kuka daga magana "kiyi hakuri aunty nasan damuwata na damunki ina kukan ne saboda an cuceki an rabaki da yanuwanki da iyayenki alhalin suna sonki , bansan yadda zan misalta miki yadda nakeji ba, aunty ki taba zuciyata kiji yadda take bugawa tayi mgnr tare da kai hannuta ta kamo hannu aunty ta d'aura daidai saitin zuciyarta dake wani irin bugawa tamkar ana buga mata guduma, tabbas aunty taji kokawar da zuciyar keyi amman bata yadda zatayi gurin raba zuciyar da damuwa addua dai ce kuma tana kanyita babu dare babu rana kuma tasan ubangijinta baxai barta haka ba batare daya duba lamarinta ba.
cikin murya me cike rudanin rayuwa maryama ta cigaba da mgn "bansa me zanyi abubuwa su dawo mana daidai ba har ki cigaba da rayuwarki kamar da? " aunty ki daina daukar iyayenki da yanuwanki a matsayin makiyanki ,iyayenki suna sonki fiyye da tinaninki ,sun nuna miki so da kauna tattare da kulawa da gata alokacin da kike zaman lafiya dasu aunty kema kanki Kinsan irin soyayyarsu garenki "aunty !!! ki daina ganin laifinsu sannan ki dai jin zafinsu dan su dauki fushi dake ?"
Su iyaye ne zasu iya yin komai suci lafiya a yanayin yadda rayuwa tazo miki cike da rudanin yaci ace zuwa yanzu kin samu y'anci ki tsinci kanki cikin farinciki da jin dad'in rayuwa kwana uku kawai da baki ga walwalata ba kin daga hankalinki inga bana cikin gidan nan ?"ina ga nabi wani na barki ya zakiji ? wallahi iyayenki suna can cikin tsananin kewarki kwatankwacin yadda kike jin namu da zaki koma garesu zasu karbeki su kuma yafe miki " kiyi hakuri aunty ki daina ganin laifinsu ta karasa fadar haka tana xubda wasu zafafan hawaye hade da rike hannun aunty gam tana me tausayawa rayuwarta ."
"Idan abubuwan dake faruwa suka cigaba da faruwa bana tinanin zuciyar dake kirjina zata cigaba da baguwa ni dai ki koma cikin yanuwanki dan Allah ki roki gafarar iyayenki su yafe miki mu cigaba da rayuwarmu kamar yadda muka saba . ahankali aunty tashiga bubbuga bayanta "kukan ya isa haka
Inshaallahu zan .. zan.. koma garesu da izinin Allah sosai aunty ta dinga rarrashinta da gaya mata maganganu masu dadi da sanyaya rai har ta soma bacci ajikita cike da samun kwanciyar hankali .
Washegari kowa yasan maryama na cikin kwanciyar hankali wanda hakan ya kwantar da hankalin babib da aunty tare suka ci abinci kamar yadda suka saba ,maryama tana zaune a falo byn tayi wanka ta shirya tana kitsa gashinta gida hud'u sakina ta shigo suka sha hirarsu duk aunty na jinsu sosai taji dadi aranta ganin maryama ta saki ranta ,har sakina ta fita ta dawo "maryama amman yau zaki islamiyya?"eh!zani idan na gama zan biyo miki sakina ta qarasa fita ita kuma ta mike ta shiga daki tai sallah ta qara shiryawa ta dauki alqurani ta fito ta tsaya a bakin part dinsu sakina tana jiranta byn ta gaishe da aunty salma sakina ta fito ta tsaya kusa da maryama tana mata magana kasa kasa aunty salma ta bisu da harara har suka fice ,ta nemi guri ta zauna zuciyarta na tafasa ."
ta rasa yadda zata kawo karshen shakuwar sakina da maryama duk duniya bata da abinda ta tsana tamkar maryama tayi shiru cikin tsanani tunani abubuwa da dama take sakawa in dai da rai da lafiya sai ta rabasu domin itace kadai hanyar da zata nunawa maryama tsangwama da tsanar datayi mata shegiyar yarinya kamar mayya ko aljanna zatace banda abun sakina ai maryama matsala ce arayuwarta, yanzu ko saurayi idan sakina tayi yayi ido biyu da maryama ai tuni zaice shi ga wacce yake so yarinyar ta cika kyau haka kamar ita tayi kanta ta fad'a acikin ranta ta mike tsaye cikin takaici to ko afa zata kaiwa kukanta , zuciyarta ta kawo mata dauki da wannan tunani aikuwa hakan shine mafuta afa shine zai kawo mata karshen komai da karshen wannan shakuwartasu mayafinta ta dauka ta yafa ta fice daga gidan tana surutai ita kadai kamar yadda na shiga na fita na rabaki da duk wanda yazo da sunan yana sonki da aure yanzu ma sai na rabaki da sakina takowani hali ki cigaba da rayuwarki Ke kadai Kmr mayya acikin gidan nan ."
