Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kuka daga magana "kiyi hakuri aunty nasan damuwata na damunki ina kukan ne saboda an cuceki an rabaki da yanuwanki da iyayenki alhalin suna sonki , bansan yadda zan misalta miki yadda nakeji ba, aunty ki taba zuciyata kiji yadda take bugawa tayi mgnr tare da  kai hannuta ta kamo hannu aunty ta d'aura daidai saitin zuciyarta dake wani irin bugawa tamkar ana buga mata guduma, tabbas aunty taji kokawar da zuciyar keyi amman bata yadda zatayi gurin raba zuciyar da damuwa addua dai ce kuma tana kanyita babu dare babu rana kuma tasan  ubangijinta baxai barta haka ba batare daya duba lamarinta ba. cikin murya me cike rudanin rayuwa maryama ta cigaba da mgn "bansa me zanyi abubuwa su dawo mana daidai ba har ki cigaba da rayuwarki kamar da? " aunty ki daina daukar iyayenki da yanuwanki a matsayin makiyanki ,iyayenki suna sonki fiyye da tinaninki ,sun nuna miki so da kauna tattare da kulawa da gata alokacin da kike zaman lafiya dasu aunty kema kanki Kinsan irin soyayyarsu garenki "aunty !!! ki daina ganin laifinsu sannan ki dai jin zafinsu dan su dauki fushi dake ?" Su iyaye ne zasu iya yin komai suci lafiya a yanayin yadda rayuwa tazo miki cike da rudanin  yaci ace zuwa yanzu kin samu y'anci ki tsinci kanki cikin  farinciki da jin dad'in rayuwa kwana uku kawai da baki ga walwalata ba kin daga hankalinki inga bana cikin gidan nan ?"ina ga nabi wani na barki ya zakiji ? wallahi iyayenki suna can cikin tsananin kewarki kwatankwacin yadda kike jin namu da zaki koma garesu zasu karbeki su kuma yafe miki " kiyi hakuri aunty ki daina ganin laifinsu ta karasa fadar haka tana xubda wasu zafafan hawaye hade da rike hannun aunty gam tana me tausayawa rayuwarta ." "Idan abubuwan dake faruwa suka cigaba da faruwa bana tinanin zuciyar dake kirjina zata cigaba da baguwa ni dai ki koma cikin yanuwanki dan Allah ki roki gafarar iyayenki su yafe miki mu cigaba da rayuwarmu kamar yadda muka saba . ahankali aunty tashiga bubbuga bayanta "kukan ya isa haka Inshaallahu zan .. zan.. koma garesu da izinin Allah sosai aunty ta dinga rarrashinta da gaya mata maganganu masu dadi da sanyaya rai har  ta soma bacci ajikita cike da samun kwanciyar hankali . Washegari kowa yasan maryama na cikin kwanciyar hankali wanda hakan ya kwantar da hankalin babib da aunty tare suka ci abinci kamar yadda suka saba ,maryama tana zaune a falo byn tayi wanka ta shirya tana kitsa gashinta gida hud'u sakina ta shigo suka sha hirarsu duk aunty na jinsu sosai taji dadi aranta ganin maryama ta saki ranta ,har sakina ta fita ta dawo "maryama amman yau zaki islamiyya?"eh!zani idan na gama zan biyo miki sakina ta qarasa fita ita kuma ta mike ta shiga daki tai sallah ta qara shiryawa ta dauki alqurani ta fito ta tsaya a bakin part dinsu sakina tana jiranta byn ta gaishe da aunty salma sakina ta fito ta tsaya kusa da maryama tana mata magana kasa kasa aunty salma ta bisu da harara har suka fice ,ta nemi guri ta zauna zuciyarta na tafasa ." ta rasa yadda zata kawo karshen shakuwar sakina da maryama duk duniya bata da abinda ta tsana tamkar maryama tayi shiru cikin tsanani tunani abubuwa da dama take sakawa in dai da