can
kuma sai ya dago kai ya dubeshi ya ce Yakai
abbana shin ka manta ne cewar ka taba
gayamini cewar bisa binciken da kayi a hallarar
tsafinka ajali ba zau taba riskar daya daga
cikinmu ba a wani wuri face a gida?? Ashe
kenan duk irin gararin da zamu shiga zamu
dawo gida a raye? Lokacin da boka sadusa ya
jin wannan batu sai ya sunkuo da kansa kas
cikin alamun kunya yai shiru yace komai ba, har
izuwa tsawon yan dakiku, sai daga can kuma ya
dago kai ya dubi halyal lokacin da kwalla ta ciko
a cikin kwayar idanunsa ya ce ya kai dana
hakika duk abinda ka fadi gaskiya ne, to amma
kuma ai bana son mu dawo gida a cikin mugun
hali rashin lpyar da zata zama sanadin
ajalinmuka hkri bazan iya yin wannan tafiya ba
tare da kai. koda jin haka sai halyal ya durkushe
kasa yana mai fashewa da kuka. al amarin
daya kara jefa sadusa da Hunaisa cikin
tsananin tausayinsa kenan. Nan dai sadusa ya
kama kadadun halyal ya tasoshi tsaye ya
sumbaci goshinsa sannan ya rungumeshi a
100
TASKARNOVELS.COM.NG
kirjinsa duk su biyun suka fashe da kuka a
lokacin guda.
Zan ci gaba.
MAZAN JIYA
Littafi na Hudu 4
Part J
Na Abdulaziz Sani m gini
Typing Abubakar Saleh AlQuyraemey
Koda ganin haka sai itama hunaisa ta rugo
garesu ta kankamesu su ukun ta tayasu kukan
sadusa ya janye jikinsa daga cikin nasu ya tafi
yana waigensu hawaye na zuba daga
idaanunsa.
Al amarin daya kara dugunzuma hankali halyal
da Hunaisa kenan suka ci gaba da matsanaicin
101
TASKARNOVELS.COM.NG
kuka suna hangen sadusa har sau da ya bace
musu da gani.
Nan fa Halyal da Hunaisa suka cigaba da kuka
suna kankame juna kamar bazasu daina ba har
izuwa tsawon kusan dakika daru biyu da sittin.
Kwatsam! Ba zato ba tsammani sai suka jiyo
takun sawu a yayin da kawunansu ke kallon
kasa, cikin sauri suka dago domin su ga wanda
ke zuwa.
Kawai sau suka ga ashe sadusa ne ya dawo
kuma ya tunkarosu hannanyesa a bude hawaye
yana shatata bisa kumatunsa.
Cikin tsananin farin ciki Halyal ya ruga izuwa
gareshi ya dada kan kirjinsa suka rungume juna
suna masu kyalkyala dariya.
* **
Tun da suka fara tafiya daga cikin gari halyal
yafara ganin abubuwan al ajabi bisa yanayin
102
TASKARNOVELS.COM.NG
tafiyar tasu domin da zarar sun yi tafiya kamar
taku goma sai yaga sun shafe nisan zira'i dari
nan da nan suka fice daga cikin gari suka nausa
cikin daji.
Ai kuwa suna shiga daji yaji sadusa ya kama
hannunsa ya rike nan fa ya jashi da gudu suka
falfala da gudu.
Wannan karo sai halyal ya sako cike da
tsananin mamaki fiye da farko domin yanzu
tafiyar sa a guda ce suke shafewa a cikin dakika
sittin kacal sai dai kawai yaga suna gifta
dazuzzuka a cikin matsananincin gudu tamkar
giftawar tauraruwa mai wutsiya.
Amma da ya tuna cewar duk wannan lamari
alamari ne na tsafi sai kawai yayi murmushi
yace
a zuciyarsa kowa da kiwon da ya karbeshi.
Haka dai sadusa da halyal suka cigaba da gudu
a cikin daji babu sassauci.
Tun safe suka fara wannan gudu amma har sai
da rana ta fadi sannan suka tsaya cak a farkon
103
TASKARNOVELS.COM.NG
wani daji mai yanayi iri dabam da na sauran
dukkan dazuzzukan Da suka wuce a baya.