Tayi sallama aka amsa mata daga ciki dan haka ta shiga ta tsaya afa da yake ciki bai amsa ba yayi gyaran murya hakan ya tabbatar mata akwai wani aciki ta dan jira na rabin awa sannan wacce take ciki ta fito suka gaisa ta fice a karo na biyu tayi sallama ta shiga cikin dakin ta durkusa ta gaishe shi yana zaune akan daddumar sallah wani katon tray mai cike da katon kasa da wuri na duba ya amsa mata cike da kulawa "meye ma sunanki yaushe rabon na sakaki a idona ?"Aunty salma tayi murmushi tace afa kenan abine sai ahankali idan ka ganmu tamu ce ta kawo mu yayi murmushi ya dan shafa gemunshi yana lashe lebensa "to ina jinki fara bayanin abinda Ke tafe dake kafin na duba naga gskyar lamari ".
Mmm sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura wa wannan 0913691 8331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 15
"Aisha , saber, da mahamud , ta gani tsaye akansu suna huci kamar zakuna cikin matsanamcin tashin hankali mara misaltuwa suna kallonta kamar zasu cinyeta ai babu shiri daga bilkisu har ussein suka mike daga jikin juna hankalinsu yayi mugu mugun tashi ."
bilkisu ta tsaya tana kalle kallen inda zata boye acikin d'akin tare da cure hannayenta waje d'aya jikinta na sake d'aukar rawa bata ta'ba shiga tashin hankali da nadama irin na ranar ba domin har ga Allah bata ta'ba tunanin zasu bibiyi takunta ba ."
Nan da nan idanunta ya kawo ruwan hawaye ba tace komai ba, ta durkusa qasa bisa gwiwo
winta dan tasan sai na lahira ya fita jin dadi mahamud ya rike kungunsa yana cigaba da kallonta ,mamakinta kawai yake dawainiya dashi idan aka fad'a masa cewar zata biyo nmj har d'akinsa bazai ta'ba yarda ba, watakilla ma da sai ya wankawa wanda ya fad'a masa hakan mari "dan girman Allah kuyi hakuri ku yafe min ku rufa min asiri kar mumy tasani ta karashe mgnr tana kuka cikin tashin hankali mahamud ya buga mata wata razananniyar tsawa data hargitsa mata lissafi "yi min shiru makira bana son jin komai daga bakinki ."
nan take tayi shiru kukanta ya qaru ta kalli inda ussein yake tsaye shima kana kallonsa kasan baya cikin natsuwarsa "mahamud tsayawa kayi kallonta bazaka fara cin ubanta tun anan ba ? Aisha ta fad'a tana mata wani irin kallo shi kuwa wanda aka kira da mahamud tunanin yake idan yace zai ta'bata to babu shakka zata mutu idan kuwa bata mutu ba zata jikata ."
"dan girman allah Aunty ai.."ai bata kai ga fad'ar abinda take son fad'a ba taji wani gigitaccen mari hagu da dama akan kuncinta "you are very stupid bilkisu , akanki aka fara soyayya?" kin haukace kin makance akan wannan banzar ,me yasa zaki mance ko ke wacece ? wato soyayya tasa kin manta matsayinki ? cikin muryar kuka tace " a'a Aunty aisha ban mance ba amman kuyi hakuri wallahi bazan sake ba "hayaniyar yan yan'uwanta ya sake d'aga mata hankali shi kuwa ussein sunkuyar da kanshi. kasa yayi yana tunanin ficewa ya bar d'akin dan yasan Allah ne kawai zai kwacesa a hannunsu ."
Kai tsaye bilkisu ta nufi bayan kofa ta boye jikinta na wani irin rawa sakamakon jiyo muryar hajiya rahma tana cewa "ina bilkisu take naga kun tsaya jugun jugun ko ta gudu ne ? kafin kace me an samu wanda yazo ya fad'a mana halin da'ake ciki a guje na bazamo na bar hajiya dan bazan iya jiranta ba kasancewar tana fama da lalurar ciwon kafa ."
