Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Hubby wane irin alƙaƙai? To gaskiya kayi ƙoƙarin rabuwa dashi bye i love u ina jiranka fa." ta faɗa tana dariya ta tinƙe kiran... Mamu ce ta shigo tana cewa"Ke Amrah maza kira Baby naji inda take kinsan halinta sarai taga damar ta fito cikin hadarin nan , kirata muji tana gidan su Basma ko ta tafi gidan Baffa nah , tin kafin umpah ya farga." Amrah tace"To Mamu bari muji wlh nima se yanzu hankali na ya bado." ta faɗa tana kiran number Mubina a kashe, tace "Mamu wlh a kashe wayar bari na kira Basma naji." ta faɗa tana shiga gun ma'adanan lumbobi, ta fito da number Basma, tai dailing. Lkc Basma ta farka taga ji da neman Mubina bata nan ta iske momy ɗaki nan ma tace bata nan maybe ta tafi gida ba tasan halinta ba...!! ta kirata da layin umpah ba'a, ɗauka, shine ta shiga tayi wanka idan ruwan ya ɗage ta tafi gidan Baffa dan tasan tana can. Tana bedroom ɗinta tana cikin toilet bayan ta gama wanka tana alwalla, taji ringing ɗin wayarta. Ta fitowa ganin Amrah ce yasa ta ɗauka tai picking ta kara a kunnenta tace"Aunty ina yini Mubina gida ta dawo ko ta tafi gidan Baffa??" Amrah tace"A'A bata zoba to bari na kirashi muji." ta faɗa tana katse kiran... tai dailing ɗin number Baffa. Wanda lokacin ya fito yana sauri zai shiga masallaci, tsohine ɗan kimanin shekaru 65 me tsukeken jiki. Se sauri yake ya shiga masallaci, yaji rurin waya yayi saurin cirota daga aljihun yay picking, ya kara a kunnensa tare da sallama. Amrah tace"ɗan tsoho Amrah ce Mubina tazo nan gidan ka?" Baffa inusa yace"Ah matar ya gida ya ruwa? A'A amaryata bata zo ba fitowa tayi ne? bata iso ba ina ga amma bari na fito masallaci zan shiga sallah har antayar." ya faɗa yana katse kiran. Amrah tace" Mamu mun shige su Mubina bata gidan su Basma bata gidan Baffa..." Mamu ta buɗe baki zatayi magana taga Umpah a tsaye a kansu ya kafe su da idanunsa ransa a mugun ɓace. Amrah tace "Umpah Baby ta kira ka ne?" bai yi masu magana ba ya juya ya fice dan masallaci zai shiga. Mamu tace taso Amrah yi maza kiyi sallah ki fito nima bari nayi sallah." ta faɗa tana ficewa daga ɗakin. Amrah ta miƙe ta sauko daga saman gadan ta shiga bathroom.......

*Labarin nan na kudi ne kan farashi me sauƙi, book 1&2 zaku same shi akan 200N kacal, ga mutanan mu na Niger zaku biya 400F, ba tsauwalawa hakan ta faru ne saboda masoyana na asali, karfa ku sake ayi baku wannna salon na daban ne, wannan karon bana cewa kome kune zaku faɗa insha Allahu, duk me bukatar siya zaku tuntuɓeni ta wannan*
*Lambobin👉🏻+22796515805/ +22792589446, karku manta nera 200 kacal zaku karanta book 1&2 ,Real ladingo na maraba da masoyanta har kullum💃🏻💃🏻💃🏻*

