dariya sannan ta
ce, na yarda da wannan labari naki amma na
tausaya miki kuma na tausayawa iyayenki da
suka yi rayuwar dole a daji sabo da tsoron
sharrin mahaifiyar Shaddadu. Lallai idan har
kina son iyayenki su sami zaman lafiya da
kwanciyar hankali dole ne ki yi iya kokarinki ki
tabbatar da cewa kin samu nasarar kashe
Jarumi Shaddadu. Wai shin ma ke ba kya so ne
ki ga mahaifnkı Sarki Laffaru ya koma birninsa
na Kufa ya karbi karagarsa ta mulki? Hakika a
duniya babu mutumin da ya fi zama abin
tausayi sama da wanda ya rasa dukiya ko mulki
domin ya dandana dadi mara misaltuwa kuma
dadin ya zo ya salwanta. A cikin wanne irin
yanayi kike tsammanın zai tsıncı kansa?
Zıya'ul Hak ta dubi Sarauniya Zubaina ta ce, ina
mai tabbatar miki da cewa ta kowanne hali sai
na ga na tabbatar da na sami nasara akan
Shaddadu da mahaifiyarsa. Yanzu ke ta yaya
kike ganin cewa za mu iya kamo Shaddadu mu
312
TASKARNOVELS.COM.NG
hallaka shi? Koda jin wannan tambaya sai
Sarauniya Zubaina ta yi murmushi sannan ta ce
binciken da na yi a cikin hallarar tsafina na gano
cewa, ba wani ba ne ya taimaki Jarumi
Shaddadu cikin wannan gari nawa ya boye shi a
sa'adda nake matukar nemansa face wata
baiwata kum karuwa mai zaman kanta wacce
ake kira Yaldisa. Akwai wani gidan sai da abinci
nawa wanda Yaldisa ce ke kula da shi, a nan ne
ta fara haduwa da Jarumi Shaddadu. Tun a
wannan gida ne na shirya masa tuggun da za a
kashe shi a dauko mini Mashinsa na Galilul
Haras a kawo mini amma sai ya tsallake
wannan tarko nawa bisa karfin dantsensa da
kuma taimakon Yaldisa inda ta dauke shi ta kai
shi can gidanta ta boye shi a cikin wani ďakı da
ke karkashin kasa. Ni da kaina tare da
Dakaruna mun shiga har cikin gidan Yaldisa
mun duba ko ina ba mu ga Jarumi Shaddadu.
Duk ban gano wannan al'amari ba sai a yau da
na tsananta bincike a cikin madubin tsafina.
Tabbas ko shakka ba na yi a yanzu haka ma duk
inda Jarumi Shaddadu yake yana tare da
Yaldisa. Abin da ya daure mini kai shi ne, na yi
iya bincikena na kasa gano a inda suke a yanzu.
313
TASKARNOVELS.COM.NG
To amma ai idan sun san wata ai ba su san wata
ba. Tun da Jarumi Shaddadu ya yi mana wuyar
gani da kamawa, ai ita Yaldisa ba za ta yi mana
wuya ba. kamata ya yi mu kamo Yaldisa mu zo
mu tsare ta anan fada kuma mu sa a yi cigiyar
cewa idan Jarumi Shaddadu bai kawo kansa
fada a cikin sa'a goma sha hudu ba za a kashe
ta ta hanyar ratayewa. Na tabbalar da cewa ba
zai iya zuba idanu yana gani a kashe ta ba
saboda halaccin da ta yi masa a zuwansa
wannan gari nawa. Lallai zai iya kokarinsa ya
ga ya ceci rayuwarta duk da cewa ba sonta yake
ba, asali ma shi bai san mene ne so ba kuma
bai taba son wata 'ya mace ba ko ya yi
sha'awarta Kin ga, da zarar Jarumi Shaddadu
ya zo fada in yana tare da Mashin Galilul Haras
za mu sa shi ya miko shi gare mu ko mu kashe
Yaldisa. Idan kuma ba ya tare da Mashin sai
mu hada karfinmu ni da ke mu yake shi, tabbas
in muka hada jarumtakarmu ni da ke sai mun
rinjayi tasa mun hallaka shi. Lokacin da Ziya'ul
