Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cikin ɓacin rai ta damƙe hannun Basma tace"wlh kika tsaya zan maki rashin mutunci wuce muje seda ya gama gulma sa zai mana mgn , inda shi jarumine fito na fito zaiyi a lokacin da Kankura gurgu yaso nakasani , dan ayi one one shi mugu da lkcn zai tare sa da mota suyi ɗauki ba dadi , amman ba ka laɓe ba sai da kaga ya tafi ka wani mana mgn kaji ɗan arrr..." Basma ko iskar da ta debosa bata kalla ba suka ida shan kwana Basma tace ƙawata ki daina cewa fa Kangiwa ne zato zunubi kida ya zamanto gaskiya." Mubina tace "mubar maganar kawai kar na miki zagin arnan da." Basma tace"na bari." Mubina ko cikin salon takunta babu abinda ya sauya haka suka karaso har get ɗin gidan su Basma guy ɗin nan na biye dasu har suka shige ciki, ya juya baya.

Masha Allah gidan ya hadu sosai babu karya ta ko ina. Hajiya lubah na zaune a parlo tana waya, Sakina na jikinta a kwance yarinya ce yar kimani 11 year, parlon suka shigo da sallama. Mubina tayi gun hajiyar tana zumburo baki tace" Ke Sakina se kina haye mana momy ko?" ta faɗa tana ture Sakinar ta shige jikin Lubah. Basma ma tazo ta rungumeta suka wani ƙamƙameta. Sakina ta bushe da dariya tace"Ƙatai basajin kunya se na gama ku da yaya Anwar." Momy tayi dariya ta rungume su tana shafa bayansu, tace"Sannunku a ƙafa kuka karaso ko?" Mubina ta ɗaga kanta tace"Momy ina yini." Lubah ta masa tace" maza ku tashi kuci abunci"Basma ta miƙe tana cewa "to bari na canza kaya ku fara ci." ta faɗa tana shiga bedroom ɗinsu. Mubina tayi wani luf jikin momy kamar mage, tana lumshe idanunta. Lubah tace"dota tashi maza kije dining ki cika cikinki nasan sarai baku tsaya kunci wani abun ba?" Mubina ta ɗaga kanta a cikin sanyi murya tace"momy bana sha'awar cin kome yanzu wlh , amman bari na ɗauko koda frech milk nasha bacci ma nake ji." ta faɗa tana janye jikinta daga na momy ta miƙe, ta nufi kitchen. Frech milk ta ɗauko tazo ta zauna kusan momy ta fara sha tana lumshe idanunta wanda suka ƙaɗe suka yi jajur. Kamal banda dariya babu abinda yake, yana driving se da yayi ta isheshi ya gintse yana driving ɗinsa a cikin nutsuwa, ransa fari fas ya ɓata ma mara kunya ranta. Wani hadadɗan gidane madede ci ya hadu ba karya, a unguwar citè nan naga Kamal ya tsaya a dede get ɗin yana zuba horn. Megadi ya buɗe masa ya shige ciki, nan farfajiyar gidan yay parking ya fito, yana riƙe da wayoyinsa bayan sun gaisa da megadi ya wuce ciki anutse yake takunsa me cike da jarumta da izza, kirjinsa me cike da yalwar gashi gwanin sha'awa se sama da ƙasa yake, Kamal ba karamin kato bane. Wani hadadɗan parlo ne me tsari, wata dattijuwa zaune ƙasa saman carpet, farin glass manne a fuskarta wata kwarya ce me zane me kyau, a gabanta tana dama fura wacce taji nonon kindirmo, wasu yara har uku sun baibayeta, maza biyu mace ɗaya, se surutu suke zuba mata. Ameer yace"Goggo Ruma zan sha fura ai baza a ba Sameera ba ko?" Lateef yace"se an bata kuji kai fura uncle Kamal ce fa ko goggo." Wata ƴar matashiyar mata ta fito zata kai 27 year tace"To maganatu in sake jin kace Kamal uncle ɗin dai yan maganatun uwa."goggo Ruma tayi dariya tace"Hafsat bake rabo da faɗa kina ji da ɗanki Kamal ko..."Sallamar Kamal ta katse ma goggo hira ta amsa, yaran suka yi kansa suna "Oyoyo uncle."ɗaya bayan ɗaya ya ɗagasu yana masu kiss ya ajiye su yana cewa"ƴan kanina yaran kirki bari na gaisa da momyna autar goggo." ya faɗa ya nufi gun Hafsat, yana murmushi kusanta ya zauna ya jingina da kafadata, yace"momy ina yini ashe kuna nan naku zuwa gidan naki fa." Hafsat ta shafi kansa tana murmushi tace"Eh gani nan munzo yini , ina yayana da aunty Mamu da Samha? Wai auta ina kabar Sumaiyya da ibrahim ɗin zan zama auta ƴan biyun goggo kake maidamu baya, se na faɗama Sumaiyya." Kamal ya miƙe yace"ni fa ba daga gida nake ba kuma na kashe wayoyina so nake nai bacci har zuwa la'asar , sorry momy Hafast kawo ibrahim namijine shine babbanku a yanzu ko goggo Rumana."ya faɗa yana zama kusa da goggo ya rungumota yana dariya, ta bugeshi tana cewa"sakeni ban saniba , idan fura ta zube fa." sakinta yay yana murmushi, yaran suka haye saman sa, seda Hafsat ta masu tsawa!! Kamal sosai yasha fura yana santin yace idan yayi aure goggo zata koyama matarsa. Bayan ya gama shan fura, ya miƙe Hafsat na tsokanar sa ya shige cikin ɗakin da yake kwanci, ɗakin yasha gyara an shimfiɗa sabon zanin gado se baza kamshi ɗakin yake, ya tube yay wanka ya saka rigar bacci dan yanada kaya a nan, ya kunna Ac ya faɗa saman gado ko 5 munite bai ba se bacci.