*💖😭KAMAL NE😭💖*

*Book 1*



NA

*Real ladingo*
*Sweet Baby💋*

Ƴar Mutan Niger🤙🏻



*Bismillahir Rahamanir Raheem*



*Free Page*


🅿️1️⃣4️⃣

Kamal Amrah na tsinke kiran ya saki lallausan murmushi, ya shiga danna horn tin karfi, se ga megadi ya bude masa tamƙameman get ɗin gidan, ya shige ciki.
Nan farfajiyar gidan yay parking ya juya ya kalli Mubina wacce take sheme a sume, kayan jikinta a jiƙe jagab sun dameta, tsaki yaja ya ɗauke idanunsa daga kallonta ya fito ya kulle motar ya nufi cikin gidan.
Parlon ya shigo shiru ba kowa se Tv, saman bene ya haura cikin saurinsa, yana hawa ya zaro key daga aljihun sa ya saka jikin kofar ya murza ya buɗe kofar yasa kai ciki, wani daddaɗan kamshi ne yake tashi cikin ɗakin kome fes a gyara, kome na ɗakin adon Maroon coulor ne, wani lumtsumeman carpet ne malale a tsakiyar katon filin ɗakin se wani makeken gado da tafkekiyar wardrobe da ta kusa cin rabin bangon ɗakin, da wasu manyan kujeru. Cikin sauri ya rage kayan jikinsa, daga shi se boxer ya shiga bathroom. Shower ya kunna kome agagguce yake, yayi wanka ya ɗaura alwalla faffaɗan kirjinsa mai yalwar ni'imar gashi se ɗigar da ruwa yake, ya daura towel ya fito. Wajan shirin ma a gaggau ce ya shirya ya murza maiyukan sa masu sanyin daɗin kamshi, ya gyara kwantacciyar sumar kansa baƙa lut, se sheki take tana walkiya sansanyan kamshi ke tashi daga cikin jikinsa. Wardrobe ɗinsa ya nufa ya buɗe wace take shaƙe da launin kaya iri iri, wata Jallabiya ruwan toka ya ciro sabuwa dalla a leda ya saka.
Ya dawo gaban dreesing mirror ya fesa sansanyan turansa, ya fice da gaggawa dan an fara sallah. Nan parlo yaga hijab saman kujera a ajiye, ya ɗauka ya fice, nan motar ya bude ya nasa hijab ɗin ya fice Masallacin. Bayan ya fito daga masallaci ya tsinkayo umpah da Abbu sabida gaggawar da yake bai masu magana ba, kuma suma basu ganshi ba, yay wuff ya shige ciki. Yana shiga ya shiga ciki bai jima ba ya fito, ya shige mota yay mata key yana ma megadi horn, ya wangame masa get ya sulala motar waje. Har yanzu su Abbun suna tsaye amman yanzu ƙoƙarin shiga mota suke wacce Haladu ya fito da ita, Kamal ya girgiza kai ya ba motar sa wuta ya fice a guje, yaga suna nunushi, murmushi yayi yana driving ɗinsa cikin nutsuwa, ya nufi hospita nan Katsina hospital kasancewar itace cikin unguwar ba nisa sosai.
Yana zuwa bayan ya shiga ciki yay parking ya ɗauki wayar sa ya kira Dr Munnir, cikin sa'a bugo ɗaya ya ɗaga, Kamal yace"Dr ykk? pls ina son room guda nazo da wata yarinya zan dubata da kaina , ta ɗan sami accident ne."Dr Munnir yace"Ok yallaɓai ba damuwa se ka shigo bari na fito na tare ka." Kamal yace"ok tnx" ya faɗa yana tsinke kiran, ya saka wayar cikin aljihunsa ya buɗe motar ya fito, ya zagaya set ɗin baya ya buɗe ya shiga ya zauna ya sanya tattausan hannayensa ya ɗagota ya tallabota jikinsa ya sanya mata hijab ɗin, ya kwantar da ita ya fito ya rankwafo ya cicciɓeta ya rungumeta ya shiga ciki. Nan A reception ya isko Dr Munnir tsaye, ya tare sa cikin gaggawa yace"Barka yallaɓai bismillah." Kamal ya bisa a bya Dr na gaba suka haura can sama. Wani hadadɗan room me gado ɗaya se fridge se Tv manne a bango, akwai kome a ciki kayan aiki na duba marasa lafiya. Suna shiga Dr ya kunna Ac, Kamal ya nufi gadan ya kwantar da ita yana ƙoƙarin jona mata wata na'ura. Dr munnir yace"Allah bada sa'ar aiki bara na wuce zan shiga tiyata ne." ya faɗa yana wuce wa. Kamal yace "Ok tnx." ya faɗa yana cire mata hajabin jikinta ya jona mata na'uran, nan ya fara ƙoƙarin ceto ranta yana bata temakon gaggawa.