rai da lafiya sai ta rabasu domin itace kadai hanyar da zata nunawa maryama tsangwama da tsanar datayi mata shegiyar yarinya kamar mayya ko aljanna zatace banda abun sakina ai maryama matsala ce arayuwarta, yanzu ko saurayi idan sakina tayi yayi ido biyu da maryama ai tuni zaice shi ga wacce yake so yarinyar ta cika kyau haka kamar ita tayi kanta ta fad'a acikin ranta ta mike tsaye cikin takaici to ko afa zata kaiwa kukanta , zuciyarta ta kawo mata dauki da wannan tunani aikuwa hakan shine mafuta afa shine zai kawo mata karshen komai da karshen wannan shakuwartasu mayafinta ta dauka ta yafa ta fice daga gidan tana surutai ita kadai kamar yadda na shiga na fita na rabaki da duk wanda yazo da sunan yana sonki da aure yanzu ma sai na rabaki da sakina takowani hali ki cigaba da rayuwarki Ke kadai Kmr mayya acikin gidan nan ." Tayi sallama aka amsa mata daga ciki dan haka ta shiga ta tsaya afa da yake ciki bai amsa ba yayi gyaran murya hakan ya tabbatar mata akwai wani aciki ta dan jira na rabin awa sannan wacce take ciki ta fito suka gaisa ta fice a karo na biyu tayi sallama ta shiga cikin dakin ta durkusa ta gaishe shi yana zaune akan daddumar sallah wani katon tray mai cike da katon kasa da wuri na duba ya amsa mata cike da kulawa "meye ma sunanki yaushe rabon na sakaki a idona ?"Aunty salma tayi murmushi tace afa kenan abine sai ahankali idan ka ganmu tamu ce ta kawo mu yayi murmushi ya dan shafa gemunshi yana lashe lebensa "to ina jinki fara bayanin abinda Ke tafe dake kafin na duba naga gskyar lamari ". Mmm sudais 💗💗💗💗💗💗      MAR'ADAMS      💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura wa wannan 0913691 8331  alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.         Page 15 "Aisha ,  saber, da   mahamud ,  ta  gani   tsaye  akansu  suna   huci   kamar   zakuna  cikin  matsanamcin  tashin  hankali   mara misaltuwa  suna   kallonta   kamar   zasu  cinyeta  ai  babu  shiri  daga  bilkisu  har  ussein   suka   mike   daga   jikin   juna  hankalinsu yayi  mugu  mugun   tashi   ."     bilkisu  ta  tsaya  tana  kalle  kallen   inda  zata  boye  acikin d'akin  tare  da  cure  hannayenta  waje   d'aya  jikinta  na sake d'aukar  rawa  bata  ta'ba   shiga  tashin  hankali  da  nadama  irin  na  ranar  ba domin  har  ga  Allah  bata  ta'ba  tunanin   zasu   bibiyi takunta  ba ." Nan da  nan  idanunta  ya   kawo ruwan  hawaye ba  tace  komai  ba, ta    durkusa qasa  bisa  gwiwo winta   dan  tasan  sai   na  lahira  ya  fita  jin  dadi  mahamud  ya  rike  kungunsa  yana  cigaba  da  kallonta  ,mamakinta  kawai   yake  dawainiya   dashi  idan  aka  fad'a   masa  cewar   zata  biyo  nmj   har  d'akinsa   bazai  ta'ba yarda  ba,  watakilla   ma  da  sai  ya  wankawa   wanda  ya  fad'a  masa  hakan   mari  "dan   girman  Allah  kuyi   hakuri   ku  yafe   min  ku rufa  min  asiri   kar  mumy   tasani  ta  karashe   mgnr   tana   kuka  cikin  tashin  hankali mahamud   ya  buga  mata  wata  razananniyar  tsawa  data  hargitsa  mata  lissafi "yi  min  shiru  makira  bana  son   jin  komai  daga  bakinki ." nan   take   tayi   shiru  kukanta ya  qaru ta   kalli  inda  ussein  yake  tsaye    shima   kana  kallonsa  kasan  baya  cikin natsuwarsa  "mahamud   tsayawa  kayi  kallonta  bazaka   fara cin  ubanta  tun  anan  ba ?  