sannan muyi
namu a karshe... Ba tare da gardamar komai ba
Hibru ya ja da baya ya dubi inmal. Kawai sai
inmal ya tunkari abkin gwaminsa Ratiju ba tare
da ya zare takobinsa ba. Koda Ratiju ya ga
inmal ya durfafoshi babu makami sai ya cika da
tsananin farin ciki sbda tunanin cewa ya sami
babbar da mar da zai yi masa kwaf daya. Cikin
hanzari Ratiju ya zare takobinsa ya falfala da
azababben gudu izuwa kan inmal yana kwarara
ihu mai tsananin firgitarwa wanda ka iya
tarwatsa gungu dakaru a filin fama.
Zan ci gaba.
MAZAN JIYA
Littafi na hudu (4)
Part C
Na Abdulaziz Sani m gini
Typing Abubakar Saleh AlQuyraemey
23
TASKARNOVELS.COM.NG
Ko gezau inmal bai yiba yaci gaba da tunkarasa
batare da yazare takobinsa ba daga cikin
kufeta. Ai kuwa suna haduwa sai ratiju ya
kawowa inmal wani irin mugun wawan sara a
wuya da dukkan karfinsa cikin bakin zafin nama
inamal ya sunkuya domin ya kauce saran
amma dukk da haka sai da kaifin takobin ratiju
ya shaftare saman kunne inmal ya yanke rabin
gashin kansa sai ga jini na diga daga kunnen
inmla a yayin da aka sami yar taraza a
tsakaninsu. Kofa inmal ya shafa kunnensa ya ji
jini kuma ya ga rabin gashin kansa a kas sai ya
fusata ainun zuciyarsa ta kama tarfafasa kamar
zata kone. Shi kuwa ratiju sai ya kama dariyar
keta da murna yna ganin cewa idan aka sake
gamuwa fara daya zai gama fa inmal. Batare da
inmal ya zare takobin tasa ba sai ya sake
durfafar ratiju al.amarin da yai matukar
dugunzuma hankalin sarki Maharaz ke nan.
Har Hibru ya fara kwalawa inma kira yana yi
masa tsawa akan ya zare takobinsa kafin su
hadu da ratiju. Inmal yayi kamar bai ji umarunin
Hibru ba ya ci gaba da tunkarar ratiju a hakan.
Ita kuwa Gimbiya mulaifa wacce ke tsaye acan
gefe daya tana kallon abin da faruwa tuni ta
24
TASKARNOVELS.COM.NG
fara kuka tun sa,adda ta ga an rutsure rabbin
gashin kan inmal kuma anyi masa rauni a
kunne. Sarki dujalu kuwa dariya yake ta
kyalkyalawa yana yiwa ratiju kirari gami da kara
masa kwarin guiwa. Dama sadaiki ratiju ya fi
Matinu karfin dantse da zafin nama shi kansa
sarki dujalu idan suna yar gwajin jarumtaka shi
da ratiju sai yayi da gaske yake samun nasara
akansa don haka a yanzu yana kyautata zato
cewa ratiju zai iya hallaka inmal duk da cewa
yayi yaki da inmal ya ga irin tsananin tasa
jarumtakar. Koda ratiju da inmal suka sake
haduwa a kari na biyu, sai ratiju ya kawowa
inmak muguwar suka a ciki. Kawai sai inmal ya
tare tsinin takobin da tafin hannayensa biyu.
Nan fa ratiju ya fara danno takobin da dukkan
karfinsa domin ya huda cikin inmal. Wohoho!
Mai karfi sai allah ya isa! Nan fa tsagwaron
karfin dantse ya fara amfani sai gashi duk su
biyun kwanjin jikinsu ya kumbura jijiyoyinsu
suka tashi suka yi burdin burdin. A lokacin
guda duk su biyun sai ga gumi na karyi musu.