Ɓangaran su umpah kuwa suna zuwa company suka taras Kamal baya nan, Abbu yace kawai su wuce police sitetion ɗin. Shine fa suka je, sukama Acp bayanin kome, nan ya haɗasu da ƴan sanda suka zo gida nan suka isko Mubina bata nan se Amrah da Mamu, umpah yake ma Mamu bayanin suna tare da ƴan sanda, nan Mamu ta bashi labarin yadda Basma ta faɗa mata. Mamu tace"Wlh kuma cewar tasha ruwan toilet karya ne irin nata , amma idan baka yarda ba kuje gidan su Basma tana can ta faɗa maka malamin , naji dai Basma tace kangiwa ne..."Nan umpah ya zaro idanu cike da mamaki!! yace" anya kuwa?" bari na kirata naji" nan ya kira number ta a kashe, ya kira wayarsa ta wajanta yaji tana amsa waya. Umpah yace"Tabbas kangiwa ɗayane maradi, Kamalu ne kenan? Tare fa muke yanzu da mahaifinsa Abubakar wannan makocin namu me kirki , amma yau da na tafka abin kunya Nusy abar maganar Baby kenan ashe lfy lau gashi ta fita yawo , bari na sallami yan sandar." ya faɗa yana juyawa. Amrah ta kyalkyale da dariya harda riƙe ciki tace "Wlh idan umpah na biya Baby se ta saka shi jin kunya."Mamu tace"hummm barshi ai tin farin maganar nasan karya take shi marinta dai da yayi har san hannunsa suka fito shine ilar amman ita taja..." Amrah ta miƙe tana dariya tace "bari na leƙa naga ya zaiyi da ƴan sandar." ta faɗa tana ficewa daga parlon.
Umpah kuwa sallamar ƴan sandar yayi yama Abbu bayanin wai Kamalu nasu ne... Habawa ai kuwa Abbu yace se an kai sa police sitetion sunji dalilin da yasa yaci zalinta. Daket umpah ya ba Abbu hakuri ya hakura nan sukayi sallama da juna Abbu yace masa zuwa dare zasuyi magana me mahimmanci... Da haka de suka rabu umpah ya koma gida, Abbu ya shiga gida shima.

