bata ta'ba expecting zata ganshi har cikin bedroom dinta ba ."
sosai ya dauki hankalinta yayi wani fresh yayi qara kyau kaman zane ta koina ya hadu matsalar dai shi din mugun miskili ne sai dai hakan ma qara masa kyau yake ahankali ya janye idanunshi acikin nata ya maida dakin yana qarewa koina kallo "Lafiya
yaya adam da wannan zuwan naka na bazata ?"
Shiru yayi yana cizan lips dinsa na kasa kafin daga bisani yace "bai kamata kiyi min wannan tmbyr ba domin kuwa Kinsan dalilin zuwana "ya fad'a alokacin daya jingina jikinsa da mirrow dinta yayi crossing leg's dinsa ya rungume hannuwansa duka a saman faffadan qirjinsa yayi da idanunshi ke kallon zara zaran yatsun kafafunsa."
da kyar ta mike daga zaunen da take tana cewa "ni ban san abinda ya kawoka ba idan dai ba kazo da niyyar karbar soyayyata bane amman kafin nan me zan kawo maka ?"yayi mata banza zuciyarsa na zafi jin yayi shiru km ta rigada tasan halinsa tayiΒ tunanin ta kawo masa ko ruwa ne har tayi taku biyu taji ya fixgota da karfi yana watsa mata wani kallo da idanunshi dake cike taf da bacin rai gbdy taji ta fara muzanta daga kallon da yake mata taji gwiwarta tayi sanyi ."Idanushi ya tsareta dashi yana kallonta yayinda gabanta ya fara faduwa tana adduar allah yasa ba wani laifi tayi masa ba ."
Sai daya gama kallonta sannan ya watsata akan katifa ta sauka da karfi sai da hantar cikinta ya kada still bai dauke idanunshi akanta ba ,nan take ta soma sheshekan kuka sannan ta fara mgn "yaya idan wani laifi nayi maka ya dace ka fad'a min amman wannan kallon naka na hargitsa min lissafi .kallonta ya cigaba da yi bai ce uffan ba har sai data gama ,cikin izza ya motsa labbansa "nasan kin san abinda kikayi sannan kuma kinsa shine dalilin zuwana " cikin mamaki da tsoro take kallonsa ya tsareta fes da idanunshi yana mata kallon banza ."
ranshi a bace ya daidaita tsayuwarsa yana cigaba da kallonta kallon dake qara kashe mata jiki da tsoratarwa "hakika kin tabbatar min da abinda kika turo min a kwanaki uku da suka gabata na zakiga byn mrym , kinyi yunkurin kasheta Kmr yadda kika kashe mubina dan tace tana sona ko?"Idanuwa ta zaro gabanta na faduwa a fili tace" na shiga uku tana dafe qirjinta tare da nuna kanta "ni din na kashe mubina sannan nayi yunkurin kashe mrym ?wani kallon banza yake mata yana jin Kmr ta raina masa wayo ne babu abinda yafi tsana sama da karya yafi son duk abinda ya tmbyeka ka fad'a masa gsky ta haka zaka samu sausauci daga garesa "ban kashe mubina ba me yasa zan kasheta ?"wallahi ban aikata komai ba sannan banyi yunkurin kashe mrym ba tabbas na tura maka sakon zanga bayanta amman wallahi ban aikata hakan ba ,amman ina da niyya to waye yasan da wannan shiri nawa da har ya rigani aiwatarwa?
"Lafiyayyen mari ya zuba mata yana cewa "ni kike wa wannan tmby ?nan take ta rude ta dafe kuncinta inda marin ya sauka abinda yafi damuna kashe mubina da kikayi me tayi miki nuzla ?kuka ta saka mashi tare da durkushewa kasa "wallahi sharri ake son min dan ban san komai akai ba .wani kallo ya watsa mata sannan ya juya mata baya "nasan tabbas kece kika kashe mubina dan hatta wukar da kika kasheta kinyi kuskuren barinta a yunkurin kashe mrym ."