Shi dai Ratiju ya kasa dannan tsinin takobin ta
shige izuwa cikin inmal. Shi kuma inmal ya kasa
kautar da takobin daga saitin cikinsa. Tsawon
25
TASKARNOVELS.COM.NG
komanin dakika dari da sittin suna tsaye kikam
a hakan kowannensu yana jin jiki har kaifin
takobin ta Ratiju ya fara yankar tafin hannun
inmal jimi ya fara diga. Kwatsam! Sai inmal ya
kwarara ubakjina a n.u ya daga takobin da shi
kansa ratiju sama yai wurgi da su. Tamkar an
cilla hoge sama hakan ratiju da takobin suka
luluka sama suka watse a saman. Kafin ratiju
ya fado kasa inmal ya daka tsalle sama ya
taresahi kawai sai ya kama kansa da hannu
biyu ya murde masa wuya. Sai gashi inmal ya
duro kasa bisa kan turba rungume da gawar
tatiju. Nan take yi jifa da gawar tamkar
tsummam, ya mike tsaye yana mai karkade
jurar jikinsa. Ai kuwa su sarki Maharaz basu san
saadda suka kaure da shewar farinciki ba suka
kama yiwa inmal kirari gami da jinjina bisa
wannan gagarumar jarumtaka da yayi. Shi kuwa
sarki dujalu da jama.arsa kamewa suka yi
kamar gumaka sbda mamaki da bakin ciki. Nan
take hawaye takaici ya zuvowa sarki dujalu
sbda ya san cewa yayi asarar babban
mayakinsa wanda bashi da kamarsa. Bayan
sarki dujalu ya gama alhinin mutuwar ratuju
izuwa tsawon yan dakiku sai ya tako kafafunsa
26
TASKARNOVELS.COM.NG
yazo tsakiyar filin dagar ya tsaya sannan ya xare
wadansu manyan takubba guda biyu dake soke
a gadon bayansa ya fuskanci sarki yaki Hibru.
Adaidai wannan lokacin ne hankalin inmal da
na Sarki Maharaz ya dugunzuma ainun suka ji
kamar su rike Hibru su hanashi tarar sarki
dujalu. Kawai sai suka ga shima Hibru ya zare
nasa takubban guda biyu ya yunkura zai tunkari
sarki dujalu. A guje inmal yasha gaban Hibru ya
dubeshi cikin tsananin damuwa yace yakai
abbana ka bani dama na karbeka a wannan
gumurzu ni na fafata da sarki dujalu. Koda jin
wnan batu sai Hibru ya yi murmushi yace yakai
dana kayi sani cewa ai bakin alkalami ya riga ta
bushe. Tun da har muka yi rantsuwa da girman
ubangikinmu Darbuza babu gudu kuma babu ja
da baya. Kamar yadda na zuba ido ka yina ka
gumurzu har kasami nasara hakan kaima zaka
zuba ido ka kalli nawa. YAU ne ranar da zan san
iyakar jarumtakata kuma ka sani cewa ko
kashe ni aka yi zan mutu ne a cikin alfharin kare
kasata gami da martabar sarautar abkna
aminina: alfarma daya nake nema a wajenka;
duk wuya duk rintsi karka bari gimbiya Mulaifa
ta rasa rayuwarta kuma in dai kayi tsawon rai
27
TASKARNOVELS.COM.NG
ka aureta ku koma birninmu ku karasa
rayuwarku ta duniya: koda gama fadin hakan
sai Hibru ya juya ya kalli abkinsa sarki Maharaz
wani kallo yayi masa mai kama dana bankwana
a cikin murmushi mai dugunzua hankali: Nan
take sarki Maharaz ya ji hawaye ya zubo asa
kua ya ji kamar ya ruga da gudu ya rike Hibru ya
hanashi karo da sarki dujalu: Nan take Hibru ya
durfafi Sarki Dujalu shima sarki dujalu sai ya
tunkaroshi kiwannensu ya taho a fusace acikin
mugun nufi amma a hankali suke tahowa cikin
nutsuwa ba tare da sauri ba; sai da yarege
saura baifi taku goa a tsakninsu ba sannan
suka ruga da gudu izuwa kan juna suka
ruguntsue da azababben yaki: Wohoho! Maza
maganin maza. Hakika idan jarumtaka ta hadu
da sadaukantaka gami da naci da tsantsar
juriya dole ne gumurzun ya yi dadin kallo kuma
ya zama abin tsaro: anfara wannan bakin
artabu tsakanin sarki dujalu da Hibru sai labri
ya zaa sabo: gaba dayan mutanen dake fili
babu wanda hankalinsa bai dugunzuma ba fiye
da ko yaushe sbo da ganin yadda jaruman biyu
suke kaiwa junansu mugayen hare hare na
musamman wanda babu mai iya yin irinsa face
28
TASKARNOVELS.COM.NG
tshon hannu bangaren yaki: duk dace wa sarki
dujalu yafi Hibru tsauntsar karfin dantse amma
sai gashi Hibru na iya kare hare harensa har ma
yana mai da martanin shi kansa sarki dujalu
yayi matukar mamkin yadda hakan ta kasance
domin yayi zaton cewa suna fara gumurzu zai
iya kuntatashi da karfin dantsensa cikin
kankanin lokaci amma sai gashi labari ya sha
bamban: Nan ta suka tashi hankalin kasa kura
ta turnuke filin yakin dudufniyar kafafuwansu
dakarar haduwar makamansu suka cika dodon
kunne kaai cw mutum dubu ne suka gwamuse
suke yakin: Sai da suka shafe sa:a uku cur!
