Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
shirin cake idonsa na hagu, koda Hasnalu ya goce sai mashin ya wuce ta saman fuskarsa ya je ya shige ta vikin wani katon dutse ya fice fit, kuma ya dawo da baya da gudu ya yo kan Hasnalu. Nan fa Hasnalu ya cigaba da yaki da wannan mashi na galilur haras, shi kuwa aljani Raugatul Agwanu sai ya tsaya cak yana kallon bakin gumurzun da ake yi tsakanin mashin galilur haras da kuma karumi Hasnalu ma'ana ya zama dan kallo babu abinda Aljani Raugatul Agwanu yake face kyalkkyala dariyar mugunta musamman da yaga cewa mashin ya kuntata Hasnalu. A daidai wannan lokaci ne su Imnal suka farfado daga dogon suman da suka yi, koda sukaga irin azababben yakin da ake yi tsakanin mashin galilur haras da jarumi Hasnalu sai suka cika da tsananin mamaki gami da tsoro, domin basu taba ganin makami kamar galilur haras wanda yake muguwar barna kamar haka, barnar data ragargaza dajin gabadaya, ta haddasa famtsamuwar narkakken dutse, b shiri 377 TASKARNOVELS.COM.NG su jarumi Imnal suka mike suka ruga da gudu izuwa can nesa kadan suka tsaya suna kallon ikon Allah, domin idan suka tsaya inda ake gumurzun narkakken ruwan dutsen ne zai dafar da su. Sai da aka kara shafe wata sa'a guda ana gumurzu tsakanin mashin galilur haras d jarumi Hasnalu har takai cewa Hasnalu ya fara gajiya, a lokacin ne kuma mashin ya kawo wa Hasnalu mugun suka a ciki ya goce cikin matukar zafin nama, amman duk da haka sai da mashin ya huda rigarsa ya fice fit, take kuwa rigar ta kama da wuta, cikin hanzari Hasnalu ya yaga rigar tasa ya jefar fa ita, a lokacin ne kuma mashin ya kara dawowa da baya ya saito kirjinsa zai tsireshi, kawai sai su Imnal suka ga Hasnalu ya mayar da takobinsa cikin kufe kuma ya runtse idanunsa yana mai karanta wata addu'a. Al'amarin da ya firgitasu kenan, gimbiya Hursiyya ta kama kwala wa Hasnalu kira daga inda suke labe cikin dimauta tana mai ce mashi ya kauce kada mashin ya soke shi. Ko juyowa ya dubeta Hasnalu baiyi ba, kuma sam babu alamar tsoron wannan mashin a tare da shi. Shiko aljani Raugatul Agwanu sai ya kama kyalkyala dariyar mugunta saboda yana ganin 378 TASKARNOVELS.COM.NG cewa tabbas wannan karon ajalin Hasnalu ya zo, koda ya rage saura baifi kamu daya ba jal tsakanin kirjin Hasnalu da mashin galilur haras sai akaga mashin ya tsaya cak a sama, shi bai gado kasa ba kum shi bai wuce ba, a sannan ne jarumi Hasnalu ya bude idanunsa kawai sai ya dafa mashin da hannunsa na dama take mashin ya dagargaje kuma ya tarwatse yayi gutsugutsun kamar kwayar zarra. Koda ganin abinda ya faru sai aljani Raugatul Agwanu ya kwarara uban ihu cikin tsananin bakin ciki har kwallar takaici ta zubo daga cikin idanunsa. Su kuwa su sarki Maharaz koda ganin wannan nasara da Hasnalu ya samu akan mashin galilur haras sai suka kama kabbara gami da yiwa Allah godiya. Nan fa aljani Raugatul Agwanu ya sake kwarara uban ihu a karo na biyu, sannan cikin tsananin fushi ya zare takobin Saiful Lujara ya afka wa jarumi Hasnalu da dukkan karfinsa suka sake kacamewa da azababben yaki. Wohoho! Hakika wuya ba a sa mata rana, maza sune maganin maza, kuma tabbas karfi yana da ranarsa, haka ma kwarewa da sanin makama a yaki tana da rana. Tabbas inba dan jarumi Hasnalu ya kasance gwarzon mayaki ba wnda 379 TASKARNOVELS.COM.NG ya saba gwagwarmaya tare da fafatawa a cikin maza ba, kuma yana hadawa da neman tsari a wajen