Hak ta ji wannan jawabi na Sarauniya Yaldisa
sai ta yi ajiyar zuciya sannan ta ce, to ke mene
ne ribarki idan muka kashe Shaddadu ba ki
sami Mashin Galilul Haras ba? Koda jin
314
TASKARNOVELS.COM.NG
wannan tambaya sai Sarauniya Zubaina ta
kama in-ina ta rasa me za ta ce, amma sai ta
wayance ta ce, ai kashe Shaddadu abu ne mai
muhimmanci a gare ni ko don saboda kwararan
dalilai guda biyu. Dalili na farko shi ne,
Shaddadu ya shigo birnina ya karya mini doka,
kuma ya nakasta mini dakaruna da yawa ya
karva mini kofar gari. Dalili na biyu kuma shi
ne, koda ba ya tare da Mashin Galilul Haras ai
Mashin yana nan a cikin Birnin nan nawa tunda
a bincikena na gani cewa Mashin ya fada cikin
wannan korama wacce kuka fada cikinta ke da
shi tun farkon fara fadanku sa'adda Mashin
Galilul Haras ya hadu da Takobinki. Ina mai
tabbatar miki da cewa ke ma yanzu gabadayan
sihirin tsafinki ya daina tasiri kamar yadda na
Jarumi Shaddadu ya daina, amma fa ki sani
cewa da zarar Mashin Galilul Haras ya dawo
hannunsa shi ke nan tsafinsa ya dawo. Don
haka, dole ne mu yi iya kokarinmu mu tabbatar
da cewa Mashin bai dawo hannunsa ba, ya
zamana cewa hannunmu ya riga nasa kaiwa kan
Mashin. Lokacin da Sarauniya Zubaina ta zo
nana zancenta sai hankalin Ziya'ul Hak ya
dugunzuma ainun ta fara tunanin cewa hada
315
TASKARNOVELS.COM.NG
kan da take kokarin yi da Sarauniya Zubaina ba
shi da wani amfani domin idan Zubaina ta
mallaki Mashin Galilul Haras tamkar ta mallaki
komai da kowa ne na duniya, don haka
mahaifinta ma da kasarsu ta Birnin Kufa za ta
dawo karkashin Sarauniya Zubaina. Nan take
wani tunani ya fadowa Ziya'ul Hak ta ce a cikin
ranta, Wai shin mene ne ya hana mahaifiyar
Shaddadu kokarin mulkar duniya a lokacin da ta
mallaki Mashin Galilul Haras?Maimakon haka,
sai ta sallama Mashin ga Shaddadu saboda
kawai ya zo ya neme ni ya halaka ni kuma ya
hallaka mahaifina? Tana cikin wannan tunani
ne Sarauniya Zubaina ta katse mata tunanin ta
dafa kafadarta ta ce, yanzu zan sa a kai ki
masauki domin ki kwanta ki huta sai gobe za mu
fita ni da ke mu aiwatar da wannan gagarumin
aiki don cika burinmu. Koda gama fadin hakan
sai Zubaina ta kirawo wata kuyangarta ta hada
ta da Ziya'ul Hak aka tafi da ita izuwa
masaukinta. Kas! Babban kuskuren da Ziya'ul
Hak ta yi shi ne, da ta manta da batun abokin
tafiyarta Aljanı Maruful Dauwaz. Kamata ya yi ta
koma can daji in da suka rabu ta sanar da shi
abın da ya faru tsakaninta da Sarauniya Zubaina
316
TASKARNOVELS.COM.NG
amma sai ta manta da hakan gaba daya. ****
Al'amarin Yaldisa kuwa ashe lokacin da Ziya'ul
Hak ta shigo fadar Sarauniya Zubaina ita ma
tana nan a cikin fadar amma ta batar da
kamanninta babu wanda ya isa ya shaida ta.
Bayan ta gama gani da sauraren duk abın da ya
faru tsakanin Ziya'ul Hak da Sarauniya Zubaina
sai ta sulale ta bar fadar, ta kunna kai izuwa
cikin daji. Idan ta yi 'yar doguwar tafiya sai ta
sami bayan dutse ko bayan bishiya ta labe har
izuwa tsawon lokaci domin ta tabbatar da cewa
babu wani dan leken asiri da ya biyo sawunta.