Suna wannan dauki ba dadi tamkar jikinsu
bana kashi da tsoka bane face na karfe zallah
sannan suka gaji: bisa dole kowannensu ya ha
da baya suja yi cirko cirko kmar zakaru suna
haki gami da kallon juna kuma kowannensu ya
jike sharkaf da zufa kamar daga cikin kogin aka
tsamosu; Abin da ya daurewa kowannensu kai
kuma ya basu haushi shine ganin yadda suka
dade suna wannan gumurzu amma dayansu
bai sami nasar koda kwarzanar jikin daya ba:
Su kansu taron rudunonin biyu dake kallon
wannan gumurzu ji suka yi kamar da can ruwan
29
TASKARNOVELS.COM.NG
masifa ake zubowa daga sama amma da
jaruman sua daina yakin sai suka ji an dauke
ruwan masifar: Sai da sarki dujalu da Hibru
suka shefe tsawon dakika dari biyar da arba:in
suna haki da hararar juna kuma kowannensu
na tunanin irin salon da ya kaata ya sauya
domin ya sai nasara: kamar hadin baki sai aka
Ga duk su biyun sun taso da gudu a lokaci guda
sun durfafi juna: gudu ne na bala i tamkar zasu
tashi sama kuma kowannensu da dukkan
karfinsa ya taho cikin mugun nufi: maimakon
su daka tsalle sama su yi mugun gamo a kasan
kowanensu ya kaiwa dan uwansa mumunnan
hari: sai ga shi kowannensu ya wuce dan
uwansa amma sai duk suka sulale kasa bisa
guiwoyinsu suka kame kamar gumaka:
Al:amarin da ya razana kowa kenan a wajen
gashi dai dukkanninsu sun rankwafar da
kawunansu kas ama basa motsi tamka babu
mai rai acikinsu, daga can sai aka ga jini na
malalowa kasa daga jikin hannun daman sarki
dujalu kuma yana rike da hannun: shi kuwa
Hibru sai aka ga jini na malalowa ta kuibin
cikinsa: jim kadan sai hannun daan na sarki
dujalu ya gutsure ya fado kasa shima ya sulale
30
TASKARNOVELS.COM.NG
kasa sumame: shi kuwa Hibru sai ya bingire
kasa ya kaa shure shuren mutuwa; cikin
tsananin dimauta sarki maharaz da inmal suka
ruga izuwa kan Hibru: tun daga nesa suka fara
rasu ihu suka fashe da kuka: a bangare sarki
dujalu kuwa dakarunsa ne suka rugo da gudu
suka daukeshi yana cikin halin suman suka
ruga dashi izuwa can cikin sansaninsu: lokacin
da inmal da sarki Maharaz suka iso kan Hibru
yana takakarin mutuwa sai suka durkusa a
gabansa suka sake fashewa da matsanaicin
kuka sbda sun lura da raunin dake kuibin cikin
nasa sun ga yayi rami zururu babu yadda za ayi
ya rayu: hannun Hibru na karkarwa ya kamo
hannun sarki Maharaz ya dora bisa kirjinsa
suka kurawa juna idanu, cikin matukar karfin
hali Hibru ya dudi baki da kyar yace yakai abkna
yau fa ranar rabuwarmu ta zo: Tabbas mutuwa
zan yi yanzu ba zan tashi ba: ina alfahari da
wannan mutuwa tawa domin na mutu ne a filin
daga bisa kare kasata da mutuncika: sannan
ina alfahari da cewar na sarewa sarki dujalu
hannun daya har ya bar duniya ba zai taba
mantawa da niba na cusa masa bakin cikin da
zai tafi da shi har kabarinsa: koda Hibru yazo
31
TASKARNOVELS.COM.NG
nan a znacesa sai sarki Maharaz ya tasoshi