" ina tafiya ina neman layin yan' uwansashi da kyar na samu ta abban sadam yana gama jin bayanina cewa yayi babu ruwansa dan yasan halinsa da tara yammata , babu yadda banyi dashi ba yace bai zuwa koina ya kashe wayarsa jin abinda ya fad'a yasa na kira yayyensa mata ."
Ina shiga unguwar naga jamaa sun yi cirko cirko!! ga manya manyan motoci na gidansu bilkisu jere a kofar gidan ,haka ina shiga cikin gidan mutane na gani makil kowa na fadar albarkaci bakinsa ,yayinda muryar mahaifiyarta ya karad'e koina acikin gidan "da gaske ne bilkisu tana cikin wannna ru'babben d'akin ? Aisha ta nuna mata bayan kofar d'akin "tana ciki kuwa ga makira nan a bayan kofa ta fad'a tana zubar da hawayen takaici ."
"inna lillahi ! hjy rahma ta furta a fili cikin tsananin tashin hankali "kunji abinda naji kuwa wallahi ji nayi zuciyata kamar ta buga ?hankalin bilkisu ya bar duniyar da muke alokacin dan sai wuri wuri da idanu take shi kansa ussein kana kallonsa kasan nadama ne acikin ransa nadama irin wacce bata da wani rana ."
" amman bilkisu bakince min kin rabu dashi ba ?jikinta na rawa ta shiga gyada mata kai alamun Eh! tana bawa mahaifiyarta hakuri da wani irin fushi ta juya inda ussein yake cike da nadama ta shiga zabzabga masa mari ta koina "bana ce maka ka rabu mun da yarinya ba ? ba banace karka sake shiga rayuwarta ba?"Ko kaga yarinyata tayi kalar wacce zaka ce kana so ? ta juya zuwa ga bilkisu " Ke yanzu har wannan qazamin ne abun so a wajenki ? ta fad'a tana sake juyowa ta d'aga hannu zata sake tsinkawa ussein mari nayi saurin rike mata hannu ina bata hakuri "kiyi hakuri hjy sam ussein bai kyauta ba daya bawa yarinyarki damar zuwa inda yake ,ya karbi laifinsa ayi masa afuwa in sha allahu hakan bazai sake faruwa ba Kinsan kowa da irin jarabawarsa dukkanin rayuwa rubutaccen lamari ne daga Allah ,kuma kowani dan Adam yasan da haka ,yanzu tunda abun ya zama haka ku bamu dama sai mu turo ayi maganar aure "."
Wani irin kallo gabadayansu suka bini dashi ,hjy rahma tace "Allah ya tsareni na had'a zuria da wannan ta nuna ussein da yatsanta tana hararsa "wallahi bilkisuna tafi karfen aurensa ki kalleta sama da qasa ki kallesa ta ina hadin yayi daidai ? duk nasan da haka hjy amman a wajenta shine daidai bugu da qari rayuwar yarinyar ku zaku duba domin ita diya mace ce zata iya fad'awa kowani hali ."
"Ba kowani hali zata fad'a ba ko mutuwa zatai sai dai ta mutu na yarda na rasata gbdy akan na bawa wannan matsiyacin aurenta ta numfasa tare da sa tafin hannunta ta share hawayen idanunta "hjy ki daina furta haka shi soyayya allah ne yake had'awa , kuma babu ruwan soyayya da tsiya ko arziki yarinyar nan tana qaunarsa shima kuma yana sonta dan girman allah ki barsu suyi aurensu kowa ya huta sannna babu wanda yasan matsiyaci ko mai arziki sai Allah sannan babu wanda yasan mai gobe zata haifar ku barsu su aure juna domin samun kwanciyar hankali ."
bata kulani ba har na dasa aya ta fuskanci bilkisu yayinda gabadaya yanuwanta kacokan suka maida hankalinsu Kan ussein duk sun qagu suga hukunci mahamud akan ussein kasancewarsa soja , hjy rahma ta matso sosai kusa da bilkisu tana cewa "ba dai ni zaki wulakanta akan namiji ba ? ."babu irin rarrashin da ban miki ba ,babu irin hakurin da ban baki ba ,me kike son dani ? "wallahi zanyi dake bilkisu , yau zaki ga tozarci ganin idanunki tunda kika nemi ki wulakantani akan wani banza can wanda ba kowan kowa bane shi ,ba kowa bane iyayensa a duk fadin garin nan hasalima rayuwarsa a banza take ."