Adai dai wanna lokacin ne ji tsananin gajiya da
kishirwa ta riskesu, ba shiri suka durkushe kasa
bisa guiwoyinsu suka kama haki sannan
kowannensu ya bude butar ruwansa ya
kwankwada, koda suka dawo cikin hayyacinsu
sosai sai suka kama kallon wannan daji da suka
tsinci kansu a cikinsa.
DAJI NE mai dauke da wandansu irin dogayen
bishiyoyi masu tsananin tsawo da ba a iya ganin
karshensu kuma ganyayen bishiyoyin masu fadi
ne sosai don haka su karawa dajin duhu ya
zama abin tsaro.
Sannan kua akwai wadansu irin duwatsu a dajin
masu wani irin sufofki na ban tsaro, wani
dutsen sai kaga yana kama da mutum wani
kamar aljan wasu kuma da dabbobi suke kama,
kai komai dakewar zuciyar mutum idan ya tsinci
kansa a cikin wannan daji sai ya razana
musaman idan ya ji irin tsananin shirun dak
cikin dajin, mutum baya jin sautin komai hatta
na tsuntsaye kuwa aa da zarar mutum ya taka
104
TASKARNOVELS.COM.NG
ganyeye bishiyoyin dajin wadanda suka fado
kasa suka bushe rumus sai kaji karar ta cika
dajin gaba daya hara da amsa kuwwa.
Nan take halyal yakamu da tsananin tsaro gaba
dayan jikinsa ya kama tsuma bai san sa adda
ya dada kankame jikin sadusa ba.
Koda ganin haka sai sadusa yai murmushi yace
saki jikinka ya kai dana kayi sani cewa indai
kana tare dani babu wani tsautsayi da zai
sameka ka sani cewa tun shigo wata sabuwar
nahiyar ne wacce ba tamu ba.
Yanzu kamata yayi mu nemi wuri mai kariya
inda zamu yadda zango tunda duhu ya soma
sannan sai nayi mana bincike na gano ko akwai
abinda muka zo nema a cikin wannan daji.
Koda gama fadin hakan sai suka mike tsaye
suka kara nausawa cikin suna ketawa ta cikin
surkuki duhuwoyi ciyayi da sako sako. Ai kuwa
sai da suka shafe lokaci mai dan tsawo suna
neman wani kogon dutse da zasu iya shiga
cikinsa su fake sakamakon hadarin da yake
barazanar zubar da ruwa a ko yaushe, tunda har
105
TASKARNOVELS.COM.NG
an fara walkoya gami da tsawa mai. ban tsoro,
wacce duk sa adda aka yita sai dai kaga halyal
na dada kankame hannun sadusa.
Abinda ya dada daure masu kai shine duk
tsawin wannan lokaci da suka shafe suna yawo
a cikin dahi ko kadangare basu gani ba.kuma
basu hadu da wani mugun abu ba, shi kansa
sadusa sai daya tambayi kansa a ckin.zuciyarsa
yace,
TO WAI SHIN MENENE YA HANA DABBOBI DA
KWARI RAYUWA A CIKIN WANNAN DAJI???
suna cikin wannan dube dube ne suka hango
wani katon kogon dutse a gabansu, cikin
hanzari suka ruga izuwa bakin kogon a lokacin
da aka fara yayyafi kua aka ci gbada tsala
wakiya da tsawa, da isarsu bakin kogon dutse
sai suka tsaya sadusa ta yi nuni da hannunsa
izuwa cikin kogon, take wani irin haske na tsafi
ya haskake cikin kogon gaba dayansu kofa suka
yi arba da
aabin da ke cikin kogon sai suka cika da
tsananin mamaki, ba komai suka gani ba face
wata yar karama aljanar duniya.
106
TASKARNOVELS.COM.NG
Kaya ne na alatu a cikin kogin tamkar turakar
wani hamshikin basarake. An shimfida dardua
ta alfarma ai dan karen laushe ta rufe
kasankogon gaba daya mai launin shudi.
A gefe daya nan a zncenta sai ta fashe da kuka
al amarin dayai matukar baiwa su sadusa
mamaki kena har suka ji sun kamu da tsananin
tausayinta daga can sau sadusa ya dubeta ya
daka mata tsawa yace yake wannan ma
abokiyar keji: shin yanzu zaki iya iya gaya mana
ko wane ne ya ajiyayeki a wannan kogon dutse
wanda muka ji kin kirashin da shugaban
azzalumai na duniya.