Can gidan su Mubina bayan Amrah da Mamu sun gama sallah, Amrah ta shirya ta sauko ƙasa, lokacin Mamu nata sintiri a tsakiyar parlo da waya a hannunta, se kai komo take.
Amrah ta iso dab da ita ta kama hannayenta tace"Mamu to ta ina zamu fara nemanta ne? Tinda ba mu san inda taje ba ita da bata yawo , nafi zargin ruwane ya tare ta a hanya bata isa can gidan Baffa ba..." Mamu tace " Yanzu ma dashi muka gama waya bata je ba Basma ma na can ta tisa su gaba tana kuka wai yanzu zasu fita neman ta , ina yaga kwarin yawo yana can ya tashi hankalin sa se faɗa yake min , ya na barta ta fita ana ruwa." Amrah tace "bari na naje gidansu Basma ko dai tana uwar ɗaka tana bacci basu saniba..."Mamu tace"Lubah ma yanzu ta kirani bata can wlh yarinyar nan bata ji inda umpah ya yarda ai mata aure kurum ta ƙarasa karatunta a ɗakin mijinta , wlh bana son rashin jin Mubina sam bana son wani abu ya sameta , amman nasan umpah bazai yarda ya aurar da ita ba..."Umpah ne ko ya katse mata hira yana shigowa yace"Wlh Nusaiba ki fita a idanuna bazan aurar da itaba!! Nawa take? yarinyar , ga katuwa nan a gabanki amman ƴar mintsilar yarinya kika sama idanu , dudu yanzu take 20 year amma sbd takura gata kamar yar 14 year a tsunbure , ina dalili se ta kammala karatunta na cika mata burinta , har wani yawo take ina take zuwa? Yanzu ma laifinki ne kina kallon hadari kika barta ta fita , ina kiran wayar yanzu tana ringing aka ki ɗagawa daga baya aka kashe , meyasa da zata fita baku faɗa min ba? Ai cewa kika yi nan gidan su Basma ne tsallaken titi , amma bata can na kira Isma'il , mun fita mubi hanya ni da Abbu ko ma dace ban amince ku fita ba kuka wani haɗe kai hammm..." ya faɗa yana ficewa a parlon.
Mamu ta saki hannun Amrah ta zauna dabas, tace"Ya Allah kasa duk inda Mubina take tana lfy kuma cikin hannun nagari Sbd Allah mace shekaru 20 a ce wai yarinya , Sun daure mata gindi shida Ablah se taɓara take ." Amrah tace"Amin Mamu insha Allah tana lfy." ta faɗa tana zama. Wayarta ta ɗauki ringing, ganin sunan *my brother* yasa tai picking ɗin call ta manna a kunne haɗe da sallama, tace "yayana barka da yamma." Kabeer daga can yay murmushi yace "Amrah ya gida fatan anyi sallah juma'ah lfy?" Amrah tace lfy lau brother ina missing ɗinka yaushe zaka zo ne?"Kabeer yace na kusa zauwa insha Allah , ina Baby ne?" Amrah tace"Wlh yaya Kabeer itace ake nema daga gidan su Basma ta fita ba'a san inda tayi ba..." Kabeer ya katseta cewar"kuke zaune gida ina umpah da Mamu ɗin?" Amrah taba Mamu wayar, ta amsa nan suka fara magana tana faɗa masa kome dake faruwa dai...

Umpah ko lkcn da ya fito har yasa Haladu ya fito da mota, nan kofar get inda Abbu yake tsaye, shine Kamal ya gansu zasu shiga mota za'a neman Mubina. Basma kuwa bayan tayi sallah la'asar ta gama ta shirya direba ya kaita gidan Baffa, lkcn Baffa inusa hankalin sa a tashe Mubina bata iso ba, ya kira Mamu tace bata gida, se ga Basma tazo neman ta ba tanan, nan ta zauna ta girka kuka inna da Baffa suna lallashinta shine ya kira Mamu yana bam bamin faɗa. nan inna da Basma da Baffa ɗin suka. shiga mota ɗireban su Basma na yawo dasu suna bin hanya wai ko sa ganta irin yanda su Umpah da Abbu suke yi...