Aisha  ta  fad'a  tana  mata  wani   irin kallo  shi kuwa wanda aka kira  da  mahamud  tunanin yake  idan  yace  zai  ta'bata to  babu  shakka  zata  mutu  idan kuwa bata  mutu  ba  zata  jikata ." "dan  girman  allah  Aunty ai.."ai  bata  kai  ga  fad'ar  abinda  take  son fad'a  ba  taji  wani   gigitaccen mari   hagu  da dama akan  kuncinta "you  are  very  stupid   bilkisu  , akanki  aka  fara  soyayya?"  kin  haukace  kin  makance  akan  wannan  banzar  ,me  yasa zaki  mance  ko  ke  wacece ?  wato soyayya  tasa  kin  manta  matsayinki ? cikin  muryar  kuka tace " a'a   Aunty  aisha   ban   mance   ba  amman  kuyi  hakuri  wallahi  bazan   sake  ba  "hayaniyar  yan   yan'uwanta  ya sake   d'aga  mata  hankali   shi kuwa   ussein  sunkuyar  da  kanshi. kasa  yayi   yana  tunanin  ficewa ya  bar  d'akin  dan  yasan Allah ne kawai  zai   kwacesa  a  hannunsu ."   Kai   tsaye   bilkisu   ta  nufi   bayan kofa  ta   boye  jikinta  na  wani  irin rawa  sakamakon   jiyo  muryar hajiya  rahma  tana  cewa "ina bilkisu  take  naga kun  tsaya  jugun   jugun  ko  ta  gudu ne ?  kafin  kace  me  an  samu  wanda   yazo ya  fad'a  mana   halin   da'ake  ciki a guje  na  bazamo  na   bar  hajiya  dan   bazan  iya   jiranta   ba kasancewar  tana  fama da  lalurar  ciwon kafa ." " ina  tafiya  ina  neman layin  yan' uwansashi   da  kyar  na  samu ta  abban  sadam  yana  gama  jin bayanina  cewa  yayi  babu  ruwansa  dan  yasan  halinsa da tara  yammata , babu  yadda banyi dashi  ba yace  bai  zuwa  koina  ya kashe  wayarsa  jin abinda  ya fad'a yasa  na  kira  yayyensa   mata ." Ina   shiga   unguwar  naga   jamaa  sun   yi   cirko   cirko!!  ga   manya  manyan   motoci  na  gidansu  bilkisu  jere a  kofar  gidan ,haka  ina  shiga   cikin  gidan  mutane  na gani  makil   kowa  na   fadar  albarkaci   bakinsa ,yayinda  muryar   mahaifiyarta  ya  karad'e  koina   acikin   gidan   "da  gaske  ne  bilkisu   tana  cikin wannna  ru'babben  d'akin ? Aisha ta  nuna  mata   bayan   kofar d'akin  "tana  ciki   kuwa  ga  makira  nan a bayan  kofa   ta  fad'a  tana   zubar  da  hawayen  takaici  ." "inna  lillahi !  hjy  rahma ta furta  a fili  cikin  tsananin  tashin hankali "kunji   abinda  naji  kuwa  wallahi  ji  nayi   zuciyata  kamar ta  buga ?hankalin  bilkisu  ya bar duniyar da  muke  alokacin  dan  sai  wuri  wuri  da  idanu  take  shi  kansa  ussein kana  kallonsa  kasan  nadama  ne  acikin   ransa  nadama  irin  wacce bata  da  wani rana ." " amman  bilkisu  bakince  min kin rabu  dashi  ba  ?jikinta  na  rawa ta  shiga  gyada  mata kai  alamun Eh! tana   bawa mahaifiyarta  hakuri  da  wani  irin  fushi  ta  juya  inda  ussein  yake   cike  da  nadama ta shiga  zabzabga  masa  mari  ta koina "bana  ce maka  ka rabu  mun  da  yarinya ba  ? ba  banace karka  sake   shiga   rayuwarta  ba?"Ko kaga  yarinyata   tayi  kalar  wacce  zaka ce  kana so ? ta  juya  zuwa  ga  bilkisu  " Ke yanzu  har  wannan  qazamin  ne  abun  so  a wajenki  ? ta  fad'a tana sake   juyowa ta  d'aga hannu  zata  sake  tsinkawa  ussein  