A haka dai ta samu ta isa har cikin wannan Kogo
wanda ta bar Jarumi Shaddadu a kwance yana
jinyar raunin da ke kansa. Da shigarta cikin
Kogon sai ta ga wayam! Babu Shaddadu babu
alamarsa a cikin Kogon. Al'amarin da yai
matukar dugunzuma hankalinta ke nan ta firgita
kuma ta dimauce. A razane ta juya ta fito daga
cikin Kogon dutsen ta wangame baki da nufin ta
kwalla masa kira, kawai sai ta gan shi tsulum!
Ya duro a gabanta daga kan wata bishiya.
Cikin tsananin farin ciki ta rungume shi, shi
kuwa sai ya kankameta a jikinsa yana mamakin
kansa domin wannan ne karo na farko da ya ji ya
317
TASKARNOVELS.COM.NG
aminta ya hada jikinsa da na 'ya mace.
Alamarin da yai matukar dugunzuma
hankalinsa ke nan ya janye jikinsa daga cikin
nata ya sunkui da kansa kas yana tunani. Ita
kanta Yaldisa ta yi tsananin mamakın yadda ta
ga har ya tsaya ta rungume shi alhalin ya tsani
ya ga mace ta kusance shi Cikin sanyın jıkı
Yaldisa ta dubi Shaddadu ta ce, Mene ne dalilın
da ya sa ka fito daga cikin Kogon dutsen nan da
na boye ka alhalin ka san cewa rayuwarka a
cikin mummunan hadari take tunda makiya
suna farautarka kamar yadda mai yunwa yake
farautar abinci? Koda jin wannan tambaya sai
Jarumi Shaddadu ya yi ajiyar zuciya cikin
alamun karayar zuciya sannan ya ce, ai dole ne
na fito daga cikin wannan Kogo saboda
hankalina ya yi mummunan tashi bisa rashin
ganin Mashina. Ki sani cewa babu inda ban
duba ba a cikin koramar nan amma ban ga
Mashin ba. A lokacin da nake neman Mashin
ne ma na ga wannan mugun Aljani abokin
tafiyar Ziya'ul Hak na buya. Shi ma babu irin
neman da bai yi ba a cikin wannan korama don
ya dauko Mashina. Tabbas inda ya gan ni da tuni
ya hallaka ni tunda ni yanzu ba ni da sauran
318
TASKARNOVELS.COM.NG
karfin sihirin da zan iya yakarsa. Ki yi sani cewa
ni yanzu ina cikin tsaka mai wuya tunda ga shi
makiyana suna farautar rayuwata ni kuma ina
farautar Mashina. Kin ga ke nan, hankalina ya
rabu gida biyu, dole ne na yi iya kokarina na zabi
abin da ya kamata na fara durfafa tsakanin
makiyana ko kuma neman Mashina. Sa'adda
Yaldisa taji wannan batu sai ita ma hankalinta
ya dugunzuma ainun ta rasa abin da ke ma ta
dadi. Nan take ta dubi Shaddadu cikin yanayin
matukar damuwa ta ce, ya kai ma'abocin kyawu
da kwarjini, ka yi sani cewa muddin ina
numfashi a doron kasa babu abin da zan bari ya
taba lafiyarka. A halin yanzu Sarauniyarmu da
abokiyar gabarka Ziya'ul Hak sun hada karfi da
karfe domin su yake ka su hallaka ka, kuma ga
dukkan alamu gobe da safe za su fito
farautarka. Ni kaina yanzu rayuwata a cikin
hadari take domin na san cewa tuni Sarauniya
ta yi bincike ta gano cewa ni ce na ke boye ka
Koda jin wannan batu sai mamaki ya kama
Jarumi Shaddadu ya yi shiru yana tunani. Daga
can sai ya dago kai ya dubi Yaldisa ya ce, wai
shin mene ne dalilin da ya sa kika siyar da
rayuwarki domin ceton tawa? Koda jin wannan
319
TASKARNOVELS.COM.NG
tambaya sai Yaldisa ta sunkui da kanta kas ta yi
shiru ta kasa ba shi amsa, daga can kuma sai ta
dago kai ta dube shi a lokacin da idanunta suka
ciko da kwallah ta ce, ya kai Jarumi abin
kwatance ka yi sani cewa ban taba jin na yi
nadamar karuwancin da nake yi ba sai bayan
haduwa ta da kai. Na yi hulda da mazaje da
yawa amma ban taba haduwa da namijin da na
ji ba na son rabuwa da shi ba face kai duk da
cewar wani abu bai taba shiga tsakanina da kai
ba kuma na girme ka da shekaru a kalla kusan
goma.Tun da na hadu da kai na ji na tsani
wannan muguwar sana'a tawa ta karuwanci
kuma na gane sewa bautar da nake yi wa
Sarauniya Zubaina ba ta da wani amfani tunda
ta kasance azzaluma kuma duk dukiyar da na
ke tara mata ba ta taba ba ni ladan dirhami daya
ba Ni nake rike da kaina ta hanuyar siyar da
jikina a wajen maza. Hatta wannan gida nawa
da na kai ka ka kwana haya nake yi a cikinsa.
