Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sannan muyi namu a karshe... Ba tare da gardamar komai ba Hibru ya ja da baya ya dubi inmal. Kawai sai inmal ya tunkari abkin gwaminsa Ratiju ba tare da ya zare takobinsa ba. Koda Ratiju ya ga inmal ya durfafoshi babu makami sai ya cika da tsananin farin ciki sbda tunanin cewa ya sami babbar da mar da zai yi masa kwaf daya. Cikin hanzari Ratiju ya zare takobinsa ya falfala da azababben gudu izuwa kan inmal yana kwarara ihu mai tsananin firgitarwa wanda ka iya tarwatsa gungu dakaru a filin fama. Zan ci gaba. MAZAN JIYA Littafi na hudu (4) Part C Na Abdulaziz Sani m gini Typing Abubakar Saleh AlQuyraemey 23 TASKARNOVELS.COM.NG Ko gezau inmal bai yiba yaci gaba da tunkarasa batare da yazare takobinsa ba daga cikin kufeta. Ai kuwa suna haduwa sai ratiju ya kawowa inmal wani irin mugun wawan sara a wuya da dukkan karfinsa cikin bakin zafin nama inamal ya sunkuya domin ya kauce saran amma dukk da haka sai da kaifin takobin ratiju ya shaftare saman kunne inmal ya yanke rabin gashin kansa sai ga jini na diga daga kunnen inmla a yayin da aka sami yar taraza a tsakaninsu. Kofa inmal ya shafa kunnensa ya ji jini kuma ya ga rabin gashin kansa a kas sai ya fusata ainun zuciyarsa ta kama tarfafasa kamar zata kone. Shi kuwa ratiju sai ya kama dariyar keta da murna yna ganin cewa idan aka sake gamuwa fara daya zai gama fa inmal. Batare da inmal ya zare takobin tasa ba sai ya sake durfafar ratiju al.amarin da yai matukar dugunzuma hankalin sarki Maharaz ke nan. Har Hibru ya fara kwalawa inma kira yana yi masa tsawa akan ya zare takobinsa kafin su hadu da ratiju. Inmal yayi kamar bai ji umarunin Hibru ba ya ci gaba da tunkarar ratiju a hakan. Ita kuwa Gimbiya mulaifa wacce ke tsaye acan gefe daya tana kallon abin da faruwa tuni ta 24 TASKARNOVELS.COM.NG fara kuka tun sa,adda ta ga an rutsure rabbin gashin kan inmal kuma anyi masa rauni a kunne. Sarki dujalu kuwa dariya yake ta kyalkyalawa yana yiwa ratiju kirari gami da kara masa kwarin guiwa. Dama sadaiki ratiju ya fi Matinu karfin dantse da zafin nama shi kansa sarki dujalu idan suna yar gwajin jarumtaka shi da ratiju sai yayi da gaske yake samun nasara akansa don haka a yanzu yana kyautata zato cewa ratiju zai iya hallaka inmal duk da cewa yayi yaki da inmal ya ga irin tsananin tasa jarumtakar. Koda ratiju da inmal suka sake haduwa a kari na biyu, sai ratiju ya kawowa inmak muguwar suka a ciki. Kawai sai inmal ya tare tsinin takobin da tafin hannayensa biyu. Nan fa ratiju ya fara danno takobin da dukkan karfinsa domin ya huda cikin inmal. Wohoho! Mai karfi sai allah ya isa! Nan fa tsagwaron karfin dantse ya fara amfani sai gashi duk su biyun kwanjin jikinsu ya kumbura jijiyoyinsu suka tashi suka yi burdin burdin. A lokacin guda duk su biyun sai ga gumi na karyi musu. Shi dai Ratiju ya kasa dannan tsinin takobin ta shige izuwa cikin inmal. Shi kuma inmal ya kasa kautar da takobin daga saitin cikinsa. Tsawon 25 TASKARNOVELS.COM.NG komanin dakika dari da sittin suna tsaye kikam a hakan kowannensu yana jin jiki har kaifin takobin ta Ratiju ya fara yankar tafin hannun inmal jimi ya fara diga. Kwatsam! Sai inmal ya kwarara ubakjina a