Koda jin haka sai wannan kyakkyawa ta cikin
keji tayi a jiyar zuciya tace sanin wanda ya
ajiyeni acikin wanna kogo dai dai yake da sanin
ranar ajalin mutum domin yakasance
GUGUWAR ANNOBA kuma GOBARA DAGA
KOGI wacce ba da magani:
Sunan wanda ya ajiyeni anan shine ALJANI
RAUGATUL AGUWANU. Koda jin wannan batu
sai boka sadusa ya mike zubur! Cikin firgici da
107
TASKARNOVELS.COM.NG
tsananin tsoro ya kama hannun halyal domin su
fice daga cikin kogon:
Karar takun sawun aljani raugatul aguwanu tasa
suka koma cikin kogon dutse da sauri suka
shige cikin karkashin wanna makeken gado na
aljanin raugatul aguwanu:
Takun sawun na Raugatul aguwanu tamkar
giwaye neke tserun gudu a cikin dajin har maya
haddasa girgizar kasa. Kai tsaye aljani raugatul
aguwanu yashigo cikin kogon nasa tya zauna
kan gefen wanna gado nasa. Kai tsaye aljani
raugatul aguwanu yashigo cikin kogon nasa tya
zauna kan gefen wanna gado nasa.
Saboda nauyinsa sai da gadon ya lotsa kasa
har su sadusa suka ji kamar wani katon dutse
ne ke shirin dannesu ya kakkarya musu
kasusuwan gadon baya. Koda kyakkyawar
yarinyar nan tacikin keji ta ga haka sai ta dubi
Raugatul Aguwanu ta bushe da dariya tace
haba ya shugabana yau kuma wahalar farautar
ce tasa ka manta ka fara zama akan teburinka
kaci yayan itatuwa? Koda jin haka sai aljani
Raugatul Aguwanu ya bushe da dariyar farin
108
TASKARNOVELS.COM.NG
ciki: Kasancewar kyakkyawar yarinyar bata
taba yi masa magana mai dadi ba a tsawon
shekaru da ya ajiyeta a cikin wanan kogon sai
yau. Cikin hanzari ya mike tsaye ya nufi inda
kujerarsa ta zama take wadda ke karkashin
wannan babban zagayayyen tebur. Kafin ya isa
kan kujerar tuni sadusa da Halyal sun fito daga
karkashin gadon sun ruga izuwa bayan tarin
dukiyar zinare sun buya. A Dai Dai wannan
lokaci ne Raugatul Aguwanu ya zauna akan
kujerar. ai kuwa sai ya shaki kamshi bil adama
a cikin kogon fiye da yadda ya saba shaka a
kullum ya tabbatar da cewa yasami baki. Nan
fa ya kama waige waige da dube dube cikinn
kogon. Koda su sadusa suka ga haka sai suka
binne kansu a cikin wannan duniya ta zinare
tamkar basu taba wanzuwa ba a wajen. Hakan
ta faru ne da taimakon karfin sihirin tsafi
sadusa. Aljani Raugatul Aguwanu ya mike tsaye
ya kama dube dube ya shiga nan ya fita can: ya
bankada ko ina amma bai ga bil adama ba
alhalin kuma yaji kamshinsu. Koda ya dago kai
suka hada ido da wanna kyakkyawar yarinya ta
cikin keji sai ta sunkui dakanta kas, abinka
mara gaskiya ko a ruwa sai ya yi jibi sai jikinta
109
TASKARNOVELS.COM.NG
ya kama tsuma. A fusace Raugatul Aguwanu ya
durfafo kejin da take cikin ya dubeta ya daka
mata tsawa yace ke tsohuwar munafuka
tabbas kin san da shigowar baki wannnan kogo
nawa amma sbda munafunci da cin mana irin
naku na mata shine kika yi shiru baki gaya mini
ba. To ki sani cewa idan har baki gaya ini inda
suka buya ba a cikin wannan kogo yanzu nan
zan fito dake daga cikin kejin nan na yayyagaki
filla filla na watsar. Ai daa na ajiyeki ne anan
kawai don ki debe mini kewa kasancewar babu
wata hallita a cikin wannan daji sai ni kadai.