Kamal se da ya kwashe 40 minutes cur yana famar ceton ranta kafin take farfadowa. Motsi ta fara tana zabura tana fizge-gizge, idanunta a rufe.
Ajiyar zuciya Kamal ya sauke ganin ashe duk sumar nan da tayi ba wani jimuwa tayi ba, tsabar farga ba ne da rikita gabanta da ya yanke ya fadi ta suma, se buguwar goshinta shiko bata jimu ba se ɗan kumburin kawai.
Na'uran ya cire mata ganin tana fizge-fizge ya rankwafa ya riƙeta, amman bata ɗaina ba, zama yayi ya riƙeta gam ya rungumota jikinsa ya matseta gam kirjinsa, ya sanya hannayensa saman lallausan gashin kanta ya tattara waje ɗaya, sbd yadda ya baje kan fuskarta yana ƙoƙarin daure mata. Mubina kuwa sam bata haiyacinta, jinta saman wani faffaɗan kirji me fitar da wani irin ni'imataccen kamshi me sanya kasala da kuma nutsuwa, sai taji tamkar mafarki se ta kara shigewa cikin jikinsa tayi luf kirjinsa, yana ƙoƙarin ɗaure mata gashin ta saƙalo hannayenta wuyansa, tana wani irin sauke numfashi haɗe da nishi ta maƙaleshi gam, fuskarta dab da tashi har tsinin hancin su na gugar juna, yayin da lallausan pink lips ɗinta yake gugar lips ɗinsa, yayin da numfashin su ya haɗe guri ɗaya Mubina ta kara manne shi tana sauke ajiyar zuciya da sauri-sauri, suna shaƙar hucin junan su, wanda sansanyan kamshin jikin Mubina ya haɗe da daddaɗan kamshin turaren Kamal ya bada wani irin kamshin dadi me ratsa zukata, duk jimawar da turaran Mubina yay a jikinta da kuma ruwan da ya taɓata amma tamkar yanzu ta fesa saboda baya fita ta sauki, yana haɗewa da na Kamal se ya bada wani irin launin kamshin dadi.
Kamal yay saurin janye kansan yana jan tsaki, yana ƙoƙarin cireta jikinsa ta saki wani ɗan ƙara ta maƙalƙale shi ta tura kanta cikin kirjinsa tana sauke wani irin zazzafan numfashi ta tura hannunta cikin suma kansa tana nishi, ta manne shi sosai kamar zata shige cikin sa, tana sauke masa wani irin huci dab da kunnen sa yana jin yadda zuciyarta ke wani irin mahaukacin bugawa da karfin gaske, ga tudun kirjinta na gugursa sosai yake jin nipples ɗinta suna takura shi...
Wani yammmmm Kamal yaji, ga tsikar jikinsa na tashi sbd yadda tabi ta kanainaye shi, tana sauke masa numfashi dab da kunnensa.
A hankali Kamal ya kusanci fuskar Mubina har suna shaƙar numfashin juna a tare, Hannunsa ya dora saman ƙugunta ya riƙeta sosai, wanda yasa ka Mubina zabura ta kara shigewa cikin jikinsa har lips ɗinta na gugar nashi yay saurin kauda kansa, Mubina can ciki tai magana cikin zallar shagwaɓa, can ƙasan maƙoshi sam Kamal bai jiba, me tace yaga bakinta na motsawa. Bakinsa ya kai dab da kunneta yay magana "Ke!! Uwar jaraba kin ko san wanda kike tare dashi?" ya faɗa a cikin wani irin cool voice.
Wanda ya kara sakata cikin wani irin yanayi feelings take ji sosai, ta ƙara manne masa a jikinsa tana hawaye tana fitar wani irin numfashi me zafin gaske, ta nitsa kanta cikin kirjinsa tana nishi se ƙamƙameshi take.