"zaki wulakantani akan wani nmj banza da wofi wallahi zanyi dake muddin kika ce shi zaki aura sai na tsine miki na tsinewa auren ,wallahi auren bazai ta'ba yin albarka tana mgn tana zabga mata mari a fuskarta da bayan hannunta , yayinda azaba tasa bilkisu ta shiga karewa dan kar marin yayi mata illa amman matar nan sai zabga mata maruka take kuma a fuska na rantse miki da girman allah maryama tayi mata mari yafi guda tara ajere ana goma ne bilkisu ta rike mata hannu kuma nasan azaba ce tasa tayi haka ,aiko matar nan ta danneta da iyakacin karfinta ta dinga dukanta tana cewa ni zaki rikewa hannu in sha allahu kema sai ya'yanki sun miki abinda kika min ,sai sun hanaki kwanciyar hankali kamar yadda kika hanani kwanciyar hankali a karshe kafa mata hakori a damtsen hannunta."
"wani irin gigitaccen qara bilkisu ta saki mai ban tausayi tana kuka tana neman d'auki gashi babu wanda ya kwaceta daga hannun mahaifiyarta sai dukanta take tana hadawa da zagi ganin haka yasa ussein ya nufi hjy rahma cikin tsananin fushi kamar mayunwanci zaki idanunshi sun kad'a sunyi jajur yasa duka hannunsa zai d'agata daga Kan bilkisu ai ganin ya ta'ba mahaifiyarsu gbdy yan'uwanta suka yo Kanshi shi da bilkisu cike da jin haushi suka dinga dukan su kamar zasu kashesu suna furta mahaifiyarmu zaka duka ? azahiri gaskiya ba wai dukanta yayi ba kawai ceton bilkisu zai yi daga dukanta, ina kuka ina basu hakuri ina qoqarin kwatarsa daga hannunsu amman ina sarkin yawo yafi sarkin karfi dan sai suka daina dukan bilkisu suka cigaba da dukansa shi kad'ai har sanda hjy ta shigo zubewa tayi kasa tana kuka tana cewa "zaku kashemun d'a ne to wallahi idan kuka kasheshi hukuma ce zata rabamu daku dan wallahil azim bazan ta'ba yarda ba ".
"kar Allah yasa ki yarda daman kece uwar matsiyaci ? "nice uwarsa kuma gatansa kuma ni d'ana ba matsiyaci bane dan me zaku masa haka ?
"ai yarku zaku jawa kunne ta daina zuwa inda yake shi meye laifinsa ? "laifinsa kulata da yake yi idan baya kulata bazata zo inda yake ba ,idan yace baya sonta karta sake zuwa inda yake ni nasan bilkisu bazata zo inda yake ba ki fad'a masa da babban murya ya rabu da kanwarmu ya zauna lafiya idan ba haka ba zamu 'batar dashi agarin nan ,kina ji kina gani zaki rasa d'anki har abada "hjy na fad'a 'yanuwan bilkisu na maida mata martani kuma basu daina dukansa ba ."
"neman layin 'yanuwasa mata na sake yi saadatu na d'auka na saka mata kuka ina cewa "bazaku zo ba sai an kashe maku da'nuwa ?dan girman allah kuzo ku hanzarta karku bari su illatashi "bilkisu cikin kuka ta rarrafa ta rike kafafun mahamud domin duk yafi dukan ussein cikin kuka tace "yaya dan girman allah kayi hakuri ka barshi karku kashe min rayuwata sannna karku rabani da dashi wallahi bashi da laifi nice mai laifi" .
"ya salam! ya furta a matukar fusace "wai bilkisu me ke damunki ne "?ta girgiza masa kai idanunta na zubar da ruwan hawaye kuyi hakuri nayi maku alkwarin bazan sake zuwa inda yake ba "muryar hjy rahma ta sake karade d'akin Aisha riko hannun makaryaciya karta gudu shi kuma sheidani ku fito min dashi yau zan nuna masa koni wacece agarin nan zanga uban da ya isa ya kwaceka Aisha ta riko hannun bilkisu gam bisa umarnin mahaifiyarsu sai dai bilkisu ta dinga turjewa nan ma wani marin aisha ta kai mata tuni daman fuskarta ta canza jini ya kwanta a duka idanunta ."