Koda jin wannan batu sai kyakkyawar ta bushe
d dariya lokaci guda kua ta fashe da kuka
sannan ta kalleshi tace ai daa na dade ina
rokonka akan ka kasheni na huta da takai ci da
bakin cikin rayuwar da ka jefani cikin amma
kaki, ka rabani da iyayena dangina da kasarmu
ka baroni da cikin jinsin mutane yan uwana ka
kawoni nan cikin wannan daji inda ko kwaro
babu bare wani dan tsuntsu wanda zai rinka jin
sautin kukansa ina jin dd cewar akwai mai rai a
kusa dani
110
TASKARNOVELS.COM.NG
Tun inayarinya karaa ka sato ni ka kawoni nan
kuma ka tsafanceni ka sani a cikin wanna keji
na zama kamar ya tsuntsuwa alhalin na
kasance bil adama. Ka cuceni cutar da bani da
halin daukar fansa face na ga ranar da Zakayi
mutuwar wulakanci : Tabbas a duniya ba a taba
samun azzalumai kamar ka ba. Ina mai
rokonka da ka hanzarta kasheni domin na huta
da wnn bakin zalunci naka. Sa adda
kyakkyawar yarinyar ta cikin keji ta zo nan a
zancenta sai aljani Raugatul Aguwanu ya kara
fusata ainun yace aikuwa yanzu nan zan ida
mugun nufina akanki. Kawai sai ya kai hannu ya
suro kejin danufin yabude ya daukota daga
cikin amma sai yaji an ce dakata ya kai
Shugaban azzalumai na duniya. Cikin hanzari
da mamaki Raugatul Aguwanu ya juyo da baya:
take yayi arba da boka sadusa da dansa Halyal
tsaye a bayansa. Raugatul aguwanu ya kurawa
boka sadusa idanu cikin tsananin mamaki har
izuwa tsawon yan dakiku yana nazarinsa sanna
yace ya kai wannan ha tsabibin boka kai kuwa
ya ya aka yi ka shigo cikin wannan daji har ka
iso nan cikin makwanci na batare dani ji motsin
shigowarku ba? Kune bil adama na biyu da
111
TASKARNOVELS.COM.NG
suka taba shigowa cikin wannan daji har suka
rayu a tsawon sama da nisan sa a guda sbda
karfin shirina gami da azababben karfin dantse
na
: wannan daji da kuka shigo shine dajin da ake
yiwa lakabi da DARUL HUSHUSHUL MAUT wato
gidan daba ashiga kuma ba a fita. Tunda nazo
na tare a wannan daji yazama nawa ni kadai
domin na kori dukkan aljanu dabbobi da
tsuntsaye gami da dukkan kwarin dake cikinsa.
Zan ci gaba.
MAZAN JIYA
Littafi na Hudu 4
Part K
Na Abdulaziz Sani m gini
Typing Abubakar Saleh AlQuyraemey
112
TASKARNOVELS.COM.NG
Fatake da matafiya kuwa hatta na jinsin aljanu
haka suka hkra da giftawa ta saman wanna daji
domin koda tsautsayi suka zo wucewar
kamawa suke da wuta su kone saidai tokarsu
tazubo kasa: kai kuwa wane irin karfin tsafi ne
da kai hka wanda har yafi nawa ka ketare duk
masifun da na zuva a wwannan daji? Lokacin
da boka sadusa yaji wannan tambaya sai yayi
murmushi cikin izza sannan ya durfafo inda
wannan tebur yake ya zauna kuma ya dauku
tuffa guda daya yakama ci tamkar a cikin
turakarsa yake sannan ya yafuto aljani
Raugatul Aguwanu da hannu yana mai kiransa:
Ba tare da gardamar komai ba Raugatul
Aguwanu ya ajiye wannan keji wanda yake
hannunsa sannan ya taho wajen sadusa ya
zauna akan tasa kujerar suka fuskaci juna
: A wannan lokaci zuciyar sadusa ta kama
dukan uku uku domin a cikin matukar tsorace
yake kawai dai banza ce ta kori wofi
113
TASKARNOVELS.COM.NG
A iya tunanin aljani Raugatul Aguwanu boka
sadusa ya fishi karfin sihirin tsafi tunda har ya
iya shigowa wannan daji na darul hushushul