n.u ya daga takobin da shi kansa ratiju sama yai wurgi da su. Tamkar an cilla hoge sama hakan ratiju da takobin suka luluka sama suka watse a saman. Kafin ratiju ya fado kasa inmal ya daka tsalle sama ya taresahi kawai sai ya kama kansa da hannu biyu ya murde masa wuya. Sai gashi inmal ya duro kasa bisa kan turba rungume da gawar tatiju. Nan take yi jifa da gawar tamkar tsummam, ya mike tsaye yana mai karkade jurar jikinsa. Ai kuwa su sarki Maharaz basu san saadda suka kaure da shewar farinciki ba suka kama yiwa inmal kirari gami da jinjina bisa wannan gagarumar jarumtaka da yayi. Shi kuwa sarki dujalu da jama.arsa kamewa suka yi kamar gumaka sbda mamaki da bakin ciki. Nan take hawaye takaici ya zuvowa sarki dujalu sbda ya san cewa yayi asarar babban mayakinsa wanda bashi da kamarsa. Bayan sarki dujalu ya gama alhinin mutuwar ratuju izuwa tsawon yan dakiku sai ya tako kafafunsa 26 TASKARNOVELS.COM.NG yazo tsakiyar filin dagar ya tsaya sannan ya xare wadansu manyan takubba guda biyu dake soke a gadon bayansa ya fuskanci sarki yaki Hibru. Adaidai wannan lokacin ne hankalin inmal da na Sarki Maharaz ya dugunzuma ainun suka ji kamar su rike Hibru su hanashi tarar sarki dujalu. Kawai sai suka ga shima Hibru ya zare nasa takubban guda biyu ya yunkura zai tunkari sarki dujalu. A guje inmal yasha gaban Hibru ya dubeshi cikin tsananin damuwa yace yakai abbana ka bani dama na karbeka a wannan gumurzu ni na fafata da sarki dujalu. Koda jin wnan batu sai Hibru ya yi murmushi yace yakai dana kayi sani cewa ai bakin alkalami ya riga ta bushe. Tun da har muka yi rantsuwa da girman ubangikinmu Darbuza babu gudu kuma babu ja da baya. Kamar yadda na zuba ido ka yina ka gumurzu har kasami nasara hakan kaima zaka zuba ido ka kalli nawa. YAU ne ranar da zan san iyakar jarumtakata kuma ka sani cewa ko kashe ni aka yi zan mutu ne a cikin alfharin kare kasata gami da martabar sarautar abkna aminina: alfarma daya nake nema a wajenka; duk wuya duk rintsi karka bari gimbiya Mulaifa ta rasa rayuwarta kuma in dai kayi tsawon rai 27 TASKARNOVELS.COM.NG ka aureta ku koma birninmu ku karasa rayuwarku ta duniya: koda gama fadin hakan sai Hibru ya juya ya kalli abkinsa sarki Maharaz wani kallo yayi masa mai kama dana bankwana a cikin murmushi mai dugunzua hankali: Nan take sarki Maharaz ya ji hawaye ya zubo asa kua ya ji kamar ya ruga da gudu ya rike Hibru ya hanashi karo da sarki dujalu: Nan take Hibru ya durfafi Sarki Dujalu shima sarki dujalu sai ya tunkaroshi kiwannensu ya taho a fusace acikin mugun nufi amma a hankali suke tahowa cikin nutsuwa ba tare da sauri ba; sai da yarege saura baifi taku goa a tsakninsu ba sannan suka ruga da gudu izuwa kan juna suka ruguntsue da azababben yaki: Wohoho! Maza maganin maza. Hakika idan jarumtaka ta hadu da sadaukantaka gami da naci da tsantsar juriya dole ne gumurzun ya yi dadin kallo kuma ya zama abin tsaro: anfara wannan bakin artabu tsakanin sarki dujalu da Hibru sai labri ya zaa sabo: gaba dayan mutanen dake fili babu wanda hankalinsa bai dugunzuma ba fiye da ko yaushe sbo da ganin yadda jaruman biyu suke kaiwa junansu mugayen hare hare na musamman wanda babu mai iya yin irinsa face 28 TASKARNOVELS.COM.NG