Samha ce zaune a parlo tana waya da Safiyya ƙanwar Abbu cewar hutu gatanan zuwa kebbi... Abbu ya shigo da sallama. Samha ta miƙe tana cewa"mamah ga Abbu ya shigo." ta ƙarasa tana faɗawa jikinsa ta kara masa wayar a kunnesa, ya fara magana"Ah Safiyya ya kebbi?" daga can tace"Yayana lafiya lau yasu goggon mu? Ga zakiyya na fa tafe tace nan zata haihu wlh ba yanda mijin baiba ta haihu nan sbd haihuwar farko ce amma tace niger zata zo gidan kawunta , Mamu ta bata kulawa." ta kai ƙarshen maganar tana dariya. Abbu yace"Gud Safiyya naji dadi sosai to mijin ya kawota da kansa saboda cikin yayi girma sosai ina Muhuseen da iyali? Dazu mun gaisa." Safiyya tace"rabona dashi shekaran jiya naje me sunan goggo ta fadi ta goce." Abbu yace "wh ai da sauƙi Allah bata lfy bari na shiga na ɗan huta." nan suka yi sallama ta kashe kiran. Ya kalli Samha yace"Ina ummah ki ne?" Samha ta saki Abbu tana dariya tace" Tana bacci fa tinda tayi sallah bari nima naje na huta , Abbu ina Yaya "Kamal ne? Ko ya tafi gidan goggo?" Abbu ya shafi kanta yace"Oho masa laifi yayi bari naje na sami mamarki muzanta , na masa mata yau zan nemi izini gun mahaifinta." ya faɗa yana haurawa saman bene. Samha tayi ihu da tsalle tana murna tace"mun kusa raƙashewa a she." ta faɗa tana nufar saman dan ta kwanta ta huta...

Basma ta jima kafin ta fito lokacin Mubina ta shanye frech milk tana gyangyaɗi har baccin ya kwasheta, momy ta gyara mata kwanciyarta ta rufa mata mayafinta tana dariya.
Basma ganin Mubina tayi bacci yasa ta kyaleta taje kan dining ta cika cikinta dam, ta ɗan fita kofar parlo tana leƙe taga garin ya fara duhu sosai akwai hadari, cikin farin ciki itama ta kwanta nan parlon sbd tana son ruwan sama sosai tace ma momy ta tasheta idan an fara ruwa... momy itama janye Sakina tayi suka shiga bedroom domin suma su ɗan taɓa barcin...

Kamal baccinsa yake cikin nutsuwa da kwanciyar hankali yana fitar da numfashi me cike da lafiya. Ameer ne ya murɗa kofar ɗakin, ya shigo da gudu yana ihu yana kiran Kamal"Uncle taso kaga garin an fara duhu kamar dare." ya faɗa yana hayewa saman gadon ya fadawa saman kan Kamal. Firgigit Kamal ya farka salati dauke a bakinsa, yace"Oh yaranan baku barin mutum ya kwanta bari ma na tafi gidan mu kawai." ya faɗa yana janye Ameer daga jikinsa ya sauko daga saman gadon, ya sanya takalminsa ya kwashi wayoyinsa ya zuba aljihu ba tare da ya kunna ba, yana yamutsa fuska sai lumlumshe tsumammun idanunsa yake, ya kama hannun Ameer suka fito. Goggo tace "amman Ameer anyi maras ji , ka tado yayan ka ai kuwa se na faɗama Hafsat." Kamal yace" tsofuwa na gudu se kin jini gobe ina mom Hafsat"? Goggo tace tana ciki wai bacci take , amman a wannan yanayin zaka fita ka bari har a lafa mana." Kamal ya galla mata harara yace "anki ɗin Abbu yanzu haka na nema na duk yasan ban wuce nan ko Company , na tafi se na dawo." ya faɗa yana sakin hannun Ameer ya rankwafa yama goggo kiss ya miƙe yana murmushi ya fice. Ameer ze bishi goggo tace"Maza dawo kasan halin gambo nemi gu zauna idan ta tashi zata kai ka..." Ameer ya dawo ya zauna. Kamal yana fita ya shiga motarsa yaja ya fice daga gidan, a guje saboda yanayin garin...