Allah da tuni aljani Raugatul Agwanu yayi masa kwab daya a wannan fafatawar da suka fara, amman duk da haka sai da kai cewa aljani Raugatul Agwanu ya zame masa alakakai, ya rasa ta inda zai bullo masa, shima kuma Aljani Raugatul Agwanu ya rasa hanyar da zai bi ya samu nasara a kansa, sai gashi takobin tasa ta Saiful Lujara da hular lamsara sun kasa tsinana masa komai, a haka sai da suka shafe sa'a guda suna wannan gumurzu. Kaico! Ance gobara daga kogi maganinta sai Allah, ba shiri aljani Raugatul Agwanu ya ja da baya ya tsaya yana haki yana kum kallln jarumi Hasnalu cikin tsananin al'ajabi, domin shi a rayuwarsa ma bai taba gajiya a filin yaki ba dan yana iya kwana arba'in yana yaki a filin daga cikin tsakiyar miliyoyin abokan gaba, amman yau gashi mutum daya jal ya gagareshi kuma ya gajiyar da shi a cikin sa'a daya da rabi. Bayan anyi kallon kallo tsakanin jarumi Hasnalu da aljani Raugatul Agwanu na taawon dakika dari uku da sittin, sai nan take hadari ya gangamo aka fara wata Irin iska mai karfi amman hakan bata sa su 380 TASKARNOVELS.COM.NG Imnal sun bar wanen da suke labe ba, saima suka nemi mafaka suka labe, babban burinsu kawai shine suga yadda karshen wannan fada zai kasance. Nan take kuwa aka fara yayyafi kadan-kadan yana mai sakkowa kasa, kawai sai ljani Raugatul Agwanu ya cire hular lamsara ya ajiyeta gefe guda, sannan kuma ya ajiye takobin Saiful Lujara a kusa da hular, ya tada kwanjinsa yayin da jijiyoyin jikinsa suka tashi suka yi burdin-burdin nan fa kirarsa ta sadaukantaka ta fito ainun, aiko sai ya takarkare ya kwarara uban ihu mai tsananin firgitarwa, duk da irin jarumtaka tasu Imnal sai da suka ji kamar su arce da gudu, domin babu wanda bai motsa ba harma da jan baya ba a cikinsu, duk da cewa suna can baya nesa a matsayin yan kallo. Shikuwa Jarumi Hasnalu ko gezau bai yi ba, kawai shima sai ya gyara tsayuwa yana mai dunkule hannunsa. Su zukatan su Imnal kuwa cike suke da mamaki har suna tambayar zukatansu cewa wai shin wacce irin dakakkiyar zuciya jarumi Hasnalu ke da ita ne, ta yaya zai tari wannan gansamemen sadaukin aljani yana matsayin biladama. Aljani Raugatul Agwanu ya dubi jarumi Hasnalu yace na ajiye dukkan 381 TASKARNOVELS.COM.NG ababan dogaron nawa da dukkan tsafina, zan yakeka da tsagwaron karfin damtsena, idan ka sa kaima ka yakeni da tsagwaron karfin damtsenka, kada kayi amfani da karfin sihirinka. Sa'ad da jarumi Hasnalu yaji wannan batu sai yayi murmushi sannan ya ce na yarda xan yakeka da tsagwaron karfin damtsen da ubangijin ya bani, kuma ina ka sani cewa ni bani da wani sihiri face karfin ubangijina da yake bani kariya daga dukkan sharrinku na aljanu... Kafin jarumi Hasnalu ya gama rufe bakinsa tuni aljani Raugatul Agwanu ya shammaceshi ya daka tsalle sama yayi masa rotse fa gwiywar hannunsa a ka, nan take Hasnalu ya sulale kasa magashiyan mugun yananyi mai kama da suma ko gushewar tunani. Nan fa hankalin su Imnal ya dugunzuma ainun, kuma suka kamu da tsananin tsoro, abinda ya basu mamaki shine kamata yayi ace kan jarumi Hasnalu ya dgargaje domin ko dutse aljani Raugatul Agwanu ya doka da wannan gwiywar hannuntasa sai dutsen ya farfashe, amman sai gashi babu abinda ya samu Hasnalu, sai dai jini da yayi fitar burgu daga cikin hancinsa gami da bakinsa. Nan take Imnal ya yunkura zai falfala da gudu domin ya 382 TASKARNOVELS.COM.NG kaiwa jarumi Hasnalu dauki, amman sai sarki