Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tausayi da kuma temako da barkwanci, bayada ɗaurin fuska kowa nashi ne banda maras kunya, kuma mace kallo ɗaya zai maki ya karanci yanayin ki, Kamal ya tsani mace maras kamun kai sam, tin shigarsa Maryam abacha da yaga take taken yawai cin yan matan ya kame kansa da girmansa barin iyamu da tin kallo ɗaya da ya mata ya karanceta, iyamu dai ita da leeza ƴan kaduna ne karatu ne ya kawosu, suna mataki na uku amma basa maida hankali. Mubina tinda take masa iskanci bai taɓa kamata ba se ranar nan a class ya kuma tabbtar ita ɗin tantiriya ce, shiko Kamal baya shiri da irin su se dai shi yasan maganinta duba da irin halittar ta ya karanceta bata hakuri tanada muguwar sha'awa, sha'awarta a kusa take, da gangan yake azabtar da ita ta wannan fannin dan ta gyara halinta, Sbd yaga a kwaita kyankyami, yana da tabbacin wuyar daya bata bazata sake shiga rayuwarsa ba... Sageer Ibrahim haifafan maradi ne hausawane nan zaria2 Sunada kudi dai dai misali gidan su kawai ya isa ka san akwai arziki dai dai misali, su biyar ne gun iyayansu mata uku maza biyu Sageer ne babba se Lukuman se bushara Rashida se auta Najwa. Sun sami tarbiya gun iyayansu me kyau da karatu me kyau tin secondary school suke tare da Kamal, Kamal bashida aboki sama da Sageer ko karatun ma tare suka tafi tunis seda Sager ya rigashi dawowo shi medicine ne kadai ya karanta, Sageer kyakyawane fari ne maras jiki yana da kirki sosai akwaishi tausayin mata sosai gashi da wasa da dariya, kusan halaiyarsu ɗaya da Kamal. Abotarsu har ta shafi iyayansu sosai ake zumunci koda yaushe suna tare ko makaranta ko company idan Sageer bashida lecturer ko baya zuwa hospital, sun shaku sosai basa boyema juna sirrin junansu, dan Kamal tin ranar da suka fara soyayya da Amrah ya faɗa ma Sageer kuma ya taya shi murna shima ya faɗa masa Mubina yake so ba tin yauba amma yake jin Sageer baiyi dace da zaɓarwa ƴaƴansa uwa ta gari ba, nan yake faɗama Sageer cewar cutie angel ko ba musulma bace wlh yana sonta zai aureta tinda Addininsa bai hana ba dan ya lura bata so ta faɗa masa gaskiya ne ya gujeta... Sageer shide dariya Kamal yake bashi son abinda baka taɓa ganiba, kuma cikin ƙanƙanin lkc. To hakan ce take faruwa, Kamal akan Angel ɗinsa dan yana son mace mai tarbiyya da kamun kai, ko ya take. Itama Amrah tana mugun son Kamal duk bata san wane iri bane amma tayi alkawali ko ya yake idan sun hadu zata soshi, Wannan shine cika ken tarihin Kamal gobe zamu koma Chapter........

*Labarin nan na kudi ne kan farashi me sauƙi, book 1&2 zaku same shi akan 200N kacal, ga mutanan mu na Niger zaku biya 400F, ba tsauwalawa hakan ta faru ne saboda masoyana na asali, karfa ku sake ayi baku wannna salon na daban ne, wannan karon bana cewa kome kune zaku faɗa insha Allahu, duk me bukatar siya zaku tuntuɓeni ta wannan*
*Lambobin👉🏻+22796515805/ +22792589446, karku manta nera 200 kacal zaku karanta book 1&2 ,Real ladingo na maraba da masoyanta har kullum💃🏻💃🏻💃🏻*