tshon hannu bangaren yaki: duk dace wa sarki dujalu yafi Hibru tsauntsar karfin dantse amma sai gashi Hibru na iya kare hare harensa har ma yana mai da martanin shi kansa sarki dujalu yayi matukar mamkin yadda hakan ta kasance domin yayi zaton cewa suna fara gumurzu zai iya kuntatashi da karfin dantsensa cikin kankanin lokaci amma sai gashi labari ya sha bamban: Nan ta suka tashi hankalin kasa kura ta turnuke filin yakin dudufniyar kafafuwansu dakarar haduwar makamansu suka cika dodon kunne kaai cw mutum dubu ne suka gwamuse suke yakin: Sai da suka shafe sa:a uku cur! Suna wannan dauki ba dadi tamkar jikinsu bana kashi da tsoka bane face na karfe zallah sannan suka gaji: bisa dole kowannensu ya ha da baya suja yi cirko cirko kmar zakaru suna haki gami da kallon juna kuma kowannensu ya jike sharkaf da zufa kamar daga cikin kogin aka tsamosu; Abin da ya daurewa kowannensu kai kuma ya basu haushi shine ganin yadda suka dade suna wannan gumurzu amma dayansu bai sami nasar koda kwarzanar jikin daya ba: Su kansu taron rudunonin biyu dake kallon wannan gumurzu ji suka yi kamar da can ruwan 29 TASKARNOVELS.COM.NG masifa ake zubowa daga sama amma da jaruman sua daina yakin sai suka ji an dauke ruwan masifar: Sai da sarki dujalu da Hibru suka shefe tsawon dakika dari biyar da arba:in suna haki da hararar juna kuma kowannensu na tunanin irin salon da ya kaata ya sauya domin ya sai nasara: kamar hadin baki sai aka Ga duk su biyun sun taso da gudu a lokaci guda sun durfafi juna: gudu ne na bala i tamkar zasu tashi sama kuma kowannensu da dukkan karfinsa ya taho cikin mugun nufi: maimakon su daka tsalle sama su yi mugun gamo a kasan kowanensu ya kaiwa dan uwansa mumunnan hari: sai ga shi kowannensu ya wuce dan uwansa amma sai duk suka sulale kasa bisa guiwoyinsu suka kame kamar gumaka: Al:amarin da ya razana kowa kenan a wajen gashi dai dukkanninsu sun rankwafar da kawunansu kas ama basa motsi tamka babu mai rai acikinsu, daga can sai aka ga jini na malalowa kasa daga jikin hannun daman sarki dujalu kuma yana rike da hannun: shi kuwa Hibru sai aka ga jini na malalowa ta kuibin cikinsa: jim kadan sai hannun daan na sarki dujalu ya gutsure ya fado kasa shima ya sulale 30 TASKARNOVELS.COM.NG kasa sumame: shi kuwa Hibru sai ya bingire kasa ya kaa shure shuren mutuwa; cikin tsananin dimauta sarki maharaz da inmal suka ruga izuwa kan Hibru: tun daga nesa suka fara rasu ihu suka fashe da kuka: a bangare sarki dujalu kuwa dakarunsa ne suka rugo da gudu suka daukeshi yana cikin halin suman suka ruga dashi izuwa can cikin sansaninsu: lokacin da inmal da sarki Maharaz suka iso kan Hibru yana takakarin mutuwa sai suka durkusa a gabansa suka sake fashewa da matsanaicin kuka sbda sun lura da raunin dake kuibin cikin nasa sun ga yayi rami zururu babu yadda za ayi ya rayu: hannun Hibru na karkarwa ya kamo hannun sarki Maharaz ya dora bisa kirjinsa suka kurawa juna idanu, cikin matukar karfin hali Hibru ya dudi baki da kyar yace yakai abkna yau fa ranar rabuwarmu ta zo: Tabbas mutuwa zan yi yanzu ba zan tashi ba: ina alfahari da wannan mutuwa tawa domin na mutu ne a filin daga bisa kare kasata da mutuncika: sannan ina alfahari da cewar na