Mubina baccin ta take me mahaukacin dadi se wani mimmiƙewa take tana ɓaƙaro kirjinta, ai kuwa se gata ta fado daga saman kujera dimm. A firgice ta buɗe manyan idanunta ta zumburo baki gaba tana riƙe ƙugunta tace"Woshhhh bayana Ashhhh naji zafi ya ma akayi na fado? tirrr." ta faɗa tana kallon Basma tana sharara bacci. Tsaki taja ta miƙe tana riƙe da kugunta ta ɗauki wayarta tayi kan Basma ta ɗaga hannunta zata shirga mata ƙulli ko me ta tuna ta fasa, ta saka takalminta ta yane kanta da ɗan gyalan Abayarta ta fice tana yamutsa fuska. Tana fitowa ta zaro idanu ganin garin yayi duhu sosai kamar dare, ga iska kaɗan-kaɗan, har an fara yaiyafi. Da ɗan saurinta ta fara tafiya tana sakin murmushi tace"Wow dama na taso Basma mun tafi gidan Baffa inusa ruwa ya bamu kashi a hanya ina son ruwa sosai , se dai duhun yayi yawa bari nayi sauri na samu adaidaita sahu." ta faɗa tana isowa bakin get ta bude kofar ƙarama ta fice..........



_*Labarin nan na kudi ne kan farashi me sauƙi, book 1&2 zaku same shi akan 200N kacal, ga mutanan mu na Niger zaku biya 400F, ba tsauwalawa hakan ta faru ne saboda masoyana na asali, karfa ku sake ayi baku wannna salon na daban ne, wannan karon bana cewa kome kune zaku faɗa insha Allahu, duk me bukatar siya zaku tuntuɓeni ta wannan*_
_*Lambobin👉🏻+22796515805/ +22792589446, karku manta nera 200 kacal zaku karanta book 1&2 ,Real ladingo na maraba da masoyanta har kullum💃🏻💃🏻💃🏻*_