Maharaz yai caraf ya rikeshi tare da cewa ai kada mage ba yanka bane tsaya dai muga abinda zai faru. A wannan lokaci aljani Raugatul Agwanu sai faman ihu yake gami da kuri da cika baki, bisa ganin yayi wa jarumi Hasnalu kaf daya ya baje a kasa yana neman shekawa barzahu, koda yaga cewa Hasnalu ba zai iya tashi ba, sai ya juya ya dauko takobin Saiful Lujara da nufin ya dawo ya daddatsa Hasnalu yayi gutsugutsun da sassan jikinsa. Aiko yana daukar takobin kafin ma ya juyo tuni jarumi Hasnalu ya mike tsaye zumbur tamkar an ja zaren baka, kawai sai ya dako tsalle sama daga inda yake ya daki bayan aljani Raugatul Agwanu, kamar daga cikin baka aka harba aljani Raugatul Agwanu aka yayi tsalle sama yaje ya gwaru da wani katon dutse, karar haduwar kirjinsa da dutsen ta cika dajin gabadaya, dutsen ya farfashe kuma ya fado kasa a matukar galabaice yana mai yin aman jini ta baki da hanci kai harma ta kunnesa ma jini ne ke bulbulowa, anan ya kama shure-shuren mutuwa sakamakon cakudewar jini da ƙwaƙwalwarsa. Cikin tsananin mamaki da farin ciki su Imnal suka rugo da gudu izuwa 383 TASKARNOVELS.COM.NG ga jarumi Hasnalu suka rungumeshi sun masu yi masa jinjina bisa Wannan gagarumar jarumtaka da ya nuna, shi kuwa Aljani Raugatul Agwanu bai shafe dakika talatin ba yana wannan shure-shuren ya zama gawa. Farin ciki a wajen gimbiya Hursiyya da su sarki Maharaz ba sai an fada ba,nan dai suka zauna gabadayansu jarumi Hasnalu ya shiga koyar da su yadda ake yin ibada kamar su; tsarki, wanka, alwala da sallah, koma ya fara koya masu karatun Alkur'ani mai girma, ya biya masu suratul fatiha da falaki da nasi, bayan nan ne yayi masu limanci suka gabatar da sallar la'asar, da aka idar da sallar akayi addu'a sai jarumi Hasnalu ya dubesu gabadayansu tare da cewa to yanzu duk wanda yake jin yunwa sai yaje ya ci, wanda kuma duk yke da bukata ya kawar da ita, domin zamu cigaba da tafiya ne, da izinin Allah zan cika alkawarina na kai kowannenku zuwa kasarsa. Cikin matukar farin ciki kowa ya bude jakar guzurinsa ya dauko abinci ya kamaci, shiko jarumi Hasnalu sai ya dauko tasbaha ya kama lazimi. Jarumi imnal, sarkk Maharaz da gimbiya Mulaifa suka ware waje guda suna cin abincinsu tare, Sadusa tare 384 TASKARNOVELS.COM.NG da dansa Halyal da gimbiya Shalbirat suma suka taru akan abinci guda. Ita kuwa Hursiyya sai ta kasa cin nata abincin, sakamakon cewa jarumi Hasnalu yaki yaci abincin kuma ya kama lazimi, kawai sai ta dauki nata abincin taje ta zauna gefen jarumi Hasnalu ba tare da ya lura da ita ba. Koda Hursiyya ta danyi motsi sai Hasnalu ya juyo ya dubeta, da dai yaga ta ajiye abincin taki ci sai ya cika da mamaki ya dubeta ya ce me yasa baki ci naki abincin ba? Da jin wannan tambaya sai gimbiya Hursiyya tayi murmushi tace ta yaya masoyi zai ji yunwa alhalin masoyinsa baya ji, ina mai tabbatar maka da cewa jina da ganina duk sun zama naka, koda kaya ce idan ta sokeka a halin yanzu nima sai naji zafin sukar a jikina, idan kaga naci wani abu yanzu to sai dai idan yare da kai ne. Sa'ad da jarumi Hasnalu yaji wannan bato sai nan take yaji kaunar Hursiyya ta baibaye ilahirin zuciyarsa kai da ransa ma gabadaya har bai san sa'ad da ya maida mata da martanin murmushi ba, kawai sai ya juyo ya fusknaceta sosai tare da tsoma hannunsa cikin abincin dake gabanta ya fara ci ya ce sa hannu muci tare, domin dai dana barki da yunwa gwara na kawar da kunya 