"Da mrym kika kashe wallahi bazai ta'ba damuna ba saboda neman kai nake daita ,ni da zaki kashe min ita amatsayinki na yartaada kafin ta zama mallakina lallai ni kuma da nayi akawarin aureki .nuzla ta sake rudewa ta gigice ta soma jan gwiwowinta ta qaraso inda yake tana kuka "na baki kwanaki goma masu zuwa ki kashe min mrym kafin ta zama mallakina batare da an samu wata hujjar cewar kece kika aikata hakan ba , sannan kada asirinki ya tono ni kuma zan aureki idan kuma kika gagara kasheta har lokacin dana baki ya cikaΒ ni kuma nayi miki alkwarin zan damkaki a hannun hukuma a kwatarwa mubina hakinta kin dai sani idan hukuma ta tabbatar da kece kika kasheta karshenki biyu ne, kisa ta hanyar rataya ko kuma zaman gidan yari na har abada muddin rai kenan yana gama fadar haka ya soma qoqarin ficewa daga dakin .."
Mmn sudais
ππππππ
MAR'ADAMS
ππππ
ππππππ
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 23
Ji tayi qasusuwan jikinta suna barazanar kasa riketa , lokaci guda zuciyarta na barazanar tarwatsewa bata san sanda ta kurma ihu da iyakacin karfinta tana d'aura hannuwanta duka bisa kanta mahaifiyarta hajiya salema ta shigo d'akin da sauri tana dubanta cikin tsananin kad'uwa da tashin hankali, zata iya cewa yanayin data ganta ciki bata ta'ba ganinta cikin irin yanayin ba sai yau wanda shine karo na farko da taga wannan yanayin atare daita , yanayi ne mai cike da firgici da tashin hankali."
Rawar da jikin nuzla yake ya qaru hjy salema ta matso kusa daita ta soma girgiza nuzla wacce ta koma tamkar mutun mutumi a wajen "nuzla nuzla!! lafiya what's wrong with you ?!me ke faruwa dake ? me adam yayi miki kike kuka haka ko ince laifin me kikayi masa dan nasan ruwa baya tsami banza tunda naganshi nasan akwai abinda kikayi masa ? ta jera mata tmbyoyin a rud'e tana riko hannunta cikin nata. nuzla tayi shiru tana wani irin kuka mai d'aga hankali "ki min magana mana ko hankalina zai kwanta ? ta mike a matukar firgice tana duban hjy salema sai dai bata iya amsa mata tmbyoyinta ba dan bata da amsar da zata bata a halin da take ciki ,dan haka ta cigaba da kallonta da rinannun idanunta dake cike da ruwan hawaye kafin daga baya ta fara kuka wiwi tana safa da marwa acikin d'akin hajiya salema na biye daita cikin tsananin damuwa ."
" tabbas idan har hasashe da yarda yaya adam akanta ya tabbata a zuciyarsa to fa tabani ta lalace ta shiga ukunta dan wallahi tasan zai iya aikata fiyye da abinda ya fad'a mata .hankalinta ya sake matukar tashi tabbas tayi niyyar aikata hakan amman daga ita sai Allah'n daya halicceta da zuciyarta da kuma yaya adam ne kawai suka sani ,"ba itace tayi kissan ba to waye yayi ?ta furta hkn a qasan ranta tana furta "wayyo allah na shiga uku ni nuzla ta ina zan fara ? waye yake son jifa rayuwata cikin maseefa ? da wani irin sauri ta nufi kofar fita hjy salema ta biyota tana kiran sunanta amman ina bata tsaya ba tunin ta kai kofar fita daga gidan ta biyo bayan ata ."
ya d'an yi nisa amman bai kurewa ganinta ba dan tana hango bayansa daga inda take ta kira sunansa da karfi cikin tsananin tashin hankali , shi kuwa ata yana jinta amman yaki waiwayowa ya cigaba da tafiya kmr baya son taqa qasa ."ta qara sauri sosai kamar zata hantsila , kallo d'aya zaka wa nuzla ka fahimci bata cikin haiyacinta da natsuwarta ."adaidai bakin kofar shiga side din mami ta iske shi tare da shan gabansa gif haka nuzla ta zube qasa bisa gwiwowinta agabansa idanunta na qoqarin sake kawo ruwa cikin wani irin murya mai gauraye da tashin hankali hade da rudani take furta "yaya ka taimakeni ka tsaya ka fahimceni karka yanke wannan hukuncin wallahi ban san komai akan lamarin nan ba."
ya tsura mata tsumammun idanunshi kafin ahankali ya soma magana cikin izza "taya zan iya yarda da hakan bayan kece da bakinki kika furta hakan kuma kika aikata ? "wallahi wallahi !! idan ka yarda da rantsuwata bani bace sam sam ban aikata abinda kake zargina akai ba hasalima ni yau tsawon kwanaki goma sha biyar kenan kafafuwana basu taka haraban gidan nan ba ina kwance bani da lafiya ."yadda take maganar zaka fahimci tana cikin rud'ani da tashin hankali kamo kafafuuwansa tayi cikin kuka tace "please yaya try to understand me bazan ta'ba aikata hakan ba kawai dai na fad'a maka haka ne dan ka tausaya min ka aureni amman ka yarda dani ban san komai akai ba ."