*💖😭KAMAL NE😭💖*

*Book 1*



NA

*Real ladingo*
*Sweet Baby💋*

Ƴar Mutan Niger🤙🏻



*Bismillahir Rahamanir Raheem*



*Free Page*


🅿️1️⃣3️⃣

Mubina cikin nutsuwa take tafiyarta, tana waige-waige tsoro ya ɗan shigeta kaɗan, saboda yanda layin yake shiru ba jama'a sbd garin yakar ɗe da hadari, yayi duhu sosai baka ganin abu da kyau, ga iska ga ɗan yaiyafi anayi gashi zowa bakin titi da ɗan ja. Cikin ikon Allah ta shanyo kwana se ga me adaidaita sahu zai nufi bakin titi, cikin murna Mubina ta fara ɗaga masa hannunta sbd an fara ruwa. Cikin sa'a kuwa ya hangota tinda nan gabanta yake tinka rowa, kuma fitilar adaidaitar a kunne ya haske ta, yana ƙoƙarin ƙarasowa. Mubina ta ja mayafinta ta rufe fuskarta tana jan tsaki tai maga iya saman lips ɗinta, tace"Kaji iskanci aikin banza kawai wlh badan a tsorace nake ba ga gari yayi duhu da sai na koya maka hankali , haka kawai ka haske min fuska..." daidai me adaidaitar ya iso yana washe baki yace"Hajiya se ina amma zaki bada jaka biyu sbd kin san halin da ake ba kowa zai ɗauki mutum yanzu ba , nima na kawo matar da zan aura ce can ƙasa sai na hayo tudun manya.." Mubina cikin jin haushin sa ta buɗe mayafin fuskarta ta kalleshi, idanu Harun niga ya zaro!! yace"Kan uba kece wlh ko me zaki bani bazan ɗauke kiba muguwar yarinya baƙar kadara , anya ke mutum ce kuwa?" ya fada yana ƙokarin tashin a daidaitar shi ya fece.
Ai kuwa jin abinda harun niga ya faɗa ya kuma tsorata!! ga Mubina ma atsora ce! take, amma se taga ta sami dama ko ba kome zata amshe adeɗetar, ta tuƙa da kanta bayan nan zata masa sufar ita ba mutum bace ba ta cinma burinta na tuƙa adedeta, taje har kofar gidan Baffa a bati ba ko sisi. Da sauri ta sanya hannunta saman fatar idanunta, ta juye fatar idanun suka bultso waje, ma'ana fatar idanunta ta sama ta juyo ta ciki ta dawo waje irin dai na yarinta da ake, nasan wasun makaranta ɗayawa zasu gane nufi na... Ta cire mayafin kanta ta daure ƙugunta, ta nasa phone ɗinta cikin bra ɗinta, ta saki gashinta yayi buzu-buzu, Mubina ta zaro idanu ta gwalo harshe waje, ta koma sufa abin tsoro! ta damƙe kwalar niga tana wata irin dariya tace"Hhhhhhh Niga ne ko yaron da ya yaso yama jikanyar tattaɓa kunne na fyade ko? Hhhhhh yau irin ku muke nema zamu yanka ku muba ɗangwandarau jininku ana bikin cika shekarun sa dubu biyu." ta faɗa tana gwagwalo harshe tana zazaro masa idanu, ga idanunta sun tara kwalla dan zafi take ji yanda ta burkita su ɗin. Harun niga cikin matsane cin tashin hanali yace"ku kuke ganinmu bamu muke ganinku ba , wlh bani bane nama jikanyar tattaɓa kunnen ki fyade ki taimaka ya mai girma aljana na tuba..." ɗauke shi Mubina tayi da mari, cikin wata irin murya tace"ka yarda yanzu na kaika gidan da abin ya faru harda kawarta ɗiyar dogarin sarkin aljanun