385 TASKARNOVELS.COM.NG na saka hannu muci tare tunda a gaban mutane ne, inda dai mun kadaita ne ba zan yadda na kusanceki haka ba. Cikin tsananin murna gami da farin ciki Hursiyya ta sanya hannunta a cikin abincin ssuka fara ci tare suna masu yi wa junansu murmushi mai nuna tsantsar so da kauna. Bayan kowa ya gama kimtsawa ne sai jarumi Hasnalu ya dubi gabadaya abokan tafiyyar ya ce yanzu ina so kuyi mani affuwa mu fara zuwa birnin su gimbiya shalbirat, domin ita ce wacce aka raba da mahaifarta da iyayenta tun tana da shekara bakwai, kuma ita ce take da burin sake saduwa da mahaifiyarta idan har tana raye. Koda jin haka sai kowa yayi kabbara aka kuma aminci da wannan magana ta jarumi Hasnalu, nan take kowa ya mike tsaye aka hau kimtsawa, bayan kowa ya gama ne jarumi Hasnalu ya shige gaba tare da falfalawa da gudu yana mai karanta wasu Addu'o'i na musamman a cikin zuciyarsa. Hakika Allah shine mai yin yadda ya so, kuma shine mai kunfa yakun, da yace kasance sai kawai abu ya kasance take. A cikin rabin sa'a su jarumi Hasnalu suka shafe tafiyar watanni tara, sai gasu a kofar gidan sarautar gimbiya shalbirat, 386 TASKARNOVELS.COM.NG duk da cewa an sauya tsarin fasalin gidan kama daga katanga, da sauransu, kuma an kawata gidan ainun ba kamar yadda yake a da ba tsawon shekaru shekaru goma sha tara baya, sai da gimbiya Shalbirat ta shaida gidan sarautar, ta tabbatar da cewa nan gidansu ne. Koda masu tsaron kofar gidan sarautar suka ga su jarumi Hasnalu tsulum a gabansu kamar aljanu, kuma basu ga ta inda suka taho ba, sannan basuga durarsu daga sama ba, sai suka kamu da tsananin tsoro jikinsu ya kama tsuma, kafin su jarumi Hasnalu suyi magana an bude masu kofa sun kunna kai ciki. Shalbirat ce ta yi masu jagora wato ta wuce gaba su kuma suna biye da ita a baya haka suka nufi fada kai tsaye. Duk inda suk wuce sai dai kaga dakaru,bayi, barori da kuyangin gidan sarautar suna ratsawa gami da basu hanya, a haka har suka isa cikin fadar inda suka iske Sarauniya Juzairat bisa karagar mulki, koda Shalbirat ta kura mata idanu sai ta shaidata, domin ita ce ta ci amanar mahaifinta ta kawar dashi daga kan mulki, ta sa masa cutar ajali, kuma itace tasa aljani Raugatul Agwanu ya saceta ya kaita can dajin darul hushushul maut. A wannan lokaci fadar 387 TASKARNOVELS.COM.NG ta cika makil da fadawa da mutanen gari, amman koda aka hango su jarumi Hasnalu sun durfafi karagar mulki, sai fadawa da dakaru suka kama mikewa tsaye suna masu ja da baya cikin matukar tsoro da razana, ya zamana cewa wannan sarauniya dake kan kujerar mulki idanunta sun zazzaro, kuma ita jikinta na tsuma kamar ace kyet ta fida da gudu. Gimbiya shalbirat ta cigaba da tunkarar sarauniya, su jarumi Hasnalu na take mata baya, a haka har sai da suka iso daf da ita, yadda ita da Shalbirat suna iya jin numfashin junansu. Shalbirat ta dubeta ta ce nice gimbiya shalbirat yar danuwanki, sarkin da kika kashe kika hau kargar mulkinsa, sannan kika sa aljani Raugatul Agwanu ya sace ni ya tafi dank can dajin darul hushushul maut, ka rabani da uwata da ubana tsawon shekara goma sha tara. Koda jin wannan batu sai sarauniya Juzairat ta dada cika da tsananin mamaki ta kura wa shalbirat idanu, alokacin da ta dada kamuwa da tsoro jikinta da baikinta suka hau rawa ta kasa cewa komai. Shalbirat ta sake dubanta a karo na biyu ta ce ni yanzu nazo maki da addinin gaskiya wato addinin