Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
can kuma sai ya dago kai ya dubeshi ya ce Yakai abbana shin ka manta ne cewar ka taba gayamini cewar bisa binciken da kayi a hallarar tsafinka ajali ba zau taba riskar daya daga cikinmu ba a wani wuri face a gida?? Ashe kenan duk irin gararin da zamu shiga zamu dawo gida a raye? Lokacin da boka sadusa ya jin wannan batu sai ya sunkuo da kansa kas cikin alamun kunya yai shiru yace komai ba, har izuwa tsawon yan dakiku, sai daga can kuma ya dago kai ya dubi halyal lokacin da kwalla ta ciko a cikin kwayar idanunsa ya ce ya kai dana hakika duk abinda ka fadi gaskiya ne, to amma kuma ai bana son mu dawo gida a cikin mugun hali rashin lpyar da zata zama sanadin ajalinmuka hkri bazan iya yin wannan tafiya ba tare da kai. koda jin haka sai halyal ya durkushe kasa yana mai fashewa da kuka. al amarin daya kara jefa sadusa da Hunaisa cikin tsananin tausayinsa kenan. Nan dai sadusa ya kama kadadun halyal ya tasoshi tsaye ya sumbaci goshinsa sannan ya rungumeshi a 100 TASKARNOVELS.COM.NG kirjinsa duk su biyun suka fashe da kuka a lokacin guda. Zan ci gaba. MAZAN JIYA Littafi na Hudu 4 Part J Na Abdulaziz Sani m gini Typing Abubakar Saleh AlQuyraemey Koda ganin haka sai itama hunaisa ta rugo garesu ta kankamesu su ukun ta tayasu kukan sadusa ya janye jikinsa daga cikin nasu ya tafi yana waigensu hawaye na zuba daga idaanunsa. Al amarin daya kara dugunzuma hankali halyal da Hunaisa kenan suka ci gaba da matsanaicin 101 TASKARNOVELS.COM.NG kuka suna hangen sadusa har sau da ya bace musu da gani. Nan fa Halyal da Hunaisa suka cigaba da kuka suna kankame juna kamar bazasu daina ba har izuwa tsawon kusan dakika daru biyu da sittin. Kwatsam! Ba zato ba tsammani sai suka jiyo takun sawu a yayin da kawunansu ke kallon kasa, cikin sauri suka dago domin su ga wanda ke zuwa. Kawai sau suka ga ashe sadusa ne ya dawo kuma ya tunkarosu hannanyesa a bude hawaye yana shatata bisa kumatunsa. Cikin tsananin farin ciki Halyal ya ruga izuwa gareshi ya dada kan kirjinsa suka rungume juna suna masu kyalkyala dariya. * ** Tun da suka fara tafiya daga cikin gari halyal yafara ganin abubuwan al ajabi bisa yanayin 102 TASKARNOVELS.COM.NG tafiyar tasu domin da zarar sun yi tafiya kamar taku goma sai yaga sun shafe nisan zira'i dari nan da nan suka fice daga cikin gari suka nausa cikin daji. Ai kuwa suna shiga daji yaji sadusa ya kama hannunsa ya rike nan fa ya jashi da gudu suka falfala da gudu. Wannan karo sai halyal ya sako cike da tsananin mamaki fiye da farko domin yanzu tafiyar sa a guda ce suke shafewa a cikin dakika sittin kacal sai dai kawai yaga suna gifta dazuzzuka a cikin matsananincin gudu tamkar giftawar tauraruwa mai wutsiya. Amma da ya tuna cewar duk wannan lamari alamari ne na tsafi sai kawai yayi murmushi yace a zuciyarsa kowa da kiwon da ya karbeshi. Haka dai sadusa da halyal suka cigaba da gudu a cikin daji babu sassauci. Tun safe suka fara wannan gudu amma har sai da rana ta fadi sannan suka tsaya cak a farkon 103 TASKARNOVELS.COM.NG wani daji mai yanayi iri dabam da na sauran dukkan dazuzzukan Da suka wuce a baya. Adai dai wanna lokacin ne ji tsananin gajiya da kishirwa ta riskesu, ba shiri suka durkushe kasa bisa guiwoyinsu