*💖😭KAMAL NE😭💖*

*Book 1*



NA

*Real ladingo*
*Sweet Baby💋*

Ƴar Mutan Niger🤙🏻



*Bismillahir Rahamanir Raheem*



*Free Page*


🅿️1️⃣1️⃣

....Isma'il Zakari gobeer shine mahaifin Basma, haifafan maradi ne goburawa ne gaba da baya, yana da kudi sosai kasancewar bamaraɗe, yawai cin mutanan maradi kasuwanci kawai suke karanta, to masha Allah shima yana da kudi sosai, yana da matarsa Lubah auran soyayya sukayi, Lubabatu kyakyawace fara yaranta duk kyanta suke ɗauka duk da Isma'il nada kyau dede misali, Basma su hudu ne wajan iyayansu babbar yayarsu tana kano da aure me suna Abida se Anwar se Basma se Sakina auta, Basma kyakyawace ba laifi farace amman ba can ba dan ko rabin farin Mubina batada, kasancewar Mubina sak balarabiya ce, Basma doguwace me dan jiki ba can ba dai tana da hanci da idanu masu kyau da diri, gaskiya Basma ma macace ta hadu ba laifi, sun hadu ne da Mubina shigarta university maryam Abacha ɗin, suka ƙulla kawance itama Basma itama tana matakin farko ne suna shirin shiga mataki na biyu. Mubina bata da kawa se Basma har gwara Basma nada kawaye tinda ita haifarfiyar gari ce, halin su ya dan sha banban da Mubina, Basma bata da surutu bata ɗaukar magana ga tsoro kullum idan Mubina tayi ɗaukar magana a kanta yake ƙarewa, Basma ga saurin kuka gata da rauni, se de itama maza basa gabanta karatun tasa gaba...