Musulunci, kuma na baki zafi ki karbi 388 TASKARNOVELS.COM.NG addinin Allah ki tsira da rayuwarki, sannan ki sauka daga kan matsayin da kike a yanzu ki dawo talaka kamar kowa ko kuma yanzu ki rasa rayuwarki? Koda jin Wannan batu sai sarauniya Juzairat ta bushe da dariyar keta ta ce tsakanina da addinin musulunci sai gaba.. Kafin ta gama rufe bakinta gimbiya Shalbirat ta juyo cikin tsananin zafin nama ta zare takobin jarumi Hasnalu ta kuma juyawa ta fille kan Sarauniya Juzairat, nan take jini yayi tsiri sama yayin da kan nata ya gangaro daga kan karagar mulki. Nan take Shalbirat ta kwala kabbara kuma ta karanta kalmar shahada ta na mai umartar gabadaya mutanen dake fadar da su biya kalmar. Ba tare da wata gardama ba gabadaya mutanen fadar suka maimaita kalmar shahada, cikin tsananin farin ciki gimbiya Shalbirat ta hau kan karagar mulki ta zauna alokacin da su jarumi Hasnalu suka cika da tsananin mamakin wannan gagarumar jarumtaka da ta yi. Zaman Shalbirat akan karagar mulki sai idanunta suka ciko da kwalla, har hawaye ya zubo mata a lokacin data gama kare wa karagar mulki da kuma fadar kallo. A sannan ne ta dubi wani dattijo a fadar ta ce ya kai waziri Lamsanu mene 389 TASKARNOVELS.COM.NG ne labarin mahaifiyata? Cikin tsananin mamaki waziri Lamsanu ya dubi gimbiya Shalbirat ya ce rankiya dade qshe ba zaki manta da kamannina ba, kiyi sani cewa mahaifiyarki ta samu tabin hankali, kuma tana can a tsare a kurkuku. Koda jin haka sai bakin ciki ya turnuke Shalbirat har hawaye ya sake zubo mata ta mike ta ce muje ka kaini inda take. Nan take Waziri Lamsanu ya wuce gaba Shalbirat dasu jarumi Hasnalu na take mashi baya, haka suka yita tafiya a gidan sarautar suna masu shiga lungu da sako na gidan sarautar har sai da suka iso inda kurkukun yake, aka kai su kofar dakin da mahaifiyar Shalbirat take. Da zuwa sai suka isketa a kwance tana bacci, gashin kanta yayi buzu-buzu ba kyan gani, ga kuma furfura duk ta rufeshi Hakazalika rigar jikinta ta yi dauda sosai har tana wari. Su duka dai da suka zibar da hawaye saboda tausayi, Shalbirat ta kira sunan mahaifiyar tata har sau uku sannan ta taso zaune tana mai kura wa Shalbirat idanu, kawai sai ta bushe da dariya ta kama surutu irn na masu tabin hankali tana mai kawo wa Shalbirat duka. Koda ganin haka sai jarumi Hasnalu ya yi sauri ya matsar da Shalbirat baya sannan ya 390 TASKARNOVELS.COM.NG shiga karanta wata addu'a yana tofawa mahaifiyar Shalbirat, aiko nan take wani nannauyan bacci ya dauketa, jim kadan ta farko tana mai tashi tsaye da kafafunta tana mai binsu da idanu daya bayan daya, koda idanunta suka yi arba da yarta Shalbirat sai ta kura mata idanu har hawaye ya zubo mata, ta nuna Shalbirat da hannu kuma ta kira sunanta tana mai cewa Yata ashe kina raye a wannan duniya, ashe zamu sake saduwa? Koda jin wannan batu sai mamaki ya kama su Jarumi Hasnalu suka yi kabbara a tare, nan take Shalbirat tasa aka bude kofar dakin da mahaifiyarta ke ciki ta ruga da gudu suka rungume juna ita da mahaifiyarta tata suka fashe da sabon kukan farin ciki. Suma su Imnal basu san sa'ad da kukan ya kwace masu ba, saboda tausayi gami da murna, a wannan rana aka kaddamar da addinin musulunci a Birnin, gimbiya Shalbirat kuma ta hau kan karagar mulki. Lokacin dasu jarumi Hasnalu suka je yi mata bankwana sai ta fashe da kuka, ta dubi Sadusa da dansa Halyal ta ce kune farkon sanadin tsirata daga