aunty iyaye suna da kimar da darajan da bazaa iya mantasu ba ."
ahankali taji sautin muryarta tana fita cikin kuka "nayi kewarka baba , nayi kewarki mamana yanzu ku har yanzu bakuyi kewata ba ?yanzu ku baku yafe min ba ko nemeni ba? wallahi ina sonku nayi kewarku ,nayi kewar kowa da kowa ta fad'a tana mai daura hoto a saman qirjinta tana shafawa tana kuka.."
Ahankali maryama ta juya tana zubar da hawaye masu zafi ta koma falo ta zauna kusa da habib tana sheshekan kuka nan take ya birkice ya soma tambayarta "heartbeat me kuma ya fara ?kukan me kike yi ? Ina aunty ?yayi mata tmbyr ajere cikin tsananin tashin hankali tasa gefen rigarta ta goge hawayen "yau aunty ta tuna da iyayenta tana daki tana kallon hotonsu tana kuka ni nasan zuciyarta na cike da qaunarsu shiyasa kaga ina son ta koma garesu ."
"habib soyayyar iyaye da yanuwa baa wasa dasu wallahi a tsakaninsu soyayya ce mai karfi ka misalta hakan akanmu musan da qaddara amman an cuci aunty an yi sanadiyyar rabata da kowa nata ,ta bar iyayenta akan soyayya gashi ta rasa soyayya taki bin umarnin iyayenta gashi duniyar taki mata dadi maryama tana kuka habib na rarrashinta har kukan nata ya ragu adaidai lokacin da sukaji tahowar aunty tayi saurin share hawayenta tana cewa ".
karka nuna mata komai da sanyi jiki ta qaraso "kun samo abinda zaku dan ci ?eh mun samu har da cinci tô maza kuci ku kwanta tayi maganr cike da rauni aunty kizo muci tare "aa ku dai kuci ku koshi aa wallahi tare zamu ci habib ya mike ya kamo hannunta ya zaunar daita ya bude kula abinci yana cewa kai abincin nan zai yi dadi maryama ta dauko spoon ta dibi abinci zata kai bakin aunty habib yayi sauri ya kwace spoon "bani ni zan bata da kaina suka sa da dariya ya soma bata abinci abaki yana fada mata kalamai masu sanyi ."
"idan nayi kudi bazan yi nesa dake ba zan kasance tare dake ,dan allah aunty ki daina damuwa akan komai kinji ki dinga tunawa cewa kina damu mu din zamu zame miki farinciki a rayuwarki Wallahi sai mun sa kinyi alfahari damu ki cigaba da addau ga heartbeat nan kwanan nan zata fara bautar qasa yanzu ma ina mata processing yadda zaa dawo daita lagos né daga adamawa wannan farinciki ya rage tarin qunar da zuciyar aunty take ciki tace "allah yayi maku albarka yayiwa rayuwarku albarka in sha allahu bazaku dangwama haka ba allah zai saukaka maku rayuwa ,Allah nake roko ya daukaka min ku na yafe maku duk abinda kuka min da wanda nasani da wanda ban sani ba suna cin abinci suna debewa juna kewa ."
******
da misalin karfe 9:00 na washegarin ranar lahadi mr ata ya fito parlour'n mami ,duk jikinsa yayi sanyi har wata katuwar rama yayi daman ya lafiyar kura ?ba wani jikin kirki bane dashi kusantowar aurensa da maryam yasashi jin kmr ana fixgar ransa ,shiru ne ya ziyarci parlour'n yana tunane tunane yana jin kamar idan ya tafi france kar ya dawo domin a lissafinsa sauran kwanaki goma cif a daura masa aure da yarinyar daya tsana fiyye da komai arayuwarsa byn kmr mintina goma mami ta qaraso da kanta ta had'o masa abun kari , chips da soyayyen kwai da ruwan tea mai kauri , ta janyo qaramin table gabansa ta ajiye kana ta zauna kusa dashi ta tsura masa ido tana kallonsa batare datace komai ba ."
ya dauki cup din tea ya kai bakinsa ya kurbi kadan yana mai runtse idanunshi shiru har wasu mintuna suka shude yana zaune itama tana zaune tana kallonsa da kyar ya bude baki "sweetheart! "kaci abinci first before anything adamcy , sannan kar naji kayi magana kaci abinci kawai yaushe rabon ka sanyawa cikinka abinci bare a samu magani yayi aiki ajikinka ? ji yadda ka dawo acikin kwanaki uku kacal ka taimakeni kaci wani abu kanshi kawai ya iya d'aga mata batare da ya kalli inda abinci yake ba, saboda sam baya jin cikinsa zai iya amsar komai shima da zata taimakesa da tasa an fasa auren nan da yarinyar an hadashi da wata zai hakura da princess dinsa ya amshi koma wacece duk da zuciyarsa princess kawai take so da son gani numfashi ya dinga saukewa ."sweetheart dina me yasa kika manna min wannan auren haka?