sarewa sarki dujalu hannun daya har ya bar duniya ba zai taba mantawa da niba na cusa masa bakin cikin da zai tafi da shi har kabarinsa: koda Hibru yazo 31 TASKARNOVELS.COM.NG nan a znacesa sai sarki Maharaz ya tasoshi zauna ya rungumeshi yana mai fashewa da sabon kuku yace yakai masoyina babban amina saboda me zaka tafi kabarni a cikin wannan duniya wacce baya da dadin zama idan babu masoyi? Ka sani cewa in banda yata ba mulaifa bani da kowa sai kai gashi zaka mutu a dai dai lokacin da zan samu duniya na yi aka sakayya bisa bautar da kayi mini a baya gai da nuna tsantsar so da kauna: ai kuwa tun da har tafiya zaka yi nia ina mai rokin darbuza da ya gaggauta dauke.... Kafin sarki Maharaz ya gama rufe bakinsa sai HIBRU yarufe asa baki da tafin hannunsa yace idan kaima ka tafi waye zai ga auren yayanmu kenan? Ya kai masoyina komai RINTSI DA TSANANI Lallai ka rayu a wannan yaki koda kuwa bamu samu nasara mallakar Takobin Saiful Lujara ba: burina kawai shine kai da inmal da gimbiya mulaifa ku koma gida a raye: Saadda Hibru yazo nan a zncensa sai sarki maharaz yasake fashewa da kuka yace yakai masoyina kayi sani cewa bakin alkalami ya bushe domin kafin mu baro gida mai girma Darbuza ya tabbatar Mini dacewa mutum hudu ne kacal zasu tsira a wannan filin 32 TASKARNOVELS.COM.NG yaki kuma mutum biyu daga cikinmu: kaga kenan a tsakanin ni inmal da mulaifa dole ne dayanmu ya mutu: koda jin wannan batu Sai Hibru ta ci gaba da kakarin mutuwa da zafi; Al amarin da ya dimauta su inmal kenan: inmal yai sauri ya karbi Hibru daha hannu sarki maharaz ya rungumeshi a kirjinsa yana mai tsala ihun bakin ciki sa;adda hawaye ke ta kwararowa daga cikin idanunsa: a sannan ne Hibru ya dan dawo cikin hakanlinsa ka dan ya dubi inmal yayi masa murmushi karfin hali yace yakai dana ka zamo mai juriya bisa rashina: ina mai fari ciki kasancewar zan mutu akan tafin hannunka kamar yadda mahaifin ya mutu akan tafin hannuna kuma a filin yaki: kaima ina maka fatan mutuwa irin ta manya mazaje a karshen rayuwarka: ina fatan baza ka manta da wasiyyata ba akan masoyiyarka mulaifa: a wannan lokaci mulaifa na can nesa da su kadan tana faman rusa kuka ta kasa karosowa inda suke : 33 TASKARNOVELS.COM.NG Zan ci gaba. MAZAN JIYA Littafi na hudu (4) Part D Na Abdulaziz Sani m gini Typing Abubakar Saleh AlQuyraemey hibru ya juyar da kansa ya dubi inda mulaifa take tsaye a lokacin da idanunsa ke ganinta dishi dishi sannan ya waigo ya dubi inmal yayi masa kallon karshe: a hakan idanunsa suka kafe yana yiwa inmal murmushi; kuma gaba dayan jikinsa ya sandare: inmal bais san cewa Hibru ya mutu ba sai daya lura da cewa idanunsa sun daina kiftawa: koda ya fahimci hakan sai ya tsandara uban ihu wanda ya firgita komai da kowa ke cikin dajin: nan take shi da sarki maharaz suka kankame gawar hibru a jinsu suna masu fashewa da matsainincin kuka: a sanna ne itaama gimbiya ta rugo sa gudu ta fada kan gawar Hibru ta tayasu kukan: 34 TASKARNOVELS.COM.NG * * * Al amarin sarki dujalu kuwa lokacin da darunsa suka daukeshi da gudu suka tafi dashi izuwa cikin sansaninsu sai aka wuce da shi izuwa cikin tintinsa aka kwantar da shi akan shimfidarsa: nan fa likitansa ya shiga aiki: bayan ya