mari  nayi saurin   rike   mata  hannu  ina bata hakuri  "kiyi   hakuri  hjy sam  ussein  bai  kyauta  ba  daya  bawa  yarinyarki damar  zuwa  inda  yake  ,ya  karbi laifinsa  ayi  masa  afuwa   in sha allahu  hakan  bazai  sake   faruwa ba   Kinsan   kowa da irin jarabawarsa  dukkanin  rayuwa  rubutaccen   lamari ne daga  Allah ,kuma   kowani  dan  Adam yasan  da  haka  ,yanzu  tunda  abun  ya  zama  haka ku bamu  dama  sai  mu  turo ayi maganar  aure "." Wani  irin  kallo  gabadayansu suka  bini  dashi  ,hjy  rahma  tace  "Allah ya  tsareni  na   had'a  zuria da wannan  ta  nuna  ussein  da  yatsanta  tana  hararsa "wallahi   bilkisuna  tafi  karfen  aurensa  ki kalleta  sama da qasa  ki  kallesa ta  ina   hadin yayi daidai  ?  duk  nasan  da  haka  hjy  amman  a wajenta  shine daidai    bugu da qari   rayuwar  yarinyar ku  zaku duba  domin  ita  diya  mace ce zata  iya fad'awa  kowani hali ." "Ba kowani  hali  zata  fad'a ba ko  mutuwa  zatai  sai dai ta mutu na yarda  na   rasata   gbdy  akan na bawa wannan   matsiyacin aurenta ta  numfasa  tare  da sa  tafin hannunta ta  share hawayen idanunta  "hjy  ki  daina furta  haka  shi  soyayya   allah ne  yake had'awa  , kuma  babu  ruwan soyayya  da  tsiya ko arziki  yarinyar  nan tana  qaunarsa  shima kuma  yana  sonta dan  girman  allah  ki  barsu  suyi  aurensu  kowa ya huta  sannna  babu  wanda  yasan matsiyaci ko  mai arziki  sai Allah  sannan babu wanda  yasan mai gobe  zata  haifar  ku barsu  su  aure juna   domin   samun  kwanciyar hankali ." bata   kulani  ba  har  na  dasa aya ta fuskanci  bilkisu  yayinda  gabadaya  yanuwanta   kacokan  suka  maida  hankalinsu Kan  ussein  duk  sun qagu  suga hukunci  mahamud  akan  ussein kasancewarsa  soja ,  hjy  rahma  ta  matso  sosai  kusa da  bilkisu tana cewa  "ba  dai  ni  zaki  wulakanta   akan namiji  ba ? ."babu  irin  rarrashin da ban miki ba ,babu  irin  hakurin da ban baki ba ,me  kike  son  dani  ? "wallahi  zanyi  dake  bilkisu , yau  zaki ga tozarci  ganin  idanunki  tunda kika nemi ki  wulakantani akan wani banza  can  wanda  ba kowan kowa  bane  shi  ,ba kowa bane  iyayensa   a  duk  fadin  garin nan hasalima rayuwarsa  a  banza take ." "zaki  wulakantani  akan  wani nmj banza da  wofi  wallahi  zanyi  dake muddin  kika  ce  shi  zaki aura sai na  tsine  miki  na  tsinewa  auren ,wallahi auren  bazai  ta'ba  yin albarka tana  mgn  tana   zabga mata  mari a fuskarta da bayan hannunta  , yayinda  azaba tasa bilkisu ta shiga  karewa  dan kar marin yayi mata illa amman matar nan sai zabga mata maruka take kuma a fuska na rantse miki da girman allah maryama tayi mata mari yafi guda tara ajere ana goma ne bilkisu ta rike mata hannu kuma nasan azaba ce tasa tayi haka ,aiko matar nan ta  danneta da iyakacin karfinta ta dinga dukanta  tana cewa ni zaki rikewa hannu in sha allahu kema sai ya'yanki sun miki abinda kika min ,sai sun hanaki kwanciyar hankali kamar yadda kika hanani kwanciyar hankali a karshe  kafa mata hakori a  damtsen  hannunta." "wani irin  gigitaccen  qara  bilkisu ta saki mai ban  tausayi  tana  kuka  tana neman  d'auki  gashi  babu wanda ya  kwaceta  daga  hannun mahaifiyarta sai