lyayena sun mutu tun ban fi shekara bakwai ba
a duniya kuma sun kasance bayın Mahaifin
Sarauniya Zubaina. Tsananin wahalar aikin
bauta ne ya zamo sanadın ajalinsu. Bayan sun
mutu ne Sarauniya Zubaina ta ci gaba da rike ni
320
TASKARNOVELS.COM.NG
a matsayin baiwarta, amma saboda sanın ina
da kyau tun a sannan ta ajiye ni a wannan gidan
abinci nata aka koya mini yadda ake dafa abinci
da siyar da shi. Ba zan taba mantawa ba
sa'adda na cika shekara goma sha biyu, lokacın
da dukkan surar jikina ta 'ya mace ta bayyana
wasu Dakarun Sarauniya Zubaina su biyu suka
yi mini fyade a wannan gidan abıncı. Ko kadan
Sarauniya ba ta hukunta wadannan Dakaru ba
da suka yi mini fyaden duk da cewar sai da na
kwana goma sha biyar a kwance ina jinyar
jikina. Bakin cikin nuna halin ko in kula da
Sarauniya ta yi ne bisa abin da ya same ni ya
zamo sanadın fara karuwancina. Har yau har
gobe idan na tuna da wannan alamari sai na ji
babu abin da na tsana a rayuwala sama da
Sarauniya Zubaina domin ita ce ta salwantar da
rayuwata. Lokacin da Yaldisa ta zo nan a
zancenta sai hawaye ya zubo mata sannan ta ci
gaba da magana tana mai cewa, ya kai
ma'abocin kyawu da kwarjini ka yi sani cewa ni
ba na neman soyayyarka a gare ni saboda in na
ce ka so ni ban yi maka adalci ba tunda ni ba
tsararka ba ce a soyayya, kuma ni mace ce
mara asali da mutunci ban dace da dan Sarauta
321
TASKARNOVELS.COM.NG
ba kamarka a yadda ka ba ni tarihin rayuwarka
amma ina da buri guda daya a rayuwata.
Wannan buri nawa kuwa shi ne, na mutu akan
tafarkın sonka kuma na ceci rayuwarka har
izuwa lokacin da za ka sami nasara akan
makiyanka. kuma ka ga Mashinka. Lokacin da
Yaldisa ta zo nan a jawabinta sai Jarumi
Shaddadu ya ji ya kamu da tsananın tausayinta
har hawaye ya zubo masa Tsawon 'yan dakiku
suna kallon junansu an rasa wanda zai ce Kala.