mautt lapiya: Abinda ya manta shine a yau ya
sha afa cewar tunda sassafe ya cire dukkan
tsaron da yasa wa dajin sakamakon wani
dogon nazari da yayi a halwar tsafi don bincike
akan yanayin da duniya kw ciki: Har yagama
binciken nasa ya tafi dajin dake gaban nasayin
farauta bai mai da sihirin tsaron ba a dajin na
darul Hushushul maut. Tun da boka sadusa
yazo duniya bai taba ganin aljanin mai girma
kirar karfi kutuciyar samartaka da tsananin
muni ba kamar Raugatul Aguwanu don haka a
cikin tsananin firgice yake da shi sbda ya san
cewa ko yaya yayi wani dan kuskure wanda
Raugatul Aguwanu ya gano cewa ya fishi karfin
sihitin take zai halaka Su shi da halyal: Bayan
sun fuskanci juna sai sadusa yace ya kai
wannan sarki jaruan aljanu na duniya ka yi sani
cewa musaman nazo wannan daji na darul
Hushushul maut domin na gana dakai
114
TASKARNOVELS.COM.NG
Tabas na san wani gagarumin al amari wanna
kai baka sani ba
Koda jin wannan batu sai aljani Raugatul
Aguwanu ya gyara zama ya tattara hankalinsa a
waje daya kuma ya nutsu sosai yana mai
sauraron boka sadusa. Sadusa yai gyaran
murya sannan yace shin kana da lbrin
gagarumin yakin da ake fafatawa yanzu hakan a
can bakon kogin Bahar Sufiya? Koda jin wanna
batu sai aljani Raugatul Aguwanu yasake gyara
zama yace kwarai kuwa na san da batun
wannan yaki wanda ake yi tsakan Sarki dujalu
da sarki maharaz, In banda abinka waye yake
shiga fadan manya? Ai dujalu da maharaz sun
fi kowa karin sihirin tsafi a wanna duniya kaf:
Shi ya sa kagani na rabe a waje daya na dawo
nan cikin daji na hakura da rayuwa acikin
mutane da yan uwana aljanu
Koda jin haka sai boka Sadusa ya kyalkyle da
dariya al amarin da yai matukar baiwa aljani
Raugatul Aguwanu mamaki kenan
115
TASKARNOVELS.COM.NG
Awannan lokaci Halyal da kyakkyawar yarinya
ta cikin keji kuwa a ckin matukar tsoro suke
domin gani suke cewar idan tusa ta karewa
bodari hallaka zaiyi
Su kansu sun fahimci cewar sadusa dai yan
dabaru yake yi domin su kubuta: Cikin alamun
dadin mamaki Raugatul Aguwanuyace yakai
wannna hatsabibin bola ina dalilin wannan
dariya taka? Sadusa ya murtuke fuska tamkar
an aiko masa da sakon mutuwa sannan yace ai
nan dajin da ka kadawo tamakar kayi gudun
gara ne ka tarar da zago: to tsaya kaji idan aka
gama wannan yaki duk wanda yasami nasara
tsakanin sarki dujalu da sarki maharaz shine zai
mallaki kayan yakin MAZAN JIYA wannan duk
kuwa ya mallaki Takobin SAIFUL LUJARA
MASHIN GALILUL HARAS da HULAR LAMSARA
sai ya mallaki kowa da komai na cikin wannan
duniya kaga kenan kai kanka sai kazama
bawansa wannan daji naka na darul Hushushul
maut sai ya zama wajen shan iskasa
116
TASKARNOVELS.COM.NG
Kai kuwa nasani cewa a dunia babu abinda ka
tsana sama da kayi bauta a karkashin wani ka fi
son rayuwarka ta kare acikin cin gashin kanka
ko ba haka bane? Koda boka sadusa yazo nan a
zancesa sai hankalin aljani Raugatul Aguwanu
ya dugunzuma ainun fiye da koyaushe a
rayuwarsa sbda ko kada bai taba tunanin
faruwar wannan al amari ba: nan take halyal da
kyakkyawar ta cije keji suka ji sun sami
nutsuwa da kwanciyar hankali bisa jin wanna
bayani da sadusa ya yiwa aljani Raugatul