Kamal ya zaro idanu waje ganin sam fa bata haiyacinta, ya fara ƙoƙarin janyeta daga jikinsa ya ɗago da kanta ya tallabo fuskarta ya zuba mata tsumammun idanunsa, yaga hawaye na kwaranya daga fuskarta, tayi saurin kifa fuskarta saman tashi tana sakin nishi ta zagaye ƙugunsa da hannayenta, zuciyarta na bugawa da karfi. Kamal ya dora hannunsa saman goshinta yana murza mata sauran kumburin yana bajewa, ƙara rungume shi tayi tana nishi a shagwaɓe tace"Aushhhh zafi bana so."ta karasa maganar cikin irin wani yanayi na sangarta ta ƙamƙameshi gam.
Kamal ganin yana kara shiga hakkinta kuma ba wani abu zai mata ba na rage zafi yasa ya daka mata tsawa"Ke!! Dallah can ɗagani uwar jaraba." ya faɗa yana hankade ta daga jikinsa, ta faɗa saman gado ya miƙe tsaye.
A mugun tsorace!! Da kuma gigiceta da mamakin abinda ke faruwa na ɗago da kaina na ganni saman gadon asibita a kusa da gurgu... Cikin rikita na fara kallon jikina na ɗago na kalleshi raina a ɓace amman banyi mgn ba sanin halinsa da kuma tuna na bugi mota ina tukin adedeta, tabbas suma nayi da sauri na sauko daga saman gadon na shiga neman mayafi na ban gani ba na duba wayata ban ganiba, na juyo na riƙe ƙuguna cike da rashin kunya, na kalleshi ya koma gefe ya haɗe hannayensa a kirjinsa ya zubamin kwartayan idanun sa fuskarsa babu alamar wasa, yayi kucin-kicin, nace"Malam ina mayafina da wayata a bani nayi gaba , kuma ta Allah ba taka ba meye ka kawoni kamin? Kenan kaine ka bugeni da mota ka sace min waya to bani abuna , kuma ka sani wlh tsoron da ka bani a mota se na ɗauki fansa , bani wayata nayi gaba." na faɗa ina girgiza ƙuguna ina murguda baki. Jin yaki magana na sake cewa"Kangiwa da kai nake wlh idan..."muryasa ta katseni ta hanyar cewa, "Ki ɗauki wannan hijabin ki saka ki rufe jikinki nan bakiyi kasuwa ba bana sha'awa a kai kasuwa , yau dani ɗan iskane da kin lalatani kin koyamin iskanci , se Allah ya sa ba haka nake ba ke kam kin shiga a uku jarabar ki tayi yawa shiyasa kike saka matsatsun kaya kina yawo da masu adedeta se akaci sa'a shima baya son busasar mace irinki , bai matsaba shine kika bugi motata kikayi suman karya dan na kawoki hospital na rage maki zafi ko? To bana yi me zan ji a ƙashi zallah , Oya sa hijab muje ki nunamin gidan ku na a jiyeki sbd nasan ko na barki ba gida zaki ba yawon ta zubar zaki."Ya karasa maganar yana ɗagamin gira tare da sakar min lallausan murmushi, ya cusa hannunsa ɗaya cikin sumar kansa yana shafawa.
Wani irin baƙin cikine da takai ci tare da bacin rai suka ziyarci zuciyata, jikina har tsuma yake na waiga naga meye a kusa da zan ɗauka na buga masa, wani ɗan ƙaramin glass table na gani na nufi gunsa da gudu na ɗauka ina cewa"Allah se na nuna maka nafika rashin mutunci sai na rutsa maka kai" na faɗa ina nufar kansa a guje.
Kamal ya kauce yana dariya yace"Ashe harda hauka ana taɓawa ok wlh kina buga min zan turmusheki anan na baki yawu kisha , nasan shi kike so." ban saurere shi ba na karaso kusa dashi na jafo masa glass ɗin da karfi, ya goce bai same shi ba table ɗin ya bigi bango ya tarwatse wani glass yayo kaina sam ban luraba seda naji ya fizgoni jikinsa munyi wajan toilet, ya haɗani da kofa ya danna min kirjinsa ya matseni daket nake numfashi.