tsaida jinin dake zuba a gundulmin hannunsa sai ya samasa magani sannan ya lulluceshi iya kirji da mayafi kowa ya fice daga cikin tanti aka bar sarki dujalu shi kadai har a sanna bai farfado daga dogon suman da yayi ba amma akwai alamar fitar numfashinsa kadan kadan: sarki dujalu bai farfado ba sai bayan saa biyu sa rabi : koda ya bude idanunsa ya tsinci kansa a cikin tantinsa a kwance sai ya cika da tsananin mamaki domin shi a zatonsa ya mutu a filin yaki: sarki dujalu ya yunkura domin ya yaye mayafinsa da aka lullbeshi da hannunsa na dama kawai sai yaji kamar bashi da hannun gaba daya: cikin tsananin firgici ya sa daya hannun nasa na hagu ya yaye mayafin take yayi arba da hannunsa na dama ya ga yazama gungulmi: sarki dujalu ya takarkare ya kwarara mugun ihu mai tsananin karfi gami da amsa kuwwa izuwa cikin dajin gaba daya: kai hataa dabbobi da aljanun dake rayuwa a cikin 35 TASKARNOVELS.COM.NG karkashin teku bahar Sufuya sai da wannan ihu na sarki dujalu ya eazansu: bayan yayi ihu kuma sai ya fashe dd matsanaici kukan vakin ciki domin wanan shine karo na farko da Taba yi masa rauni a filin yaki a iya tsawon rayuwarsa duk da cewar ya halarci yakukuwa sama da guda dari a rayuwarsa : kuma tunda uwarsa ta haifeshi bai taba zubar da hawayen takaici ba sai yau: cikin wannan hali ne shugaban Dakarunsa na jinsin Aljanu wanda ake kira BARUZUL MADWAN yashigo cikin tantin ya zube kasa ya kwashi gaisuwa yace Ya shugabana yanzu mene ne abin yi tsakaninmu da su waye zai sami damar shiga cikin wannan kogi na Bahar Sufiya don dauko Takobin saiful Lujara tsakanin mu da su; tunda anyi yarjejeniya bisa cewar wadanda suka yi nasara a yakin mutum uku uku sune zasu dauko takobin kuma gashi yanzu kamar RAGAS akayi tunda kai suma kayi a filin yakin shi kuma Hibru mutuwa yayi: Page 33 Koda jin wannan batu sai farin ciki ya lulube sarki dujalu bisa jin cewar yasamin nasarar kashe Hibru amma 36 TASKARNOVELS.COM.NG kuma da ya dubi gundulmi hannunsa sai ya sake kamuwa da tsananin bakin ciki: Tsawon tan dakiku sarki dujalu yana tunani bai baiwa aljani barzul madwan amsar tambayarsa ba sai daga can ya dago kai ya dubeshi yace ya kai shugaban dakarun aljanu kayi sani cewa a halin yanzu yarjejeniyar da ke tsakaninmu da su sarki maharaz ta rushe wannan yaki ya zama danye don haka za ayi hutu na tsawon kwna uku domin na baiwa avkan gabamu damar da zasu sami saukin dacin rashin da suka yina babban masoyinsu: dalilina anan shine abin kunya ne a gareni na yakesu a lokacin da zukatansu ke cike da rauni: lallai na fi son na yakesu a lokacin da suke cikin nutsuwarsu sbda haka yanzu kaje ka sa a rubuta takarda a kaiwa abkan gaba bisa wannan hukuci da nayanke. Aljani barzul madwan ya risina yace angama ya shugabana: kawwai sai ya bace bat! Daga cikin tanti tamkar bai taba wanzuwa ba a ciki * * * * bayan su sarki Maharaz sun kwashe gawarwakin dakarunsu mutum biyu da aka kashe; wato gawar sarki yaki Hibru data 37 TASKARNOVELS.COM.NG Barde Kursham sun koma cikin sansaninsu sai aka shiga gidimar binne gawar: nan fa kowa da kowa ya kama kuka kamar ba za a daina ba: babu wanda zai fi baka tausayi ma sama da sarki Maharaz domin har birgima ya kama ya a kasa sai da