suki suki duk yunwa ta gama cinyesa tayi maganar cikin daga murya ".
"Dan allah kiyi hakuri karki saka aunty cikin fadan nan habib yayi Kuskure amman kiyi hakuri bazai sake ba habib ka bata hakuri ".
"What!"
"Allah ya tsareni na bawa wannan matar hakuri kar allah yasa tayi hakuri ko ki fitar mana da wannan mahaukaciyar matar koni yanzu najata na fitar daita sha shar mata mara sallah mai dotti kawai hannu aunty salma ta daga zata wanke masa mari taji ya rike mata hannu sannan ya tsura mata idanunshi cikin sarkewar murya yace "kin gama ta'ba lafiyar kowa acikin gidan nan yanzu ke har yanzu a tunaninki kin kai matsayin da zaki cigaba da marena na kyaleki ? tô idan kina wannan tunanin ki daina yanzu dan zaki ya girma ya wuce wannan tozarcin dan bake ba hatta wanda ya ajiyeki acikin gidan nan kanin mahaifina kenan ba bai isa ba bare ke banza jaka dabba mai hali irin na dabbobi mara hankali ."
a fusace ta fixge hannunta tare da cewa "da uwarka kakeyi itace jaka dabba ai ,dan marasa mutunci irin tsiya irin jaraba tana fada yana maida mata ita kuwa maryama sai faman kuka take tana bawa aunty salma hakuri data gaji ma sai tayi shiru kawai tana kuka tana kallon fuskar habib dake tsine mata yana hadawa da yaranta da kaf dangin mahaifinsu da yasan basa qaunarsu a maganganunsa ta fahimci babu wanda ya tsana kamarsu aunty salma ta fice cikin fushi ta bar dakin cike da tsananin damuwa ."
Maryama ta zauna jagwaba akan kujera tana mai runtse idanunta habib ya lumshe idanunshi "shiyasa kullum suke takura miki wannan sanyin naki yayi yawa ki zama mutun ki nuna masu zamani ki nuna ma kema yar zamani ce sai ku dawo daidai dasu ba kullum ki zauna kina asarar hawayenki a banza ba .""haba after dad mutunci aunty zamu duba yanzu kasan halin matar nan sai taje tayi mana wata kullaliyar a wajen baba gali ".
"taje dan kutumar ubanta shima dan kutumar ubansa yazo daidai nake da kowa allah ya taimakesa yazo idan ban raba masa kanshi gida hudu ba kice Shege ne , anan zan jira zuwansa ya fad'a yana huci tmkr zaki ta mike ta kamo hannunsa ta zaunar dashi ta zauna kusa dashi tana shafa masa baya dan ta fahimci ya dauki zafi dayawa "kayi hakuri komai me wucewa ne wata rana sai labari abinda ya baka dariya wata shi zai saka kuka ka bar aunty salma da duk wanda zai fad'a son rashi acikin gidan nan akanmu."
ita fa aunty salma bata da laifi gani tayi yanuwan mahaifinmu suna yi mana yau da sun ga kima da darajanmu wallahi bata isa ba amman nasan wata rana idan ance tayi bazatayi ba kayi hakuri kaji danuwana rarrashinsa tayita har ya sauko tace "kaje kayi sallah nima zanje nayi kafin aunty su dawo ni na godewa allah ma da bata nan bare taga abun bakinciki kuma allah yasa kar aunty salma ta fad'a wa baba gali "ta fad'a masa mana Ke kike tsoronsa yazo ni yau a gida ma zanyi sallah ina jiran duk abinda zasu dashi bari ma naje na nemo atakobina wacce zan fellewa mutun kai dashi ."
"Dan girma Allah kayi hakuri meye hadinka da takobi kai ba dan daba ba "na zama yau "allah ya tsareni allah kiyaye bazaka zama haka ba Kiyi adduar karsu zo da hauka ya fad'a tare da shigewa dakin aunty kofar tabi da kallo kafin daga baya ta mike taje tayi alwala ta fita ta tada sallah tana cikin sallah tajiyo sallamar aunty tana kiran sunanta tana jin habib ya fita yana cewa "sallah take aunty sannu da zuwa "
"Yauwa habib a she kana gida ?nima ban jima da shigowa ba ina kika je ne ?kai habib zaka fara tambayoyinka kenan babu damar kaga na fita murmushi yay yana sake cewa "aunty ina kike je ?munje duba jikin hafsat ne ta haihu amman cs aka mata ".bai sake cewa komai ba saboda ya fahimci kowace hafsa take nufi diyar aunty fatima yayar mahaifinsu aunty ta mike ta shige dakinta domin yin sallah ."
