tashi
mu cigaba da tafiya. Koda jin haka sai Hursiyya
ta dubi Hasnalu cikin yanayin tsoro ta ce da shi
ai abune mai hadari mu cigaba da wannan
tafiya a haka, kana tare da danyen ciwo a
jikinka, akwai bukatar ka yi jinya koda na tsawon
sa'a goma sha biyar ne. Koda jin haka sai
Hasnalu yayi murmushi sannan ya ce yanzu
kina nufin kice idan na cigaba da tafiya da
wannan ciwon a haka wani abu zai taba lafiyata
kenan? Hursiyya tace ai bama abinda zai taba
lafiyarka ba ma, idan har ka cigaba da tafiya a
haka zaka ma iya rasa rayuwarka gabadaya.
Koda jin haka sai Hasnalu ya sake yin murmushi
a karo na biyu sannan ya karanta wata addu'a
ya tofa akan raunin nasa sannan ya mike ya
dubi Hursiyya da aljani Radiyan ya ce to ni dai
zan cigaba da tafiya, ko dai ku tashi mu tafi tare
ko kuma ku sameni a gaba, yana gama fadar
hakan sai ya kama hanya ya nausa cikin
wannan kogon dutsen mai duhu wnada
wadannan birirrikan suka fito daga ciki. Koda
ganin haka sai aljani Radiyan da Hursiyya suma
suka tashi da sauri suka bi bayanshi. Sai da
suka shafe rabin sa'a suna tfiya a cikin wannan
261
TASKARNOVELS.COM.NG
kogon dutsen amman basu hadu da komai ba
face kwarangaloli na sassan jikin biladama
wanda wadannan birirrika suka kashe, a sannan
ne suk gane cewa ashe wannan kogon dutsen
gari ne guda na birirrikan. Suna fitowa daga
cikin kogon sai kuma suka tsinci kansu a wani
dajin daban ba wancan ba, kawai sai suka
hango cibiyar tekun bahar sufiya ruwana nata
fanjam-fanjam kamar zai zo inda suke ya
shafesu. Nan take kuma suka rinka jiyo ihu
gami da kururuwar mazaje acan kasa-kasa
alamar cewar har yanzu fa ana kafsa wannan
azababben yakin acan bakin tekun. Koda iyo
wannan sauti sai Hasnalu ya waigo da sauri ya
dubi Hursiyya kawai sai yaga ta tsugunna a kasa
tana haki saboda gajiya, shi kuwa aljani Radiyan
ya koma gefe daya ya zauna harma ya fada cikin
kogin tunani. Hasnalu ya matsa kusa da
Hursiyya ya dubeta y ce ga dukkan alamu dai
muna daf da riskar inda ake yin wannan yaki,
dan haka sai kuzo mu karasa da sauri. Koda jin
haka sai Hursiyya ta dubeshi cikin alamun
tsananin mamaki tace wai kai wane irin mutum
ne wanda baya gajiya, ni abinda ma yake bani
mamaki game da kai shine yadda ka kasa
262
TASKARNOVELS.COM.NG
sarewa alhalin cewa kana dauke da rauni a
jikinka, koda ta zo nan a zancenta sai ta dubi
raunin nasa take kuwa ta sha mamaki, domin
kuwa raunin ya kame harma ya bushe kai kace
dama ya dade a jikinsa ba sabo bane. Al'amarin
da yayi matukar girgiza Hursiyya kenan, ta dubi
jarumi Hasnalu ta ce yaya aka yi wannan raunin
naka ya warke da gaggawa haka, tamkar ma ba
yau ka same shi ba? Koda ya ji wannan
tambaya sai Hasnalu yayi murmushi ya ce
wannan shine iko irin na ubangijina, dan haka
yanzu na cika sharadi na biyu da ke tsakaninmu
saura sharadi na uku wanda daga shi sai ki karbi
addinina kamar yadda muka yi alkawari.
Hursiyya ta maida mashi da martanin
murmushi tace tabbas zancenka dutse ne.
Lokacin da aljani Radiyan ya ji wannan batu sai
hankalinsa ya kara dugunzuma ya tabbatar da
cewa lallai dan bai dauki matakin gaggawa ba
akan jarumi Hasnalu to fa duk shirinsa sai ya
tarwatse. Hasnalu ya zauna daf da Hursiyya ya
dubeta ya ce ina ganin dai cewa yanzu tafiyar da
ta rage mana mu riski bakin tekun nan da ake
wannan yaki baya wuce ta rabin sa'a ba, tunda
daga inda muka baro zuwa kin tekun kunce
263
TASKARNOVELS.COM.NG
mani tafiyar sa'a guda ce kuma gashi mun shafe
kusan rabin sa'a a iya tafiyar da muka yi. Jin
hakan ne yasa Hursiyya ta yi murmushi sannan
tace tabbas gama babbar alama na muna iya
jiyo sautin ihun mazaje daga can filin dagar
gami da karafkiyar karafa, sai dai fa abinda ya
bani mamaki shine ban ji karaji gami da rurin
aljanu ba wanda shine ya kamata yafi amsa
kuwwa da cika kunne. Koda jin wannan batu sai
Hasnalu ya jinjina kai sannan ya ce aikuwa indai
akwai aljanu a wannan yaki kuma ya zamana
cewar bama jiyo rurinsu gami da karajinsu to
babu mamaki an kashesu gabadayansu.