aka rirrikrshi aka shiga bashi baki sbda jiya yiya tsani kansa gwara ma ace shima ya mutu ya huta da bakin ciki: Lokacin da aka sanya Hibru a cikin kabarinsa aka rufeshi sai inmal da sarki maharaz suka kwana akan kabarin suja cigaba da kuka ba sassauci: akan kabarin suka kwna suna kukan har sai da alfirjir ya keto sannan aka zo aka kwashesi sumammu aka kaisu cikin tanti aka kwantar: da kyar da sindin goshi gimbiya Mulaifa ta ceto rayuwarsu: bayan sun dawo hayyancisu ne aka kawo musu abin kalaci dama a jiya da daddare ma basu ci komai ba: nan fa gardama ta karke a tsakaninsu da mulaifa suka ce ba zasu ciba: Gimbiya Mulaifa ta zare wata karaar wuka mai tsananin kaifi da tsini ta saita cikintana kuka tace idan har baza ku cin abinci ba lallai zata kashe kanta: nan fa suka kama cin abinci bisa dole har sai da suka koshi: gama cin abinci nasu ke da wuya sai ga wani badakare Mai 38 TASKARNOVELS.COM.NG suna GAIYABU ya shigo cikin tanti rike da wasika a hannunsa: Gaiyabu ya zube kasa gaban sarki maharaz ya kwashe gaisuwa sannan ya mika masa wasikar: nan take sarki maharaz ya warware wasikar ya karanta a fili kamar haka; SAKO DAGA SARKI DUJALU: ZUWA GA SARKI MAHARAZ BABBAN ABOKIN GABATA: YAKAI WANNAN SARKI KAYI SANI CEWA ABINDA YA FARU TSAKANINMU DA KU BA KOMAI BANE FACE SHARAR FAGE: NA SANCEWA NA KUNSA MUKU GAGARUMIN BAKIN CIKI BISA NASARAR DA NA SAMU TA KASHE SARKI YAKINKA; KUMA BABBAN MASOYINKA HIBRU TO AMMA NIMA HIBRU YA TAFI YA BARNI DA TABON BAKIN CIKI DA HAR ABADA BA ZAN MANTA DASHI BA TUNDA YARABANI DA HANNUNA GUDA DAYA: TABBAS NAYI JINJINA GA MAMACI HIBRU DOMIN SHI NE JARUMI NA FARKO WANDA YA TABA SAMUN DAMAR YI MIN RAUNI A FILIN DAGA KUMA NA YI ALKWARI KODA BAYAN WANNA YAKI NE ZAN ZIRYACI KABARIN HIBRU NA YI MASA JINJINA: INA MAI SANAR DAKAI CEWA BISA GUMURZUN DA AKA YI A JIYA MU DAKU BABU WANI SAKAMAKO FACE RAGAS SABODA 39 TASKARNOVELS.COM.NG HAKA ZAMU CI GABA DA WANNAN YAKI NAN DA CIKAR KWANA UKU SBDA NAFI SON NAYI YAKIN DA KU A LOKACIN DA KUKE DA NATSUWA BA YANZU BA DA KUKE CIKIN DAMUWA DA ALHINI: INA FATAN ZA KU KARBI WANNAN SHAWARA TAWA HANNU BIYU Koda sarki maharaz ya zo nan a karatun wasikar sai yamike tsaye zumbur a fusace ya yayyaga wasikar sannan ya yunkura da nufin yafita waje ya sa a fara shirye shiryen yaki cikin hanzari inmal ya sha gabansa yace ya shugabana ka tausasa zuciyarka ka dau hkr sau tari yanke hukunci a lokacin da rai ya fusata baya haifar da komai face nadama da asara: muyi amfani da shawarar wanan abokin ga namu mujira izuw tsawon kwna ukun: koda jin wanna batu sai sarki maharaz ya duci inmal cikin alamun tsananin damuwa yace yakai magajin sarkin yaki shin baka da tunanin cewa sarki dujalu so yake ya yaudaremu ya yi amfani dawann dama ya kawi mana harin sumamea cikin kwana ukun nan yadda zai iya murkusheu 40 TASKARNOVELS.COM.NG a cikin kankanin lokaci? Inmal ya numfasa yace haba ya shugabana ai babu wani motsi wanda sarki da dakarunsa za suyi ba tare da mun gani ba tunda daga nan sasaninmu muna hangensu suna hangenmu, dare da ranan masu gadi suna lura: ka kara hakuri ya shugabana har ixuwa lokacin da wadannan kwanki zasu ciki ni ina ji a jikina cewar mune zamu sami nasarar dauko takobin