Suna shiga umpah yana fitowa cikin shirin zuwa juma'a, cikin wata dakekiyar shadda fara tas ɗinkin gari da janfa, se haskawa yake yana zuba kamshi, kallo ɗaya zaka masa kasan shiɗin balarabe ne.
Waya manne a kunnensa yana magana cikin harshen larabci yana murmushi, ganin motar su Mubina ta shigo ya nufi gun motar, cikin harshen larabci yana cewa"Ablah ga Baby sun taso bari na bata wayar kusha hira kafin a taso daga masallaci kunsha hira." ya faɗa yana dimfara motar su Mubina wacce Haladu yake ƙoƙarin parking. Mubina ta janye jikinta daga jikin Basma ta ɗago da kanta ta hango umpah na tafe yana waya, ai ko parking Haladu bai gama ba ta ɓalle murfin motar ta fito ta cire takalmin ƙafarta, ta cire mayafinta tayi jifa dashi, ta ɓare baki ta fashe da uban kuka ta runtuma da gudu tayi wajan umpah tana kururuwa tana cewa" Wayyo umpah malam ya kashe maka ƴa ya tozar tani ya bani guba nasha wada nasan ta fara aiki a jikina lokaci kaɗan zata kasheni..." ta faɗa tana saki wani uban ihuuuu me haɗe da kururuwa.!! Umpah saboda tsabar kaduwa wayar ya saki ya nufi gun Mubina da gudu yana cewa" uban waye shiɗin? waye ubansa a garin maradi da har zai nakasa min yarinya?" Mubina tana isowa ta fada jikin umpah tana kururuwa! umpah ya rungumeta yana faɗin" *Lailaha ilallahu muhammdun rasulillah sallalahu alaihi wassalam!*" Baby me nake gani kumatunki sun kumburo fuskarki tayi ja haka? Uban waye shiɗin? wanda ya mareki? Wlh yanzu kotu ce zata raba mu dashi." ya faɗa yana bubbuɗe hanci yana kara duba ɗiyar tasa. Mubina kuwa jin haka yasa ta kara ɓarkewa da kuka tace" Wayyo cikina bayana kaina wayyo , umpah bana gani da kyau mari sha13 yamin ya duramin ruwan toilet yace idan bam shaba zai kasheni wai ya tsaneni." ta faɗa tana kururuwa.! Su Basma ne da Haladu suka iso gurin Basma tana hawaye tausayin jin Kamal mari 13 yama Mubina ya bata ruwan toilet tasha...
Gabaki ɗaya Ma'aikatan gidan sukayo caaa. Hankalin umpah ya tashi matuƙa se lailaya ashar yake, ya tattare hannun rigar sa ya cicciɓeta ya rungumeta ya nufi mota yana cewa "Haladu maza buɗe mota muje hospital a dubata kafin na dawo daga masallaci muja shari'a , da wanda ya nemi hallaka min yarinya..." Mubina jin umpah ɗinta zaije masallacin juma'ah yasa ta tsayar da kukan tace" umpah zan jure kaje masallacin ka dawo daga can kayi Addu'ar neman nasara idan mun tsaya kotu gaban alkali." Haladu da Basma suka zaro idanu tare da sauran ma'aikatan gidan cike da mamaki. Umpah yace" Muje hospital Auta kar gubar dauɗar da ya baki ta fara tasiri a cikin ki." ya faɗa yana nufar mota.
Mubina ta saki kukan shagwaɓa tace"umpah ciwon ya lafa nide kaje masallaci ka dawo se muje hospital daga can mu wuce kotu kawai." sanin halin ƴarsa yasa ya sauketa ya kama hannunta suka nufi ciki, se lokacin yaga Basma tana shara kwalla ya bata hannunsa ɗaya yace "zo dota kema ya zalum ceki waye shiɗin? wlh se ya kwana a hannun yan sanda." Basma ta kama hannun umpah zatayi magana wayarsa da take yashe a kasa ta dauki ringing, da sauri Basma ta sake shi ta ɗauko wayar ta beƙa masa, ya amsa yaga Ablah ce yay saurin picking ɗin call ɗin ya kara a kunnesa yana cewa" Ablah kiyi hkr wlh wani shegen yaro ne ya mari Baby mari goma sha13 lokaci ɗaya." daga can wata kyakyawar dattijuwar zata kai 60 year balarabiya zaune cikin wani hamshaƙin parlo, ta zabura daga zaune da take tayi tsaye ta saki tasbahan hannunta, cikin masifa ta fara magana da harshen larabci" Abdul wlh idan kabar yaronan bai kwana agidan yari zan kwana da fushinka me zafi a gaggauta kamashi ko ɗan gidan waye , maza-maza kana tasowa daga juma'ah kar abarshi ya sake awa gabanan ba tare da an kamashi ba , waye ubansa a niger ɗin? Da har zai taɓa jikin Mubina maza bata wayar kuma a kaita hospital a duba marin idan bai lalata mata ido ba ko ya taɓa mata kwakwaluwa , a jikin Mubina ina abin bugo." ta faɗa tana sakin kuka.
Umpah ya zaro idanu yace"Yau fa na shige su wani tsautsayi yasa na faɗa don Allah Ablah kiyi hakuri za a aiwatar da kome" ya janye wayar a kunnensa ya bama Mubina wayar yace"Baby ki lallaɓa Ablah don Allah kice mata har an kama yaron agaba zamu ayi shari'a." Mubina ta shagwaɓe tana turo baki tace"Tom umpah zan lallaɓata amma se an kamashi mugune bayada tausayi." ta faɗa tana kama hannun Basma suka nufi can ciki tana kara wayar a kunnenta, tace "Ablah nah yi hakuri bari kukan yanzu zan baki labarin abinda ya faru anfa kama shegen yana hannun yan sanda , karki tashi hankalin ki bari na shiga nayi wanka na kiraki musha hira." ta faɗa tana tsinke kiran, tana yamutsa fuska se wani ɗingisawa take. Basma tace" Wai harda dukanki yayi?" Mubina tayi banza da ita. Umpah ya bisu da kallo yana cewa daga masallaci police sitetion zan wuce muzo da yan sanda ki faɗi malamin muje har gidansa a kama shi." ya faɗa yana juyowa gun direba yace"Haladu maza muje masallaci lokaci ya ƙure min." ya faɗa yana sauri se baza riga yake ransa a ɓace. Haladu yay gudu ya bude masa wata zungureriyar mota ya shiga baya ya zauna ya rufe ya zagaya y shiga mata key suka mufi bakin get...