Ya dago haɓata cikin raunaniyar murya yace"bakida hankali da glass ɗin ya sameki ba ƙaramin rauni zaki jiba , masifiya kawai uwar fitinar tsiya busassa kawai jiki ba tsoka." ya faɗa yana hankaɗeni daga jikinsa nayi tagal-tagal zan faɗi ƙasa, nayi saurin riƙe kofar toilet, cikin masifa nace "Eh ina ruwan ka in mutu ma mana mugu a zalumi barawon phone wlh bazan barka ba..." shiru nayi da bakina ganin ya juyo ya nufoni, na ƙame cike da tsoro ina ƙoƙarin ja baya, amman har ya iso ya damko kafaɗata ya miƙar dani ya sakeni ya dora hannunsa duka biyu a bango ya rufeni ruf.
Ƙoƙarin bin ta ƙasansa nake ya kamo gashin kaina na saki kara ina dukan sa, ya riƙe hannuna ya ɗago haɓata yana kara kusanto fuskarsa dab da tawa, muna shagar hucin juna, nayi saurin kauda kaina ina murguda baki nace"Sakeni ni ba ƴar iska bace wlh baka isa ka iskan tani ba , da wani bakinka me wari sakeni dallah malam..." Tafin hannunsa ya dora saman bakina ya rufe min, na fara ƙoƙarin cizon sa ina kiciniyar yadda zan kwaci kaina, duk da ba wani riƙeni yay ba rumface kawai yay min da kirjinsa babu inda zan bi na fita, se haɓata da ya riƙe ya kuma rufemin baki yana ƙara kusanto fuskata.
Cikin ɗaga murya yace"wato dai kina son nasha bakin ki na dura miki sweet yawuna kisha sbd yana miki sugar sosai ko?" ya faɗa yana ƙoƙarin haɗe fuskarmu, idanu na zaro ina kirgiza kaina alamu A'A amman bai fasa kusanto fuskata ba nima ban fasa ƙoƙarin kwacewa ba, amman se da ya haɗe ya wani zubamin fitinannun idanunsa yana goga lips ɗinsa saman nawa, naji wata lema-lema ashe yawun sa ne ya zaro harshe ya fara gogamun saman lips ɗina, dukansa na fara a saman kirjinsa ina hawaye na jimƙe bakina gam ta yadda ƙazamin yawun sa bazai shiga bakina ba, ina dukan sa. Yay saurin janye fuskarsa a tawa ya matsa can gefe yana kyalkyala dariya yace"Jarababbiya wlh bazan baki ba haukan karya kike kina so wlh." ya faɗa yana juyawa ya nufi saman gadan ya ɗauko hijab.
Wani irin haushi yasa na cire takalmin ƙafata gudu na bishi da gudu nayi kansa ina kecewa da kukan takai ci ina cewa"Wlh ko maza sun ƙare baka isa ka sakani naji wani abu ba kai a suwa? Wlh kayi kaɗan baka abinda nake so a tare dakai kamin kaɗan wlh..."Wata uwar tsawa!! Ya bugamin yana cewa"Ke!! Wlh kika kuskura kika karaso guna se kinyi nadama , zan cire miki iskancin dake damunki wlh zan baki mamaki rashin kunyarki ta isheni daga yanzu nama kina alkawalin duk abinda zai sameki bazan sake shiga zabgarki ba." cak na tsaya da takalmin a hannuna ina shasheƙar kukana na kauda kaina daga kallonsa. Banji isowarsa ba se da naji yana sakamin hijab, bayan ya saka min ya kama hannuna me takalmin ya zare takalmin ya sunkuya ya kama ƙafata nayi baya zan faɗi yay saurin riƙoni ya kama hannuna guda ya dora saman ƙafaɗarsa bai min magana ba, haka nima banyi magana ba kuma ban kalleshi ba, kuma ban riƙe kafadar ba. Ganin ina tagal-tagal yasa ya miƙe tsaye sai ji nayi ya ɗaukeni cak kamar ƴar tsana ya nufi saman gado dani ya ajiyeni ya kama ƙafata ya saka min takalmin, baiyi magana ba ya sauke ni ya kama hannuna muka fara tafiya na fizge hannuna ya juyo a fusace ya ɗaukeni da gigitaccen mari ya fizgoni jikinsa yace"Wlh idan kika yi wasa zan baki mamaki yanzu nama kaina