suka kama haki sannan kowannensu ya bude butar ruwansa ya kwankwada, koda suka dawo cikin hayyacinsu sosai sai suka kama kallon wannan daji da suka tsinci kansu a cikinsa. DAJI NE mai dauke da wandansu irin dogayen bishiyoyi masu tsananin tsawo da ba a iya ganin karshensu kuma ganyayen bishiyoyin masu fadi ne sosai don haka su karawa dajin duhu ya zama abin tsaro. Sannan kua akwai wadansu irin duwatsu a dajin masu wani irin sufofki na ban tsaro, wani dutsen sai kaga yana kama da mutum wani kamar aljan wasu kuma da dabbobi suke kama, kai komai dakewar zuciyar mutum idan ya tsinci kansa a cikin wannan daji sai ya razana musaman idan ya ji irin tsananin shirun dak cikin dajin, mutum baya jin sautin komai hatta na tsuntsaye kuwa aa da zarar mutum ya taka 104 TASKARNOVELS.COM.NG ganyeye bishiyoyin dajin wadanda suka fado kasa suka bushe rumus sai kaji karar ta cika dajin gaba daya hara da amsa kuwwa. Nan take halyal yakamu da tsananin tsaro gaba dayan jikinsa ya kama tsuma bai san sa adda ya dada kankame jikin sadusa ba. Koda ganin haka sai sadusa yai murmushi yace saki jikinka ya kai dana kayi sani cewa indai kana tare dani babu wani tsautsayi da zai sameka ka sani cewa tun shigo wata sabuwar nahiyar ne wacce ba tamu ba. Yanzu kamata yayi mu nemi wuri mai kariya inda zamu yadda zango tunda duhu ya soma sannan sai nayi mana bincike na gano ko akwai abinda muka zo nema a cikin wannan daji. Koda gama fadin hakan sai suka mike tsaye suka kara nausawa cikin suna ketawa ta cikin surkuki duhuwoyi ciyayi da sako sako. Ai kuwa sai da suka shafe lokaci mai dan tsawo suna neman wani kogon dutse da zasu iya shiga cikinsa su fake sakamakon hadarin da yake barazanar zubar da ruwa a ko yaushe, tunda har 105 TASKARNOVELS.COM.NG an fara walkoya gami da tsawa mai. ban tsoro, wacce duk sa adda aka yita sai dai kaga halyal na dada kankame hannun sadusa. Abinda ya dada daure masu kai shine duk tsawin wannan lokaci da suka shafe suna yawo a cikin dahi ko kadangare basu gani ba.kuma basu hadu da wani mugun abu ba, shi kansa sadusa sai daya tambayi kansa a ckin.zuciyarsa yace, TO WAI SHIN MENENE YA HANA DABBOBI DA KWARI RAYUWA A CIKIN WANNAN DAJI??? suna cikin wannan dube dube ne suka hango wani katon kogon dutse a gabansu, cikin hanzari suka ruga izuwa bakin kogon a lokacin da aka fara yayyafi kua aka ci gbada tsala wakiya da tsawa, da isarsu bakin kogon dutse sai suka tsaya sadusa ta yi nuni da hannunsa izuwa cikin kogon, take wani irin haske na tsafi ya haskake cikin kogon gaba dayansu kofa suka yi arba da aabin da ke cikin kogon sai suka cika da tsananin mamaki, ba komai suka gani ba face wata yar karama aljanar duniya. 106 TASKARNOVELS.COM.NG Kaya ne na alatu a cikin kogin tamkar turakar wani hamshikin basarake. An shimfida dardua ta alfarma ai dan karen laushe ta rufe kasankogon gaba daya mai launin shudi. A gefe daya nan a zncenta sai ta fashe da kuka al amarin dayai matukar baiwa su sadusa mamaki kena har suka ji sun kamu da tsananin tausayinta daga can sau sadusa ya dubeta ya daka mata tsawa yace yake wannan ma abokiyar keji: shin yanzu zaki iya iya gaya mana ko wane ne ya ajiyayeki a wannan kogon dutse wanda muka ji kin kirashin da shugaban azzalumai na duniya. Koda jin