Byn mintuna goma maryama ta fito daga dakinta zuwan dakin aunty duk jikinta a sanyaye lokacin aunty tana kan dadduma ta idar da sallah tana dai zaune "aunty sannu da zuwa "yauwa my princess ya zaman gida ?ta gyada mata kai alamun Lfy!"ya na ganki wani iri ko akwai abinda me damunki ne ?tayi shiru kawai tana jin faduwar gaba "kin dan daura mana wani abu kuwa ?ta bude bakinta ahankali tana shirin bawa aunty amsa suka jiyo hayaniya shiru tayi tare da kasa kunne muryar baba gali ne ta mike da sauri jikinta har rawa yake ta nufi kofar fita itama aunty ta biyo bayanta a tsakiyar falon suka gansa tsaye tare da aunty salma da aunty hassana sai hargagi suke tamkar wasu karnuka yayinda habib ya shiga kitchen ya dauko zabgegiyar takobinsa mai tsine ya koma bakin dakalin kofar fita ya zauna yana wasa takobinsa ,aunty hasana ta nufo inda yake shi kuwa habib kanshi na kasa yana cigaba da wasa takobinsa jira kawai yake suyi masa wata maganar banza ."
Aunty ta kalli maryama ta kalli habib tana bukatar qarin bayani cikin fusata aunty salma tace babu irin qare maku zagin da wannan tantirin yaron bai yi ba ta uwa ta uba har da ce mana dabbobi jakuna aunty hasana tace "da ubansa yake Shege dan Shegiya "da sauri ya mike yana zagayesu da takobi kiiiii kake jin tsinin bakin takobi asimintin falon basu ba hatta aunty da maryama sun tsorata "kai ko ka fara shaye shaye ne ko meye ?"da sauri ya juyo kan baba gali da yayi mgn fuskarsa a tsuke alamun bai son ya kawo masa raini "dan ubanka da kake zare masa idanu ka dauka zamu ji tsoronka ne ?"
"a'a nasan bakwa jin tsorona kamar yadda nima yanzu babu wannan tsoron duk wanda ya nemi zaman lafiya ayi wanda yace sabanin haka yake bukata bismillah ni bazan bata bakina ba sassara mutun kawai zanyi na aika sa lahira ."ya fad'a yana tsoka takobi daidai kafar baba gali ."
Da wani saurin gabadayansu suka ja baya suna kallonsa da mamaki kamar yadda aunty Ke kallonsa "tunda ku kun zama ahlin sheidan bakwa jin wani yare sai na dabbobi bismillah nima zan nuna muku akwai digon wannan dabbar ajikina ,tunaninku me zakuyi da kuka wani kwaso jiki gbdynku kuka zo ?
"To wallahi yau koni ko ku duk wanda ya zagi uwata da yaruwata sai na yanke masa harshe byn na raba kanshi gida hudu ."
zaro idanuwa sukayi suna sake ja baya dan ya daga takobin hannunsa daga aunty hassana har aunty salma suka koma bayan baba gali suka boye cikin karfin halin yace " bamu bane dabbobi da uwarka kake aiko jin haka Ke da wuya habib yayi kansa gadan gadan zai sara mata takobi aunty ta rike masa hannu tana zabga masa mari cikin muryar kuka tace "meke damunka habib ta fad'a tana kwace takobin tayi jifa dashi "zaka kasheni ne ?
"Ai da zai kashe dabba irinki da mun samu kwanciyar hankali "inji cewar aunty salma .
aunty kina jinsu ko bani takobina na sassara
shegu yan kutumar uba .."inna lillahi wa inna ilaihi rajiun allahumma ajirni fi musibatihi Waklifli khairan minha tana gama fadar haka ta durkushe kasa tana cewa "yanzu habib irin tarbiyar dana baka kenan ?maryama ta durkusa kusa daita tana mai rike hannunta tana ma habib wani irin kallo mai cike da tashin hankali ".