" sweetheart zaki kasheni da kanki wallahi at least ki sake gara min dama koda na tsawon wata guda ne ."
"to me zan maka adamcy nah daya wuce haka ?
"me kake son nayi idan banyi maka haka ba ?
gani nayi kana neman hargitsa min kwakwaluwa da qarar da rayuwarka a banza "me kake tunani mutane zasu ce idan bakayi aure adaidai wannan lokacin ba ? wallahi zaka shiga zargin mutane ,mutun har mutun kamamme kamar ka ka zauna babu aure ko kana neman mata ne adamcy bansani ba da kake gudun aure ."
wani irin kallo yayi mata mai nuna mata bayayi "to idan bakayi me kake jira ?maryam yaruwarka ce fa "yanzu kai kafi son ka dauko min suruka daga waje alhalin ga wacce tasan darajata take sona nake sonta diyar danuwana yanzu idan an fasa auren nan me kake son na cewa mutane da yan'uwana ,dan Allah dan annabi in banda da rigima irin naka ba me ye laifin maryam ..?
"wani far yayi da idanu zuciyarsa na dokawa da numfashinsa da yayi kokarin d'aukewa yayi saurin dawowa dashi gangar jikinsa sannan yace "sweetheart ni bance tana da laifi ba amman ki duba lamarin da kyau tunda nace bana sonta ai sai a hakura kawai kowa ya kawo zabinsa . "kai rufe min baki ban son shirme banza, ka daina ganin ka had'a komai kana da kudi kayi tunani zaka iya juya ni ."Wannan aure sai anyi shi muddin ina raye ."
ya marairace muryarsa sosai tmkr mai shirin zubar da hawaye sannan yace "wai sweetheart me yasa kike ganin kmr wannan yarinyar ce kawai zata iya kulawa dake ? Allah sweetheart ki daina mata kallon haka saboda irinsu sune masu bawa dangi kunya wallahi duk lokacin da naji kince min itace zata san darajarki bakinciki nake ji kmr na kashe kaina saboda ni duk macen dana kawo miki dolenta ta soki tayi miki biyayya bama Ke ba sweetheart hatta yayyuna biyu din nan dolenta ta bisu lalacewar mace daga miji ne ni kuma bazan ta'ba bada wannan damar ba .. "
"Sauran kwanaki goma a daura maka aure da maryam a lissafina gobe ko jibi jirginka zai cale zuwa qasar france fatana allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya shahida ta gama shirya komai na aure fatan alkhairi da dawo da niyyar angeancewa lafiya and if you do anything stupidty I will del with you kai ma kasani ina sonka fiyye da tunaninka amman hakan baya hana idan kayi ba daidai ba naki hukuntaka tana qoqarin mikewa hisham ya shigo ya gaishe da mami cike da girmamawa sannan ya zauna kusa da ata daya runtse tsumammun idanunsa tun byn da mami ta soma magana "yaakayi mutumina ya karfin jikin hope you are getting better?"numfashi kawai ya sauke wanda Ke nuna masa alamun ya amsa hisham ya cigaba da magana "har yanzu sultan da fahad basu dawo da komai ba fa Kmr ma sun dauki abun matsayin shiririta tsabgogin gabansu kawai suke."
"ina sane da komai kai kasan bana canza maganata ina jiran na dawo daga france ne suna zaune suna hira mb ya shigo haka ma yaya Ibrahim ya shigo duba jikin mr ata tare da aunty abida har da yesmin wacce ta dane jikin mr ata haka ma yammatan gidan
d'aya byn daya suka dinga shigowa suna gaisheshi da kyar yake bude bakinsa yana amsa musu cikin rashin sakin fuska , cikin wasu mintuna aka cika gaban mr ata da kayan motsa baki , amman babu abinda yaci illa coffee daya dinga tsiyaya a cup yana kurba ahankali ahankali shima yana sha ne kawai saboda sabon da yayi dashi ."