haka sai wannan kyakkyawa ta cikin keji tayi a jiyar zuciya tace sanin wanda ya ajiyeni acikin wanna kogo dai dai yake da sanin ranar ajalin mutum domin yakasance GUGUWAR ANNOBA kuma GOBARA DAGA KOGI wacce ba da magani: Sunan wanda ya ajiyeni anan shine ALJANI RAUGATUL AGUWANU. Koda jin wannan batu sai boka sadusa ya mike zubur! Cikin firgici da 107 TASKARNOVELS.COM.NG tsananin tsoro ya kama hannun halyal domin su fice daga cikin kogon: Karar takun sawun aljani raugatul aguwanu tasa suka koma cikin kogon dutse da sauri suka shige cikin karkashin wanna makeken gado na aljanin raugatul aguwanu: Takun sawun na Raugatul aguwanu tamkar giwaye neke tserun gudu a cikin dajin har maya haddasa girgizar kasa. Kai tsaye aljani raugatul aguwanu yashigo cikin kogon nasa tya zauna kan gefen wanna gado nasa. Kai tsaye aljani raugatul aguwanu yashigo cikin kogon nasa tya zauna kan gefen wanna gado nasa. Saboda nauyinsa sai da gadon ya lotsa kasa har su sadusa suka ji kamar wani katon dutse ne ke shirin dannesu ya kakkarya musu kasusuwan gadon baya. Koda kyakkyawar yarinyar nan tacikin keji ta ga haka sai ta dubi Raugatul Aguwanu ta bushe da dariya tace haba ya shugabana yau kuma wahalar farautar ce tasa ka manta ka fara zama akan teburinka kaci yayan itatuwa? Koda jin haka sai aljani Raugatul Aguwanu ya bushe da dariyar farin 108 TASKARNOVELS.COM.NG ciki: Kasancewar kyakkyawar yarinyar bata taba yi masa magana mai dadi ba a tsawon shekaru da ya ajiyeta a cikin wanan kogon sai yau. Cikin hanzari ya mike tsaye ya nufi inda kujerarsa ta zama take wadda ke karkashin wannan babban zagayayyen tebur. Kafin ya isa kan kujerar tuni sadusa da Halyal sun fito daga karkashin gadon sun ruga izuwa bayan tarin dukiyar zinare sun buya. A Dai Dai wannan lokaci ne Raugatul Aguwanu ya zauna akan kujerar. ai kuwa sai ya shaki kamshi bil adama a cikin kogon fiye da yadda ya saba shaka a kullum ya tabbatar da cewa yasami baki. Nan fa ya kama waige waige da dube dube cikinn kogon. Koda su sadusa suka ga haka sai suka binne kansu a cikin wannan duniya ta zinare tamkar basu taba wanzuwa ba a wajen. Hakan ta faru ne da taimakon karfin sihirin tsafi sadusa. Aljani Raugatul Aguwanu ya mike tsaye ya kama dube dube ya shiga nan ya fita can: ya bankada ko ina amma bai ga bil adama ba alhalin kuma yaji kamshinsu. Koda ya dago kai suka hada ido da wanna kyakkyawar yarinya ta cikin keji sai ta sunkui dakanta kas, abinka mara gaskiya ko a ruwa sai ya yi jibi sai jikinta 109 TASKARNOVELS.COM.NG ya kama tsuma. A fusace Raugatul Aguwanu ya durfafo kejin da take cikin ya dubeta ya daka mata tsawa yace ke tsohuwar munafuka tabbas kin san da shigowar baki wannnan kogo nawa amma sbda munafunci da cin mana irin naku na mata shine kika yi shiru baki gaya mini ba. To ki sani cewa idan har baki gaya ini inda suka buya ba a cikin wannan kogo yanzu nan zan fito dake daga cikin kejin nan na yayyagaki filla filla na watsar. Ai daa na ajiyeki ne anan kawai don ki debe mini kewa kasancewar babu wata hallita a cikin wannan daji sai ni kadai. Koda jin wannan batu sai kyakkyawar ta bushe d dariya lokaci guda kua ta fashe da kuka sannan ta kalleshi tace ai daa na dade ina rokonka akan ka kasheni na huta da takai ci da bakin cikin