Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
suki suki duk yunwa ta gama cinyesa tayi maganar cikin daga murya ". "Dan allah   kiyi  hakuri  karki saka aunty cikin fadan nan habib yayi Kuskure amman kiyi hakuri bazai sake ba habib ka bata hakuri ". "What!" "Allah ya tsareni na bawa wannan matar hakuri kar allah yasa tayi hakuri ko ki fitar mana da wannan mahaukaciyar matar koni yanzu najata na fitar daita sha shar mata mara sallah mai dotti kawai hannu aunty salma ta daga zata wanke masa mari taji ya rike mata hannu sannan ya tsura mata idanunshi cikin sarkewar murya yace "kin gama ta'ba lafiyar kowa acikin gidan nan yanzu ke har yanzu a tunaninki kin kai matsayin da zaki cigaba da marena na kyaleki ? tô  idan kina wannan tunanin ki daina yanzu dan zaki ya girma ya wuce wannan tozarcin dan bake ba hatta wanda ya ajiyeki acikin gidan nan  kanin mahaifina kenan ba bai isa ba bare ke banza jaka dabba mai hali irin na dabbobi mara hankali ." a fusace ta fixge hannunta tare da cewa "da uwarka kakeyi itace jaka dabba  ai ,dan marasa mutunci irin tsiya irin jaraba tana fada yana maida mata ita kuwa maryama sai faman kuka take tana bawa aunty salma hakuri data gaji ma sai tayi shiru kawai tana kuka tana kallon fuskar habib dake tsine mata yana hadawa da yaranta da kaf dangin mahaifinsu da yasan basa qaunarsu  a maganganunsa ta fahimci babu wanda ya tsana kamarsu aunty salma ta fice cikin fushi ta bar dakin cike da tsananin damuwa ." Maryama ta zauna jagwaba akan kujera tana mai runtse idanunta habib ya lumshe idanunshi "shiyasa kullum suke takura miki wannan sanyin naki yayi yawa ki zama mutun ki nuna masu zamani ki nuna ma kema yar zamani ce sai ku dawo daidai dasu ba kullum ki zauna kina asarar hawayenki a banza ba .""haba after dad mutunci aunty zamu duba yanzu kasan halin matar nan sai taje tayi mana wata kullaliyar a wajen baba gali ". "taje dan kutumar ubanta shima dan kutumar ubansa yazo daidai nake  da kowa allah ya taimakesa yazo  idan ban raba masa kanshi gida hudu ba kice Shege ne , anan zan jira zuwansa ya fad'a yana huci tmkr zaki ta mike ta kamo hannunsa ta zaunar dashi ta zauna kusa dashi tana shafa masa baya dan ta fahimci ya dauki zafi dayawa "kayi hakuri komai me wucewa ne wata rana sai labari abinda ya baka dariya wata shi zai saka kuka ka bar aunty salma da duk wanda zai fad'a son rashi acikin gidan nan akanmu." ita fa aunty salma bata da laifi gani tayi yanuwan mahaifinmu suna yi mana yau da sun  ga kima da darajanmu wallahi bata isa ba amman nasan wata rana idan ance tayi bazatayi ba kayi hakuri kaji danuwana rarrashinsa tayita har ya sauko tace "kaje kayi sallah nima zanje nayi kafin aunty su dawo ni na godewa allah ma da bata nan bare taga abun bakinciki  kuma allah yasa kar aunty salma ta fad'a wa baba gali "ta fad'a masa mana Ke kike tsoronsa yazo ni yau a gida ma zanyi sallah ina jiran duk abinda zasu dashi bari ma naje na nemo atakobina wacce zan fellewa mutun kai dashi ." "Dan girma Allah kayi hakuri meye hadinka da takobi kai ba dan daba ba "na zama yau "allah ya tsareni allah kiyaye bazaka zama haka ba Kiyi adduar karsu zo da hauka ya fad'a tare da shigewa dakin aunty kofar  tabi da kallo kafin daga baya ta mike taje tayi alwala ta fita ta tada sallah tana cikin sallah tajiyo sallamar   aunty tana kiran sunanta  tana jin habib ya fita yana cewa "sallah take aunty sannu da zuwa " "Yauwa habib a she kana gida ?nima ban jima da shigowa ba ina kika je ne ?kai habib zaka fara tambayoyinka kenan babu  damar kaga na fita murmushi  yay yana sake cewa "aunty ina kike je ?munje duba jikin  hafsat ne ta haihu amman cs aka mata ".bai sake cewa komai ba saboda ya fahimci  kowace hafsa take nufi diyar aunty fatima yayar mahaifinsu aunty ta mike ta shige dakinta domin yin sallah ." Byn mintuna goma maryama ta fito daga dakinta  zuwan dakin aunty  duk jikinta a sanyaye lokacin aunty tana kan dadduma ta idar da sallah tana dai zaune  "aunty sannu da zuwa "yauwa my princess ya zaman gida ?ta gyada mata kai alamun Lfy!"ya na ganki wani iri ko akwai abinda me damunki ne ?tayi shiru kawai tana jin faduwar gaba "kin dan daura mana wani abu kuwa ?ta bude bakinta ahankali tana shirin bawa aunty amsa suka jiyo hayaniya shiru tayi tare da kasa kunne muryar baba gali ne ta mike da sauri jikinta har rawa yake ta nufi kofar fita itama aunty ta biyo bayanta a tsakiyar falon suka gansa tsaye tare da aunty salma da aunty  hassana sai hargagi suke tamkar wasu karnuka yayinda habib ya shiga kitchen ya dauko zabgegiyar takobinsa mai tsine ya koma bakin dakalin kofar fita  ya zauna  yana wasa  takobinsa ,aunty hasana ta nufo inda yake shi kuwa habib kanshi na kasa yana cigaba da wasa takobinsa  jira kawai yake suyi masa wata maganar banza ." Aunty ta kalli maryama ta kalli habib tana bukatar qarin bayani cikin fusata aunty salma tace babu irin qare maku zagin da wannan tantirin yaron bai yi ba ta uwa ta uba har da ce mana dabbobi jakuna aunty hasana tace "da ubansa yake Shege dan Shegiya "da sauri ya mike yana zagayesu da takobi  kiiiii kake jin tsinin bakin takobi asimintin falon basu ba hatta aunty da maryama sun tsorata "kai ko ka fara shaye shaye ne ko meye ?"da sauri ya juyo kan baba gali da yayi mgn fuskarsa a tsuke alamun bai son ya kawo masa raini "dan ubanka da kake zare masa idanu ka dauka zamu ji tsoronka ne ?" "a'a nasan bakwa jin tsorona kamar yadda nima yanzu babu wannan tsoron duk wanda ya nemi zaman lafiya ayi wanda yace sabanin haka yake bukata bismillah ni bazan bata bakina ba sassara mutun kawai zanyi na aika sa lahira ."ya fad'a yana tsoka takobi daidai kafar baba gali ." Da wani saurin gabadayansu suka ja baya suna kallonsa da mamaki kamar yadda aunty Ke kallonsa "tunda ku kun zama ahlin sheidan bakwa jin wani yare sai na dabbobi bismillah  nima zan nuna muku akwai digon wannan dabbar ajikina  ,tunaninku me zakuyi da kuka wani kwaso jiki gbdynku kuka zo ? "To wallahi  yau koni ko ku duk wanda ya zagi uwata da yaruwata sai na yanke masa harshe byn na raba kanshi gida hudu ." zaro idanuwa sukayi suna sake ja  baya dan ya daga takobin hannunsa daga aunty hassana har aunty salma suka koma bayan baba gali suka boye cikin  karfin halin yace " bamu bane dabbobi da uwarka kake aiko jin haka Ke da wuya habib yayi kansa gadan gadan  zai sara mata takobi  aunty ta rike masa hannu tana zabga masa mari cikin muryar kuka tace "meke damunka habib ta fad'a tana kwace takobin tayi jifa dashi  "zaka kasheni ne  ? "Ai da zai kashe dabba irinki da mun samu kwanciyar hankali "inji cewar aunty salma . aunty kina jinsu ko bani takobina na sassara shegu yan kutumar uba .."inna lillahi wa inna ilaihi rajiun allahumma ajirni fi musibatihi   Waklifli