"Bazan ta'ba yarda dake ba domin nasan zaki iya aikata taadanci makamancinsa koma fiyye dashi a halin yanzu ba wannan magiyar bace ta kamaceki ki fara shirin yadda zaki aiwatar da aikin dana baki idan kuma zaki tonawa kanki asiri nΓ© tun yanzu bismillah ." jikinta da muryarta na rawa tace "baxan damu ba koda asiri zai tono dan ban aikata komai ba bare naji tsoron fallasa kuma Allah shine sheidata ban aikata ba amman zaka iya bincike akan wanda ya aikata abinda kake zargina akai amman ni bani bace kuma duk inda zaa kaini zan tsaya ne akan gskyta bazan ta'ba karban laifin da bani na aikata ba ."
a natse ya soma daga kafafunsa dan wucewa ya barta dan ya gaji da jin sautin muryarta da kukanta yana shiga kanshi over ,yaga tana qoqarin jan gwiwowinta domin biyosa ya kalli securities din dake tsaye a wajen "karku sake ku barta ta shigo ciki "okay yallabai an gama ya shege ciki ya barta durkushe tana kallonsa tmkr wani sabuwar halittta a wajenta ."mikewa tayi tare da cure hannayenta waje daya tana bugawa da juna bata ta'ba shiga tashin hankali da nadama irin ta yau ba har ga allah bata san haka abun zai rikice ya dawo kanta ba ta dauka idan ta fad'a masa haka zataci bulus ne ashe masefa zai zame mata ashe bazataci bulus ba wahala zata sha ?"me yasa batayi shiru da bakinta ba ?me yasa ta gaza hakuri har sai data fito ta fad'a masa shirinta gashi ta kai kanta ta baro ? kaicona ni nuzla bakina ya janyo min matsefa na tarowa kaina bala'i da kaina ta sauke ajiyar zuciya tare da furzar da zazzafar iska daga bakinta ."
"Ai kam wallahi sai dai yayi mata duk abinda zai mata idan ta kama ma ya mikata ga hukuma amman bazata ta'ba aikata abinda yake bukata ba sannan bazata ta'ba karban laifinta ba sai dai idan kasheta zaayi akasheta ta yarda amman bazata cika masa burinsa ba, shi idan har da gaske yake baya qaunar maryam din ya aikata lahira da kashi ba sai ya had'a daita ba da sauri ta juya ta soma tafiya kamar zata tuntsura kasa sai kace mahaukaciya ta shigo gidansu inda ta iske mahaifiyar tsaye cikin zullumi ."
Tana ganinta ta qaraso gareta tana tmbyrta nuzla ta zauna akan kujera jagwaba tana fidda numfashi duk tmbyr da mahaifiyarta take mata bata kulata ba illa hawaye dake zubar mata "wani laifi kikayi wa adam ?tayi shiru kawai batare da tace uffan ba hjy salema tace "to da alamun laifin mai girma kikayi masa yasa har ya biyoki "kamar ta bayyanawa mahaifiyarta halin da take ciki kafin ya damkata hannun hukuma a kashe mata ita a banza a wofi amman ta kasa dan gaskiya bazata iya ba domin tasan irin qaunar dake tsakaninsu kasancewarta auta a wajenta ,banda kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun babu abinda take furtawa tare da dafe kanta dake mata wani irin sara Kmr zai rabe gida biyu hjy salema ta barta ta koma dakinta dan ta fahimci laifi tayi masa mai girma wanda yasa ta kasa furta wa ."