rayuwar da ka jefani cikin amma kaki, ka rabani da iyayena dangina da kasarmu ka baroni da cikin jinsin mutane yan uwana ka kawoni nan cikin wannan daji inda ko kwaro babu bare wani dan tsuntsu wanda zai rinka jin sautin kukansa ina jin dd cewar akwai mai rai a kusa dani 110 TASKARNOVELS.COM.NG Tun inayarinya karaa ka sato ni ka kawoni nan kuma ka tsafanceni ka sani a cikin wanna keji na zama kamar ya tsuntsuwa alhalin na kasance bil adama. Ka cuceni cutar da bani da halin daukar fansa face na ga ranar da Zakayi mutuwar wulakanci : Tabbas a duniya ba a taba samun azzalumai kamar ka ba. Ina mai rokonka da ka hanzarta kasheni domin na huta da wnn bakin zalunci naka. Sa adda kyakkyawar yarinyar ta cikin keji ta zo nan a zancenta sai aljani Raugatul Aguwanu ya kara fusata ainun yace aikuwa yanzu nan zan ida mugun nufina akanki. Kawai sai ya kai hannu ya suro kejin danufin yabude ya daukota daga cikin amma sai yaji an ce dakata ya kai Shugaban azzalumai na duniya. Cikin hanzari da mamaki Raugatul Aguwanu ya juyo da baya: take yayi arba da boka sadusa da dansa Halyal tsaye a bayansa. Raugatul aguwanu ya kurawa boka sadusa idanu cikin tsananin mamaki har izuwa tsawon yan dakiku yana nazarinsa sanna yace ya kai wannan ha tsabibin boka kai kuwa ya ya aka yi ka shigo cikin wannan daji har ka iso nan cikin makwanci na batare dani ji motsin shigowarku ba? Kune bil adama na biyu da 111 TASKARNOVELS.COM.NG suka taba shigowa cikin wannan daji har suka rayu a tsawon sama da nisan sa a guda sbda karfin shirina gami da azababben karfin dantse na : wannan daji da kuka shigo shine dajin da ake yiwa lakabi da DARUL HUSHUSHUL MAUT wato gidan daba ashiga kuma ba a fita. Tunda nazo na tare a wannan daji yazama nawa ni kadai domin na kori dukkan aljanu dabbobi da tsuntsaye gami da dukkan kwarin dake cikinsa. Zan ci gaba. MAZAN JIYA Littafi na Hudu 4 Part K Na Abdulaziz Sani m gini Typing Abubakar Saleh AlQuyraemey 112 TASKARNOVELS.COM.NG Fatake da matafiya kuwa hatta na jinsin aljanu haka suka hkra da giftawa ta saman wanna daji domin koda tsautsayi suka zo wucewar kamawa suke da wuta su kone saidai tokarsu tazubo kasa: kai kuwa wane irin karfin tsafi ne da kai hka wanda har yafi nawa ka ketare duk masifun da na zuva a wwannan daji? Lokacin da boka sadusa yaji wannan tambaya sai yayi murmushi cikin izza sannan ya durfafo inda wannan tebur yake ya zauna kuma ya dauku tuffa guda daya yakama ci tamkar a cikin turakarsa yake sannan ya yafuto aljani Raugatul Aguwanu da hannu yana mai kiransa: Ba tare da gardamar komai ba Raugatul Aguwanu ya ajiye wannan keji wanda yake hannunsa sannan ya taho wajen sadusa ya zauna akan tasa kujerar suka fuskaci juna : A wannan lokaci zuciyar sadusa ta kama dukan uku uku domin a cikin matukar tsorace yake kawai dai banza ce ta kori wofi 113 TASKARNOVELS.COM.NG A iya tunanin aljani Raugatul Aguwanu boka sadusa ya fishi karfin sihirin tsafi tunda har ya iya shigowa wannan daji na darul hushushul mautt lapiya: Abinda ya manta shine a yau ya sha afa cewar tunda sassafe ya cire dukkan tsaron da yasa wa dajin sakamakon wani dogon nazari da yayi a halwar tsafi don bincike akan yanayin da duniya kw ciki: Har yagama binciken nasa ya tafi dajin dake gaban nasayin