khairan minha tana gama fadar haka ta durkushe kasa tana cewa "yanzu habib irin tarbiyar dana baka kenan ?maryama ta durkusa kusa daita tana mai rike hannunta tana ma habib wani irin kallo mai cike da tashin hankali ". "Me  yasa bazaka koyi danne fushinka ba ?me yasa zaka min haka habib ? me nayi maka dana cancanci haka habib ? "Kuji makira ina allonki allonki yana jahannama ,makira  mata kin gama koya masa yadda zai ci mutunci mutune shine  yanzu kizo kina kukan munafurci yau zamanku ya qare acikin gidan nan ku hada ina ku ina ku ku bar mana gidan nan mun gaji da ganinku daga Ke har wadan nan mataiyatan yayan naki bama bukatarku."inji cewar baba gali ." nan da nan habib yayi kan baba gali duk da yaso ya rabu dashi ganin mahaifiyarsa tana kuka dan a duniya babu abinda ya tsana sama yaga ana cin mutunci mahaifiyarsa da yar uwarsa baya son ana zagar masa su bare a zagi qaddararta da binta da muyagun kalamai ko zubar hawayenta  ,wuyan baba gali yake shirin damka ya jiyo sautin muryar aunty cikin kuka tana cewa "wallahi habib idan ka ta'ba shi sai na tsine maka albarka "cak ya tsaya yana kallon baba gali ido cikin ido jikinsa na wani irin rawa tamkar mazari ." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗      MAR'ADAMS      💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access  idan an tura sai a turawa wannan  09136918331  alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.              Page 16 Ahankali   maryama   ta  mike  daga  cinyar  umma   hawaye  ne  sha'be sha'be  akan   kuncinta ta tsurawa umma  manyan    idanunta  wad'an da   suka   canza   kala  tana kallonta   batare  da   tace  uffan  ba  ,duk  yadda  taso  ta daure  ta  tsaida  hawayenta  kasawa   tayi  hawaye  take   zubarwa  sosai  cikin  tashin  hankali  mai  tsanani ita  kad'ai  tasan  halin  bakinciki  data  tsinci   kanta   ciki   adalilin   jin  labarin   iyayenta ."labarinsu  yayi  matukar  d'aga  mata  hankali "a  she  wahaalarsu  da  tsanar  da'aka yi  musu   acikin  family's  ta  samo  asali  ne  daga  soyayyar  iyayensu ?  haka nan  taji   tausayin  kansu  na   sake  shigarta   . "      Koina   ajikinta   yayi  sanyi  yayinda   falon  ya  d'auki  shiru  ,yadda  maryama  tayi  shiru tana zubar da  ruwan hawaye  tana sake tariyo  halin  da  iyayenta  suka tsinci  kansu  adalilin  soyayya haka ma  umma  bata  sake  cewa  komai  ba  " ahankali  wani  irin  so  da  qaunar   mahaifiyarta da qaninta  habib   ya  qara  shigarta"  allah  sarki  aunty  "hakika  kinga   rayuwa,  hakika   ahlinki  sun  d'auki  zafi  dayawa  akanki  ." "hukuncinsu  yayi tsanani  dayawa  domin  allah Ke had'a  soyayya  alokacin  daya so ba  dabarar  mutun  ba  ,ba  son ran mutun  bane  ,domin  kuwa  idan da  dabarar  mutun  ne  ko  son ran mutu da  mutanen  duniya  dayawa  basu  tsinci  kansu  cikn ta ba ." a qalla  sun  d'auki  minti  goma a haka  suna  kallon  juna   sannan  maryama ta  lumshe  idanunta da sukai   jajur  alamun  tarin  quna da bakinciki ahankali  umma  ta  numfasa  "maryama !  ta  kira sunanta  a  natse , ahankali  ta motsa  lip's  dinta  alamun ta amsa dan  zafin  da  zuciyarta  keyi  ya danne  fitowar  muryarta "ki  godewa  allah  ba  kuka ya  kamata kiyi   ba  maryama."     "ki  godewa  allah  daya  qaddara  aure  a tsakanin  iyayenki  da  har  aka sameku  ta  hanyar  sunanh "  "Alhmd!ta  furta  a can kasan   makoshinta   tana  dafe  kanta  dake  sara da mugun karfi "ya  kai  ki godewa  allah  ki  sake  gode  masa  ko  bai  kai ba ? kanta  ta  gyada  mata  alamun "eh!. "To  ki  manta  da  duk  abinda na  fad'a  miki  muje  Kiyi  sallah  kici  abinci  ki kwanta ki huta "  da  karfi  maryama  ta  fizgo  magana  "bazan  iya manta komai  ba ,a halin  yanzu  ma   ganin  komai   nake kamar   a yanzu  ya  faru  har  nayi  danasani  umma nayi  danasani   jin  wannan  mummunar   labarin  rayuwa  irin  rayuwar   da  iyayena  sukayi  rayuwar kaskanci  ne a wajena."     "why  umma? "me  yasa  komai yake  faruwa  damu haka ?ahankali  ummah  ta  shafa  kanta zuwa gadon bayanta  tare da cewa "kiyi  hakuri  maryama kowa da  kalar  irin  tasa  qaddara a yanzu  jajurcewa  zaki qara  akan  wanda  kikayi  har kika samu  cikar  burinki  na  zamowa  cikakkiyar  mai  ilimin  lissafi  ,kiyi  qoqari  ki tsaya  bisa  kafafunki  domin  tallafawa  rayuwar   mahaifiyarki   daya  qaninka   domin  ina  hango  tarin nasara  da  kwanciyar  hankali  atattare  dake , bilkisu  na  bukatar  farinciki  ,maryama  nasan  da sannu  zaki  zamewa  bilkisu  sanyin  idaniya  amman  fa  sai kin manta  komai  maryama  kin rungumi  qaddarar  rayuwarku ." "Na  yarda  da  qaddara  ummah  domin  yana  daga  cikin cikar  imani  mutun , na yarda da qaddara  amman  umma  aunty  tayi  kuskure  arayuwarta  bance  laifi   bane  dan  taso mahaifina  amatsayin  da  yake amamn  iyaye  fa  umma ? "manzon   sallahu  alaihi  wa salam  yace "ridal  lahi  fi ridal walidaini , wa sakad'ul  lahi fi sakad'il  walidai ."yarda  allah  yana  tare  da  yarda  iyaye, haka zalika fushin  allah yana  tare  da  fushin  iyaye  allah  ya  fifita  iyaye  akan  komai most  especially  uwa ummah ,babu  uwar da  taza ji  dadin irin rayuwar da  aunty  tayi ." umma  tayi  shiru  kawai  tana sauraronta "misali  na kwatantawa  aunty  irin  abinda  tayiwa iyayenta ya  zataji ? na  kawo  mata  in responsible  man  nace  naji  nagani  sai  shi  duk  tarbiyar da tayi  tsawon  shekaru  tana  bani nasa  kafa na  rugujeta ya zataji ?" magana  ta   gaskiya   iyeyenta  da yan' uwanta   sun d'auki  zafi  dayawa  amman  aunty  ta fisu  laifi  kuma  lallai  ya  kamata  taje  ga  iyayenta  ta  roki  gafararsu sannan  ta  koma  cikin  danginta zuciyarta ta  samu  salama ."    "wallahi  yadda  nake  jin  habib araina  bazan  iya  barinsa  saboda  wani  ba  bare  iyayena  da suka kawoni duniya ba ,abun  da ciwo  ummah  ba  kamar  yadda  kuka  d'auka  bane  kema  uwa ce ummah , aunty  ta  kona  zuciyar mahaifiyarta   dayawa,  yanzu na gano duk  aunty  ce  silar  shigarmu   cikin   matsala , iyayenta  na  can  suna  fushi daita  har  yau  ta  yaya   kike tunanin zataji  dadi ?"ta  yaya  kike  tunani  zan  iya  bata  farinciki  byn  ga  inda  zata samu  fiyye  da  nawa  ."? maryama  ta  kalli  umma  cikin  sarewa  ta cigaba  da  magana " umma  abun na  da matukar  ciwo  irin  ciwon  dake  cin  zuciya da  bargo  ,ciwo  ne da  bashi da  magani  da   mafuta  har  sai  ka  had'u  da  mahad'inka , shiyasa a kullum  idan  na  kalli  aunty  sai naji  tamkar  tana  boye  mana  wani  abu  mai  mahimanci  ga  rayuwarta , ashe  gsky  né  hakika bakinta  bazai  iya  furta  mana komai  akan  rayuwarta  ba  matsawar  ita  din  uwa  ta  gari  ce , dan   allah  umma  Kiyi   min  