zauna ya rungumeshi yana mai fashewa da
sabon kuku yace yakai masoyina babban
amina saboda me zaka tafi kabarni a cikin
wannan duniya wacce baya da dadin zama
idan babu masoyi? Ka sani cewa in banda yata
ba mulaifa bani da kowa sai kai gashi zaka
mutu a dai dai lokacin da zan samu duniya na yi
aka sakayya bisa bautar da kayi mini a baya gai
da nuna tsantsar so da kauna: ai kuwa tun da
har tafiya zaka yi nia ina mai rokin darbuza da
ya gaggauta dauke.... Kafin sarki Maharaz ya
gama rufe bakinsa sai HIBRU yarufe asa baki da
tafin hannunsa yace idan kaima ka tafi waye zai
ga auren yayanmu kenan? Ya kai masoyina
komai RINTSI DA TSANANI Lallai ka rayu a
wannan yaki koda kuwa bamu samu nasara
mallakar Takobin Saiful Lujara ba: burina
kawai shine kai da inmal da gimbiya mulaifa ku
koma gida a raye: Saadda Hibru yazo nan a
zncensa sai sarki maharaz yasake fashewa da
kuka yace yakai masoyina kayi sani cewa bakin
alkalami ya bushe domin kafin mu baro gida
mai girma Darbuza ya tabbatar Mini dacewa
mutum hudu ne kacal zasu tsira a wannan filin
32
TASKARNOVELS.COM.NG
yaki kuma mutum biyu daga cikinmu: kaga
kenan a tsakanin ni inmal da mulaifa dole ne
dayanmu ya mutu: koda jin wannan batu Sai
Hibru ta ci gaba da kakarin mutuwa da zafi; Al
amarin da ya dimauta su inmal kenan: inmal yai
sauri ya karbi Hibru daha hannu sarki maharaz
ya rungumeshi a kirjinsa yana mai tsala ihun
bakin ciki sa;adda hawaye ke ta kwararowa
daga cikin idanunsa: a sannan ne Hibru ya dan
dawo cikin hakanlinsa ka dan ya dubi inmal
yayi masa murmushi karfin hali yace yakai dana
ka zamo mai juriya bisa rashina: ina mai fari
ciki kasancewar zan mutu akan tafin hannunka
kamar yadda mahaifin ya mutu akan tafin
hannuna kuma a filin yaki: kaima ina maka
fatan mutuwa irin ta manya mazaje a karshen
rayuwarka: ina fatan baza ka manta da
wasiyyata ba akan masoyiyarka mulaifa: a
wannan lokaci mulaifa na can nesa da su
kadan tana faman rusa kuka ta kasa karosowa
inda suke
:
33
TASKARNOVELS.COM.NG
Zan ci gaba.
MAZAN JIYA
Littafi na hudu (4)
Part D
Na Abdulaziz Sani m gini
Typing Abubakar Saleh AlQuyraemey
hibru ya juyar da kansa ya dubi inda mulaifa
take tsaye a lokacin da idanunsa ke ganinta
dishi dishi sannan ya waigo ya dubi inmal yayi
masa kallon karshe: a hakan idanunsa suka
kafe yana yiwa inmal murmushi; kuma gaba
dayan jikinsa ya sandare: inmal bais san cewa
Hibru ya mutu ba sai daya lura da cewa
idanunsa sun daina kiftawa: koda ya fahimci
hakan sai ya tsandara uban ihu wanda ya firgita
komai da kowa ke cikin dajin: nan take shi da
sarki maharaz suka kankame gawar hibru a
jinsu suna masu fashewa da matsainincin
kuka: a sanna ne itaama gimbiya ta rugo sa
gudu ta fada kan gawar Hibru ta tayasu kukan:
34
TASKARNOVELS.COM.NG
* * * Al amarin sarki dujalu kuwa lokacin da
darunsa suka daukeshi da gudu suka tafi dashi