farauta bai mai da sihirin tsaron ba a dajin na darul Hushushul maut. Tun da boka sadusa yazo duniya bai taba ganin aljanin mai girma kirar karfi kutuciyar samartaka da tsananin muni ba kamar Raugatul Aguwanu don haka a cikin tsananin firgice yake da shi sbda ya san cewa ko yaya yayi wani dan kuskure wanda Raugatul Aguwanu ya gano cewa ya fishi karfin sihitin take zai halaka Su shi da halyal: Bayan sun fuskanci juna sai sadusa yace ya kai wannan sarki jaruan aljanu na duniya ka yi sani cewa musaman nazo wannan daji na darul Hushushul maut domin na gana dakai 114 TASKARNOVELS.COM.NG Tabas na san wani gagarumin al amari wanna kai baka sani ba Koda jin wannan batu sai aljani Raugatul Aguwanu ya gyara zama ya tattara hankalinsa a waje daya kuma ya nutsu sosai yana mai sauraron boka sadusa. Sadusa yai gyaran murya sannan yace shin kana da lbrin gagarumin yakin da ake fafatawa yanzu hakan a can bakon kogin Bahar Sufiya? Koda jin wanna batu sai aljani Raugatul Aguwanu yasake gyara zama yace kwarai kuwa na san da batun wannan yaki wanda ake yi tsakan Sarki dujalu da sarki maharaz, In banda abinka waye yake shiga fadan manya? Ai dujalu da maharaz sun fi kowa karin sihirin tsafi a wanna duniya kaf: Shi ya sa kagani na rabe a waje daya na dawo nan cikin daji na hakura da rayuwa acikin mutane da yan uwana aljanu Koda jin haka sai boka Sadusa ya kyalkyle da dariya al amarin da yai matukar baiwa aljani Raugatul Aguwanu mamaki kenan 115 TASKARNOVELS.COM.NG Awannan lokaci Halyal da kyakkyawar yarinya ta cikin keji kuwa a ckin matukar tsoro suke domin gani suke cewar idan tusa ta karewa bodari hallaka zaiyi Su kansu sun fahimci cewar sadusa dai yan dabaru yake yi domin su kubuta: Cikin alamun dadin mamaki Raugatul Aguwanuyace yakai wannna hatsabibin bola ina dalilin wannan dariya taka? Sadusa ya murtuke fuska tamkar an aiko masa da sakon mutuwa sannan yace ai nan dajin da ka kadawo tamakar kayi gudun gara ne ka tarar da zago: to tsaya kaji idan aka gama wannan yaki duk wanda yasami nasara tsakanin sarki dujalu da sarki maharaz shine zai mallaki kayan yakin MAZAN JIYA wannan duk kuwa ya mallaki Takobin SAIFUL LUJARA MASHIN GALILUL HARAS da HULAR LAMSARA sai ya mallaki kowa da komai na cikin wannan duniya kaga kenan kai kanka sai kazama bawansa wannan daji naka na darul Hushushul maut sai ya zama wajen shan iskasa 116 TASKARNOVELS.COM.NG Kai kuwa nasani cewa a dunia babu abinda ka tsana sama da kayi bauta a karkashin wani ka fi son rayuwarka ta kare acikin cin gashin kanka ko ba haka bane? Koda boka sadusa yazo nan a zancesa sai hankalin aljani Raugatul Aguwanu ya dugunzuma ainun fiye da koyaushe a rayuwarsa sbda ko kada bai taba tunanin faruwar wannan al amari ba: nan take halyal da kyakkyawar ta cije keji suka ji sun sami nutsuwa da kwanciyar hankali bisa jin wanna bayani da sadusa ya yiwa aljani Raugatul Aguwanu musamman da suka gayadda jinkisa yai sanyi kuma hankalinsa ya tsahi. Tsawon yan dakiku Raugatul Aguwanu yana nazari tunani har maya mike tsaye yakama kai kawo yana ciza ya tsa. daga bisani sai ya koma kan kujerarsa ya zauna kusa da sadusa ya dubeshi ya ce yakai wannan takadarin boka kayi sani cewa hakika kazo mini da babban al amari wanda yafi gaban tunaniba da