rai ki  raba  zuciyarta  da  wannnan rayuwar  idan  kuma  baki  yi  ba ni  zanyi  ,zan  rabata da  nauyin  dake   daskare  a  qirjinta ." Tana  gama  fadar  haka ta  mike  a hankali  tana  share hawayen idanunta  da  suka  gagara tsayawa  tana  jin  wani  zafi a qirjinta , bazata  cigaba da d'aukar  wannna  nauyin  ba , koda  aunty bata  amince  ta  koma  ga yan'uwanta  ba ,lallai  ita   zata nemosu  a duk  inda  suke  acikin garin  nan  ."muryarta  a sanyaye  tace "umma ni   zan  wuce  sai   da  safe  " kai  kawai  ummah   ta   gyada  mata  sannan   maryama   ta  fara  tafiya  umma   tayi   shiru   tabi   bayanta da  kallo  tana  kallon  yadda  take d'aga  zara  zaran yatsun kafafunta da  kyar  tamkar  wacce  bata  da laka ."   " A inda  ta  bar  mahaifiyarta anan  ta  sameta  tare  da  habib suna  hira  da  alamun shi  baya cikin  damuwa   kamar  ita." bata   tsaya  ba  byn  tayi  sallama tace  "aunty  sai  da  safe  tana gama  fadar  haka  ta  wuce  ta  nufi   d'akin   baccinta  bayanta suka   bita  da  kallo , yanayinta  kad'ai  ya  fahimtar  da  aunty  akwai  tarin  damuwa  atattare daita  shiru  kawai  tayi  tana  tunani "har  yaushe  maryama zata yi  farinciki  arayuwarta  ?". A natse  aunty  ta  mike tabi  bayan maryama  tana  jin  tsinkewar zuciya  haka  shima  habib  akan kujerar  da  take  zama  idan  zatai zane  suka  isketa  ta  dafe  kanta  tana  sheshekar  kuka  atare  suka qaraso  suka  zauna  abakin  gado  suna   fuskantarta  shigowarsu  yasa  ta   tsaida  kukanta   wanda taso tayisa  sosai  har  taji natsuwar zuciyar."     dogon  numfashi  aunty  taja tare  da  cewa "na  shiga  uku ni bilkisu   " ta furta cikin tsananin tashin hankali dan  bata  qaunar  abinda  zai d'agawa  yaranta  hankali  shi  kuwa  habib  hannun  maryama  ya  kamo  cikin  nashi  ya  damke da  karfi  cikin   tsananin  tashin hankali " heartbeat  meke damunki ?." muryarta  a  raunane tace  "babu  komai after dad "ya  babu  komai  zaki  shigo cikin damuwa  , yanzu  mun shigo mun ganiki  kina  kuka  amman  kice  babu  komai  ki fad'a min idan akwai  abinda  ke  damunki  ." shiru  tayi  tana  cigaba  da  shesheka "ki  sani  bamu saba  boyewa  juna  komai  ba  idan kika  min  haka  baki  min  adalci  ba  ,ko  km damuwar  dazu ce  ? still  dai  shiru tayi  ,sosai  suka  d'aga  hankalinsu  ita  kuma  taki  cewa  komai  sai faman  ajiyar  zuciya  ta  saukewa ." damke  hannunta  ya sake  yi  sosai  yana  rokonta "dan allah   heartbeat  karki  daga  mana hankali  ki fad'a min kukan me  kike yi  ?kallonsa  kawai  tayi  tana lumshe idanuwanta ganin yadda  hankalinsa yay matukar  tashi da yadda ya  d'aga  hankalinsa  ya matukar bata  tausayi  daman kuma haka ne idan daya yana cikin damuwa dole ne daya shima ya tsinci kanshi cikin damuwa."   "Yanzu princess bazaki koyi dauriya akan kowacce irin damuwa bace domin ki tsira da rayuwarki da rayuwarmu gabadaya ,Ke kenan kullum cikin zubar da hawaye akan damuwa me yasa zaki dinga asarar hawayenki  tare da qoqarin kashe kanki abanza ."