"Me yasa bazaka koyi danne fushinka ba ?me yasa zaka min haka habib ? me nayi maka dana cancanci haka habib ? "Kuji makira ina allonki allonki yana jahannama ,makira mata kin gama koya masa yadda zai ci mutunci mutune shine yanzu kizo kina kukan munafurci yau zamanku ya qare acikin gidan nan ku hada ina ku ina ku ku bar mana gidan nan mun gaji da ganinku daga Ke har wadan nan mataiyatan yayan naki bama bukatarku."inji cewar baba gali ."
nan da nan habib yayi kan baba gali duk da yaso ya rabu dashi ganin mahaifiyarsa tana kuka dan a duniya babu abinda ya tsana sama yaga ana cin mutunci mahaifiyarsa da yar uwarsa baya son ana zagar masa su bare a zagi qaddararta da binta da muyagun kalamai ko zubar hawayenta ,wuyan baba gali yake shirin damka ya
jiyo sautin muryar aunty cikin kuka tana cewa "wallahi habib idan ka ta'ba shi sai na tsine maka albarka "cak ya tsaya yana kallon baba gali ido cikin ido jikinsa na wani irin rawa tamkar mazari ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 16
Ahankali maryama ta mike daga cinyar umma hawaye ne sha'be sha'be akan kuncinta
ta tsurawa umma manyan idanunta wad'an da suka canza kala tana kallonta batare da tace uffan ba ,duk yadda taso ta daure ta tsaida hawayenta kasawa tayi hawaye take zubarwa sosai cikin tashin hankali mai tsanani ita kad'ai tasan halin bakinciki data tsinci kanta ciki adalilin jin labarin iyayenta ."labarinsu yayi matukar d'aga mata hankali "a she wahaalarsu da tsanar da'aka yi musu acikin family's ta samo asali ne daga soyayyar iyayensu ? haka nan taji tausayin kansu na sake shigarta . "
Koina ajikinta yayi sanyi yayinda falon ya d'auki shiru ,yadda maryama tayi shiru tana zubar da ruwan hawaye tana sake tariyo halin da iyayenta suka tsinci kansu adalilin soyayya haka ma umma bata sake cewa komai ba " ahankali wani irin so da qaunar mahaifiyarta da qaninta habib ya qara shigarta" allah sarki aunty "hakika kinga rayuwa, hakika ahlinki sun d'auki zafi dayawa akanki ."
"hukuncinsu yayi tsanani dayawa domin allah Ke had'a soyayya alokacin daya so ba dabarar mutun ba ,ba son ran mutun bane ,domin kuwa idan da dabarar mutun ne ko son ran mutu da mutanen duniya dayawa basu tsinci kansu cikn
ta ba ."
a qalla sun d'auki minti goma a haka suna kallon juna sannan maryama ta lumshe idanunta da sukai jajur alamun tarin quna da bakinciki ahankali umma ta numfasa "maryama ! ta kira sunanta a natse , ahankali ta motsa lip's dinta alamun ta amsa dan zafin da zuciyarta keyi ya danne fitowar muryarta "ki godewa allah ba kuka ya kamata kiyi ba maryama."
"ki godewa allah daya qaddara aure a tsakanin iyayenki da har aka sameku ta hanyar sunanh " "Alhmd!ta furta a can kasan makoshinta tana dafe kanta dake sara da mugun karfi "ya kai ki godewa allah ki sake gode masa ko bai kai ba ? kanta ta gyada mata alamun "eh!.
"To ki manta da duk abinda na fad'a miki muje Kiyi sallah kici abinci ki kwanta ki huta " da karfi maryama ta fizgo magana "bazan iya manta komai ba ,a halin yanzu ma ganin komai nake kamar a yanzu ya faru har nayi danasani umma nayi danasani jin wannan mummunar labarin rayuwa irin rayuwar da iyayena sukayi rayuwar kaskanci ne a wajena."
"why umma? "me yasa komai yake faruwa damu haka ?ahankali ummah ta shafa kanta
zuwa gadon bayanta tare da cewa "kiyi hakuri maryama kowa da kalar irin tasa qaddara a yanzu jajurcewa zaki qara akan wanda kikayi har kika samu cikar burinki na zamowa cikakkiyar mai ilimin lissafi ,kiyi qoqari ki tsaya bisa kafafunki domin tallafawa rayuwar mahaifiyarki daya qaninka domin ina hango tarin nasara da kwanciyar hankali atattare dake , bilkisu na bukatar farinciki ,maryama nasan da sannu zaki zamewa bilkisu sanyin idaniya amman fa sai kin manta komai maryama kin rungumi qaddarar rayuwarku ."