hangena don haka sai nayi bincike na tabbatar da gaskiyarsa 117 TASKARNOVELS.COM.NG To wai shin idan har abindaka fada min gaskiyane to yaya zan iya kubuta kena Ni dai kam da dai na zauna a karkashin wani mulkeni gwara na kashe kaina domin ban ga anfani wannan tsananin karfin dantsen nawa gai da karfin sihirina wanda na shafe sama da shekaru arba in ina yawon nemansa a cikin duniya Sadusa ya gyada kai yace tabbas kayi gaskiya: Amma ina mai tabbatar maka dacewa ni ina da mafita a gareka amma sai bayan ka gama bincikenka kaga gaskiyar wannan al amari sannan zan gaya maka mafitar kuma bisa wani sharadi Koda jin haka sai aljani Raugatul Aguwanu ya kyalkyale da dariya sanna yace hakika yai na gamu da sarkin wayo: Ti amma fa kasani ramin karya kurarre ne idan har duk abinda kazo mini dashi ba gaskiya bane asirinka zai tonu 118 TASKARNOVELS.COM.NG idan kuwa asirinka ya tonu da kai da wancan kyakkyawan dan naka sai nayi muku mugun kisan gilla irin wanda ba taba yiwa wani mahaluki ba a doron kasa : kafin Aljani Raugatul Aguwanu ya gaa rufe bakinsa tuni boka sadusa ya dakamasa tsawa yana mai cewa kai matsoracin aljani wanda yakasa fita filin daga inda manya mazaje ke fafatawaa: ina mai horonka da ka iya bakinka ka saisaita lafazinka a gareni in ba haka ba kuwa yanzu nan zan fusata na koneka kua na kone gaba dayan wannan daji dakake matukar kauna kamar yadda uwa keson danta Dajin wannan jawabi sai Raugatul Aguwanu ya dan tsorata don haka sao ya sunkui da kansa kas cikin alamun girmamawa yace kayi mini uzuri ya kai takadarin boka ka sani fa ni haka halina yake bana son raini. Yanzu dai ni a koshe nake zan sha giya domin na kwanta na yi barci sosai sai dare ya tsala sannan zan tashi nayi 119 TASKARNOVELS.COM.NG bincike a Hallarar tsafina bisa wannna sabon al amarin daka zo mini da shi Abinda nake bukata da ku shine ya yin dana fara barci bana bukatar naji matsin komai ko yaya yakee domin idan har na farka bana iya komawa barci Kai idan da hali ma ku fita daga waje kuje ku yawata a cikin dajin nan har izuwa lokacin da zan tashi daga barcina ina mai tabbatar muku da cewa akwai abbuwan al ajabi da yawa a cikin daji nan wadanda zasu debe muku kewa izuwa lokacin tashina daga barci: Koda jin wannan batu sai sadusa yayi murmushi sannan yace ka san ance da dan gari akan ci gari: Me zai hana fito da wannan kyakyawar yarinya daga cikin keji domin tayi mana jagora a cikin wannan daji tunda ta fimu saninsa? Sa adda aljani Raugatul 120 TASKARNOVELS.COM.NG Aguwanu yaji wannan bukata ta sadusa sai yai shiru ya juya al amarin a cikin zuciyarsa kuma ya kurawa sadusa idanun cikin alamun Rashin Yarda daga can sai yace Menene tabbacin cewa ba yaudarata za kuyi ba ku gudu da Gimbiya SHALBIRAT? Kai sani cewa da raina babu wani abu na biyu da nakeso sama da ita. Sadusa yai murmushi yace Ai inda don ita na zo wannan daji da baza kazo ka riskemu ba a cikin kogonka tunda ina da karfin sihirin da zan iya saceta: Raugatul Aguwanu ya gyada kai cikin alamun nuna gamsuwa amma a can karkashin zuciyarsa Dari dari yake yi : Kawai sai yayi kuru ya sa danyatsansa guda ya bude kejin da gimbiya Shalbirat ke ciki: Shabiyat ta taka dan yatsan Raugatul Aguwanu cikin tsananin farin ciki mara misaltuwa sbd tsawon