Mubina ko sallama ba tayi ba ta fado parlon. Basma ce tayi sallama. Amrah na zaune ta dora kanta jikin Mamu suna hira su ta uwa da ɗiya.
Mamu ta amsa sallamar tace"Oyoyo ƴan matana sannun ku." Mubina ta fado jikin Mamu ta ruƙunƙumeta gam ta saki kukan shagwaɓa. Mamu da Amrah suka riƙeta suna tamyarta" Baby yau kuma keda wa har ta saka mana ke kuka?" Mubina ta shige jikin Mamu tana shasheƙar kuka taki magana. Amrah ta rungumota tace" Ki faɗa mana ke dawa?" Basma ta zauna tace Aunty Amrah ba maca bace ita da Sir Kangiwa ne tai masa laifi shine ya haɗamu ya mana hukunci amma ita harda mari..." Amrah tace"Kan uba saboda me zai mareta horanta aka bashi? Waye kangiwar?" Mamu tace" Baby kin masa ɓarna ne ko ko kuwa rashin kunya?" Mubina ta janye jikinta daga na Mamu tana kuka tace"Ni ban masa kome ba kawai ya kware wajan iya zalumci ne , har fa ruwan toilet ya dura mani..." Mamu ta kalleta da sauri tana zare idanu dan yanzu kuma ta gama gano ƴarta harda karya ta feso. Mubina sama ta haye tana rere kukanta. Amrah ta miƙe ta bita a baya, Mamu tace" karki je ta haukace ma mutane har uban yaji barta zan lallaɓata , zo zauna ." Amrah ta dawo ta zauna tace" Basma ki faɗa mana abinda kika sani idan ya kamata umpah yaji yaje ya masa magana tinda ba horo ba aka bashi ba." Basma tace"Aunty gaskiya umpah ya sani fa ta faɗa masa kome har Ablah ma taji kuma mune bamuda gaskiya..." Nan ta zaiyane masu kome da Mubina take ma Kamal a cikin class.
Mamu ta zaro idanu ta rabka salati ta fara tafa hannuwa, tace" abinda kuke kenan a makarantar ko? Ai kuwa wlh kadan ya mata da yaci ƙaniyarta ne Baby bata ji." ta faɗa tana tagumi. Amrah tace" Baby bataji gashi umpah yaji harda Ablah nasan kuwa zugashi zatayi tace a kwato mata hakkinta..." Mamu tace "No zan faɗa masa gaskiya abinda Basma ta faɗa , se dai marin da ya mata yayi yawa gaskiya naji abun har raina , bana son na nuna mata ne ta kara narkewa ." ta faɗa tana miƙewa ta nufi kitchen. Basma miƙewa tayi ta nufi saman bene gun Mubina. Mubina tana hawa sama ta cire kayan jikinta tin a kofa tayi zigidir ta shiga bathroom.
Tana zuwa ta cika bath ta zuba sabulu me kamshi na ruwa ta shige ciki ta lumshe idanunta ruwan na ratsata, tana ciza lips ɗinta nippels ɗinta ya buɗe yayi wani irin tsine se tagwayen ajiyar zuciya take saukewa, tana mimmiƙewa a cikin ruwan hawaye na sintiri saman fuskarta, ta tura hannunta ɗaya cikin lallaunsa gashinta wanda ya jiƙe da ruwa tana cakuɗawa, tana ciza lips ɗinta, cikin sanyin murya me haɗe da ƴar shasheƙar kuka tace" Allah ya isana ya Allah kabi min hakkina insha Allahu bazan sake kula gurgu ba tinda shi bayada imani da tausayin mace , na tsaneka zanyi ta Addu'a Allah ya maka abinda ka min mugu ɗan iska kwarton banza... Wlh ka guji ramuwar gaiyya zaka shiga kunci ɗan gurgu kawai , wlh na tsaneka fiye da mutuwata..." bugun kofar da Basma tayi ma kofar toilet, yasa Mubina yin shiru ta bude shanyayyun idanunta wanda suka rune sukayi jajur saboda jaraba, ta miƙe da sauri ta fito daga cikin ruwan ta tsaya gaban shower ta kunna madanin shower ɗin ruwan na zuba tsakiyar kanta, kunsa 5 munites ta kashe tayi alwalla ta janyo towel ta daura a jikinta ta dauki karamin towel ta daure kanta ta bude kofar ta fito.