Parlour'n ya dan rage mutane ya saura daga hisham sai ata nuzla da diyana har ma da mrym da nana hauwa'u suka shigo parlour'n bakinsu d'auke da sallama hisham na ganin nuzla ya saki fuskar ganin masoyi yarsa gbdy suka hada baki wajen yi ma mr ata ya jiki banda nuzla Kmr koda yaushe da kyar ya amsa masu hisham yana kallon fuskar nuzla yayinda nuzla taja ta tsaya daga gefe can ta jingina bayanta da bango ta rungume hannuwanta duka bisa kirjinta tare da tsura ma mr ata fararen idanunta tana kallonsa cike da matsanancin soyayyarsa yadda ko kallon mrym da zai aura bai yi ba abun yayi mata dadi sosai yadda bai son mrym abun na mata dadi har yana bata kwarin gwiwa dan tun daga ranar daaka saka ranar aurenau take jin haushinta sannan take cikin damuwa mai tsanani ."
ahankali ta bud'e bakinta tace "yaya sannu ya jiki banza yayi mata Kmr bai ji ba nan kuwa yaji sarai hisham yayi qasa da murya yace "ata ana maka sannu da jiki "naji !ya fad'a atakaice dan ya fahimci wani abu a attare daita ba tun yau ba yana hankalce da irin kallon da take masa a duk sanda zasu hadu tun a office din aunty shahida yaso yaci ubanta allah ya taimaketa "take gabanta ya shiga fad'uwa sbd fargaba dan ganin ko kallon inda take tsaye bai ba illa kur'ban ruwan coffee daya cigaba dayi kuma taji amsar daya bawa hisham kuma tasan sauran ma
sunji abinda ya fad'a ."
ahankali ta juya ta nufi kofar fita cikin bacin rai sannan sauran yanuwanta suka biyo bayanta "amman ai ya kamata ka amsawa gimbiyata ya sake yin mgn can qasa"gsky hisham baka da hankali km kana bani kunya yanzu kai da gaske sonta kake "?sosai ma kuwa ina sonta sai dai ita bata sona ..""what ?" Wallahi haka ta fad'a ai naso bikin a hadashi da naka amman ya zanyi tunda tace bata só na hakura amman nasan sonta ne zai kasheni "amman shine ka kyaleta baka ci ubanta ba?
aa babu wannan ai kai ma kasan yadda soyayya take ka duba yadda baka son mrym kake son yarinyar mafarkinka "ka daina kawo wannan misalin ni bana son wannan yarinyar ita ma kuma bata sona kaga akwai matsala wajen namu hadin ko ka fahimceni ."?
"Misali ina sonta to ya zama dole dan ubanta ta soni sannan misali da'ace tana sona nima bazan dinga jin tsanarta haka ba duk da nasan nawa rashin son ne babban matsala dan ita prentending ne kawai nasan babu macen da zata kalleni tace wai bata sona dama ne kawai bata samu ba ,ya fad'a yana jan tsaki ka kira min auta "me zata maka ?Kai dai kira min ita kawai yau yarinyar nan zataci ubanta da me tafika da zata ce bata sonka ?shiru hisham yayi yana kallonsa a she haka ata yake sonshi jiki a sanyaye ya dauki wayarsa ya kira nana hauwa'u cikin kankanin lokaci ta bayyana a falon "yaya gani "je kizo min da nuzla yanzu yanzu kafarta kafarki "okay yaya ta juya da sauri ."su kuma suka cigaba da tautaunawa ."
Bayan mintuna goma sai gasu sun shigo nana hauwa'u ta kama gabanta ta bar nuzla tsaye cike da fargaba ta dan saci kallon hisham dake zaune taga ya sakar mata murmushi ta kalli mr ata taga ya hade rai sai kafarsa daya yake girgizawa har kusan mintuna shabiyar tana tsaye sannan tace "yaya gani wai ..."da sauri ya dakata daita ta hanyar daga mata "waye wannan ?ya nuna mata hisham dake zaune "yaya hisham ".