"Na yarda da qaddara ummah domin yana daga cikin cikar imani mutun , na yarda da qaddara amman umma aunty tayi kuskure arayuwarta bance laifi bane dan taso mahaifina amatsayin da yake amamn iyaye fa umma ? "manzon sallahu alaihi wa salam yace "ridal lahi fi ridal walidaini , wa sakad'ul lahi fi sakad'il walidai ."yarda allah yana tare da yarda iyaye, haka zalika fushin allah yana tare da fushin iyaye allah ya fifita iyaye akan komai most especially uwa ummah ,babu uwar da taza ji dadin irin rayuwar da aunty tayi ."
umma tayi shiru kawai tana sauraronta "misali na kwatantawa aunty irin abinda tayiwa iyayenta ya zataji ? na kawo mata in responsible man nace naji nagani sai shi duk tarbiyar da tayi tsawon shekaru tana bani nasa kafa na rugujeta ya zataji ?" magana ta gaskiya iyeyenta da yan' uwanta sun d'auki zafi dayawa amman aunty ta fisu laifi kuma lallai ya kamata taje ga iyayenta ta roki gafararsu sannan ta koma cikin danginta zuciyarta ta samu salama ."
"wallahi yadda nake jin habib araina bazan iya barinsa saboda wani ba bare iyayena da suka kawoni duniya ba ,abun da ciwo ummah ba kamar yadda kuka d'auka bane kema uwa ce ummah , aunty ta kona zuciyar mahaifiyarta dayawa, yanzu na gano duk aunty ce silar shigarmu cikin matsala , iyayenta na can suna fushi daita har yau ta yaya kike tunanin zataji dadi ?"ta yaya kike tunani zan iya bata farinciki byn ga inda zata samu fiyye da nawa ."?
maryama ta kalli umma cikin sarewa ta cigaba da magana " umma abun na da matukar ciwo irin ciwon dake cin zuciya da bargo ,ciwo ne da bashi da magani da mafuta har sai ka had'u da mahad'inka , shiyasa a kullum idan na kalli aunty sai naji tamkar tana boye mana wani abu mai mahimanci ga rayuwarta , ashe gsky né hakika bakinta bazai iya furta mana komai akan rayuwarta ba matsawar ita din uwa ta gari
ce , dan allah umma Kiyi min rai ki raba zuciyarta da wannnan rayuwar idan kuma baki yi ba ni zanyi ,zan rabata da nauyin dake daskare a qirjinta ."
Tana gama fadar haka ta mike a hankali tana share hawayen idanunta da suka gagara tsayawa tana jin wani zafi a qirjinta , bazata cigaba da d'aukar wannna nauyin ba , koda aunty bata amince ta koma ga yan'uwanta ba ,lallai ita zata nemosu a duk inda suke acikin garin nan ."muryarta a sanyaye tace "umma ni zan wuce sai da safe " kai kawai ummah ta gyada mata sannan maryama ta fara tafiya umma tayi shiru tabi bayanta da kallo tana kallon yadda take d'aga zara zaran yatsun kafafunta da kyar tamkar wacce bata da laka ."
" A inda ta bar mahaifiyarta anan ta sameta tare da habib suna hira da alamun shi baya cikin damuwa kamar ita." bata tsaya ba byn tayi sallama tace "aunty sai da safe tana gama fadar haka ta wuce ta nufi d'akin baccinta bayanta suka bita da kallo , yanayinta kad'ai ya fahimtar da aunty akwai tarin damuwa atattare daita shiru kawai tayi tana tunani "har yaushe maryama zata yi farinciki arayuwarta ?".
A natse aunty ta mike tabi bayan maryama tana jin tsinkewar zuciya haka shima habib akan kujerar da take zama idan zatai zane suka isketa ta dafe kanta tana sheshekar kuka atare suka qaraso suka zauna abakin gado suna fuskantarta shigowarsu yasa ta tsaida kukanta wanda taso tayisa sosai har taji natsuwar zuciyar."
dogon numfashi aunty taja tare da cewa "na shiga uku ni bilkisu " ta furta cikin tsananin tashin hankali dan bata qaunar abinda zai d'agawa yaranta hankali shi kuwa habib hannun maryama ya kamo cikin nashi ya damke da karfi cikin tsananin tashin hankali " heartbeat meke damunki ?." muryarta a raunane tace "babu komai after dad "ya babu komai zaki shigo cikin damuwa , yanzu mun shigo mun ganiki kina kuka amman kice babu komai ki fad'a min idan akwai abinda ke damunki ."