izuwa cikin sansaninsu sai aka wuce da shi
izuwa cikin tintinsa aka kwantar da shi akan
shimfidarsa: nan fa likitansa ya shiga aiki:
bayan ya tsaida jinin dake zuba a gundulmin
hannunsa sai ya samasa magani sannan ya
lulluceshi iya kirji da mayafi kowa ya fice daga
cikin tanti aka bar sarki dujalu shi kadai har a
sanna bai farfado daga dogon suman da yayi ba
amma akwai alamar fitar numfashinsa kadan
kadan: sarki dujalu bai farfado ba sai bayan saa
biyu sa rabi : koda ya bude idanunsa ya tsinci
kansa a cikin tantinsa a kwance sai ya cika da
tsananin mamaki domin shi a zatonsa ya mutu
a filin yaki: sarki dujalu ya yunkura domin ya
yaye mayafinsa da aka lullbeshi da hannunsa
na dama kawai sai yaji kamar bashi da hannun
gaba daya: cikin tsananin firgici ya sa daya
hannun nasa na hagu ya yaye mayafin take yayi
arba da hannunsa na dama ya ga yazama
gungulmi: sarki dujalu ya takarkare ya kwarara
mugun ihu mai tsananin karfi gami da amsa
kuwwa izuwa cikin dajin gaba daya: kai hataa
dabbobi da aljanun dake rayuwa a cikin
35
TASKARNOVELS.COM.NG
karkashin teku bahar Sufuya sai da wannan ihu
na sarki dujalu ya eazansu: bayan yayi ihu
kuma sai ya fashe dd matsanaici kukan vakin
ciki domin wanan shine karo na farko da Taba yi
masa rauni a filin yaki a iya tsawon rayuwarsa
duk da cewar ya halarci yakukuwa sama da
guda dari a rayuwarsa
: kuma tunda uwarsa ta haifeshi bai taba zubar
da hawayen takaici ba sai yau: cikin wannan
hali ne shugaban Dakarunsa na jinsin Aljanu
wanda ake kira BARUZUL MADWAN yashigo
cikin tantin ya zube kasa ya kwashi gaisuwa
yace Ya shugabana yanzu mene ne abin yi
tsakaninmu da su waye zai sami damar shiga
cikin wannan kogi na Bahar Sufiya don dauko
Takobin saiful Lujara tsakanin mu da su; tunda
anyi yarjejeniya bisa cewar wadanda suka yi
nasara a yakin mutum uku uku sune zasu
dauko takobin kuma gashi yanzu kamar RAGAS
akayi tunda kai suma kayi a filin yakin shi kuma
Hibru mutuwa yayi: Page 33 Koda jin wannan
batu sai farin ciki ya lulube sarki dujalu bisa jin
cewar yasamin nasarar kashe Hibru amma
36
TASKARNOVELS.COM.NG
kuma da ya dubi gundulmi hannunsa sai ya
sake kamuwa da tsananin bakin ciki: Tsawon
tan dakiku sarki dujalu yana tunani bai baiwa
aljani barzul madwan amsar tambayarsa ba sai
daga can ya dago kai ya dubeshi yace ya kai
shugaban dakarun aljanu kayi sani cewa a halin
yanzu yarjejeniyar da ke tsakaninmu da su sarki
maharaz ta rushe wannan yaki ya zama danye
don haka za ayi hutu na tsawon kwna uku
domin na baiwa avkan gabamu damar da zasu
sami saukin dacin rashin da suka yina babban
masoyinsu: dalilina anan shine abin kunya ne a
gareni na yakesu a lokacin da zukatansu ke
cike da rauni: lallai na fi son na yakesu a
lokacin da suke cikin nutsuwarsu sbda haka
yanzu kaje ka sa a rubuta takarda a kaiwa
abkan gaba bisa wannan hukuci da nayanke.