Mahamud kuwa qarasawa yayi inda ussein yake yace ya kama kunnensa ussein ya kama kunensa cikin kaduwa dan gbdy bai fahimci abinda yake nufi ba mahamud yace "you're very stupid I mean kayi frog jump Aishat ashe ma illiterate ne wallahi ko da wasa naji ka qara shiga harkar bilkisu zan mugun baka mamaki "mugun ma illiterate katon jahili liability kawai a haka zamu bashi aurenta sai kace kwakwaluwarmu ta juye ai har abada ,ka wuce dashi kaci ubansa ta yadda ko mai kama daita ya gani da mugun mugu zai arce ."
bilkisu na kuka ussein na frog jump nima ina biye dasu ina basu hakuri haka hjy hakuri take basu hankalinta a tashe muna fitowa kofar gida sai ga saadatu da fatima a rude basu tsaya neman baasi ba dan na rigada na fad'a masu komai sausauci suke neman masa amman mutanen nan suka ki banda cin mutunci babu abinda suke zubawa unguwa kuwa ya cika makil da jama'a yan kallo kowa na fadin albakacin bakinsu wasu suna ganin daidai ne matakin da suka dauka dayawa kuma laifin bilkisu suke gani ."
wani abu mai daci yan'uwansa suka hadiye tare da matsowa inda mahamud yake yana laftawa ussein belt a gadon bayansa "yanzu ina zaku dashi ?In ji cewar fatima tayi maganar cikin tsananin fushi "zamu tafi dashi inda zamu sake koya masa hankali," ya fad'a cike da gadara da isa "amman yana da kyau mu san inda zaku da d'anuwanmu kafin ku wuce dashi? Eh ! yana da kyau sai dai bani da wannan lokacin 'batawa idan aka koya masa hankali zaa iya sanar daku kuzo ku d'auki abinda ya saura ajikinsa "
Hjy kuka saadatu kuka haka ma fatima muna cikin wannan halin sai ga gali yace shine yayansa suyi hakuri su bar komai a hannunsa zai sa ya rabu daita rabuwa ta har abada ,mahamud yace "da dai ya fiyye masa kwanciyar hankali dan wallahi na sake dawowa akan case din nan sai dai ku dauki gawarsa" gali yace "to mun gode komai yazo karshe bilkisu ta bude idanunta da suka mata nauyi wani marayan kuka ta fashe dashi tana shesheka tana kallon kowa wanda ni nasan kukan da take alokacin bai wuce na rabuwa da ussein ba ."
fatima ta watsa mata harara hade da kallon banza tana cewa "kukan uwar me zakiyi wa mutane duk bake kika jawo masa matsala ba yana zaman zamansa muguwa azzaluma kin janyo yanuwanki sun wulakanta mana d'anuwan an tozarshi, tunda muke anan unguwar aka haifemu muka girma mukayi aure baa ta'ba wulakantamu ba sai yau kuma duk akanki ,kinsa ana dukansa kamar an samu ganga na rantse da girman allah matukar ussein..."
saurin toshe mata baki nayi ina cewa fatima karki rantse ,cikin fushi ta cire min hannu "ki barni aunty nayi magana kalli yadda fuskarsa tayi duk jini saboda Allah yau ayita ta qare ta kama kanta ta daina zuwa inda yake ,yanzu da suka zo suna hargagin banza da wofi da wulakanci shi meye laifinsa? yarinyarsu ya dace suyi wa magana ta daina zuwa inda yake dan muddin ta sake zuwa inda yake kafin ku dauki mataki mu zamu dauka dan ba daga sama ya fado ba azzaluman banza kawai kuma allah ya isa tsakaninmu daku tana fad'a aisha na fad'a."dan girman allah fatima karki sake cewa komai zo muyi magana na janyo hannunta " babu inda zani aunty ayita ta qare gwama su san muma bama son wannan diyar tasu kuma komai zai faru ..."
na sake toshe mata baki "dan Allah ki bar mgnr nan sulhu ake nema ."