Basma na zaune bakin gado, ido suka haɗa da Mubina wacce tayi kicin-kicin da fuska tana zumburo baki. Basma ta miƙe tana danne dariyarta tace"sannu Mubee ya naga kinyi kuka? Bari nayi alwalla nazo na wuce gida." ta faɗa tana shiga bathroom. Mubina ta goge jikinta ta busar da gashinta ta shafa masa mai me kamshi ta ɗaure shi da ribbon amma taki yarda ta kalli madubu ta murje jikinta da maiyuka masu sanyin dadi da taushi, ta nufi wardrobe ɗinta ta buɗe ta kurama uban tulin kayan idanu, ta yamutsa fuska ta beƙa hannunta ta janyo wata Abaya red me masifar kyau tasha adon duwatsu, saman a matse ƙasan ya dan buɗe kadan ta zaro mayafinta ɗan guntune bayada girma ta cire towel ɗin ta yada shi ƙasa, har zata saka rigar taji breast ɗinta na masifar ƙaiƙayi se motsi yake, tsaki tayi ta ciro bra ta saka se lumshe idanu take ta saka Abayar, wow nace Sbd tayi mata masifar kyau ta kamata daga sama sosai kirjinta kamar ya fasa rigar ya fito ƙasan ya dan buɗe amma kuma daga ƙugunta ya ɗan kamata hips ɗinta ya fito, tayi masifar kyau ta nufi kan Dreesing mirorr ta dauki turarenta mai sanyin dadi ta fesa ta yane kanta da ɗankwalin. Basma ce ta fito ta isko Mubina saman dadduma zaune da Alqura'ani a hannunta tana karatu cikin zazzaƙar muryata tana karanta suratul Yasin. Basma gun jakarta ta nufa ta buɗe ta zaro wayarta ta duba taga lokacin sallah yayi an taso juma'ah, ta ɗauki ɗayar dardumar ta shimfiɗa ta tayar da sallah.
Umpah ana tashi daga masallaci nan suka hadu da Abbu yake bashi labarin abinda wani malamin su Mubina ya mata har da ruwan toilet ya bata, karan sa zai kai. Abbu ya jajanta yace su wuce Company gurin Kamal yasan yana can yanzu, Kamal ya sami malamin yaji dalili akan me zai mari karamar yarinya har mari 13 da bata ruwan toilet daga can idan sun faɗama Kamal ɗin, kila ya san malamin daganan suje kawai police sitetion ɗin, suyi karansa, shine fa direct sukayi Company, daga can suyi police sitetio a basu yan sanda a tafi da Mubina ta faɗi abinda malamin ya mata a hukuntashi...🤔
Mubina tana gama sallah tace da Basma " Tashi muje gidan ku daga can zan shiga a dedeta na tafi gidan Baffa Inusa a can zan kwana yau." ta faɗa tana lumshe idanu. Basma ta ɗauki jakarta tace"muje kalli mom se kirana take wlh." ta faɗa tana tafiya. Mubina bata sake magana ba ta ɗauki wayarta ta kashe ta kaita ƙasan pillow ta ajiye. Amrah da sauri ta sallame tace"Baby ina zaki a haka kalli yanda idanunki suka yi Ja ki kwanta mana." ta faɗa tana miƙewa ta rungume Mubina ɗin. Mubina tace" eh yanzu zan dawo ai rakiya zanyi in dai baki ji me nace ba." ta faɗa tana janye jikinta daga na Amrah ta mata kiss a goshi tace" se na dawo." ta kama hannun Basma suka fito. Parlon ba kowa se wayar umpah na ta ringing, Mubina tayi saurin ɗauka tai piciking ɗin call ɗin ta kama hannun Basma tana cewa"Mamu idan kin fito na raka Basma gida a ƙafa zamu fita tinda ba nisa." ta faɗa tana manna wayar a kunneta suka fice daga cikin parlon.
Kamal ko lokacin da aka gama sallar, hospital suka nufa shida Sageer yaga wata mata wacce take fama da ciwon zuciya ga
basuda kudin aikin da za'a mata nan yasa hannu akan zai biya kome, duk da Sageer yace zai mata, daga nan sukayi sallama cewar zasu haɗu 5 pm akwai hira ta musamman.