Nuzla ta rufe idanunta gam tana jin yadda maganarsa ke tashi acikin kunnuwanta da zuciyarta so take ta sakawa gangar jikinta hakuri da jarumta har zuwa waadin daya dibar mata ya cika amman ta kasa bata jin zata iya, a halin yanzu ma ba mgnr aurensa bace a gabanta illa mafuta lallai tana bukatar mafuta ta mike tsaye tana zariya acikin parlour'n "ko na gudu ne na bar gidan ne ?ta tmbyi kanta ,gudunki bashine mafuta ba nuzla hakan ma qara min laifi zai yi idan kuma maganar ta fito shikenan kin tabbata mai laifi a wajen kowa dakinta ta shiga tayi zaman dirshan tana saqa da warwara ni dai wallahi nasan bani na kashe mubina ba haka zalika banyi yunkurin kashe mrym ba ,"shin ta ina zan fara ?ni kaina ina bukatar gano wanda yayi hakan , ta lumshe idanunta tana tunani dan dole tayi bincike dan gani wacce tayi yunkurin kashe mrym kuma ko wacece acikin estate dinsu take km itama tana son adam ne Kmr yadda take son shi jikinta ya dauki zafi sosai ."
Zaune mr ata yake akan kujera kushin dake d'akinsa yayi zurfi cikin duniyar tunani yayinda hankalinsa gabadaya ke sake tashi a duk sanda ya tuna da maganar aurensa da mrym sai ya dinga jin hankalinsa na sake tashi , yayinda a kullum ya daura kwayar idanunshi akan yarinyar sai ya dinga jin tsananin tsanarta ,shi da kansa ya kasa sanin takamaimain dalilin dayasa yake jin tsananin tsanarta haka dan bazai ce dan rashin tsawonta bane da kuma kasancewar ta fara bane ya janyo haka yanayinta dai ya taimaka wajen tsanarta ne ,duk yadda yake qoqarin yakice tsanarta da sanyata ko kadan acikin ransa zuciyarsa taki amince da zamanta a tsakaninsa tafe tafe har tunaninsa ya kawo kan zanen wukar dake ajiye akan bedside dinsa wanda aka kashe mubina daita kuma ake qoqarin kashe mrym dashi shine ya zana ya ajiye a wajensa kafin a mika wukar ga hukuma ."
ahankali ya sauke naunauyen ajiyar zuciya ya sake gyara zamansa sosai akan kujerar da yake zaune tunanin duniya yayi akan wacce tayi karfin halin shigo masa gida da taadanci , baya da tabbacin ko nuzla ce domin kuwa har ya gama kallon mai shi ta camerar d'akinsa bai iya gane ko wacece ba zargin nuzla kawai yake bisa yanayin jikin wacce ta shigo da kuma furucin bakinta amman bashi da tabbas akanta bincike ne kawai zai tabbatar masa daita ce ko kuwa wata ce dabam ta kashe mubina km tayi yunkurin kashe mrym "idan wata ce dabam meye dalilinta ?meye hujjarta ? me yasa take yunkurin aikata hakan ?iya tunaninsa yanzu ya fara gane wasu abubuwa akan me kisan wala akanshi ake yi kisan kmr yadda kwakwaluwarsa take haska masa wala kuma wani laifin suka aikata mata take masu dauki dayday ,cikin sanyi jikin nan nasa tamkar mara laka ya matso ya kunna CCTV camera .
idanunsa kawai ya zubawa camerar yana kallon wacce ta shigo masa gida cikin bakaken kaya wondo da riga gabadaya babu inda ta bari wanda zai kafa hujja akanta amman dai tabbas yanayinta ya nuna macece "to wacece wannan yarinyar ?tunaninsa ma yadda ta iya shigowa securities din bakin kofar shigowa basu ganta ba ? ko da yake ta yuwu wani abun tayi masu amfani dashi domin gusar da hankalinsu dan kuwa duk tashin hankali daaka shiga bacci suke basa ma cikin haiyacinsu har sai da aka taimaka masu ,tunda yake a rayuwarsa bai taba ganin mai kaifin baseera irin na yarinyar ba Sannan tunda yake bai taba samun kansa cikin damuwa irin na lokacin ba ,sam sam ya qasa kwanciya yayi bacci sai wurin karfe biyu saura bacci barawo yayi awon gaba dashi ."
bangaren nuzla ma yadda taga safiya haka taga dare ga wani zazzafan zazzabi daya rufeta kafin gari ya waye ta sake yin wata doguwar rama jikinta ya dauki zafi kamar garwashin wuta dan haka dole da gari ya waye aka kira doctor ya dubata nan ya tabbatar masu da damuwa ce dan har jininta ya hau ya wuce kaida yayi ja hankalinta akan yawon tunani sannan ya daura mata drip ya kama gabansa hjy salema ta tsura mata ido kawai tana kallon yadda numfashinta ke fita da kyar ta riko hannunta cikin nata zafin jikinta ya ziyarci tafin hannun hjy salema bata son ganinta cikin damuwa da tashin hankali duk sai taji itama ta shiga damuwa yanzu da tana da dama data cire mata ciwon ta dawo dashi kanta "nuzla !."ta kira sunanta ta bude idanunta dake lumshe ta zubawa mahaifiyarta "meke damunki ko akan hisham ne ?ta gyada mata kai kawai alamun "eh! .