Ethoipia , har jikanta yaje ya ceceta , bari muje kaga gidan daga can se mu kaika gurin sarkin yanka ya maka sallatu a maka askin mutuwa , dan bama kashewa se an ma mutum kaciya da askin mutuwa , maza koma baya bani gaban na tuka muje gidan da kaso kama jikanyar tattaɓa kunnena fyaɗe , maza shiga baya zauna wlh idan kayi ƙoƙarin guduwa zamu lauye ka mu maido ma mafitsaraka goshinka ." ta faɗa tana sakin sa tana gwagwalo masa idanu da harshe.
Niga wanda ya gama rikita cikin rawar jiki ya miƙe ya dira bayan adedeta jikinsa na kyarrrrrma.
Mubina ta gyara idanunta tana kumshe dariyarta, ta kunna adedeta sahun ta fizgeta da karfin gaske ta tafi a guje, ta nufi bakin titi. kuma a lokacin aka saki ruwan sama me karfin gaske irin me iskar nan sosai. Harun banda rawar jiki da zufa da take keto masa babu abinda yake har ya fara ɗigar fitsari, saboda yadda Mubina take tukin bada wasaba tana magana ita ɗaya tana cewa"Sarkin wanzanman aljanun arewa maso kudu ka gyara askarka mun kamo kwarton jikanyar tattaba kunne na , za'a masa sallatu da aski kafin mun kashe shi." ta faɗa tana ƙoƙarin shan kwana ta hau saman titi, dan bata ganin gabanta sosai saboda ruwan da ake zabgawa ga duhu tamkar dare... A daidai lokacin kuma Kamal ya danno hancin motar sa kwanar, idanu ya zaro ganin mace na tuƙa adedeta, ƙoƙarin kaucewa yake daket ya samu ya ɗan kauce ya basu guri su wuce. ganin harda namiji... Ai kuwa Mubina itama sai ƙoƙarin jan burki take adedeta taki tsayawa, ta fasa ihuuuu tana ƙoƙarin direwa ƙasa. Niga yace"don Allah karki kasheni tinda ke ko kinyi hatsarin ba mutuwa zakiyi ba." ya faɗa yana wutsulowa waje. Mubina kuwa tayi muguwar tsorata! ta gigice ta rasa abin yi, saboda faɗuwar gaban da tayi ganin adedetar taki tsawa kuma niga ya dire ya fadi ƙasa, se kiran umpah da Mamu da Amrah da yaya Kabeer da Baffa inusa take, tana ƙoƙarin tsayar da adedetar tama rasa ta ya zata dire irin yanda niga yay... Kamal yayi saurin yin baya da motar yana zaro idanu ganin Mubina ce, ya furta"Ya Salam Allah me iko mai halitta kala-kala anya kuwa yarinyar n..." bai idasa maganar ba ta bugi motar sa da adedeta sahun, ta fasa ihuuuu! tayi baya ta faɗi bata ko motsi... Niga ya dora hannuwa akai yace"Allah ka fitar dani wlh zaiyi wuya nakai gobe , ganin hatsarin mutanan ɓoye ba abu bane me kyau." ya faɗa jikinsa na kyarma. Kamal ya ɗauki bazara ya budeta ya fito ya shiga duba gaban motarsa inda ta buga har ta ɗan lankwasa kaɗan, yaja tsaki ya nufo gunsu. Niga ya ƙarema Kamal kallo yace" wa'innahu sulemanu wa'innahu bissmillahir rahamanir rahim, don Allah ku rabu dani , jikanta karka cutar dani wlh ban ma kakarka kome ba." ya faɗa yana zube ƙasa sumamme fitsari na tsiyaya, amma bazaka ganeba saboda ruwan sama da ake ya jiƙashi jagab.