alkawalin kaiki har gidan ku idan kika ki nunamin kuma zan kaiki gidana ne , na turmusheki na baki abar da kike so oya muje ki nuna min gidan ku." yana faɗin haka ya janyeni daga jikinsa ya kama hannuna ya damƙe cikin nashi wani irin gumi na ratsa tafukan hannuwanmu. Kukana na haɗiye nace"Allah ya isana ban yafe ba insha Allah se ka gani a kwaryar cin tuwonka , mugun azalumi..." yanda ya juyo ne yasa na haɗiye maganar na kauda kaina nayi saurin ɓoyewa bayansa. Kai ya girgiza ya janyoni na dawo gaban sa, ya buɗe kofar yana riƙe da hannuna muka fito.
Muna fita na cika da mamaki ganin hospital ɗinmu ne amman nayi shiru.
Office ɗin Dr Munnir muka shiga, yana ta rubuce-rubuce cikin takardu. Yana ganina yace"Ah Baby auta wai daman kece aka kawo? wlh ban lura dake ba sam" ya faɗa yana miƙewa yace da gurgu"yallaɓai kaine ka bugeta to a ɗiyar me hospital ɗince , ɗiyar Abdulrahim Kabeer algèrie ce , amman ƴan gidan su basu da labari ko?"."Kamal cike da mamaki yace "No wanda kake faɗa Abokin Abbu ne kuma nasan yaransa masu hankali ne da tarbiyya da nutsuwa , basa yawon ta zubar, kai ba wannan ba ni zan wuce kayi lissafin duk abinda ya kama ka kirana bata buƙatar magani bata jimu ba, se anjima." ya faɗa yana jaye da hannuna, cikin tsiwa nace" se ka hana ya zama ubana kuji shi kai to shiɗin ubana ne , nayi yawon ta zubar ɗin yawon dandi nake karewar ta zubar karshen rashin tarbiyya kuwa tsirara nake yawo kaji malam , da banyi niyar nuna ma gidan muba amman yanzu se na nunama... " Na faɗa ina mintsinin hannunsa da yake cikin nawa, bai koyi gezoba ya kaɗa kafaɗarsa yace" Banda lokacin ki." ya faɗa yana jana muka fito. Dr Munnir ya koma ya zaun yana dariya yaci gaba da rubuce rubucen sa. Muna zuwa gun motarsa na gane da itace ya tunzurani ɗazu kuma itace na bugi adedeta da ita.
Buɗewa yay ya tunkuɗani gaban motar se da na dan bugu nace "Allah ya isa mugu kawai." bai ko kalleni ba ya zagaya ya shiga motar gun zaman direba yay mata key ya fizgeta da karfi ya nufi bakin get, aka wangale masa get, ya fice a guje. Tinda muka fito bai kalleni ba driving ɗinsa yake a cikin nutsuwa, nima nai banza dashi na kame kaina. Can naji sautin muryasa ƙasa-ƙasa yace"Gantalala ina ne wajanku?" Ban kula shiba na kauda kaina ina kallon titi.
Ya sake cewa" Ok bazaki faɗa ba to bari na kaiki gidana muyi kwanan dadiro se kimin tausa da wannan busassan hannun naki..." cikin ɓacin rai na juyo na fara dukansa na wawuri kunnensa da cizo. Da karfi ya taka burki yana cewa"Sakeni ko kiga yadda zan miki duran yawu nasan shine kike so kin kasa dangana jarababbiya..." sakinsa nayi ina matsar kwalla na haɗa kaina da guiwa ina sauke numfashi da karfin gaske. Da sauri na ɗago nace masa"Ali ɗan tsoho zaka kaini gidan ɗan Algerie." na faɗa ina goge kwalla idanuna na kalli titi.
Kamal kuwa se yanzu yake kallon tsantsar kamarta da Umpah da wannan yayar tata to amma ya akayi bai taɓa ganinta ba? Shi se yanzu ma hanklin sa ya bada da sunan da take aiki dashi a makaranta, tabbas ɗiyarsa ce... Kallonta yayi ya taɓe baki yace" Ashe

Please Login or Register in order to submit comment