Saiful Lujara a cikin wannan kogi: koda inmal yazo nan a zancensa sai Gimbiya mulaifa mata dubeshi tace kayi amfani da shwarar inmla ya kai abbana domin ina gainin cewa itace zata fiye mana alheri: koda gama fadin hakan mulaifa ta kama hannun inmal taja shi suka fice daga cikin tantin suka bar sarki maharaz a tsaye cikin tsananin da muwada takaici WANNAN SHINE ABINDA YAFARU A CAN BAKIN KOGIN BAHAR SUFIYA BAYAN ANCI GABADA FAFATA YAKKI TSAKANIN RUDUNAR SARKI MAHARAZ DA RUNDUNAR SARKI DUJALU A KARO NA BIYU 41 TASKARNOVELS.COM.NG * * * * * AL:AMARIN Gimbiya Hursiya Kuwa; lokacin da aljani burzaru ya nufi can birnin da ira ta tabbatar da cewa an rabata Da sarki kenan sai ta fashe da matsaininci kukana bakin ciki: Bata gushe ba tana kukan hat aljni Barzaru ya sauketa a tsakiyar gidan sarautar tasu Koda bayi kunyangi barori da dakarun tsaro na gidan suka ganta sai duk suka zube kasa a gabnta suna kwasar gaisuwa ko kallomsu ba tayi ba sai ta juya a fusace tashige izuwaa can cikin gidan sarautar da sauri: duk sa adda ta waigo bayanta sai ta ga aljani Barzaru nabiye da ita: Al'amarin da yai matukar ba ta mamaki da tsoro kenan. nan take ta gane cewa lallai sarki ne ya umarci barzaru da ya sa ido akanta don kada ta sulale ta koma can sansani yaki: Nan fa Hursiya taji hankalinta ya dugunzuma ainun kuma ta kudurce a ranta cewar takowanne hali sai ta san yadda tayi ta subecewa barzaru takoma can sansanin yaki sbda gwara itama ta mutu a can da dai azo mata da labarin mutuwar sarki tunda bata da kowa a duniya sai shi. kai tsaye Gimbiya Hursiyya ta wuce izuwa 42 TASKARNOVELS.COM.NG cikin turakarta. tana shiga ciki ta mai da kofa tarufe bam da karfi cikin fishi sannan ta fada kam gadonta ta kwanta ruf da ciki ta fashe da sabon kuka: Shi kuwa aljani barzaru a kofar turakar yaja ya tsaya kuma ya kame kamar gunki yana muzurai ko yaushe idanunsa na kallon gabas da yamma kudu da arewa don hada gimbiya Hursiya ta Shamaceshi ta fice ba tare da sani ba: su kuwa fadawan sarki dujalu wadanda aka barwa jiran gari koda suka ji cewar gimbiya Hursiya ta dawo daga sansanin yaki ita kadai? Sai suka cika da tsananin mamaki suka dugungumo gaba daynasu syka zo ganin gimbiya. koda suka aika da manzo a gareta bisa zuwansu sai ta aiko a gay musu cewa baza ta gana dakowa ba sai gobe da safe a fada: Al:amarin da yai matukar dugunzuma hakalinsu kenan suka rasa abinda ke musu dadi sabo sa su kawai so suke suji matsayin da ake ciki a can sansanin yaki: Shin sarki Dujalu yana nan a raye ko kuwa ya mutu? MASU IYA MAGANA SUN CE IDAN KAGA KARE YANA SHINSHINA TAKALMI TO SO YAKE ZAI DAUKA. tunda gimbiya Hursiyya taji cewa yan majalisar sarki sun kagu da su yi magana da ita sai jikinta 43 TASKARNOVELS.COM.NG ya bata cewar so suke suci amanar sarki, ma'ana idan suka ji sarki ya mutu sai su yi sauri su nada wanda suke son ya gajeshi acikinsu batare da sun bata sarautar bakamar yadda yake aka ida: Koda aiyana hakan sai hankalin Hursiya ya sake dugunzuma ainun domin ta fahimci cewar lallai tana ciki hadari domin idan ta fadawa yan majalisar gaskiya al amari cewar bata san abinda ya faru a filin yakin ba tunda bata gani da idanunta zasu zata karya take su dauka cewa lallai