hannun azzalumi aljani Raugatul Agwanu, bani da bakin yi maku godiya face addu'ar Allah ya saka maku 391 TASKARNOVELS.COM.NG da mafificin alheri. Ba tare da bata lokaci ba su Hasnalu suka yi mata sallama suka tafi, ana isa birnin sarki Dujalu nan ma aka kaddamar da addinin musulunci amman gimbiya Hursiyya bata karbi sarauta b sai aka ba Sadusa. Waziri da jama'arsa kuwa suka bashi hadin kai. A sannan ne aka shiga dakin tarihi na gidan sarautar inda aka gano wannan littafin mai dauke da tarihin kamannin mahaifin Hasnalu da kuma inda kabarinsa yake, nan take aka dunguma aka tafi wajen, koda aka tona saman kabarin sai aka yi arba da fuskar mahaifin Hasnalu lafiyarta sumul ko kwarzanewa bata yi ba, kamar ma asannan ne aka binne shi, kuma kamanninsu iri daya ne sak da jarumi Hasnalu tamkar an tsaga kara, bambancinsu kawai na shekaru ne. Koda jama'a sukaga wannan gawa cikin koshin lafiya alhalin ta kusa shekaru talatin a binne sai suka cika da al'ajabi aka kama hailala da kabbara, aka kuma sallama Wa Allah bisa ikonSa. Hasnalu ya kura wa mahaifinsa idanu yana mai zubda hawaye ya ce ya kai abbana ban taba ganinka ba sai labarinka da mahaifiyata ta bani, rayuwarka gaba daya ta gushe a cikin yada Addinin Allah, yau gashi 392 TASKARNOVELS.COM.NG Allah ya cika mani burina naga fuskarka da idanuna kafin mutuwata. Burina ya cika, fatana nima Allah ya dau raina a irin wannan tafarki naka, nan take ya mayar da kasar kabarin ya rufe sannan yayi masa addu'a. Kamar yadda aka kaddamar da addinin musulunci a birnin Sarauniya Shalbirat da birnin sarki Dujalu haka akaje birnin sarki Maharaz aka kaddamar da shi, kuma duk d cewa jarumi Imnal da gimbiya Mulaifa sun kasance yara a sannan aka daura masu aure, akayi gagarumin shagalin biki a gaban jarumi Hasnalu da gimbiya Hursiyya. Lokacin da Hasnalu da gimbiya Hursiyya suka zo zasu yi wa su Imnal da sarki Maharaz bankwana domin su tafi izuwa can nahiyar su jarumi Hasnalu inda acan ne Hursiyya zata karasa sauran rayuwarta ta duniya sai su duka suka kama kuka saboda bakin cikin rabuwa da juna, sarki Maharaz ya rungume jarumi Hasnalu yana mai cewa ya kai jarumin jarumai, kaine ka tsamoni daga cikin duhun jahilci ka haskake mana wannan nahiya gaba daya da hasken musulunci, hasken ilimi kuma haske na gaskiya, tabbas har abada ba zamu taba mantawa da kai ba, kuma har mu mutu zamu 393 TASKARNOVELS.COM.NG rinka tunawa da kai muna alfahari da kai, idan ka amince ina so tun gabanin ku barmu a daura aurenka da gimbiya Hursiyya a gaban idanunmu domin mu zama sheda kuma ku tsira daga dukkanin wani tsautsayi na sharrin shedan dana zuciya, tunda zaku kadaita a cikin wannan doguwar tafiya da zaku yi izuwa nahiyarku. Koda sarki Maharaz yazo nan a zancensa sai jarumi Hasnalu yaji matukar farin ciki, kuma ya kama yin godiya ga sarki Maharaz bisa hango masu abinda zai fiye masu alheri. Nan take aka daura auren jarumi Hasnalu da gimbiya Hursiyya bisa ka'idar addinin Musulunci, bayan nan sai suka yi bankwana su sarki Maharaz suna zubar da hawaye suma suna zubarwa, har jarumi Hasnalu da Hursiyya sun juya zasu tafi sai kawai sarki Maharaz ya kira sunan Hursiyya ta juyo ta dubeshi ya ce da ita ya ke yata in da tambaya a gareki? Tambaya ta farko ita ce wane irin darasi kika samu a cikin hikayar jarumi shaddadu, kuma wane ilimi kika gani a cikin tamu rayuwar ni da fan uwanki sarki Dujalu? Koda jin wadannan