"Very good meye a tsakaninku ?nothing ta bashi amsa atakaice ba hisham ba hatta mr ata sai daya dago tsumammun idanunshi ya tsura mata yana kallonta "kika ce nothing kenan baki san yana sonki ba ?nasani but na fad'a masa gaskiya ni bana son shi dan ..."enough ! bana bukatar jin maganarki ko wani abu kije ki fara shirin aurensa nan da kwanaki goma ." cikin firgici da tashin hankali ta shiga d'aga kafafunta zuwa inda yake zaune "me yasa yaya ?" dan Allah kayi hakuri karka min haka wallahi ni bana son shi a matukar tsawace yace "nace karki sake fad'ar wata magana anan , karki sake kula kowa acikin masu sonki shima wanda kike so ki kashe soyayyarsa acikin zuciyarki ki so wanda yake sonki .."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 20
jikinta na wani irin rawa ta k'araso ta durkushe a gabansa har bata san sanda ta d'aura hannuwanta duka bisa cinyoyinsa tana kallon cikin kwayar idanunsa da suka rikid'e suka canza kala a wulakance ya zame jikinsa yana mai kawar da fuskarsa gefen hisham dake zaune tmkr mutun mutumi yana kallonsu cike da matsanancin tashin hankali ,shi kuwa mr ata alamun baya son kallon fuskarta ne yasa shi maida idanunshi kan hisham ".
"dan allah dan Allah !! yaya adam kayi hakuri ta kai hanuta tana qoqarin juyo da fuskarsa gareta domin su fuskanci juna , zuciyarta na wani irin bugawa da karfin gaske take kallonsa haka ma hisham zuciyarsa ce take ta bugawa fiyye da kaida ya soma jin wani sauyi na daban a gabadaya ilahirin jikinsa wanda ke gauraye da tsantsar tashin hankali, shi kuwa mr ata mamakinta yasa gbdy ya qasa magana duk da maganar yake son yi .
Kwayar idanunta suka cicciko da ruwan hawaye muryarta a sarke tace "dan Allah yaya kayi hakuri karka bari wannan auren ya kasance domin zuciyata bazata iya d'aukar wannan nauyin ba, wata razananniyar tsawa ya buga mata wanda ya kamata ace ta tsorata ta dawo da hankalinta jikinta amman ina sai ma sake narkewa tayi a wajen zuciyarta babu tsoron komai acikinta , muryarsa a kausashe yace " tashi ki bar nan ki kuma fara shirinki kamar yadda na fad'a miki oya leave ."
"dan Allah ka saurareni yaya "ya girgiza mata kai yana cewa " I don't want to listing anything from you just leave now "dan allah yaya adam kayi hakuri ka saurareni akwai maganar da idan na fad'a maka nasan zaka fahimceni "ata dan Allah ka barta ta fad'i abinda ke zuciyarta Hisham yayi maganar yana qarewa jikin nuzla dake rawa tmkr mazari da kallo , yadda take cikin tashin hankali haka shima ya tsinci kanshi cikin tashin hankali mai tsanani har yana jin ma kamar ya cire mata nata damuwar ya qarawa kanshi "
Hisham yayi tsuru tsuru yana jira yaji abinda zata fad'a ,yayinda mr ata bai ce uffan ba ya yunkura ya mike tsaye ya kwashi wayoyinsa ya fara taka kafafunsa da kyar zai bar wajen kasancewar bai son yawon magiya bare irin nata dake hargitsa kwakwaluwa nuzla tayi saurin shan gabansa tana fad'in "yaya karka wuce ka bar zuciyata cikin maseefa tayi maganar cike da tausayawa ,bai yi mata magana ba ya cigaba da tafiya yana mata gargadi da hannunsa alamun ta shiga hankalinta , bata daddara ba ta sake shan gabansa dan gbdy zuciyarta ta rigada ta bushe babu abinda take qoqarin aikatawa face ta bayyana masa ciwon dake cikin zuciyarta ."
Ya tsaya kawai yana mata wani mugun kallo
yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa muryarta cike da rauni da buqatar atausaya mata ta fara magana "bazan iya jure ciwon rabuwa da wanda nake só na auri wanda kake só ba ta karasa mgnr tana rungumeshi ajikita tana kuka a matukar zuciye ya fixgeta daga jikinsa yana sake furzar da iske "are you out of your sense ?ni sa'anki ne da kike shiga gabana? " ko ina wasa dake ne da ina magana kina magana ? ya fad'a yana kawar da fuskarsa akanta domin dai zuciyarsa ta fara tausaya mata tausayawar da bata da wani amfani dan bazai ta'ba iya mata taimakon da take nema daga garesa ba ."