itama da kyar ta tsira kuma an kashe sarki da mukarrabansa: ama da Hursiya ta tuna cewa ai tana tare da aljani Barzaru babban jarumi kuma sadauki mai watsa maza babbn hadimi sarki dujalu mai amana sai hankalinta ya dan kwanta sbda ta san cewa zai kareta daga dukkan wani mugun abu amma kuma sai ta fara tunasnin hanyar da zata bita koma can sansanin yakin domin zamanta a can zai fiye mata kwnciyar hankali. Kashe gari da safe bayan Gimbiya Hursiya ta gama kintsawa tayi kalaci sai ta caba ado sanna ta nufi fada fuskarta cike da annuri tana takawa dai dai tamkar taron dawisu ta rinka tafiya cikin izza da jin kamshi: da shigarta cikin 44 TASKARNOVELS.COM.NG fadar sai ta iske gaba dayan yan majalisar a zaune sun yi tsuru tsuru suna jira isowarta: koda suka ga gimbiya a cikin fara ada nishadi sai hankalinsu ya dugunzuma ainun suka fara tunanin cewa lallai sarki dujalu ne yake samun nasara acan filin yakin: Dama bayan tafiyar sarki dujalu da rundunarsa ta yaki sai yan majalisar suja yi taro na sirri a tsakaninsu inda suka gaiyato wani amintaccen bokansu mai suna IRMAS BINI KAIBUR suka umarceshi daya yi musu bincike akan abinda zai faru a can bakin kogin Bahar sufiya: Koda boka Irmas ya dauko madubin tsafinsa ya shafeshi da hannun hagu domin yaga abinsa zai faru sai nan take madubin tsafin yayi bindiga ya farfashe: Al:amarin da yai matukar razana boka irmas da yan majalisar kenan suka firgita ainun: Har yan majalisar sun yunkura zasu mike tsaye su fice da gudu dga cikin dakin tsaro sai boka irmas ya daka musu tsawa yace kowa ya zauna a inda yake in bahaka ba kuwa babu wanda zai koma gidansa a raye: Koda jin hakan sai kowa ya koa inda yake ya zauna: boka irmas yai gyaran murya sannan ya dubi gaba dayan yan majalisar yace yaku shuganbanina kuyi sani 45 TASKARNOVELS.COM.NG cewa babu wani matsafi a wannan nahiya mai karfin sihiri dayakai na sarki dujalu sbda haka ya boye duk abinda ke faruwa a cam bakin tekun bahar sufiya ga dukkan wani mahaluki dake cikin wannan nahiya: bisa wannan dalili ne kuka ga madubin tsafina yai bindiga; yanzu hanya daya ce zamu bi my iya ganewa idan sarki dujalu yana samun nasara a filin yaki ko baya samu: Nan gaba a lokacin da yakin ya fara tsauri lallai akwai mutumin da zai dawo daga can filin yakin wandas ya kasance makusanci na sarki ya hau kan karagar sarki ya zauna: to tabbas rudunarmu basu da saa kuma baza su dawo ba a raye, idan kuwa yaki zama akan karagr sarki to tabbas sarki dujalu zai dawo gida a raye: Kofa gimbiya Hursiya taga yan majalissar sun kura mata idanu sai hankalinta ya dugunzuma ta dada tabbatar da cewa lalai akwai wani mugun abu da ke ransu. Awannan Lokaci aljani barzaru na biye da ita yana take mata bayan don tabbatar da tsaro amma babu mai ganinsa face gimbiy Harsiya kadai, har Gimbiya hursiya ta nufi inda karagar sarki take da nufin ta zauna sai aljani barzaru yi sauri ta sha gabanta yayi mata nuni da jada taje ta 46 TASKARNOVELS.COM.NG zauna akan karagar. Batare da gardamar komai ba kuwa ta sauya wuri taje ta zauna akan kujerar da ta saba zama ko da yaushe a fadar kamar kullum: koda ganin haka sai jikin yan majalisar ya yi sanyi gaba dayansu sai murna takoma

Chapter 2 of 18