dukanta  take tana hadawa  da  zagi  ganin  haka yasa ussein  ya  nufi   hjy rahma cikin tsananin  fushi  kamar mayunwanci zaki  idanunshi  sun kad'a sunyi jajur   yasa  duka hannunsa zai d'agata  daga  Kan  bilkisu ai  ganin ya  ta'ba  mahaifiyarsu  gbdy yan'uwanta  suka yo Kanshi shi da  bilkisu  cike  da  jin haushi suka dinga dukan su  kamar zasu kashesu suna furta mahaifiyarmu zaka  duka ? azahiri gaskiya ba wai dukanta yayi  ba  kawai ceton bilkisu zai yi  daga dukanta, ina kuka ina basu  hakuri ina qoqarin kwatarsa daga hannunsu amman ina sarkin yawo yafi sarkin karfi dan sai suka daina dukan bilkisu suka cigaba da dukansa  shi kad'ai har sanda hjy  ta shigo zubewa tayi kasa tana kuka tana cewa "zaku kashemun d'a ne to wallahi idan kuka kasheshi hukuma ce zata rabamu  daku dan wallahil azim  bazan ta'ba  yarda ba ". "kar Allah yasa ki yarda daman kece uwar matsiyaci ?  "nice  uwarsa  kuma  gatansa kuma ni d'ana ba matsiyaci bane dan me zaku masa haka ? "ai yarku zaku jawa kunne ta daina zuwa inda yake shi meye laifinsa ? "laifinsa kulata da yake yi idan baya  kulata bazata zo inda yake ba ,idan yace baya sonta karta sake zuwa inda yake ni nasan bilkisu bazata zo inda yake  ba ki fad'a masa da babban murya ya rabu da kanwarmu  ya zauna lafiya idan ba haka ba zamu 'batar dashi agarin nan ,kina ji kina gani zaki rasa d'anki har abada  "hjy  na fad'a 'yanuwan bilkisu na maida mata martani kuma basu daina dukansa ba ." "neman layin 'yanuwasa mata na sake yi saadatu na d'auka na saka mata kuka ina cewa "bazaku zo ba sai an kashe maku da'nuwa ?dan girman allah kuzo ku hanzarta karku bari su illatashi "bilkisu cikin kuka ta rarrafa ta rike kafafun mahamud domin duk yafi dukan ussein cikin kuka tace "yaya dan girman allah kayi hakuri ka barshi karku kashe min rayuwata sannna karku rabani da dashi wallahi bashi da laifi nice mai laifi" . "ya salam! ya furta a matukar fusace "wai bilkisu me ke damunki ne  "?ta girgiza masa kai idanunta na zubar da ruwan hawaye  kuyi hakuri nayi maku alkwarin bazan sake zuwa inda yake ba "muryar hjy rahma ta sake karade d'akin Aisha riko hannun makaryaciya  karta gudu shi kuma sheidani ku fito min dashi yau zan nuna masa koni wacece agarin  nan zanga uban da ya isa ya kwaceka Aisha ta riko hannun bilkisu  gam bisa umarnin mahaifiyarsu sai dai bilkisu ta dinga turjewa nan ma wani marin aisha ta kai mata tuni daman fuskarta ta canza jini ya kwanta a duka idanunta ." Mahamud kuwa qarasawa  yayi inda ussein yake yace ya kama kunnensa ussein ya kama kunensa cikin kaduwa dan gbdy bai fahimci abinda yake nufi ba mahamud yace "you're very stupid I mean kayi frog jump Aishat ashe ma illiterate ne wallahi ko da wasa naji ka qara shiga harkar bilkisu zan mugun baka mamaki  "mugun ma illiterate katon jahili liability kawai a haka zamu bashi aurenta sai kace kwakwaluwarmu ta juye  ai har abada ,ka wuce dashi kaci ubansa ta yadda ko mai kama daita ya gani da mugun mugu zai arce ." bilkisu na kuka ussein na frog jump nima ina biye dasu ina basu hakuri haka hjy hakuri take basu hankalinta a tashe muna fitowa kofar gida sai ga saadatu da fatima a rude basu tsaya  neman baasi ba dan na rigada na