shiru tayi tana cigaba da shesheka "ki sani bamu saba boyewa juna komai ba idan kika min haka baki min adalci ba ,ko km damuwar dazu ce ? still dai shiru tayi ,sosai suka d'aga hankalinsu ita kuma taki cewa komai sai faman ajiyar zuciya ta saukewa ." damke hannunta ya sake yi sosai yana rokonta "dan allah heartbeat karki daga mana hankali ki fad'a min kukan me kike yi ?kallonsa kawai tayi tana lumshe idanuwanta ganin yadda hankalinsa yay matukar tashi da yadda ya d'aga hankalinsa ya matukar bata tausayi daman kuma haka ne idan daya yana cikin damuwa dole ne daya shima ya tsinci kanshi cikin damuwa."
"Yanzu princess bazaki koyi dauriya akan kowacce irin damuwa bace domin ki tsira da rayuwarki da rayuwarmu gabadaya ,Ke kenan kullum cikin zubar da hawaye akan damuwa me yasa zaki dinga asarar hawayenki tare da qoqarin kashe kanki abanza ."?
"Gara dai ki fada mata gsky aunty domin ita rayuwar nan da take ganinta wani lokacin idan abubuwa suka wa mutun tsanani dole mutu ya rage wasu abubuwa domin tsira da rayuwarsa da lafiyarsa."
hawayen da take qoqarin maidawa ne suka samu nasarar gangarowa bisa kuncinta cikin sauri tashiga gogewa wasu na sake gangarowa duk yadda suka dinga kwantar da kai da murya dan suji damuwarta amman taki fad'a masu komai domin da zarar ta bude baki hawaye da sheshekan kuka Ke hanata magana dole tasa suka daga mata kafa suka fice d'aya bayan d'aya daga dakin da zumar zasu lalla'bata gobe ta fad'a masu dalilin kukan ."
tafi mintuna goma byn fitar aunty da habib zaune sannan ta yunkura ta tashi tana sauke naunayen ajiyar zuciya ta shiga bayi ta d'auro alwala ta fito ta gabatar da sallahr magariba da isha'i tare da shafa'i da wutiri byn ta idar ta koma kan katifa ta zauna tare da jingina bayanta da pillow ta rungume hannuwanta duka a qirjinta ."
ahankali ta runtse idanunta tana tariyo komai daya faru dasu tun suna yara "Kenan adalili rasa mahaifi da kaka yasa rikonsu ya dawo hannun abban sadam ."tun tana qarama yar shekara hud'u a duniya ta taso cikin so daga bangaren abban sadam da umma da mahaifiyarta amman daga bangaren aunty hassana da sauran 'yan'uwan mahaifinta kuwa saboda haushin da kiyayyar mahaifiyata yasa suka dinga nuna masu tsana da tsamgwama , sun ci wuyarsu sosai most especially Ita ganin kiyayyar dangin mahaifinsu da irin tsanar da baba gali yayi masu ya bawa aunty salma damar cin kashi akansu da mahaifiyarta ."
tun daga lokacin kuruciya har zuwa girmanta abinda yake rage mata zafin gidan shine soyayyar umma bancin ita kowa a gidan baya sonsu amman kuma wani lokaci shi kanshi baba gali ya kan tausaya masu in dai ba fad'a sukai da sakina ba ko yarshi qarama ba , idan tayi mata laifi ta d'an daketa shine zai fito da 'bacin ransa har ya fito da zallar kiyayyarsa ,kuma tun da ta lura son ya'ya ne dashi domin ba ita ba ko uwar data tsugunna ta haifesu baya raga mata akan ya'yansa ."
"yayan baba gali uku ne aliyu sakina wacce sa'artace sai mai bi mata salamatu wacce taci sunan hajiya kakarsu ana kiranta da shukura bata fi shekara sha bakwai ba a yanzu ,itama babu yabo babu fallasa suna d'an shiri daita sai dai idan taga uwarta na fushi da zagina bata hanata sai ma dai ta zugata domin itama tana nuna kishinta akainta idan taga umma tana tarairayata ko wani ."
Baba gali dinki yake ada rasuwar abban sadam yasa gidan buredi da rikonsu ya koma hannunsa alhamdulillah babu laifi ita din mai qokari ce ta kowani fanni boko da arabic ga baiwar zane da Allah ya bata ."