Kamal yace"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!! Wannan yaron bashi bane ya kusa mata fyade? Kuma na gansu yanzu? A gaskiya wannan yarinya bata da hankali ko kuma nace tarbiyya." ya faɗa yana nufar niga ya sunkuya ya kara kunnen sa yaji baya numfashi, tura masa yatsarsa cikin kofar hancin sa da karfin gaske, se gashi ya sauke ajiyar zuciya saboda ruwan saman da yake dukan sa. Niga yace"Don Allah jikan aljana kar kumin kaciya da aski inada duka..." Kamal yace daka masa tsawa"Kai!! Dallah bana son hauka uban waye aljanin?" Nan cikin rawar jiki harun niga ya zaiyanewa Kamal kome. Kamal ya jinjina kai yace"Tab to Allah ya kyauta ni ban haɗa iri da itaba ni mutum ne itama mutum ce se dai ita daban take da mutane , bata da hankali tashi maza ka wullota waje ka dauki adedetar ka ka tafi wlh idan ka daka ta wannan sheɗaniyar yarinyar to tabbas zata hallaka ka karka sake tsayawa idan ta tsayar da kai , ko kadai kuna iskanci ne kai da ita?" Niga yace "wlh ko ɗaya ranar ma tsutsayi ne." Kamal yace"Wlh ka kiyayi zini da ƴaƴan mutane , kaji tsoron Allah." ya faɗa yana juyawa ya nufi motar sa ko kallon gurin Mubina bai ba. Niga ya miƙe cikin rawar jiki ruwa ya gama jibgar sa, ya nufi adedeta ɗin yana zuwa ya ganta rabinta a ƙasa a waje rabi a cikin a dedeta ya leƙa da kyau yaga bata motsi amma tsoron sharri irin nata, yasa ya juya da gudu ya nufi Kamal wanda yake ƙoƙarin shiga mota. Yace "Don Allah yallaɓai temaka min wlh bata motsi inajin da ta bugu da motar ka taji ciwo." Kamal yace "No ba ruwana shiga sabgar wannan yarinyar wlh haɗarine ibilisuwa ce..." ya faɗa yana shiga mota. harun niga hankalin sa a tashe ya sunkuya ya riƙe ƙafafun Kamal, ya kece da kuka yana roƙonsa ya raba shi da ita ya temaka ko hospital ya kaita se ayi cigiyar iyayanta. Kamal ya jinjina kai yace"Ok sakeni ni ba asibitin da zan kaita muje na temaketa don Allah ba dan itaba." ya faɗa yana fitowa daga motar. Harun dadi kamar ya kashe shi zai rabu da jaraba.
Kamal isa gurin ya sunkuya ya janye bazara sa, ya kare mata kallo yaga bata numfashi, gashinta ya rufe mata fuska ya soma jiƙewa, ya saka hannun ya janye gashin yaga goshinta ya ɗan kumburo, baki ya taɓe haɗe da fesar da wani irin numfashi me zafi, ya sanya tattausan hannunsa ya ciccibeta ya miƙe da ita, ya rungumota kirjinsa, rigarta da ta jiƙe ta lafe a jikinta nipples ɗinta sunyi wani irin tsini sun manne a rigarta wada tai nasara jiƙewa. Kamal ya dora tattausan hannunsa a saman goshinta ya murza da karfi yana lailawa, kumburin ya ƙura mata fitinannun idanunsa, cike da haushinta, sosai yake murza goshin nata har ƙullutun ya fara bajewa, ya ƙara manneta jikinsa, A hankali ya fara mgn kamar me ciwon baki yace"Mace kamar ƴar tsanar wasan yara se fitinar tsiya , Allah yasa kina da rabon shiriya." ya faɗa yana yamutsa fuska ya nufi motarsa da ita. Niga ai Kamal na cirawa ya faɗa cikin adedeta nan yaga tafkekiyar wayar yako ɗauka ya saka aljihu yace"wlh naci blusu akan wuyar da kika bani ƴar banzar yarinya zaki ga sakaiyya wlh zaki gani bade bakida mutumci ba."ya faɗa yana fizgar a dedetar.
Kamal yana isa mota ya bude set ɗin baya ya kwantar da ita ya rufe, ya zagaya ya shiga ya fizgi motar yabar gurin. Kuma a lokacin ruwan saman ya ɗauke sakammakon kiran sallah da ake ta la'asar. Kamal ganin ruwan ya tsaya cak lkc ɗaya ya fara gudu sosai ya dafe kansa da hannunsa ɗaya, yana muriƙar mamakin wasu irin iyaye ne wannan da basa kula da ƴarsu, wacce Allah ya basu amana amman sun barta ta tambaɗe haka tana tuƙin adedeta a saman titi. A hankali ya furta"Tabbas yarinyar nan bata da iyaye inko tanada to basu bata tarbiyya ba , mace da aka santa da kamun kai da mutunci , a yanzu na gano takura ko horo baza su saka yarinyar nan ta nutsuba kamar ma haukatata suke shirin yi , abu mafi sauki a sami me sata a jiki yana nusar da ita ko Allah yasa ta shiryu , amma tabbas rayuwarta tana cikin garari waye zai temake ta waye ne...? Sageer ne tabbas Sageer ne...." Ya faɗa yana zura hannunsa cikin aljihu ya zaro waya ya kunna, nan take ya shiga neman layin Sageer amma duka layinsa har uku a kashe.
Tsaki Kamal yay ya jiye wayar saman kujera, bai ɗauke hannunda ba ya dafe kansa yana fesar da iskar bakinsa waje, a hankali ya furta "oh my god yanzu meye abun yi? Bari dai nayi sallah na kai ki hospital , na temaka miki karki min mushe a mota , gantalaliya kawai..."Ko gama janye hannunsa bai ba daga ajiye wayar ta ɗauki ringing, ya kalli screen ɗin wayar yaga sunan *my cutie angel* na yawo saman screen ɗin wayar, hannu yasa ya ɗauka yay picking ɗin call ɗin ya manna wayar kunnesa tare da cewa"My angel nah ykk ya garin ku mu munsha ruwa sosai fa." ya faɗa cikin cool voice ɗinsa me ratsa jini da tsoka.
Amrah daga can da take kwance hadadɗan bed ɗinsu ta naɗe cikin lallusan bargo ta lumshe idanunta tana jin muryashi na ratsa jininta da bargonta da tsokarta.
Cikin sanyi murya haɗe da ƴar shagwaɓa tace"My hubby ina yini i miss you rabon muyi mgn tin safe , nayi ta kiranka bana samun ka lfy?" ta karasa maganar a shagwaɓe. Kamal da yake dab da isowa get ɗin gidan su ya saki sansanyan murmushi yace"uhm uhm my cutie soryy mana banda kukan da zai zautani irin wannan shagwaɓa , so yanzu ki kashe an jima zamu yi mgn yanzu zanyi sallah ne bayan haka ina tare da alƙaƙai har na rabu dashi kar a mun mushe a mota , zan kira ki an jima." ya faɗa yana murmushi. Amrah tace"Ok amman

Please Login or Register in order to submit comment