Mubina suna fitowa ma'aikatan gidan suna gaisheta da jiki da mamakin maras lfy ce taci kwalliya haka? Mubina banza ta musu suka fice a ƙafa, tinda gidan babu nisa sosai titi kawai za'a tsallaka, suyi ƴar tafiya.
Tafe suke cikin nutsuwa Mubina jikinta sai motsawa yake masha Allah, tamkar tarwada hips ɗinta ya fito, ɗuk da ta rufe dede kirjinta da ɗan gyalan amma hakan bai hana tudun nonuwanta fitoowa ba kallo ɗaya zaka mata kasan Allah ya mata manyan nonuwa masu lafiya. A cikin nutsuwa yake driving waya manne kunnansa yana sakin ƙayattacen murmushi, cikin amo murya sa me daɗin sauraro yace "goggo nah wlh bacci ne cike da idanuna gani nan na kusa isowa fa bazai wuce tafiyar 3 munites ba , a kunna min daddɗan turaren wutar nan fura kada a sa min ƙanƙara wlh mura nake ji tin jiya , bye se na iso." ya faɗa yana tsinke kiran. Ya karya kwanar titin ya tsinkayo su Mubina, suna tahowa kallo ɗaya ya mata ya ganeta saboda face ɗin motar sa suke tahowa, yanda take takunta cike da jiji da kai se dai fuskarta ba walwala waya manne a kunneta tana mgn, ga takalmin ƙafarta da tsini, kirjinta se kaɗawa yake, hips ɗinta ya fito, se kallan baiwar kyanta jama'a suke, wani matashi na biye dasu a mota. Kamal ya zaro fitinanun idanunsa, yace"Ikon Allah wannan yarinyar ashe har yawon banza take haka wai ina iyayanta ne? Suka barta ta lalace gata jarababbiya , basa tsoron ta ɗauko masu abin kunya , kai Allah ka shiryemu amma nan babu tarbiyya bari kiga na hargitsa miki lisafi tinda baki san waye ba bare ki ɗauki fansa , masifafiya zakiyi zawo yanzu , muga karya tafiyar iskanci bari na fanshe ɓarnar da kika min." ya faɗa ya sakin murmushin mugunta ya saki hanya yay kanta a guje. Basma ta fasa ihu tace"Mubina kauce mota..." Mubina ganin mota tayi kansu ta fasa uban ihu! tace"Ablah hatsari..."ta saki wayar umpah ta faɗi ƙasa jikinta na rawa........