Ita dai Yaldisa sai farın cıkı da mamaki suka
kama ta a lokacin da ta ga hawaye na zuba daga
cikin idanun Shaddadu. Abin da ta fara
tambayar kanta shi ne, wai shin wannan
hawayen na Shaddadu da ya zubo na tausayinta
ne ko kuwa na kamuwa da sonta ne? Nan ta
kasa bai wa kanta amsa, amma sai ta Kudurce a
ranta cewa har abada ba za ta taba mancewa
da wannan hawaye ba na farin cıkı. ko iya shi ta
samu a wajen Shaddadu ta san za ta tabu da shi
a cikin farin cikın ya tausaya mata a rayuwa ko
kuma ya so ta. Bayan Jarumi Shaddadu ya yi
dan dogon tunani da nazari a cıkın zuciyarsa sai
ya dubi Yaldisa ya ce, ya ke wannan
ma'abocıyar kyau da karamci ki yi sani cewa,
322
TASKARNOVELS.COM.NG
kin yı mını taimako a rayuwa irin wanda ni ma
har abada ba zan taba mantawa da shi ba kuma
kin nuna mini Kauna kwatankwacin irin wadda
babu wanda ya taba nuna mini face mahaifiya
ta. Ina fatan na saka miki da abın da ba za ki
taba mantawa da shi ba. Tabbas na tausaya
mikı matuka bisa yadda rayuwarki ta kasance
kuma na gamsu cewar kaddara ce ta salwantar
da rayuwarki. Hakika ba ki da wani abokin
gaba a doron Kasa wanda ya fi Sarauniya
Zubaina. Ina so ki sani cewa, matsoraci ba zai
taba zama gwani ba. Na fuskanci cewa ke ma
kina da jarumtaka gami da taurin zuciya daidai
gwargwadon irin ta ki, saboda haka, ina so ki zo
mu hada karfi da karfe mu tunkari gıdan
Sarauniya Zubaina yanzu mu yake ta ita da
abokiyar gaba ta, a yi ta ta kare, ko mu ko su. Ni
na san cewa zan ıya yakarsu da tsagwaron
jarumtaka ta domin na samı cıkakken horon
Yaki a Wajen maharfiyata. Tabbas ba ni da
burin da ya fi na daukı fansa a kan Ziya'ul Hak
bisa abin da mahaifinta ya yi wa mahaifiyata, ya
kashe dukkan zuri'arta kuma ya yi ma ta fyade
aka samı cıkına. Wani lokacın idan na tuna
cewa ina farautar rayuwar mahaifina da
323
TASKARNOVELS.COM.NG
kanwata ne sai na ji na kamu da tsananın bakin
ciki. Amma kuma idan na tuna da irin
wulakancin da aka yi wa mahaifiyata gami da
bakin cikin da aka cusa mata sai na ji na tsani
Mahaifin nawa da yar uwata Ziya'ul Hak. Koda
Jarumi Shaddadu ya zo nan a zancensa sat ya
fashe da kuka. Alamarın da ya karya zuciyar
Yaldisa ke nan ta kamu da tananın tausayinsa
ba ta san sa'adda ta rungume shi ba ita ma ta
fashe da kukan. Jim kadan sai ta janye jikinta
daga cikin nasa suka fuskanci juna ta ce, yanzu
idan muka yi kundunbala muka je muka tari su
Sarauniya Zubaina da yaki to mene ne makomar
Mashinka wanda ya fada cikin wannan korama?
Shin ba ka zaton cewa zai iya fadawa hannun
abokan gabarmu? Sa'adda Jarumi Shaddadu
ya ji waďannan tambayoyi guda biyu sai ya yi
ajiyar zuciya sannan ya ce, tabbas irin neman
da na yiwa wannan Mashi nawa a cikin wannan
korama inda yana cikinta da tuni na gan shi.
Haka kuma idan Mashin ya fada hannun abokan
gabata da tuni sun gano inda nake sun zo sun
hallaka ni. A cikin biyu dole ne ya zamo daya,
wato ko dai ruwa ya tafi da Mashin ya nutse a
cikin Teku, ko kuma wadansu aljanun masu
324
TASKARNOVELS.COM.NG
tsananin rabo sun tsince shi. Ni a ganina abin
kunya ne na koma gida wajen mahaifiyata na
sanar da ita cewar wannan Mashi ya salwanta a
hannuna bayan tun ina yaro karami take horar
da ni Yaki da jarumta domin na kare kaina da
wannan Mashi kuma na hallaka abokiyar
gabata. Masu iya magana sun ce, Sai an
gwada akan san na kwarai. Yanzu ina neman
alfarma ta karshe a wajenki da ki raka ni izuwa
gidan Sarautar Sarauniyarku a yanzu domin na
yake ta tun gabannin gari ya waye su fito yakata,
saboda an ce, Ka kashe makiyinka kafin shi ya
kasheka. Ba wai ina son ki raka ni ba ne domin
ni kadai ba zan iya ba, a'a sai don saboda ke kin
san sirrin gidan Sarautar kuma an ce, da dan
gari akan ci gari. Koda jin wannan batu sai
farin ciki ya lullube Yaldisa ta ce, ai dama na
gaya maka cewa raina da jikina duk na sallama
su a ceton taka rayuwar. Hakika ni ma yanzu na
gane cewa ba mu da wani zabi wanda ya fi mu
tunkari masifar tun gabannin ta tunkaromu.