Aljani barzul madwan ya risina yace angama ya
shugabana: kawwai sai ya bace bat! Daga cikin
tanti tamkar bai taba wanzuwa ba a ciki
* * *
* bayan su sarki Maharaz sun
kwashe gawarwakin dakarunsu mutum biyu da
aka kashe; wato gawar sarki yaki Hibru data
37
TASKARNOVELS.COM.NG
Barde Kursham sun koma cikin sansaninsu sai
aka shiga gidimar binne gawar: nan fa kowa da
kowa ya kama kuka kamar ba za a daina ba:
babu wanda zai fi baka tausayi ma sama da
sarki Maharaz domin har birgima ya kama ya a
kasa sai da aka rirrikrshi aka shiga bashi baki
sbda jiya yiya tsani kansa gwara ma ace shima
ya mutu ya huta da bakin ciki: Lokacin da aka
sanya Hibru a cikin kabarinsa aka rufeshi sai
inmal da sarki maharaz suka kwana akan
kabarin suja cigaba da kuka ba sassauci: akan
kabarin suka kwna suna kukan har sai da alfirjir
ya keto sannan aka zo aka kwashesi sumammu
aka kaisu cikin tanti aka kwantar: da kyar da
sindin goshi gimbiya Mulaifa ta ceto rayuwarsu:
bayan sun dawo hayyancisu ne aka kawo
musu abin kalaci dama a jiya da daddare ma
basu ci komai ba: nan fa gardama ta karke a
tsakaninsu da mulaifa suka ce ba zasu ciba:
Gimbiya Mulaifa ta zare wata karaar wuka mai
tsananin kaifi da tsini ta saita cikintana kuka
tace idan har baza ku cin abinci ba lallai zata
kashe kanta: nan fa suka kama cin abinci bisa
dole har sai da suka koshi: gama cin abinci
nasu ke da wuya sai ga wani badakare Mai
38
TASKARNOVELS.COM.NG
suna GAIYABU ya shigo cikin tanti rike da
wasika a hannunsa: Gaiyabu ya zube kasa
gaban sarki maharaz ya kwashe gaisuwa
sannan ya mika masa wasikar: nan take sarki
maharaz ya warware wasikar ya karanta a fili
kamar haka; SAKO DAGA SARKI DUJALU:
ZUWA GA SARKI MAHARAZ BABBAN ABOKIN
GABATA: YAKAI WANNAN SARKI KAYI SANI
CEWA ABINDA YA FARU TSAKANINMU DA KU
BA KOMAI BANE FACE SHARAR FAGE: NA
SANCEWA NA KUNSA MUKU GAGARUMIN
BAKIN CIKI BISA NASARAR DA NA SAMU TA
KASHE SARKI YAKINKA; KUMA BABBAN
MASOYINKA HIBRU TO AMMA NIMA HIBRU YA
TAFI YA BARNI DA TABON BAKIN CIKI DA HAR
ABADA BA ZAN MANTA DASHI BA TUNDA
YARABANI DA HANNUNA GUDA DAYA: TABBAS
NAYI JINJINA GA MAMACI HIBRU DOMIN SHI
NE JARUMI NA FARKO WANDA YA TABA
SAMUN DAMAR YI MIN RAUNI A FILIN DAGA
KUMA NA YI ALKWARI KODA BAYAN WANNA
YAKI NE ZAN ZIRYACI KABARIN HIBRU NA YI
MASA JINJINA: INA MAI SANAR DAKAI CEWA
BISA GUMURZUN DA AKA YI A JIYA MU DAKU
BABU WANI SAKAMAKO FACE RAGAS SABODA
39
TASKARNOVELS.COM.NG
HAKA ZAMU CI GABA DA WANNAN YAKI NAN
DA CIKAR KWANA UKU SBDA NAFI SON NAYI
YAKIN DA KU A LOKACIN DA KUKE DA
NATSUWA BA YANZU BA DA KUKE CIKIN
DAMUWA DA ALHINI: INA FATAN ZA KU KARBI
WANNAN SHAWARA TAWA HANNU BIYU
Koda sarki maharaz ya zo nan a karatun
wasikar sai yamike tsaye zumbur a fusace ya
yayyaga wasikar sannan ya yunkura da nufin
yafita waje ya sa a fara shirye shiryen yaki
cikin hanzari inmal ya sha gabansa yace ya
shugabana ka tausasa zuciyarka ka dau hkr sau
tari yanke hukunci a lokacin da rai ya fusata
baya haifar da komai face nadama da asara:
muyi amfani da shawarar wanan abokin ga
namu mujira izuw tsawon kwna ukun: koda jin
wanna batu sai sarki maharaz ya duci inmal
cikin alamun tsananin damuwa yace yakai