"Halan akan maganar adamu yazo jiya ?ta sake gyada mata kai kawai dan bazata iya magana hjy salema ta numfasa kana ta cigaba da magana "me yasa zaki saka maganar aranki har haka ?tunani shine abu na farko dake fara nukurkusa rayuwar dan adam ,kiyi hakuri ki fallawa allah komai shi keyi a lokacin da yaso haka shi Ke hanawa alokacin daya so fatana Ki barwa allah lamarinki Kiyi addua abinda yafi zama alkhairi atsakaninki dashi Allah ya tabbatar mana, amman ina kyautata zaton zaki ji dadi agidansa zaki samu kwanciyar hankali a hannunsa domin hisham yaron kirki ne amman dai mu cigaba da addua mu barwa allah komai nuzla ta runtse idanunta kawai tana ji da abinda ya dameta ."
tun safe mami da mrym har ma da nana hauwa'u suka shiga kitchen suna had'awa ata breakfast suna hira ,mami ta fito tana amsa wayar hajiya nuriyya wanda adaidai lokacin ata ya sauko hannunwansa duka acikin aljihun wondonsa, sanye da riga brown colour mai hannun long sleeve da dogon wando baki "eh ke dai nuriyya abinda ya faru kenan wallahi acikin estate din nan ne amman yanzu tunda ya dawo in sha allahu bazai wuce a saka sati uku zuwa hudu ba ba ,eh babu damuwa tunda open ticket zakuyi nan ata ya wuce yayi nufi hanyar dakin jim dinsa domin motsa jiki ."
Har yayi taku biyu ya soma jiyo sautin magana kasa kasa kuma abinda yaja hankalinsa shine sunansa da yaji an kira ,ya dan dawo baya kad'an ya tsaya ya kasa kunne yana jin tautaunawarsu "matar yaya adamcy ikon allah miko min kayan ingredient din can na zuba ko ke kadai zaki hadawa mijinki breakfast na cire hannuna na kama gabana?"kai sister kina son kasheni da raina ."
"dan nace matar yaya adamcy ikon allah shine zan kasheki da ranki ?mrym ta gyada mata kai alamun Eh ! ai in sha allahu sai anyi wannan auren ko ana so ko baa so kuma muna bayan ki kamar doro ki zuba mulkinki son ranki a gidansa dan kinci dubu sai ceto babu abinda zai faru "Allah yasa sister dan irin mijin da nake so kenan .
"gashi kuwa kin samu kin yiwa sauran mata zarra ,na yiwa sauran mata zarra ko na fisu shiga matsala ?kina ganin dadi zanji a gidansa ni tun yanzu na fara tunanin yadda tunani da damuwa zai haukatani a gidansa ga rashin sonshi da bana yi ga matsalar taurin kai da wanne zan ji ? ." kina bani mamaki wani lokacin kamar ba mace ba ai ina gaya miki tsab zai sauke komai mrym ta girgiza mata kai kawai tana cewa "taimaka ki zuba min maggie dai dan ni ban san dalili ba duk yadda zan saka maggie a miyya sai yayi yawa ."
"gsky matsalarki kenan sister mman da sannu zaki qara samun gogewa agidan yayana ,wannan yaya dai ana sona dashi shi kuma baya sona,ana son na shiga gidansa shi kuma yace aa wanne zaayi aciki ? "Ke manta dashi wuyarta ayi auren ,ko da yaushe sister haka kike fad'a min wani lokacin sai naji na amince da samu natsuwa ,wani lokacin kuma sai naji hankalina yayi kololuwar tashi ni kaina zan so na ganni a matsayin matarsa dan nasan da sannu zan iya son shi da yana son kenan matsalata a halin yanzu rashin sΓ³n da ....."