Abu daya kawai da ma nake shakka, kuma ba
wani abu bane face karfin sihirin tsafin
Sarauniya Zubaina, to amma a yanzu haka ma
wata dabara ta fado mini zan san abin da zan yi
325
TASKARNOVELS.COM.NG
akan hakan. Ai Sarauniya Zubaina ta yi sake
Dan Zaki ya girma, domin ta raini ajalinta da
hannunta. Tun da na fara girma na yi hankali
kuma na gano cewa Sarauniya Zubaina
abokiyar gabata ce ba masoyiya ta ba na shiga
bincike akan sanin sirrinta. Ban san dukkan
sirrinta ba, amma na san wadansu da yawa.
Baya ga wannan, ina mai tabbatar maka da
cewa zan yi matukar ba ka mamaki a wannan
Yaki da za mu je mu yi a gidan Sarautar tamu.
Yanzu dai sai mu gaggauta shiryawa domin mu
san abin yi. Nan take suka fara shirya kayan
Yaki. Yaldisa ta sake komawa cikin gari a cikin
bad-da-kama ta shiga kasuwa ta siyo Kwari da
Baka gami da wadansu irin sinadarai na kayan
Yaki wadanda ita ta san abin da za ta yi da su,
sannan ta siyo wa Jarumi Shaddadu riga da
wando na karfe gami da garkuwa ta karfe, ita
ma ta siyowa kanta kayan karfen sannan ta
sake komawa can dajin cikin wannan Kogon
dutse. Shi kansa Shaddadu da ya ga irin kayan
Yakin da Yaldisa ta siyo musu sai da ya yi
matukar mamaki domin da yawa daga cikin irin
kayan Yakin ko a gidan Sarautar Birnin Kufa bai
taba ganin irin su ba tun daga yarintarsa har
326
TASKARNOVELS.COM.NG
izuwa girmansa. Sai da Yaldisa ta shafe sama
da sa'a guda tana koyawa Shaddadu yadda za
su yi amfani da wadannan sinadaran na kayan
Yaki. Bayan nan ne suka sanya wadannan
kayan Yakin na karfe a jikinsu, Shaddadu ya
rataya Takobinsa a baya kuma ya zuba wukake
a jikinsa gami da Adduna guda biyu kuma ya
goya jakar sinadarin kayan Yakin a bayansa.
Ita kuwa Yaldisa wannan Baka ta rataya a
bayanta gami da jakar Kwari wacce ke dauke da
kibiyoyi masu yawan gaske. Ita dai wannan
Baka ta Yaldisa Baka ce ta musamman wacce
ta kasance katuwar gaske kuma zaren jan ta
mai matukar tauri ne da kauri, sai kato ya cika
kato sannan zai iya tabe ta. Hakika duk wanda
ya ga Jarumi Shaddadu da Yaldisa a wannan
shiga dole ne ya razana domin shigar ta kara
musu kwarjini ainun, musamman ma shi Jarumi
Shaddadun wanda kirarsa ta kasance ta
sadaukai, kuma kirar ta sake bayyana a fili
karara. Bayan sun gama kintsawa sai suka
yanke shawarar su sauya wuri a cikin dajin su je
su nemi wani wuri mai duhuwa su biya sai dare
ya tsala Sannan su kai MAMAYAR BAZATO izuwa
gidan Sarautar. Wannan shi ne abin da ya faru
327
TASKARNOVELS.COM.NG
tsakanin Jarumi Shaddadu da karuwa Yaldisa
bayan ta ceto rayuwarsa a daji sakamakon
masifaffen Yakin da ya faru tsakaninsa da
Jaruma Ziya'ul Hak. **** Al'amarin Aljani
Maruful Dauwaz kuwa, lokacin da ya rabu da
Jaruma Ziya'ul Hak. ya ga cewa ta tafi ta ci gaba
da wanann Yaki ita kadai ba tare da taimakonsa
ba sai hankalınsa ya dugunzuma ya shiga sakesaken zuci da tunani Koda ya tuna cewa da shi
da Ziya'ul Hak yanzu duk ba su da sauran karfin
sihirin tsafi a jikinsu tunda shi ma an doke shi
da Mashin Galilul Haras har ma an balla masa
kashin kafadarsa kuma ba shi da tababcin cewa
Jarumi Shaddadu na tare da Mashinsa sai
hankalınsa ya dugunzuma kuma zuciyarsa ta
karaya da sa ran samun nasara akan Shaddadu.