Cikin ko in kula hjy rahma tace da wa zakuyi sulhu ?"kema Kinsan ruwa ba sa,an kwado bane baku kai wannan matsayin ba yanzu ma wannan maganar da nake duk sai na fashesa akan wannan matsiyacin "nayi tsuru tsuru ina dubanta "tsayuwar me kukeyi ku taho min dashi da sauri gali ya qaraso inda take hjy ai mun gama magana da yaronki, dan allah hjy kiyi hakuri ,in sha allahu tunda muka shiga cikin zance komai yazo karshe zanyi magana dashi "babu irin hakurin da baa bawa hajiya rahma ba amman tace sam sai an tafi dashi haka muna ji muna gani aka watsa useein abayan boot din mota aka wuce da
ussein ."
Kuka sosai maryama take kamar alokacin komai ya faru Kwantar da kanta umma tayi akan cinyarta tana rarrashinta "tabbas Aunty masoyiya ce ta gaskiya ,ta so mahaifinmu a halin babu ,ta zauna dashi har karshen rayuwarsa wallahi ba kowani d'an mai kudi bane mutumin kirki kamarta ,ta tsaya ta dubi mahaifinmu da kalmar so ta gaskiya
sai dai akwai illa umma Aunty ta jefa rayuwarta cikin matsala wanda a yanzu take shan wahala ".
" tabbas shine gskiyar dana dade ina nuna mata "baa jayayya da iyaye data yi hakuri tabi umarnin iyayenta tabbas zasu sauko dan kansu kasancewar akwai rabo a tsakaninta da mahaifinku ,cikin muryar kuka tace "mune silar jefa rayuwar mahaifiyarmu cikin wahala ko ? ta fad'a tana sheshekar kuka "karki ce haka maryama haka tata qaddarar take ,ita qaddara gata ko arziki ko nasaba bai isa ya canza maka ba ."umma ta numfasa sannan ta cigaba da magana ".
Bangaren su bilkisu kuwa tunda suka dauki hanya yan'uwanta suke magana suna zagin ussein cikin kuka bilkisu Ke rikon su "ku sani ussein bai muku laifin komai ba dan allah karku hukuntashi akan abinda bai yi ba" mari mahaifiyarta ta kifa mata haka ma aisha dan ubanki ki kama mana baki har suka kai gida zaginta suke direba na ajiyesu ya wuce da mahamud da ussein ."
a matukar gigice bilkisu tabi byn motar da kallo cikin tsananin firgici, keyarta suka tasa sai cikin bangaren hjy rahma ."Suna shiga part din hjy rahma suka turata daki suka daureta da igiya tamau sukasa saber ya dinga dukanta adaure tun tana ihu har tazo ta kasa a yadda ta fad'a min cewa tayi har da barkono mahaifiyarta ta nika tasa mata a gabanta da cikin idanunta wanda yasa tayi suman wuncin gadi ."
Bangaren mu rana babu wanda ya samu sukuni acikinmu gali yafi kowa shiga damuwa safa da marwa yake yana cewa "ban ta'ba kawowa araina duk hakurin dana basu ba zasu hakura ba , na dauka maganata zai sa su hakura amman ina kamar sake fusata mahaifiyarta nayi wadan nan mutane sam basu da imani ."wallahi basu da imani gali inji cewar hjy ka kalli irin duka da sukayi yarinyar nan bilkisu ko rikonta suke bai dace suyi mata irin wannan dukan ba ."
"wallahi ku sheida bilkisu bazata sha wannan wahalar a banza ba komai zai faru sai useein ya aureta ba dai bakinciki su kenan ba saboda suna takama da kudi ,ni bana da kudi amman ina da Allah alfarma annabi da alqurni sai wannan auren ya tabbata ko ina raye ko byn na mutu mutane sam babu imani aransu bazai hakura da aurenta ba sai dai su mutu fatima zatayi magana ta dakatar daita "banason jin komai daga bakinku sai fatan wannan auren ya tabbata ."
abban sadam ya fito daga bayi daman zagayawa yayi yace "har yanzu bazaku hakura da wannan maganar ba ? hjy tace "taya zaa hakura?" da sukutun fa suka wuce min dashi ?naga diyarsu ce tunda sunce basaso tarayyarsu a hakura mana "bazaa hakura ba bilkisu bazata sha wahala akan ussein ya tafi a banza ba ina sonta tunda tana son jinina ta gama min komai ni yanzu ta'bo min abokika Abdul zanyi magana dashi babu irin kiran da baayiwa Abdul ba amman wayar bata shiga ranar hjy bata runtsa ba kwana tayi tana kaiwa allah kukanta ."
Washegari ana idar da sallahr asuba tasa aka cigaba da trying dinsa amman shiru baya shiga sai karfe
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 23 Chapter of 43