Aguwanu musamman da suka gayadda jinkisa
yai sanyi kuma hankalinsa ya tsahi. Tsawon
yan dakiku Raugatul Aguwanu yana nazari
tunani har maya mike tsaye yakama kai kawo
yana ciza ya tsa. daga bisani sai ya koma kan
kujerarsa ya zauna kusa da sadusa ya dubeshi
ya ce yakai wannan takadarin boka kayi sani
cewa hakika kazo mini da babban al amari
wanda yafi gaban tunaniba da hangena don
haka sai nayi bincike na tabbatar da gaskiyarsa
117
TASKARNOVELS.COM.NG
To wai shin idan har abindaka fada min
gaskiyane to yaya zan iya kubuta kena Ni dai
kam da dai na zauna a karkashin wani mulkeni
gwara na kashe kaina domin ban ga anfani
wannan tsananin karfin dantsen nawa gai da
karfin sihirina wanda na shafe sama da shekaru
arba in ina yawon nemansa a cikin duniya
Sadusa ya gyada kai yace tabbas kayi gaskiya:
Amma ina mai tabbatar maka dacewa ni ina da
mafita a gareka amma sai bayan ka gama
bincikenka kaga gaskiyar wannan al amari
sannan zan gaya maka mafitar kuma bisa wani
sharadi
Koda jin haka sai aljani Raugatul Aguwanu ya
kyalkyale da dariya sanna yace hakika yai na
gamu da sarkin wayo: Ti amma fa kasani ramin
karya kurarre ne idan har duk abinda kazo mini
dashi ba gaskiya bane asirinka zai tonu
118
TASKARNOVELS.COM.NG
idan kuwa asirinka ya tonu da kai da wancan
kyakkyawan dan naka sai nayi muku mugun
kisan gilla irin wanda ba taba yiwa wani
mahaluki ba a doron kasa
: kafin Aljani Raugatul Aguwanu ya gaa rufe
bakinsa tuni boka sadusa ya dakamasa tsawa
yana mai cewa kai matsoracin aljani wanda
yakasa fita filin daga inda manya mazaje ke
fafatawaa: ina mai horonka da ka iya bakinka
ka saisaita lafazinka a gareni in ba haka ba
kuwa yanzu nan zan fusata na koneka kua na
kone gaba dayan wannan daji dakake matukar
kauna kamar yadda uwa keson danta
Dajin wannan jawabi sai Raugatul Aguwanu ya
dan tsorata don haka sao ya sunkui da kansa
kas cikin alamun girmamawa yace kayi mini
uzuri ya kai takadarin boka ka sani fa ni haka
halina yake bana son raini. Yanzu dai ni a koshe
nake zan sha giya domin na kwanta na yi barci
sosai sai dare ya tsala sannan zan tashi nayi
119
TASKARNOVELS.COM.NG
bincike a Hallarar tsafina bisa wannna sabon al
amarin daka zo mini da shi
Abinda nake bukata da ku shine ya yin dana
fara barci bana bukatar naji matsin komai ko
yaya yakee domin idan har na farka bana iya
komawa barci
Kai idan da hali ma ku fita daga waje kuje ku
yawata a cikin dajin nan har izuwa lokacin da
zan tashi daga barcina
ina mai tabbatar muku da cewa akwai
abbuwan al ajabi da yawa a cikin daji nan
wadanda zasu debe muku kewa izuwa lokacin
tashina daga barci: Koda jin wannan batu sai
sadusa yayi murmushi sannan yace ka san
ance da dan gari akan ci gari: Me zai hana fito
da wannan kyakyawar yarinya daga cikin keji
domin tayi mana jagora a cikin wannan daji
tunda ta fimu saninsa? Sa adda aljani Raugatul
120
TASKARNOVELS.COM.NG
Aguwanu yaji wannan bukata ta sadusa sai yai
shiru ya juya al amarin a cikin zuciyarsa kuma
ya kurawa sadusa idanun cikin alamun Rashin
Yarda daga can sai yace Menene tabbacin
cewa ba yaudarata za kuyi ba ku gudu da
Gimbiya SHALBIRAT? Kai sani cewa da raina
babu wani abu na biyu da nakeso sama da ita.