tambayoyi sai hawaye ya zubo daga cikin idanun Hursiyya domin babu wanda ya taba mata irin wannan 394 TASKARNOVELS.COM.NG tambaya face sarki Dujalu. Hursiyya ta yi ajiyar numfashi sannan ta ce ya kai abbana ka sani cewa a cikin hikayar jarumi shaddadu na fahimci cewar zalunci da son zuciya basa haifar da komai face nadama da kaskanci gami da dunbin wahala kamar yadda karshen rayuwar sarki Laffaru ta kasance, tunda a farkon rayuwarsa karfin mulki, dana jarumtarsa hadi da na sihiri sun sa masa isgilanci har yana cin zalin al'umma, ganin cewa babu wani da ya isa ya taka masa birki, amma sai gashi ya mace ta rabashi da mulkinsa, karfinsa da duk daukakarsa, kuma ta jefashi a cikin tsananin wuya da rashin kwanciyar hankali har izuwa karshen rayuwarsa. Darasi na biyu a cikin wannan labari shine abu ne mara kyau mutum ya tsananta gaba a tsakaninsa da wani, kamar yadda Sharlis da Laffaru suka tsananta gaba a tsakaninsu har ga yayansu, wanda sai ga shi a karshe yayan nasu sun kamu da son juna kuma suka zabi su mutu tare dan kawo karshen gabar iyayen nasu, abinda ya cusa wa iyayen bakin ciki kenan suka kashe kansu, suka rasa komai ba tare da burin dayansu ya cika ba. Dangane da ilimin dana samu game da rayuwar dan 395 TASKARNOVELS.COM.NG uwana Dujalu da taka rayuwar shine na fahimci cewar wanda duk bai gode Wa Allah ba bisa baiwar da yayi masa ta arziki da daukaka, har yake harin ya samu wadda tafi wannan to karshensa nadama gami da hasara, tunda gashi kai da shi duk kunyi mummunar asara ta dukiya da rayukan jama'a kuma burinku bai cika ba, haka kuma na samu babban ilimi na kadaita Allah, ikonsa da isarSa akan komai da kowa, tunda gashi matsafa da aljanu sun kasa dauko kayan yakin mazan jiya a cikin tekun bahar Suffiya, amman sai gashi wanda yayi imani da Allah ya kadaitashi ya dauko su salim alin, kamar yadda ake cire silin gashi daga cikin tandun mai, hakika ubangijin musulunci shine buwayi gagara misali, wanda duk yayi imani da shi ya kubuta kuma ya tsira daga dukkanin sharri, wanda kuma ya bujire masa ya hadu da masifa da halaka. Koda Hursiyya ta zo nan a jawabinta sai sarki Maharaz ya cika da tsananin murna gami da farin ciki, yace AlhamduLillahi tabbas kin samu duk irin darasin daya kamata ki samu a cikin wadannan labarai, albishir din da zanyi maki shine kije ki nemi wani littafi mai suna Tsatsuba tabbas zakiji labarin Sadauki 396 TASKARNOVELS.COM.NG Hulkas na birnin Romaniya a cikinsa tunda dai dan uwanki sarki dujalu bai samu damar baki labarin ba ajali ya riskeshi. Koda jin haka sai farin ciki ya lullube gimbiya Hursiyya ta ce aiko in sha Allah duk inda Littafin Tsatsuba yake zan nemeshi domin na karanta tarihin Sadauki Hulkas mai hular lamsara n birnin Romaniya. Nan take Jarumi Hasnalu da gimbiya Hursiyya suka sake yi wa sarki Maharaz sallama suka tafi suna masu waigensa har suka fice daga fadar tasa, gabadaya suka nausa izuwa cikin daji suna masu falfalawa da azababben gudu, cikin yarda da huwacewa ta Allah suka nufi nahiyar su jarumi Hasnalu inda zasu cigaba da rayuwa bisa tafarkin addinin Muslunci. AlhamduLillahi nanne karshen wannan littafi na mazan jiya da fatan kunji dadin wannan littafi wanda Abdulaziz Sani madakin gini ya rubuta ni kuma Abubakar Saleh Alquyraemey na jagoranci typing insa nake cewa mu hadu da ku a wani littafin. 397 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF

Chapter 17 of 18