fad'a masu komai  sausauci suke neman masa amman mutanen nan  suka ki banda cin mutunci babu abinda suke zubawa  unguwa kuwa ya cika makil da jama'a yan kallo kowa na fadin albakacin bakinsu wasu suna ganin daidai ne matakin da suka dauka dayawa kuma laifin bilkisu suke gani  ." wani abu mai daci yan'uwansa suka hadiye  tare da matsowa  inda mahamud yake yana laftawa ussein belt a gadon bayansa "yanzu ina zaku dashi ?In ji cewar fatima  tayi maganar cikin tsananin fushi "zamu tafi dashi inda zamu sake koya masa hankali,"  ya fad'a cike da gadara da isa "amman yana  da kyau mu san inda zaku da d'anuwanmu kafin ku wuce dashi?  Eh ! yana da kyau sai dai  bani da wannan lokacin  'batawa idan aka koya masa hankali zaa iya sanar  daku kuzo ku d'auki abinda ya saura ajikinsa " Hjy kuka saadatu kuka haka ma fatima muna cikin wannan halin sai ga gali yace shine yayansa suyi hakuri su bar komai a hannunsa zai sa ya rabu daita rabuwa ta har abada ,mahamud yace "da dai ya fiyye masa  kwanciyar hankali dan wallahi na sake dawowa akan case din nan sai dai ku dauki gawarsa" gali yace "to mun gode komai yazo karshe bilkisu ta bude idanunta da  suka mata nauyi  wani marayan kuka ta fashe dashi tana shesheka tana kallon kowa wanda ni nasan kukan da take alokacin bai wuce na rabuwa da ussein ba ." fatima ta watsa mata harara hade da kallon banza tana cewa  "kukan uwar me zakiyi wa mutane duk bake kika jawo masa matsala ba  yana zaman zamansa muguwa  azzaluma kin janyo yanuwanki sun wulakanta mana d'anuwan an tozarshi, tunda muke anan unguwar aka haifemu muka girma mukayi aure baa ta'ba wulakantamu ba sai yau kuma duk akanki ,kinsa ana dukansa kamar an samu ganga na rantse da girman allah  matukar ussein..." saurin toshe mata baki nayi ina cewa  fatima karki rantse  ,cikin fushi ta cire min hannu "ki barni  aunty nayi magana kalli yadda fuskarsa tayi duk jini saboda Allah yau ayita ta qare ta kama kanta ta daina zuwa inda yake ,yanzu da suka zo suna hargagin banza da wofi da wulakanci shi meye laifinsa? yarinyarsu ya dace suyi wa magana ta daina zuwa inda yake dan muddin ta sake zuwa inda yake kafin ku dauki mataki mu zamu dauka dan ba daga sama ya fado ba azzaluman banza kawai kuma allah ya isa tsakaninmu daku tana fad'a aisha na fad'a."dan girman allah fatima  karki sake cewa komai zo muyi magana na janyo hannunta " babu inda zani aunty ayita ta qare gwama su san muma bama son wannan diyar tasu kuma komai zai faru ..." na sake toshe mata baki "dan Allah ki bar mgnr nan  sulhu ake nema ." Cikin ko in kula hjy rahma tace  da wa zakuyi sulhu ?"kema  Kinsan ruwa ba sa,an kwado bane baku kai wannan matsayin ba yanzu ma wannan maganar da nake duk sai na fashesa akan wannan matsiyacin "nayi tsuru tsuru ina dubanta "tsayuwar  me kukeyi ku taho min  dashi da sauri  gali ya qaraso inda take hjy ai mun gama magana da yaronki, dan allah hjy kiyi hakuri ,in sha allahu tunda muka shiga cikin zance komai yazo karshe zanyi magana dashi  "babu irin hakurin da baa bawa hajiya rahma ba amman  tace sam sai an tafi dashi haka muna ji muna gani aka watsa useein abayan boot din mota aka wuce da ussein ." Kuka sosai maryama take kamar alokacin komai