shekaru goma sha bakwan da ta yi a wannan daji na Darul Hushushul maut a cikin kejin ta yisu bata taba fitowa ba waje 121 TASKARNOVELS.COM.NG : A sannan ne Raugatul Aguwanu ya sauke tafin hannunsa kasa ta dir: Sai gata yar motsitsiya a gaban sadusa tamkar dan karamin bera Duk wannan abu dake faruwa Halyal na tsaye a can gefe daya ya kurawa Shalbiyat idanu yana mai matukar al Ajabi bisa ganin tsananin kyawunta wanda yake ganin cewa ko Gimbiya Hursiya kanwar sarki dujalu Albarka Lokacin da Shalbirat ta duro kasa daga kan tafin hannun Raugatul Aguwanu sai ta kaa raawa da tsalle doin murna kuma ta fasge da kukan farin ciki: A sannan ne aljani Raugatul Aguwanu ya dubi sadusa yace Ga masoyiyata Gimbiya Shalbirat na fito da ita kua na damkata amana a hannunka: ka tafi da ita izuwa cikin daji ku yawata daga nan har izuwa wayewar gari: Koda gama fadin hakan sai aljanin Raugatul Aguwanu ya nufi inda aka ajiye wani katon tulu wanda sbd girmansa da nauyinsa kato arba in bazasu iya rabashi da kasa ba ama shi da yan yatsu biyu ya daga tulun: Ashe tulun 122 TASKARNOVELS.COM.NG cike yake da ruwan gida kawai sa i ya kafa bakin tulun a bakinsa ya kama sha kwal kwal karar tafiyar ruwan giyar a cikin cikinsa tamkar ruwan tekune ya balle yana shatata izuwa cikin teku Raugatul Aguwanu bai sauke tulun giyar kasaba sai da yaji babu sauran digo daya na ruwan giya sannan ya ajiyeshi a kas ya tafi izuwa kan wannan katon gado nasa na alfarma yana layi yakife kasa: ko dakika goma bayi ba ya kama wani irin gagarumin Munshari : koda ganin faruwar hakan sai gimbiya shalbirat ta yunkura a fusace ta zare wata wukar sihiri ta aljani Raugatul Aguwanu dake kugunsa daga sama da nufin ta caka masa ita a kirjinsa sai boka sadusa yai wuf ya rike hannunta sanan ya karbe wukar ya mai da ira cikin kufenta da ke jikin Raugatul Aguwanu Sadusa yayiwa Shalbirat da Halyal nuni da suyi shiru kuma kada suyi wani kyakkyawar motsi: Nan take yajasu suka fice daga cikin kogon gaba daya: Sai da suka yi nisa da inda kogon 123 TASKARNOVELS.COM.NG dutsen yake inda basa iya hangoshi sannan suka zauna domin su dan huta: za;ansu ke da wuya sai Shalbirat ta fashe da matsanincin kuka Al amarin da yai matukar dugunzuma hankalin su Halyat kenan suka shiga rarrashinta suna tamyarta dalilin kukan nata: Da kyar suka shawo kanta ta daina kukan sannan tace ba komai ne yasa kuka ga ina wannan kuka ba face tsananin bakin cikin kun hanani kashe aljani Raugatul Aguwanu domin ya salwantar da rayuwata kuma ya kunsa min bakin cikin da Har na mutu babu wata fansa da za ta kankareshi: Kuyi sani cewa ni ce ya guda daya a wajen mahaina sarki sharyalu na Birnin taukib: babu irin kalar gatan da ban gani ba a duniya kuma a nahiyar damuke babu wani sarki mai karfin mulki da tarin dukiya irin ta mahaifina: Mahaifin nawa bashi da kowa a duniya face wata kanwaesa mai suna JUZAIRAT ta ri ga mahaifina yin aure da shekara shida amma bata taba samun haihuwa ba har mahaifina yazo ya yi auren ka haifeni: Al amarin da yajefa 124 TASKARNOVELS.COM.NG juzairat cikin tsananin bakin ciki kenan sbda bata da wani buri wanda ya fi ta haifi dan da zai gaje sarauta. babu irin asirin da juzairat ba tayiwa mahaifiyata ba akan kada tasamu ciki gami da kulle kulle