Alokacin baya kullum ta allah sai aunty tayi masu special lesson ita da habib kusan kokarinta ta samu ne a wajen mahaifiyarta ,duk unguwar da makarantarsu ana maganarsu akan ilimi bokon da suke dashi haka duk gidan ba masu jin turanci kamar ita da habib ko wani abu za'a tambaya ita ko habib ake tambaya mahaifiyarsu ta tsaya masu akan karatunsu shiyasa ma education dinsu yayi very fast kuma à sanadiyar qoqarinta ita da kawarta subai'a yasa gwanati ta dauki nauyin karatunsu zuwa lagos state university ".
bangaren sakina da sauran yaran gidan matsalar iyayensu ne dan basa maida hankali akan karatun yaransu gashi sam basu da isashen ilimin boko ko Arabic barin ma aunty salma karta ji labari ba arabi ba boko sai uban girman kai ,sau tari idan shukura tazo koyon wani abu a wajenta bata só sai ta nuna ai itama tasani dan me zatazo wajenta akarshe idan tayi mata zero take samu a makaranta shiyasa da yarinyar ta gane ta daina bata idan tace ta kawo kai tsaye take ce mata bataso zero zataci ."
hatta alwala ba daidai aunty salma take yi ba kuma sallah ma bata dameta ba ,tun suna yara baba gali Ke mata fad'a akan tarukun sallah din da take yi amman taki ta daina shi kansa daya gaji sai ya rabu daita ya dinga Kwa'bar yaransa da yin sallah sanin in har dan uwarsu ne sai dai kar su yi babu abinda ya dameta dan idan ma koyi zasu yi daita sai dai su koyi taruku sallah."
Su kuwa aunty bata yarda tana gama dauro alwala zata tura habib zuwa masalaci ita km ta umarceta taje tayi alwala sannan a kullum dare auty ta kan fito tsakar gidan tare dasu har sakina kasancewar tana qaunarta ta koya masu darasin lissafi , tana daukar lokaci akansu har sai taga sun gane sannan ta bukaci wanda yake da damuwa a bangaren karatunshi ko baka da matsala zatai 'yan tambayoyi ana bata amsa idan bata gamsu da amsar ba ta qara yi masu bayani , bangaren karatun alqurni kafin suyi bacci sai aunty tasa sun karanta izawaka da tabaraka kafin su kwanta da safe kuma sai sunyi murajaa alqurni sannan su shirya su wuce school ko islamiyya ."
A ranar batayi isashen bacci ba ga tsananin tunani ga kwadayin son ganin yan'uwan mahaifiyarta gargadin kanta ta shigayi akan fad'awa soyayya da ma ko waye idan kuma soyayyar ta zama dole sai dai tayi a gidan aurenta ga duk wanda ta aura har asuba tayi maryama batai wani yi baccin kirki ba shiyasa kiran sallahr farko acikin kunnenta akayi ta gyara kwanciyar ta koma ta kwanta bacci kad'an tayi ta lalubo wayarta ta duba taga biyar da rabi saura lokacin sallah yayi dan har an tada sallah a matsalacin unguwarsu ."
a hankali ta mike zuciyarta cike da damuwa bakinta dauke da adduar tashi daga bacci ta kai tafukan hannunta tana shafa fuskarta sannan a natse ta zuro kafafunta ta sauko ta shiga bayi ta dauro alwala ta fito cike da sanyin jiki ta gabatar da sallah asuba byn ta idar ta d'auko alqurni ta soma karatu cikin suratul baqara anatse ta kai idanunta ga window d'akin taga gari ya fara sha tayi azkar din safe tana nan zaune tana lazimi har shida saura sannan ta koma ta kwanta akan sallaya nan da nan bacci mai nauyi ya dauketa ba ita ta tashi ba sai goma saura ."
Ta mike da kyar bakinta dauke da salati sakamakon qirjinta dake wani irin bugawa ta
gyara gadonta ta fita ta dauko tsintsiyar shara
ta share d'akin ta fito har falo ta shiga d'akin mahaifiyarta bata ganta ba tasan may be ko tana byn gida wajen yin wanki ,dan wannan kaida ne kullum safiya sai tayi wanki kayanta wani lokacin da nasu ta share d'akin tasss ta fito da sharan zuwa falo ta shiga kitchen ta hada kayan wanke wanke ta wanke atake ta goge koina ta sharo sannan ta hada da share falo tayi mopping ta koma daki ta cire kayan jikinta ta shiga wanka bata wani jima ba tayi alwala ta fito kai tsaye ta shimfida daddumar sallah ta sallacci salatul duhu byn ta idar ta shirya kanta ta kwanta lamo cikin zullumi ta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 43