Hisham ya rasa meke faruwa atsakaninsu babu abinda zuciyarsa bata kissa masa ba a zaune da yake tmkr an dasashi irin kallon da take ata da rungumar da tayi masa ya fara gasgata zuciyarsa akan abinda bai niyyar yarda dashi ba yaso ya mike ya qarasa zuwa inda suke tsaye yasan ko akan me take masa magiya har da runguma amman hakan nan yaji gara ya cigaba da zama a inda yake zai fiyye masa alkhairi kuma bugu da qari yayi imani ata bazai ta'ba aikata komai ba face abinda yasan zai zamewa rayuwarsa farinciki he really trust him mutun ne shi mai kyakkyawar zuciya akanshi ."
Hawaye na gangaro mata bisa kuncinta yayinda magana ya fara fitowa daga bakinta "ina qaunar ka yaya ? bai yi mamakin jin fitowar hakan daga bakinta ba domin ya rigada ya gama karantata tsab "na sani sai akayi yaya ?ya fad'a yana kallonta yana jin kamar ya soma yar yarfa mata maruka ta dawo haiyacinta "dan Allah yaya karka ce min a'a ! a kowani hali zan kasance tare da kai " ta maimaita hkn a fili yafi sau goma tana mai kai hannu ta shafa kasumbar dake kwance a fuskarsa ji yayi kamar ta shafa masa garwashin wuta ,shi fa duk duniya babu macen da yake jin zata ta'ba shi yaji wani abu ajikinsa sai princess ita ma din yanzu ya soma gogeta a zuciyarsa da rayuwarsa ."cikin fita haiyacinta
ta riko fuskarsa sosai ta sanya kwayar idanunta dake tsiyaya ruwan hawaye acikin nasa " ban san hka soyayyarka tayi tasiri acikin zuciyata ba sai dana qasa amsar soyayyar kowa ."
"Ban san tasirin soyayyarka ta kai mizanin da zan iya rasa rayuwata ba sai da naji zaka min nisa , yaya kaine duniyata ruhina yana tare da kai ako da yaushe , nayi yunkurin bayyana maka soyayyata a tun lokacin da mubina Ke mutuwar sonka amman na gaza aikata hakan ina ganin cewar zan iya cire soyayyarka na cigaba da rayuwata amman still na qasa domin kuwa every each second nake jin sonka na qaruwa a cikin zuciyata , ina ta qoqarin sheida maka halin da zuciyata take ciki kwatsam kuma sai ga batun aurenka da marsi bance ka bar marsi ba amman dan allah ka had'amu ka auremu " rokonki bai kar'bu ba bare wata alfarmar ya kamata ku koyi yadda ake iya control din zuciya "ka taimakeni ban san ya zanyi ba " kar allah yasa ki sani ya fad'a yana jan tsaki ."
kuka take sosai tana kallonsa tmkr ranar ta fara ganinsa shi kuwa haushi ne ya turnikesa a wajen zuciyarsa banda tuttukin bakinciki babu abinda yake , a ganinsa ma ta balain rainashi
shi zata kalla tace tana so alhalin ga hisham dake mutuwar sonta? "kayi hakuri dan girman Allah nasan zakayi tunanin komai akaina wallahi haka ne , dan na rigada na haukace akanka bazan iya jurar abinda nake ji akanka ba sannan bazan iya amsar soyayyar yaya hisham ba ,dan kona auresa gangar jikina ya aura zuciyata da komai nawa yana gareka da kawai zan iya rayuwa ..."