Nan take ya yanke shawarar ya koma can. dajin
da suka baro Sarki Laffaru da matarsa ya sanar
da su halin da ake ciki domin idan suna da wata
dabarar da za a yi a cim ma buri su fada masa.
Ai kuwa nan take ya bude fuka-fukansa ya tashi
sama ya luluka a cikin gajimare yana mai tsala
azababben gudu na gaban kwatance domin ya
isa can dajin akan lokaci. Kash! Rashin sani ya
li dare duhu. Inda Aljanı Maruful Dauwaz ya san
328
TASKARNOVELS.COM.NG
gaibu da bai taba yin wannan ganganci ba na
komawa dajin da su Sarkı Laffaru suke domin ya
sanar da su halın da 'yarsu Ziya'ul Hak ke ciki
ba. ** A can Birnin Kufa kuwa, tun daga ranar
da Jarumi Shaddadu ya bar gida sai Sharlisa ta
rinka yin mugayen mafarkai a kansa tana yawan
ganinsa a cikin garari da tashin hankali amma a
duk sa'adda ta tuna cewa ai yana tare da
Mashin Galilul Haras sai hankalinta ya kwanta
don ta san cewa babu wani tsautsayi da zai
taba lafiyarsa ko rayuwarsa. Lokacı da ta ci
gaba da yin irin waďannan mugayen mafarkai ba
kakkautawa sai hankalinta ya dugunzuma ainun
ta rasa sukuni saboda haka sai ta dauko
madubin tsafinta ta shiga bincike. Ai kuwa nan
take ta ga duk abin da ya faru ga Shaddadu tun
daga farkon tafiyarsa kawo izuwa saukarsa a
Birnin Sarauniya Zubaina da irin bakin artabun
da ya yi da Ziya'ul Hak da kuma halin da ake ciki
na yanzu cewar, ya yi shirin Yaki shi da YALDISA
su biyu kacal! Za su je su Yaki Sarauniya
Zubaina da Ziya'ul Ilak a cikin dare. Koda gama
ganin wannan alamari sai hankalin Sharlisa ya
dugunzuma ainun, bakin ciki ya turnuke ta, nan
fa ta yanke hukuncin ta tashi ta yi shiri ta tafi
329
TASKARNOVELS.COM.NG
izuwa Birnin Sarauniya Zubaina domin ta kai wa
danta dauki. Amma babban tashin hankalin
shi ne, karfin sihirin tsafinta ba zai iya kai ta
garin ba a cikin yıni daya ba dole sai ta shafe
kwana uku tana tafiya, ke nan kafin ta je komai
zai iya faruwa, ma'ana za a iya kashe mata da a
ruguza ma ta dukkan shirinta da burinta. Nan
take ta aiyana a ranta cewar kamata ya yi ta fara
biyawa ta jejin da su Sarki Laffaru suke ta yake
su ta kashe su shi da matarsa kawai domin ta
fara rage takaici, amma kuma da ta tuna cewa
ba za ta iya shiga dajin da suke ha sai ta sake
kamuwa da tsananin bakın ciki. Babu ma abın
da ya fi daga mata hankali sama da batan
Mashin Galilul Haras. Nan take Sharlisa ta
shiga cikin dakin halwar tsafinta ta yi gagarumin
shirin Yaki da tafiya sannan ta fito ta hau kan
wani sabon Tsuntsun tsafi ya tashi da ita sama
suka luluka a cikin gajimare. *** Lokacin da
Aljani Maruful Dauwaz ya isa dajin da su Sarki
Laffaru suke, koda suka hango shi yana
saukowa kasa shi kadai babu Jaruma Ziya'ul
Hak a tare da shi sai hankalinsu ya dugunzuma
ainun nan take suka mike tsaye zumbur! daga
bakin bukkarsu suka rugo izuwa gare shi suka
330
TASKARNOVELS.COM.NG
tambaye shi ina 'yarsu take, a cikin hadin baki.