magajin sarkin yaki shin baka da tunanin cewa
sarki dujalu so yake ya yaudaremu ya yi amfani
dawann dama ya kawi mana harin sumamea
cikin kwana ukun nan yadda zai iya murkusheu
40
TASKARNOVELS.COM.NG
a cikin kankanin lokaci? Inmal ya numfasa yace
haba ya shugabana ai babu wani motsi wanda
sarki da dakarunsa za suyi ba tare da mun gani
ba tunda daga nan sasaninmu muna hangensu
suna hangenmu, dare da ranan masu gadi suna
lura: ka kara hakuri ya shugabana har ixuwa
lokacin da wadannan kwanki zasu ciki
ni ina ji a jikina cewar mune zamu sami nasarar
dauko takobin Saiful Lujara a cikin wannan
kogi: koda inmal yazo nan a zancensa sai
Gimbiya mulaifa mata dubeshi tace kayi
amfani da shwarar inmla ya kai abbana domin
ina gainin cewa itace zata fiye mana alheri:
koda gama fadin hakan mulaifa ta kama
hannun inmal taja shi suka fice daga cikin
tantin suka bar sarki maharaz a tsaye cikin
tsananin da muwada takaici
WANNAN SHINE ABINDA YAFARU A CAN
BAKIN KOGIN BAHAR SUFIYA BAYAN ANCI
GABADA FAFATA YAKKI TSAKANIN RUDUNAR
SARKI MAHARAZ DA RUNDUNAR SARKI
DUJALU A KARO NA BIYU
41
TASKARNOVELS.COM.NG
* * * * * AL:AMARIN Gimbiya Hursiya Kuwa;
lokacin da aljani burzaru ya nufi can birnin da
ira ta tabbatar da cewa an rabata Da sarki
kenan sai ta fashe da matsaininci kukana bakin
ciki: Bata gushe ba tana kukan hat aljni Barzaru
ya sauketa a tsakiyar gidan sarautar tasu
Koda bayi kunyangi barori da dakarun tsaro na
gidan suka ganta sai duk suka zube kasa a
gabnta suna kwasar gaisuwa ko kallomsu ba
tayi ba sai ta juya a fusace tashige izuwaa can
cikin gidan sarautar da sauri: duk sa adda ta
waigo bayanta sai ta ga aljani Barzaru nabiye da
ita: Al'amarin da yai matukar ba ta mamaki da
tsoro kenan. nan take ta gane cewa lallai sarki
ne ya umarci barzaru da ya sa ido akanta don
kada ta sulale ta koma can sansani yaki: Nan
fa Hursiya taji hankalinta ya dugunzuma ainun
kuma ta kudurce a ranta cewar takowanne hali
sai ta san yadda tayi ta subecewa barzaru
takoma can sansanin yaki sbda gwara itama ta
mutu a can da dai azo mata da labarin
mutuwar sarki tunda bata da kowa a duniya sai
shi. kai tsaye Gimbiya Hursiyya ta wuce izuwa
42
TASKARNOVELS.COM.NG
cikin turakarta. tana shiga ciki ta mai da kofa
tarufe bam da karfi cikin fishi sannan ta fada
kam gadonta ta kwanta ruf da ciki ta fashe da
sabon kuka: Shi kuwa aljani barzaru a kofar
turakar yaja ya tsaya kuma ya kame kamar
gunki yana muzurai ko yaushe idanunsa na
kallon gabas da yamma kudu da arewa don
hada gimbiya Hursiya ta Shamaceshi ta fice ba
tare da sani ba: su kuwa fadawan sarki dujalu
wadanda aka barwa jiran gari koda suka ji
cewar gimbiya Hursiya ta dawo daga sansanin
yaki ita kadai? Sai suka cika da tsananin
mamaki suka dugungumo gaba daynasu syka
zo ganin gimbiya. koda suka aika da manzo a
gareta bisa zuwansu sai ta aiko a gay musu
cewa baza ta gana dakowa ba sai gobe da safe
a fada: Al:amarin da yai matukar dugunzuma
hakalinsu kenan suka rasa abinda ke musu
dadi sabo sa su kawai so suke suji matsayin da
ake ciki a can sansanin yaki: Shin sarki Dujalu
yana nan a raye ko kuwa ya mutu? MASU IYA
MAGANA SUN CE IDAN KAGA KARE YANA
SHINSHINA TAKALMI TO SO YAKE ZAI DAUKA.