saurin datse harshenta tayi da karfi sakamakon ganin mutun tsaye ta bayan nana hauwa'u daman ta juya da niyyar fuskantar nana hauwa'u ne shirunta yasa nana hauwa'u tace "lafiya sister kikayi shiru ? bata iya bata amsa ba illa numfashi data dauke da karfi tana cigaba da kallon bayanta ."
ya tako a natse ya shiga cikin kitchen din sosai kamshin daddan turare da takun da nana hauwa'u taji yasa ta dan juyo ,ta dan tsorata da ganinsa nan take gabanta yayi wani irin mummunar fad'uwa amman sai ta dake ta bude baki da sauri tana cewa "san ..sannu ya.. "saurin d'aga mata hannu yayi yana qara had'e fuska , nana hauwa'u tayi taku biyu zata bi gefensa ta wuce domin ta tsira da lafiyarta taji yace "munafukar allah Koma ki tsaya wato kina d'aya daga cikin masu bawa wannan guntuwar mummunar yarinyar kwarin gwiwar aurena ? tayi saurin girgiza masa kai alamun a'a "zan kifa miki mari yanzu idan kika sake girgiza min kai koni saanki ne ? ta sake girgiza masa kai cikin tsananin tsoro ."
"Kika ce da zarar anyi aure shikenan?idanuwanta sukayo waje wani gumi ya soma tsatsafo mata akan hanci ,sannan kika ce ta manta dani wuyarta ayi auren ni zaa manta dani ?yayi maganar a matukar tsawace cikin bacin rai ,dan allah yaya kayi hakuri nifa ba wani abu nake nufi da hakan ba ina qoqarin gyara au...."ai wani mugun kallo da yayi mata batasan sanda tayi shiru ta qara shiga hankalinta ba ,kinga nayi miki kamata da irin mazan da zarar anyi aure shikenan ?ko kinga nayi miki kama da bawan mace ?ta girgiza masa kai alamun a'a ki shiga hankalinki wallahi idan ba haka nayi sadaka dake na bawa duk wanda naga dama aurenki mu huta sha sha banza da wani katon bakinki a wajen ."
ita kam mrym hannuwanta duka tasa ta rufe fuskarta sakamakon hawayen daya cika mata ido idan akwai abinda ta tsana a kalamansa gareta bai wuce munzantata ta hanyar zagin halittar da Allah yayi mata "Ke kuma na dawo kanki nan da wasu kwanaki zaki zama mata agareni ban isa na hana hakan faruwa ba amman kamar yadda kika furta tunani da damuwa ne zai haukataki a gidana tabbas haka ne domin bakinciki da damuwa zaki aura bani adam ba ,daman tunda kika shiga rayuwata kema kinsan bazakiyi farinciki arayuwarki ba, har karshen rayuwarki a wahala zaki qare a gidana gara ma kije kiyi kuka da Kururuwan a fasa auren nan shine kawai mafuta agareki da kwanciyar hankalinki nonsense kawai da bata san me take yi ba ,yanzu ke kina ganin kin dace dani ?common maggie baki iya sakawa acikin abinci ba sai an taimaka an saka miki stupid girl kawai wallahi gara ki taimaki kanki tun wuri yana gama fadar hk ya juya ya fita daga kitchen din yana jan tsaki ."
kuka mrym ta qarasa fashewa dashi ta koma bayan kofar kitchen ta hade kanta da bango tana jin wani irin zafi mai radadi duk da yadda take jin rashin sonshi amman haka ta bawa zuciyarta hakuri ta karbi aurensa amman shi burinsa yaci mutuncinta ya tozarta tasan yadda ya fad'a haka ne zai kasance rayuwar bakinci zatayi a gidansa zai hanata kwanciyar hankali da walwala ,zai hanata sukuni da jin dadi cike da jin haushi nana hauwa'u tace meye kuma abun kuka ? kina jin tsoron yaya fiyye da kaida ,"shiyasa naga kin iya mutsa masa alokacin da yake magana yake ci min mutunci , ko kin iya taka masa burki alokacin da yake cin zarafina ?tayi mgnr cikin bancin rai tana mai juyowa gbdy ta fuskance nana hauwa'u hawaye na zuba akan kuncinta."
"Sarai kijin abinda ya fad'a yanzu ,kuma Kinsan zai iya aikata fiyye da abinda ya fad'a ,shikenan nan ni haka rayuwata zata qare , kisa hannu sister ki saurari zuciyata kullum cikin bugawa take da karfi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 32 Chapter of 43