Sadusa yai murmushi yace Ai inda don ita na zo
wannan daji da baza kazo ka riskemu ba a cikin
kogonka tunda ina da karfin sihirin da zan iya
saceta: Raugatul Aguwanu ya gyada kai cikin
alamun nuna gamsuwa amma a can karkashin
zuciyarsa Dari dari yake yi
: Kawai sai yayi kuru ya sa danyatsansa guda ya
bude kejin da gimbiya Shalbirat ke ciki:
Shabiyat ta taka dan yatsan Raugatul Aguwanu
cikin tsananin farin ciki mara misaltuwa sbd
tsawon shekaru goma sha bakwan da ta yi a
wannan daji na Darul Hushushul maut a cikin
kejin ta yisu bata taba fitowa ba waje
121
TASKARNOVELS.COM.NG
: A sannan ne Raugatul Aguwanu ya sauke tafin
hannunsa kasa ta dir: Sai gata yar motsitsiya a
gaban sadusa tamkar dan karamin bera
Duk wannan abu dake faruwa Halyal na tsaye a
can gefe daya ya kurawa Shalbiyat idanu yana
mai matukar al Ajabi bisa ganin tsananin
kyawunta wanda yake ganin cewa ko Gimbiya
Hursiya kanwar sarki dujalu Albarka
Lokacin da Shalbirat ta duro kasa daga kan
tafin hannun Raugatul Aguwanu sai ta kaa
raawa da tsalle doin murna kuma ta fasge da
kukan farin ciki: A sannan ne aljani Raugatul
Aguwanu ya dubi sadusa yace Ga masoyiyata
Gimbiya Shalbirat na fito da ita kua na damkata
amana a hannunka: ka tafi da ita izuwa cikin
daji ku yawata daga nan har izuwa wayewar
gari: Koda gama fadin hakan sai aljanin
Raugatul Aguwanu ya nufi inda aka ajiye wani
katon tulu wanda sbd girmansa da nauyinsa
kato arba in bazasu iya rabashi da kasa ba ama
shi da yan yatsu biyu ya daga tulun: Ashe tulun
122
TASKARNOVELS.COM.NG
cike yake da ruwan gida kawai sa i ya kafa bakin
tulun a bakinsa ya kama sha kwal kwal karar
tafiyar ruwan giyar a cikin cikinsa tamkar ruwan
tekune ya balle yana shatata izuwa cikin teku
Raugatul Aguwanu bai sauke tulun giyar
kasaba sai da yaji babu sauran digo daya na
ruwan giya sannan ya ajiyeshi a kas ya tafi
izuwa kan wannan katon gado nasa na alfarma
yana layi yakife kasa: ko dakika goma bayi ba ya
kama wani irin gagarumin Munshari
: koda ganin faruwar hakan sai gimbiya
shalbirat ta yunkura a fusace ta zare wata
wukar sihiri ta aljani Raugatul Aguwanu dake
kugunsa daga sama da nufin ta caka masa ita a
kirjinsa sai boka sadusa yai wuf ya rike
hannunta sanan ya karbe wukar ya mai da ira
cikin kufenta da ke jikin Raugatul Aguwanu
Sadusa yayiwa Shalbirat da Halyal nuni da suyi
shiru kuma kada suyi wani kyakkyawar motsi:
Nan take yajasu suka fice daga cikin kogon
gaba daya: Sai da suka yi nisa da inda kogon
123
TASKARNOVELS.COM.NG
dutsen yake inda basa iya hangoshi sannan
suka zauna domin su dan huta: za;ansu ke da
wuya sai Shalbirat ta fashe da matsanincin
kuka
Al amarin da yai matukar dugunzuma hankalin
su Halyat kenan suka shiga rarrashinta suna
tamyarta dalilin kukan nata: Da kyar suka
shawo kanta ta daina kukan sannan tace ba
komai ne yasa kuka ga ina wannan kuka ba
face tsananin bakin cikin kun hanani kashe
aljani Raugatul Aguwanu domin ya salwantar
da rayuwata kuma ya kunsa min bakin cikin da
Har na mutu babu wata fansa da za ta
kankareshi: Kuyi sani cewa ni ce ya guda daya a
wajen mahaina sarki sharyalu na Birnin taukib:
babu irin kalar gatan da ban gani ba a duniya
kuma a nahiyar damuke babu wani sarki mai
karfin mulki da tarin dukiya irin ta mahaifina:
Mahaifin nawa bashi da kowa a duniya face
wata kanwaesa mai suna JUZAIRAT ta ri ga
mahaifina yin aure da shekara shida amma
bata taba samun haihuwa ba har mahaifina
yazo ya yi auren ka haifeni: Al amarin da yajefa
124
TASKARNOVELS.COM.NG