Ta riko hannunsa hawaye na zuba daga idanunta ta soma tafiya dashi taku d'aya biyu yayi ya tsaya cak , itama ta tsaya suna fuskantar hisham naunaye ajiyar zuciya ta sauke tana goge hawayen dake tsiyaya ,ahankali ata ya zare hannunsa dake cikin nata ya yarfar sannna ya zura cikin aljihun wondonsa yana jan tsaki "ya hisham! ta kira sunansa a kid'eme "banyi niyyar fito da sirrin dake zuciyata ba amamn ya zama dole na fad'a maka tunda na fad'awa yaya adam babu komai acikin zuciyata sai..." karki kuskura kiyi wannan ganganci dan kome zaki yi tawa zuciyar bazata amince ba "to kuwa gara ka ksheni da hannunka na huta dan nima bazan iya auren yaya hisham ba , yana sona ni kuma kai nake so.."you're very stupid Kiyi maza ki danna madannin gogewa ki gogeni arayuwarki da zuciyarki dan ni mallakin mafarkina ce " yana gama fad'ar haka ya juya ya haye sama yana taka step yana magana " hisham ka manta da shirmen wannan yarinyar ka soma naka shirin domin wannan auren ko zata mutu sai anyisa useless girl kawai ga inda ake sonku aka damu daku amman ku dinga kai kanku inda bazaa ta'ba sonku ba nonsense "
Hisham ya runtse idanuwanshi "kenan hasashensa ya tabbata , zarginsa ya zama gasky kenan akan ata yake shan wulakanci da tsana da wahala a wajenta ? ,"ya kalleta cike da tausayawa yace "daman ata Kike so ?jikinta yayi mugu mugun sanyi ta rasa me zata cewa hisham illa ta runtse idanunta gam tana jin zafi da ciwo mara iyaka a zuciyarta ,ta durkushe qasa tana kuka tana nemawar kanta mafuta dan dole tasan abun yi kafin a had'ata aure da hisham shima ya durkushe gabanta ya dago ha'barta ya sanya kwayar idanunshi cikin nata , tai saurin buge masa hannu tana kallonsa cike da tsantsar tsana "ka kyaleni ni wallahi bana sonka tunda burinka kenan na soka , dan girman allah ka rabu dani ka manta dani, ka manta da maganar ka ta'ba sona arayuwarka , ka mantani ta qarasa fad'ar haka tana fidda huci mai zafi ."
"Dan allah kiyi hakuri nasan irin ciwo da zafin da Kike ji acikin zuciyarki ciwo ne kwatankwacin wanda nake ji acikin zuciyata nasan zafin ciwo da radadin kana son wani baya sonka ,wallahi na tausaya miki amman me yasa nuzla ?"me yasa sai ata zuciyarki zata kamu da so byn ni ina qaunarki ya kai hannunsa yana share mata hawaye"ata bashi da wannan lokacin wahalar da kanki da zuciyarki kawai zakiyi babu wannan tausayin a zuciyarsa a karshe ya rungumeta ajikinsa tsam yana shafa bayanta ahankali ahankali babu yadda ta iya dole ta kasance rungume ajikinsa domin tana bukatar wanda zai rarrasheta kuka take sosai tana rungume ajikinsa "ki daina kuka nuzla dan zuciyata bazata iya ganin hawayenki da damuwarki ina matukar sonki da zaki bani dama da sannu zaki daina son ata ki soni ya fad'a yana qara rungumeta gam ajikinsa ahankali ya mike tsaye tare daita ya nufi kofar fita tun kafin mutane su shigo su fahimci halin da suke ciki ."
Washegarin da misalin karfe tara na dare ata ya shiga d'akin mami sanye cikin fararen kayan bacci wondo da riga , hannunsa rike da black cup dinsa dake dauke da ruwan coffee ,yayinda dayan hannunsa Ke cikin aljihun wondonsa ya samu mami tsaye a gaban wordrobe dinta tana qoqarin rufewa tana ganinsa ta sakar masa murmushi tana cewa "Masha allah adamcy nan ya karfin jikin ?alhamd sweetheart ya qoqari dani ?kwana nawa ya saura ai Allah Allah nike Kayi tafiyar nan ka dawo mu sha biki ranar bani da dama zan aurar da d'a daya tilo ya girgiza kai kawai yana ajiye cup din hannunsa akan bedside dinta ya tsura mata tsumammun idanunshi yana kallonta tmkr wani maraya "yaakayi adamcy nan duk sanda kayi haka akwai abinda kake son fad'a "haka ne sweetheart kin fi kowa sanin halina alfarma nazo nema ."
"Alfarmar kuma ?mami ta maimaita abinda ya fad'a
"Eh ina neman wata alfamar a wajenki sweetheart "ina sauroronka Allah yasa zan iya ,ya marairaice murya sosai kafin ya soma mgn "dan darajan Allah sweetheart ki qara min lokacin auren nan wallahi wallahi wallahi !!! kinji na rantse miki zan auri yarinyar nan zabinki , wasu yan kwanakin kawai zaki qara min har naje na dawo dan zan dauki lokaci a france daga nan ma zan wuce hollond yi wasu abubuwa masu mahimanci a yanzu na samu sauyin lokaci amman kuma idan kina ganin zaa iya yin komai ko bana nan fine na amince a daura auren ayi komai amman da zaa
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 26 Chapter of 43