? "Gara dai ki fada mata gsky aunty domin ita rayuwar nan da take ganinta wani lokacin idan abubuwa suka wa mutun tsanani dole mutu ya rage wasu abubuwa domin tsira da rayuwarsa da lafiyarsa." hawayen da take qoqarin maidawa ne suka samu nasarar gangarowa bisa kuncinta cikin sauri tashiga gogewa wasu na sake gangarowa duk  yadda  suka dinga kwantar da kai da murya dan  suji  damuwarta amman   taki  fad'a masu komai domin da zarar ta bude baki hawaye da sheshekan kuka Ke hanata magana dole tasa suka daga mata kafa suka  fice  d'aya  bayan  d'aya daga dakin  da zumar  zasu  lalla'bata  gobe ta fad'a  masu dalilin kukan  ." tafi  mintuna  goma  byn fitar aunty  da  habib   zaune  sannan  ta  yunkura  ta  tashi  tana  sauke naunayen  ajiyar  zuciya ta shiga bayi  ta d'auro  alwala ta  fito ta gabatar  da  sallahr magariba da isha'i  tare  da  shafa'i  da  wutiri byn  ta  idar  ta  koma  kan  katifa ta  zauna  tare  da  jingina bayanta da  pillow  ta  rungume hannuwanta  duka  a qirjinta ." ahankali  ta  runtse  idanunta  tana tariyo  komai  daya  faru  dasu tun suna  yara  "Kenan  adalili  rasa  mahaifi  da  kaka  yasa  rikonsu  ya dawo  hannun  abban  sadam  ."tun  tana   qarama yar shekara hud'u a  duniya ta  taso cikin so daga  bangaren  abban sadam da umma  da  mahaifiyarta   amman  daga   bangaren  aunty  hassana  da  sauran  'yan'uwan  mahaifinta   kuwa  saboda  haushin  da kiyayyar  mahaifiyata  yasa  suka dinga   nuna  masu  tsana  da tsamgwama ,  sun ci wuyarsu  sosai  most  especially  Ita   ganin kiyayyar  dangin  mahaifinsu  da irin  tsanar  da  baba  gali  yayi masu  ya  bawa  aunty  salma  damar  cin kashi  akansu  da mahaifiyarta ." tun  daga  lokacin  kuruciya har zuwa  girmanta  abinda  yake  rage mata  zafin  gidan  shine soyayyar umma  bancin  ita  kowa a gidan baya   sonsu amman kuma  wani lokaci   shi   kanshi  baba gali  ya kan  tausaya masu  in dai ba fad'a sukai  da  sakina  ba ko  yarshi qarama  ba , idan  tayi  mata  laifi ta  d'an  daketa  shine   zai  fito da 'bacin  ransa  har  ya  fito  da  zallar  kiyayyarsa  ,kuma  tun da ta lura  son ya'ya ne  dashi domin ba ita ba  ko uwar  data  tsugunna ta haifesu  baya  raga  mata  akan ya'yansa  ." "yayan  baba  gali  uku  ne aliyu sakina  wacce sa'artace  sai mai bi mata  salamatu  wacce  taci  sunan hajiya  kakarsu  ana  kiranta da shukura  bata  fi  shekara sha bakwai  ba a yanzu ,itama babu yabo  babu  fallasa  suna  d'an  shiri  daita  sai  dai  idan  taga uwarta  na  fushi  da  zagina bata hanata  sai  ma  dai  ta zugata domin  itama  tana  nuna kishinta akainta  idan  taga  umma tana tarairayata ko wani ." Baba  gali  dinki  yake  ada  rasuwar abban  sadam  yasa   gidan  buredi da  rikonsu  ya  koma  hannunsa  alhamdulillah  babu  laifi  ita  din mai  qokari  ce  ta  kowani fanni boko da arabic ga baiwar zane da Allah  ya  bata ." Alokacin  baya  kullum  ta  allah  sai  aunty  tayi  masu  special  lesson  ita  da  habib  kusan kokarinta ta samu ne a wajen mahaifiyarta  ,duk  unguwar da makarantarsu  ana  maganarsu akan  ilimi  bokon  da suke dashi haka  duk  gidan  ba masu  jin   turanci  kamar  ita  da  habib ko wani  abu  za'a  tambaya  ita ko habib  ake  tambaya mahaifiyarsu ta  tsaya  masu  akan  karatunsu shiyasa  ma  education  dinsu  yayi  very  fast  kuma à sanadiyar qoqarinta ita da kawarta subai'a yasa gwanati ta dauki nauyin karatunsu zuwa lagos state university ".    