Koda jin wannan tambaya sai Aljanı Maruful
Dauwa ya sunkui da kansa kas cikin alamun
tsattanin damuwa ya kasa cewa komai.
Al'amarin da ya dugunuma hankalin Laffaru da
matarsa ke nan suka fara tunanın ko Ziya'ul Hak
ta mutu ne. Cikin fushi Sarki Laffaru ya dora
hannunsa a kan kafadar Marutul Dauwaz ya
daka masa tsawa ya ce, ya kai Sarkin Jaruman
aljanu, yaya za mu ba ka amanar yarmu amma
ka dawo ka yi mana shiru ba ka sanar da mu
halin da take ciki ba? Da jin wannan batu sau
Aljani Maruful Dauwazya dago kai ya dube su ya
ce, yarku tana nan a cikin Koshin lafiya kuma a
raye, amma tana cıkın TSAKA MAI WUYA. Ni
kaina na hadu da tashin hankali wanda ya fi
Karfina. Nan take Maruful Dauwaz ya kwashe
labarin duk abin da ya faru a can Birnin
Sarauniya Zubaina ya shaida musu, har da irin
BAKIN ARTABUN da aka yi tsakanin Jarumi
Shaddadu da Ziya'ul Hak, har aka buga masa
Mashin Galilul Haras a kafada kashınsa ya
karye ya zube kasa sumamme, kawo izuwa
lokacın da Sarauniya Zubaina da Ziya'ul' Hak
suka hada kai domin su hallaka Shaddadu
331
TASKARNOVELS.COM.NG
amma duk da haka babu tabbacin Shadaddu
yana tare da Mashinsa ko baya tare da shi.
Koda jin wannan batu sai hankalin Sarki Laflaru
da na matarsa ya kara dugunzuma fiye da ko
yaushe suka rasa abin da ke musu dadi. Nan
dai Laffaru da matarsa suka koma gefe daya
suka shiga yin shawara a tsakaninsu inda
Ramlatul Siyam ta dubi Sarki Laffaru cikin
tsananın damuwa sa'adda Kwalla ta cika
idanunta ta ce, ya kai mijina, ka yi sani cewa
idan har yarmu ta kasa hallaka wannan yaro
Shaddadu bisa taimakon Sarauniya Zubaina to
fa shi zai sami nasarar hallaka su, da zarar ya
hallaka su kuwa zai nemi duk inda muke ya zo,
kuma tunda yana tare da Mashin Gaililul haras
zai iya zuwa har nan ya yi mana kisan gilla ko
kuma ya kama mu ya kai mu har can Birnin Kufa
gaban Sarauniya Sharlis ta yi mana kisan
wulakanci. Da dai haka ta faru gare mu gwara
mu bi Aljani Maruful Dauwaz i zuwa Birnin
Sarauniya Zubaina a yi-ta-ta-kare a gaban
idanunmu. Ni kam a yanzu na sami nutsuwa
guda daya da ya zamana cewa sihirin tsafin
Shaddadu da na Ziya'ul Hak duk sun daina
tasiri. Fatana kawai shi ne ya zamana cewa
332
TASKARNOVELS.COM.NG
Shaddadu bai ga Mashinsa ba, babu mamaki
ruwa ya batar da Mashin a cikin Tekun.
Lokacin da Ramlatul Siyam ta zo nan a
zancenta sai Sarki Laffaru yai shiru yana tunani
har izuwa lokaci mai dan tsawo daga can sai ya
baro wajen
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 18