Hursiyya ta jinjina kai ta ce kwarai kuwa na
yarda da zancenka, idan kuwa haka ne kaga
kenan yakin yazo da sauki tunda yanzu ya rage
tsakanin mutane kawai, kuma lallai ana daf da
kareshi don haka zaifi mana kyau mu tashi mu
karsa can din da sauri. Koda jin wannan batu
sai aljani Radiyan ya takarkare ya bushe da
wata mahaukaciyar dariya, al'amarin da yasa
Hasnalu da Hursiyya suka juyo da sauri kenan
suna masu kallonshi cike da mamaki, Hursiyya
ta ce da shi ya kai Radiyan ina dalilin wannan
dariya taka ? Maimakon Radiyan ya bata amsar
264
TASKARNOVELS.COM.NG
tambayarta sai ya sake bushewa da dariya a
karo na biyu, lokacin guda kuma ya murtuke
fuska ya ce yanzun nan nima nayi bincike a cikin
madubin tsafina naga cewa lallai an kashe gaba
daya aljanun da suke a wannan tsibiri na kogin
bahar sufiya, a halin yanzu babu sauran aljani a
wannan daji gabadaya face ni da kuma Aljani
Raugatul Agwanu, yanzu kuma gashi zan riga
Raugatul Agwanu zuwa bakin wannan teku,
tunda shi yana can yana bacci bai farka ba,
tunda a halin yanzu sihirin tsafi ya daina aiki
acan filin yakin babu wanda ya isa ya ganni,
kunga kenan zan iya zuwa na shiga cikin takun
salin alin ba tare da wani ya ganni ba na lalubo
inda takobin take, da zarar na daukota shikenan
na zama sarkin duniya kuma yanzu zan bace
maku da gani babu yadda zaku yi da ni. Babban
burina na biyi shine na mallakeki ki zama abar
debe mani kewa kamar yadda shalbirat ta debe
wa aljani Raugatul Agwanu kewa tsawon
shekaru gom sha bakwai, kinga idan na
mallakeki babu mai iya rabamu har abada sai
dai ajali tunda na mallaki takobin Saiful Lujara
na zama sarkin duniya. Sa'ad da aljani Radiyan
yazo nan a zancensa sai takaici ya lullube
265
TASKARNOVELS.COM.NG
gimbiya Hursiyya har idanunta suka ciko da
kwalla, ta dubeshi tace ashe daman yaudarata
ka yi kenan, wannan shine burinka a cikin
wannan tafiya ban sani ba, hakika ka cika maci
amana shugaban azzaluman duniya. Koda jin
haka sai aljani Radiyan ya cigaba da kyalkkyala
dariyar mugunta. Ita kuma gimbiya Hursiyya sai
ta kama kukan bakin ciki, kawai sai ta ji jarumi
Hasnalu ya kira sunan aljani Radiyan yana mai
daka masa tsawa gamk da cewa ya kai Radiyan
kayi dukkan abinda kaga dama amman ka sani
cewa da izinin ubangijina ba zaka samu nasara
ba. Koda gama fadin haka sai Hasnalu ya zauna
a kasa dirshan gaban gimbiya Hursiyya kuma ya
lankwashe kafafunsa sannan ya runtse
idanunsa ya kama karanta wata addu'a ta
neman taimakon Allah a cikin zuciyarsa. Shiko
aljani Radiyan sai ya cigaba da kyalkkyala
dariyarsa ta mugunta, a lokacin ne kuma
hankalin gimbiya Hursiyya ya dugunzuma
ainun, tsoro ya baibayeta kuma jikinta ya kama
rawa, haka dai aljani Radiyan ya cigaba da
kyalkkyala wannan dariya har izuwa tsawon yan
dakiku, katsam kuma sai yayi girgiza ya zama
guguwa, take guguwar tayi kan gimbiya Hursiyya
266
TASKARNOVELS.COM.NG
zata sureta cikin zafin nama jarumi Hasnalu ya
zare takobinsa ya kai wa wannan guguwa
wawan sara ba tare da ya bude idon nasa ba,
kawai sai suka ji aljani Radiyan ya rusa uban ihu
daga can kuma sai suka ji karar faduwarshi
kasa. Hasnalu ya bude idanunsa yaga gawar
aljani Radiyan a kasa gangar jikinsa ta rabu gida
biyu. Koda gimbiya Hursiyya tayi arba da gawar
aljani Radiyan ya kwance sai ta rungume
Hasnalu ta kuma fashe da kukan murna hadi da
yi masa godiya bisa ceton rayuwarta da yayi
daga sharrin aljani Radiyan. Cikin sauri
Hasnalu ya janye jikinsa daga nata ya ce ai ba ni
bane abin godiya face ubangijina, wai shin kin
manta ne cewa a baya kema
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 18