tunda gimbiya Hursiyya taji cewa yan majalisar
sarki sun kagu da su yi magana da ita sai jikinta
43
TASKARNOVELS.COM.NG
ya bata cewar so suke suci amanar sarki,
ma'ana idan suka ji sarki ya mutu sai su yi sauri
su nada wanda suke son ya gajeshi acikinsu
batare da sun bata sarautar bakamar yadda
yake aka ida: Koda aiyana hakan sai hankalin
Hursiya ya sake dugunzuma ainun domin ta
fahimci cewar lallai tana ciki hadari domin idan
ta fadawa yan majalisar gaskiya al amari cewar
bata san abinda ya faru a filin yakin ba tunda
bata gani da idanunta zasu zata karya take su
dauka cewa lallai itama da kyar ta tsira kuma
an kashe sarki da mukarrabansa: ama da
Hursiya ta tuna cewa ai tana tare da aljani
Barzaru babban jarumi kuma sadauki mai
watsa maza babbn hadimi sarki dujalu mai
amana sai hankalinta ya dan kwanta sbda ta
san cewa zai kareta daga dukkan wani mugun
abu amma kuma sai ta fara tunasnin hanyar da
zata bita koma can sansanin yakin domin
zamanta a can zai fiye mata kwnciyar hankali.
Kashe gari da safe bayan Gimbiya Hursiya ta
gama kintsawa tayi kalaci sai ta caba ado
sanna ta nufi fada fuskarta cike da annuri tana
takawa dai dai tamkar taron dawisu ta rinka
tafiya cikin izza da jin kamshi: da shigarta cikin
44
TASKARNOVELS.COM.NG
fadar sai ta iske gaba dayan yan majalisar a
zaune sun yi tsuru tsuru suna jira isowarta:
koda suka ga gimbiya a cikin fara ada nishadi
sai hankalinsu ya dugunzuma ainun suka fara
tunanin cewa lallai sarki dujalu ne yake samun
nasara acan filin yakin: Dama bayan tafiyar
sarki dujalu da rundunarsa ta yaki sai yan
majalisar suja yi taro na sirri a tsakaninsu inda
suka gaiyato wani amintaccen bokansu mai
suna IRMAS BINI KAIBUR suka umarceshi daya
yi musu bincike akan abinda zai faru a can
bakin kogin Bahar sufiya: Koda boka Irmas ya
dauko madubin tsafinsa ya shafeshi da hannun
hagu domin yaga abinsa zai faru sai nan take
madubin tsafin yayi bindiga ya farfashe:
Al:amarin da yai matukar razana boka irmas da
yan majalisar kenan suka firgita ainun: Har yan
majalisar sun yunkura zasu mike tsaye su fice
da gudu dga cikin dakin tsaro sai boka irmas ya
daka musu tsawa yace kowa ya zauna a inda
yake in bahaka ba kuwa babu wanda zai koma
gidansa a raye: Koda jin hakan sai kowa ya koa
inda yake ya zauna: boka irmas yai gyaran
murya sannan ya dubi gaba dayan yan
majalisar yace yaku shuganbanina kuyi sani
45
TASKARNOVELS.COM.NG
cewa babu wani matsafi a wannan nahiya mai
karfin sihiri dayakai na sarki dujalu sbda haka
ya boye duk abinda ke faruwa a cam bakin
tekun bahar sufiya ga dukkan wani mahaluki
dake cikin wannan nahiya: bisa wannan dalili
ne kuka ga madubin tsafina yai bindiga; yanzu
hanya daya ce zamu bi my iya ganewa idan
sarki dujalu yana samun nasara a filin yaki ko
baya samu: Nan gaba a lokacin da yakin ya fara
tsauri lallai akwai mutumin da zai dawo daga
can filin yakin wandas ya kasance makusanci
na sarki ya hau kan karagar sarki ya zauna: to
tabbas rudunarmu basu da saa kuma baza su
dawo ba a raye, idan kuwa yaki zama akan
karagr sarki to tabbas sarki dujalu zai dawo
gida a raye: Kofa gimbiya Hursiya taga yan
majalissar sun kura mata idanu sai hankalinta
ya dugunzuma ta dada tabbatar da cewa lalai
akwai wani mugun abu da ke ransu. Awannan
Lokaci aljani barzaru na biye da ita yana take
mata bayan don tabbatar da tsaro amma babu
mai ganinsa face gimbiy Harsiya kadai, har
Gimbiya hursiya ta nufi inda karagar sarki take
da nufin ta zauna sai aljani barzaru yi sauri ta
sha gabanta yayi mata nuni da jada taje ta
46
TASKARNOVELS.COM.NG
zauna akan karagar. Batare da gardamar komai
ba kuwa ta sauya wuri taje ta zauna akan
kujerar da ta saba zama ko da yaushe a fadar
kamar kullum: koda ganin haka sai jikin yan
majalisar ya yi sanyi gaba dayansu sai murna
takoma
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 18