*Labarin nan na kudi ne kan farashi me sauƙi, book 1&2 zaku same shi akan 200N kacal, ga mutanan mu na Niger zaku biya 400F, ba tsauwalawa hakan ta faru ne saboda masoyana na asali, karfa ku sake ayi baku wannna salon na daban ne, wannan karon bana cewa kome kune zaku faɗa insha Allahu, duk me bukatar siya zaku tuntuɓeni ta wannan*
*Lambobin👉🏻+22796515805/ +22792589446, karku manta nera 200 kacal zaku karanta book 1&2 ,Real ladingo na maraba da masoyanta har kullum💃🏻💃🏻💃🏻*

*💖😭KAMAL NE😭💖*

_*Book 1*_



_NA_

*Real ladingo*
*Sweet Baby💋*

_Ƴar Mutan Niger_🤙🏻



```IDAN KANA SON KAGA ASALIN MASOYAN KA DA ZALLAR KAUNAR DA AKE NUNA MAKA TA ZAHIRI DA TA BAƊINI, TO SAI KIN FARA SIYAR DA BOOK, NAN NE ZAKIGA HAKIƘANIN MASONYAN ASALI NA GASAKIYA, MASOYANA INA ALFAHARI DAKU, BANI DA BAKIN MAKU GODIYA SAI DAI NACE ALLAH YABAR ZUMUNCI, DAN ZO MUCI TUWO YAFI TUWON DADI, WALLAHI INA MATUƘAR GODIYA MUCH LOVE MASOYAN ASALI🤝🏻🤝🏻🤝🏻😍```..


_*Bismillahir Rahamanir Raheem*_



_*Free Page*_


_🅿️1️⃣2️⃣_


Mubina ta gigice tama rasa inda zata bi, dan motar gunta ta nufo gadan-gadan, tayi saurin kaucewa gefe da bai bita ba amman ya sake binta, duk inda tabi nan Kamal yake bi, kuma yaki bugeta se kewaya gun suke. Mubina gajiya ta fara yi, tsaye tayi cak cike da masifa da rashin kunya ta riƙe ƙugunta tana shasheƙa, tace" Ko uban waye wlh bazan gudu ba idan ka fasa kaɗeni kaki Allah da manzon sa." ta faɗa tana ƙarƙaɗa ƙugunta tayi tsaye kyam a gurin. Kamal ya bushe da dariya ya sake nufarta gadan-gadan, tako ki gusawa ta ware hannayenta tace"idan kai ɗan halak ne kabi ta kaina wake da zunubi...?" ta fada tana lumshe idanunta. Kamal ya zaro idanu yana dariya yace" ƴsr bala'i bazan kashe kiba zan dai baɗeki da kura nayi gaba naci bulus." ya faɗa yana tashin ƙura yay kanta gadan-gadan yana dariya. Basma ta rikice tayo kan motar a guje tana cewa" koji mugun mutum waye ne? me ta maka da zaka nemi kasheta." kafin take isowa tuni Kamal ya kai ga Mubina, saura kiris ya bugeta yaja burki da karfin gaske, yay baya yana dariya ya baɗeta ko da ƙura kasancewar gurin akwai rere. Mubina jin bai bugeta ba yasa ta bude idanunta ta kalli motar, amman sbd glass ɗinta me duhune ba'a ganin na ciki se na waje. Sukuyawa tayi tana cewa"wlh se ka sani idan ba tsoro ba ka fito ka baiyana kanka mana , kaga bala'i da masifa yau." ta faɗa tana cika hannayenta da ƙasa da wani katon dutsi tayi kan motar Kamal, amman kafin take isowa ya fizgi motar da karfin gaske ya waske ya barsu da ƙura. Basma ta riƙota tace"Mu barshi da Allah ko waye zubar da ƙasar mu tafi Allah zai saka miki." ta faɗa tana kakaɓe ma Mubina hannunta, da jikinta ta kama hannunta kenan wayar umpah da take hannun Basma wace Mubina ta yada ta a ƙasa ta soma ringing, Basma ta bata"Amshi Ablah ce." Mubina ta kalli tsirarin mutanan dake kallan su tace" uban me ake kallo jikinmu? ko munyi abun kunya ne? Kai wlh mutane basa rasa abin gulma , ki bari Basma ina cikin mugun ɓacin rai yanzu bazan iya magana ba , amman duk ranar da na hadu da wannan mutumin wlh zai san ya taɓo giɗan rina..." tace to ai akwai irin motocin babu yanda za'ayi kisan waye tinda bai bari munga number motar ba , inda kinga fuskarsa ne ko yaya amma motocin ai ko Sir kangiwa na da irinta fa ko yau da irinta yazo makaranta..." Mubina ta damƙe hannun Basma da karfi cikin ƙaraji tace"Wlh shine tabbas shine amman wannan karon zaiyi da nasani maras anfani..." Basma tace"A'A karki yanke hukunci kai tsaye mana taya zaki ce shine? Bayan kinsan baya shiga shirgin mutane se an taɓoshi , ai bamu tabbatar ba..." Mubina cikin ƙaraji tace"ubanki Basma kajimi da ƴar iska waye ɗan iska a garinan idan ba ɗan gurgu ba?. "Wlh shine"ta faɗa tana ciza lips ɗinta na ƙasa. Basma zatayi magana wayar hannunta ta sake ɗaukan ruri, tace" Ngd da zagi kawas pls ɗauki ki kwantar mata da hankali cewar ba ke bace kinga mashin ya faɗi ne shine kika cemata hatsari." Mubina ta amsa tai picking, ta manna a kunnata tace"Ablah karki tashi hankalin ki bani bace wasu masu mashin ne kinji my Ablah nah." daga can Ablah ta sauke ajiyar zuciya tace"Alhmdllh Mubeena bari zan ɗan kwanta anjima zan kiraki kiba Abdul wayarsa kinji." Mubina ta ɗaga kai tana sauke numfashi tace"Ok bye" ta faɗa tana katse kiran. Wannan saurayin da yake binsu a mota yay parking gabansu ya janye galss ya masu sallama. Mubina ko kallo saboda tana

Please Login or Register in order to submit comment