ya faru Kwantar da kanta umma tayi akan cinyarta tana rarrashinta "tabbas Aunty masoyiya ce ta gaskiya ,ta so mahaifinmu a halin babu ,ta zauna dashi har karshen rayuwarsa wallahi ba kowani d'an mai kudi bane mutumin kirki kamarta ,ta tsaya ta dubi mahaifinmu da kalmar so ta gaskiya sai dai akwai illa umma Aunty ta jefa rayuwarta cikin matsala wanda a yanzu take shan wahala ". " tabbas shine gskiyar dana dade ina nuna mata "baa jayayya da iyaye data yi hakuri tabi umarnin iyayenta tabbas zasu sauko dan kansu kasancewar akwai rabo a tsakaninta da mahaifinku ,cikin muryar kuka tace "mune silar jefa rayuwar mahaifiyarmu cikin wahala ko ? ta fad'a tana sheshekar kuka "karki ce haka maryama haka tata qaddarar take ,ita qaddara gata ko arziki ko nasaba bai isa ya canza maka ba ."umma ta numfasa sannan ta cigaba da magana ". Bangaren su  bilkisu kuwa tunda suka dauki hanya  yan'uwanta suke magana suna zagin ussein cikin kuka bilkisu Ke rikon su "ku sani ussein bai muku laifin komai ba dan allah karku hukuntashi akan abinda bai yi ba"  mari mahaifiyarta ta kifa mata haka ma aisha dan ubanki ki kama mana baki har suka kai gida zaginta suke direba na ajiyesu ya wuce da mahamud da ussein ." a matukar gigice bilkisu tabi byn  motar da kallo cikin tsananin firgici, keyarta suka tasa sai cikin bangaren hjy rahma ."Suna shiga part din hjy rahma suka turata daki  suka daureta da igiya tamau sukasa saber  ya dinga dukanta  adaure  tun tana ihu har tazo ta kasa a yadda ta fad'a min cewa tayi har da barkono  mahaifiyarta ta nika tasa mata a gabanta da cikin idanunta wanda yasa tayi suman wuncin gadi ." Bangaren mu rana  babu wanda ya samu sukuni  acikinmu gali yafi kowa  shiga damuwa safa da marwa yake yana cewa "ban  ta'ba kawowa araina duk hakurin dana  basu ba zasu hakura ba , na dauka maganata zai sa su hakura amman ina kamar sake fusata mahaifiyarta nayi wadan nan mutane sam basu da imani ."wallahi basu da imani gali inji cewar hjy ka kalli irin duka da sukayi yarinyar nan bilkisu ko rikonta suke bai dace suyi mata irin wannan dukan ba ." "wallahi ku sheida bilkisu bazata sha wannan wahalar a banza ba komai zai faru sai useein ya aureta ba dai bakinciki su kenan ba saboda suna takama da kudi ,ni bana da kudi amman ina da Allah alfarma annabi da alqurni sai wannan auren ya tabbata ko ina  raye ko byn na mutu mutane sam babu imani aransu bazai hakura da aurenta ba sai dai su mutu fatima zatayi magana ta dakatar daita "banason jin komai daga bakinku sai fatan wannan auren ya tabbata ." abban sadam ya fito daga bayi daman zagayawa yayi yace "har yanzu bazaku hakura da wannan maganar ba ? hjy tace "taya zaa hakura?" da sukutun fa suka wuce min dashi ?naga diyarsu ce tunda sunce basaso tarayyarsu a hakura mana "bazaa  hakura ba bilkisu bazata  sha wahala akan ussein ya tafi a banza ba ina sonta tunda tana son jinina ta gama min komai ni yanzu ta'bo min abokika Abdul zanyi magana dashi babu irin kiran da baayiwa Abdul  ba amman wayar bata shiga ranar hjy bata runtsa ba kwana tayi tana kaiwa allah kukanta ." Washegari ana idar da  sallahr asuba tasa aka cigaba da trying dinsa amman shiru baya shiga sai karfe

Chapter 23 of 43