da makirce makirce na zahiri amma duk butaka bata biya ba Kai sai da takai ta kawo juzairat tana nuna kiyayyerta ga samun juna biyun mahaifiyata a filin har maifina ya fahimta amma bai taba nuna mata damuwarsa ba sbd tsananin son da yake mata: Lokacin da na isa shekara ba kwai a duniya lavarin tsananin kyawuna ya bazi ko ina a nahiyar ya zamana cewa tun a sannan ya yan sarakai da yan mayan attajirai sun fara zuwa neman aurena sai hankalin juzairat ya dugunzuma ainun kuma ta tsaneni fiye da komai: A wannan lokaci tsufa ya fara riskar mahaifina kuma gashi kullum yana cikin fama da lalura ta rashin lafiya iri iri: gaba daya likitocin mahaifina sun kasa gane abinda ke damunsa don haka suka daina bashi magani aka rinka kiran bokaye kowa yana yin iya bakin kokarinsa amma babu sauki 125 TASKARNOVELS.COM.NG A wannan lokacin na shaku da mahaifina ainun fiye da yadda na shaku da mahaiyata domin dare. Da rana bana yarda na nisanra dashi sau tari sai bayan nayi barci akan kirjinsa sannan mahaifiyata take zuwa ta daukeni ta tafi dani izuwa kan gadonta ta shimfideni Wani dare wanda shine daren mummunan bakin ciki a Tarihin rayuwata wato daren da ba zan taba mancewa dashi ba: Ina kwance akan gado MAHaifina muna ta wasa dariya sai ciwo ya taso asa har ya mike zaune da kyar ya zama tari har da aman jini Al amarin da ya dugunzuma hankalina kenan na fara kuka kuma na yunkura da nufin naje na kirawo mahaifiyata amma sai mahaifina ya yi wuf ya riko hannuna a lokacin da shima ya kama zubar da hawaye 126 TASKARNOVELS.COM.NG Cikin karfin hali yadubeni yace yake yata kiyi sani cewa bakin alkalami ya riga ya bushe mutuwa zanyi kuma yanzu nan ba dadewa ba: Koda jin wanna batu sai na cika da tsananin mamaki na kasa tambayarsa dalilin da yasa ya fadi haka: Mahaifi nawa ya kankameni a kirjinsa ya fashe da matsananincin kuka har izuwa lokaci mai tsawo Daga can sai ya janyeni daga jikinsa muka fuskacin juna yace yake yata ki saurara da kyau kiji abinda zan gaya miki Kinga wannan rashin lapiya da na dade a kwance ina fama da ita ba wani bane yasa mini ita ba face yar uwata juzairat koda jin wanna batu sai idanuna suka zazzaro jikina ya kama tsuma sbd tsananin mamaki da tsoro, mahaifina yacigaba da cewa juzairat tayi 127 TASKARNOVELS.COM.NG mini asiri ne ta hanyar amfani da wani azzaluin aljani wai shi Raugatul Aguwanu Duk mutumin da wannan aljani ya shafa har abada ba zai warke ba daga cuta sai dai ajali aljani Raugatul Aguwanu bai amince zai yi wannan mummunan aiki ba sai bisa sharadin cewa za a mallaka masa ke kyauta domin kyawunki: ina tabbatar miki da cewa nan da cikar sa a uku zan mutum kuma junaizar da aljani Raugatul Aguwanu suna nan suna jiran cikar wannan lokaci domin juzairat ta sami damar hawa karagata ta mulki shi kuma aljani Raugatul Aguwanu ya sami damar daukeki ya tafi dake izuwa can wani sihirtaccen daji wanda baya shiguwa inda zai tsareki: Na san zakiyi mamaki bisa yadda akayi nasan duk wannan al amari to na sani ne ta hanyar wanin shahararren bokon boka wanda yazo ya dubani 128 TASKARNOVELS.COM.NG Hatta lokacin da juzairat ta gana da aljani Raugatul Aguwanu sai da yanuna mini a cikin madubin tsafinsa kuma ya tabbatar mini da cewar bakin alkalami ya bushe

Chapter 5 of 18