juzairat cikin tsananin bakin ciki kenan sbda
bata da wani buri wanda ya fi ta haifi dan da zai
gaje sarauta. babu irin asirin da juzairat ba
tayiwa mahaifiyata ba akan kada tasamu ciki
gami da kulle kulle da makirce makirce na
zahiri amma duk butaka bata biya ba
Kai sai da takai ta kawo juzairat tana nuna
kiyayyerta ga samun juna biyun mahaifiyata a
filin har maifina ya fahimta amma bai taba
nuna mata damuwarsa ba sbd tsananin son da
yake mata: Lokacin da na isa shekara ba kwai a
duniya lavarin tsananin kyawuna ya bazi ko ina
a nahiyar ya zamana cewa tun a sannan ya yan
sarakai da yan mayan attajirai sun fara zuwa
neman aurena sai hankalin juzairat ya
dugunzuma ainun kuma ta tsaneni fiye da
komai: A wannan lokaci tsufa ya fara riskar
mahaifina kuma gashi kullum yana cikin fama
da lalura ta rashin lafiya iri iri: gaba daya
likitocin mahaifina sun kasa gane abinda ke
damunsa don haka suka daina bashi magani
aka rinka kiran bokaye kowa yana yin iya bakin
kokarinsa amma babu sauki
125
TASKARNOVELS.COM.NG
A wannan lokacin na shaku da mahaifina ainun
fiye da yadda na shaku da mahaiyata domin
dare. Da rana bana yarda na nisanra dashi sau
tari sai bayan nayi barci akan kirjinsa sannan
mahaifiyata take zuwa ta daukeni ta tafi dani
izuwa kan gadonta ta shimfideni
Wani dare wanda shine daren mummunan
bakin ciki a Tarihin rayuwata wato daren da ba
zan taba mancewa dashi ba: Ina kwance akan
gado MAHaifina muna ta wasa dariya sai ciwo
ya taso asa har ya mike zaune da kyar ya zama
tari har da aman jini
Al amarin da ya dugunzuma hankalina kenan
na fara kuka kuma na yunkura da nufin naje na
kirawo mahaifiyata amma sai mahaifina ya yi
wuf ya riko hannuna a lokacin da shima ya
kama zubar da hawaye
126
TASKARNOVELS.COM.NG
Cikin karfin hali yadubeni yace yake yata kiyi
sani cewa bakin alkalami ya riga ya bushe
mutuwa zanyi kuma yanzu nan ba dadewa ba:
Koda jin wanna batu sai na cika da tsananin
mamaki na kasa tambayarsa dalilin da yasa ya
fadi haka: Mahaifi nawa ya kankameni a
kirjinsa ya fashe da matsananincin kuka har
izuwa lokaci mai tsawo
Daga can sai ya janyeni daga jikinsa muka
fuskacin juna yace yake yata ki saurara da kyau
kiji abinda zan gaya miki
Kinga wannan rashin lapiya da na dade a
kwance ina fama da ita ba wani bane yasa mini
ita ba face yar uwata juzairat
koda jin wanna batu sai idanuna suka zazzaro
jikina ya kama tsuma sbd tsananin mamaki da
tsoro, mahaifina yacigaba da cewa juzairat tayi
127
TASKARNOVELS.COM.NG
mini asiri ne ta hanyar amfani da wani azzaluin
aljani wai shi Raugatul Aguwanu
Duk mutumin da wannan aljani ya shafa har
abada ba zai warke ba daga cuta sai dai ajali
aljani Raugatul Aguwanu bai amince zai yi
wannan mummunan aiki ba sai bisa sharadin
cewa za a mallaka masa ke kyauta domin
kyawunki: ina tabbatar miki da cewa nan da
cikar sa a uku zan mutum kuma junaizar da
aljani Raugatul Aguwanu suna nan suna jiran
cikar wannan lokaci domin juzairat ta sami
damar hawa karagata ta mulki shi kuma aljani
Raugatul Aguwanu ya sami damar daukeki ya
tafi dake izuwa can wani sihirtaccen daji wanda
baya shiguwa inda zai tsareki: Na san zakiyi
mamaki bisa yadda akayi nasan duk wannan al
amari to na sani ne ta hanyar wanin
shahararren bokon boka wanda yazo ya dubani
128
TASKARNOVELS.COM.NG
Hatta lokacin da juzairat ta gana da aljani
Raugatul Aguwanu sai da yanuna mini a cikin
madubin tsafinsa kuma ya tabbatar mini da
cewar bakin alkalami ya bushe
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 18