bangaren sakina da  sauran  yaran  gidan  matsalar  iyayensu ne dan  basa  maida hankali  akan karatun  yaransu  gashi  sam  basu da  isashen  ilimin  boko ko Arabic barin  ma  aunty  salma  karta ji labari  ba  arabi ba boko sai  uban girman  kai  ,sau  tari  idan shukura tazo   koyon  wani  abu a wajenta bata  só  sai  ta  nuna  ai  itama tasani  dan  me  zatazo  wajenta akarshe  idan  tayi  mata  zero take samu  a makaranta shiyasa da  yarinyar  ta gane ta daina  bata  idan tace ta kawo kai  tsaye  take ce  mata  bataso   zero  zataci ." hatta  alwala  ba  daidai aunty salma  take yi ba  kuma sallah ma bata  dameta  ba  ,tun  suna yara baba  gali Ke  mata   fad'a  akan tarukun  sallah din  da take yi amman  taki  ta  daina  shi  kansa daya  gaji  sai ya  rabu  daita ya dinga  Kwa'bar  yaransa da yin sallah  sanin  in  har  dan uwarsu ne sai  dai kar su yi  babu abinda ya  dameta dan  idan ma  koyi zasu yi  daita  sai  dai su  koyi taruku sallah." Su  kuwa  aunty  bata yarda tana gama  dauro  alwala  zata  tura habib  zuwa  masalaci  ita km ta umarceta taje  tayi  alwala sannan  a  kullum  dare auty  ta kan fito  tsakar  gidan  tare dasu  har  sakina  kasancewar  tana  qaunarta  ta  koya  masu  darasin lissafi , tana  daukar  lokaci akansu  har sai  taga sun gane sannan ta bukaci  wanda yake da damuwa a bangaren  karatunshi ko baka da matsala  zatai  'yan  tambayoyi  ana  bata amsa  idan bata gamsu da  amsar  ba ta qara yi masu  bayani , bangaren  karatun alqurni kafin  suyi  bacci  sai  aunty tasa sun  karanta izawaka  da tabaraka kafin  su  kwanta  da  safe kuma sai  sunyi murajaa  alqurni sannan su shirya su wuce  school  ko islamiyya ." A ranar batayi  isashen  bacci ba  ga tsananin  tunani  ga  kwadayin son  ganin  yan'uwan  mahaifiyarta  gargadin  kanta  ta shigayi   akan fad'awa  soyayya  da ma ko waye idan  kuma  soyayyar ta zama dole sai  dai  tayi a gidan aurenta  ga duk wanda ta aura har  asuba  tayi maryama batai   wani  yi  baccin  kirki  ba shiyasa  kiran  sallahr  farko  acikin kunnenta  akayi   ta  gyara kwanciyar  ta koma  ta  kwanta bacci   kad'an  tayi ta  lalubo wayarta  ta  duba  taga biyar da  rabi   saura  lokacin  sallah yayi dan har an  tada sallah a matsalacin unguwarsu ." a hankali ta  mike  zuciyarta cike da damuwa bakinta dauke da  adduar   tashi  daga  bacci ta kai tafukan hannunta tana shafa fuskarta sannan a natse ta zuro kafafunta ta sauko ta  shiga  bayi ta dauro alwala ta fito cike da sanyin jiki ta  gabatar da sallah asuba  byn ta idar  ta d'auko  alqurni ta soma karatu  cikin suratul  baqara anatse ta  kai idanunta  ga  window d'akin taga gari ya  fara sha tayi azkar  din safe tana nan zaune tana lazimi har shida  saura sannan ta koma ta kwanta akan sallaya nan da nan  bacci mai nauyi ya dauketa ba ita ta tashi ba sai goma saura ." Ta  mike da  kyar  bakinta  dauke da  salati  sakamakon qirjinta dake wani irin bugawa ta  gyara gadonta ta fita ta dauko tsintsiyar  shara ta  share d'akin  ta fito har falo ta shiga d'akin  mahaifiyarta  bata  ganta ba   tasan may be ko tana byn gida wajen yin wanki ,dan wannan kaida ne  kullum safiya sai  tayi  wanki  kayanta wani   lokacin  da nasu  ta  share d'akin  tasss ta fito da  sharan zuwa falo ta  shiga  kitchen ta hada kayan wanke wanke ta wanke atake  ta goge koina ta sharo sannan ta hada da share falo tayi mopping ta koma daki ta cire kayan jikinta ta shiga wanka bata wani jima ba tayi alwala ta fito kai tsaye ta shimfida daddumar sallah ta sallacci salatul duhu byn ta idar ta shirya kanta ta kwanta lamo cikin zullumi ta

Chapter 20 of 43