Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
aunty iyaye suna da kimar da darajan da  bazaa iya mantasu ba ." ahankali taji sautin muryarta tana fita  cikin kuka "nayi  kewarka baba , nayi kewarki mamana yanzu ku har yanzu  bakuyi kewata ba ?yanzu ku baku yafe min ba ko nemeni ba? wallahi ina sonku nayi kewarku ,nayi  kewar  kowa da kowa  ta fad'a tana mai daura hoto a saman  qirjinta tana shafawa tana kuka.." Ahankali maryama ta juya tana zubar da hawaye masu zafi ta koma falo ta zauna kusa da habib tana sheshekan kuka nan take ya birkice ya soma tambayarta "heartbeat me kuma ya fara ?kukan me kike yi ? Ina aunty ?yayi mata tmbyr ajere cikin tsananin tashin hankali tasa gefen rigarta ta goge hawayen "yau aunty ta tuna da iyayenta tana daki tana kallon hotonsu tana kuka ni nasan zuciyarta na cike da qaunarsu shiyasa kaga ina son ta koma garesu ." "habib  soyayyar  iyaye  da  yanuwa  baa  wasa  dasu wallahi a tsakaninsu soyayya ce mai karfi ka misalta hakan akanmu musan da qaddara  amman an cuci aunty an yi sanadiyyar rabata da kowa nata ,ta bar iyayenta akan soyayya gashi ta rasa soyayya taki bin umarnin iyayenta gashi duniyar taki mata dadi maryama tana kuka habib na rarrashinta har kukan nata ya ragu adaidai lokacin da sukaji tahowar aunty tayi saurin share hawayenta tana cewa ". karka nuna mata komai da sanyi jiki ta qaraso "kun samo abinda zaku dan ci ?eh mun samu har da cinci tô maza kuci ku kwanta tayi maganr cike da rauni aunty kizo muci tare "aa ku dai kuci ku koshi aa wallahi tare zamu ci habib ya mike ya kamo hannunta ya zaunar daita ya bude kula abinci yana cewa kai abincin nan zai yi dadi maryama ta dauko spoon ta dibi abinci zata kai bakin aunty habib yayi sauri ya kwace spoon "bani ni zan bata da kaina suka sa da dariya ya soma bata abinci abaki yana fada mata kalamai masu sanyi ." "idan nayi kudi bazan yi nesa dake ba zan kasance tare dake ,dan allah aunty ki daina damuwa akan komai kinji ki dinga tunawa cewa kina damu mu din zamu zame miki farinciki a rayuwarki Wallahi sai mun sa kinyi alfahari damu ki cigaba da addau ga heartbeat nan kwanan nan zata fara bautar qasa yanzu ma ina mata  processing yadda zaa dawo daita lagos né daga adamawa wannan farinciki  ya rage tarin qunar da zuciyar aunty take ciki  tace "allah yayi maku albarka yayiwa rayuwarku albarka in sha allahu bazaku dangwama haka ba allah zai saukaka maku rayuwa ,Allah nake roko ya daukaka min ku na yafe  maku duk abinda kuka min da wanda nasani da wanda ban sani ba suna cin abinci suna debewa juna kewa ." ****** da misalin karfe 9:00 na washegarin ranar lahadi mr ata ya fito  parlour'n  mami  ,duk  jikinsa yayi sanyi har wata  katuwar  rama  yayi  daman ya lafiyar kura ?ba wani jikin kirki bane dashi  kusantowar aurensa da maryam yasashi jin    kmr  ana  fixgar  ransa  ,shiru ne  ya  ziyarci  parlour'n yana tunane  tunane yana jin kamar idan ya tafi france  kar  ya  dawo  domin a lissafinsa sauran kwanaki goma cif a daura masa aure da yarinyar daya tsana fiyye da komai arayuwarsa   byn  kmr  mintina goma mami  ta qaraso  da kanta ta  had'o masa abun kari , chips  da soyayyen kwai  da  ruwan tea mai kauri , ta janyo qaramin table  gabansa ta  ajiye kana ta zauna kusa dashi ta tsura masa ido tana kallonsa batare datace komai ba ." ya dauki cup din tea ya kai bakinsa ya kurbi kadan yana mai runtse  idanunshi  shiru har wasu mintuna suka shude yana zaune itama tana zaune tana kallonsa da kyar ya bude baki "sweetheart! "kaci abinci first before anything adamcy , sannan kar naji  kayi  magana  kaci abinci  kawai yaushe rabon ka sanyawa cikinka  abinci  bare a samu magani yayi aiki ajikinka ? ji yadda ka dawo acikin kwanaki uku kacal  ka taimakeni kaci wani abu  kanshi  kawai ya iya d'aga mata batare da ya kalli inda abinci yake ba, saboda sam  baya jin cikinsa  zai iya amsar komai  shima da zata taimakesa da tasa an fasa auren nan da yarinyar an hadashi da wata zai hakura da princess dinsa ya amshi koma wacece  duk da zuciyarsa princess kawai take so da son gani numfashi ya dinga  saukewa ."sweetheart  dina me yasa  kika  manna min wannan auren  haka? " sweetheart  zaki  kasheni da kanki wallahi at least ki sake gara min dama koda  na  tsawon wata guda ne  ." "to me  zan  maka adamcy nah daya wuce haka ? "me  kake  son  nayi  idan  banyi maka  haka ba ? gani nayi  kana  neman hargitsa min kwakwaluwa da qarar da rayuwarka a banza "me kake tunani mutane zasu ce idan   bakayi aure adaidai wannan lokacin ba ? wallahi zaka shiga zargin mutane ,mutun har mutun kamamme kamar ka ka zauna babu aure ko kana neman mata ne adamcy bansani ba da kake gudun aure ." wani  irin kallo yayi mata mai nuna mata bayayi "to idan bakayi me kake jira ?maryam  yaruwarka ce fa "yanzu kai kafi son ka dauko min suruka daga waje alhalin ga wacce tasan darajata take sona nake sonta diyar danuwana yanzu idan an fasa auren nan  me kake son na cewa mutane da yan'uwana ,dan Allah dan annabi in banda   da rigima irin naka ba me ye laifin maryam ..? "wani far yayi da idanu zuciyarsa na dokawa  da numfashinsa da yayi kokarin d'aukewa yayi saurin dawowa dashi gangar jikinsa sannan yace "sweetheart  ni bance tana da laifi ba amman  ki duba lamarin da  kyau  tunda nace bana sonta ai  sai a  hakura kawai  kowa ya kawo zabinsa . "kai rufe min baki ban son shirme banza, ka daina ganin ka had'a komai kana da kudi  kayi tunani zaka iya  juya ni  ."Wannan  aure sai  anyi shi muddin ina raye ." ya marairace muryarsa  sosai  tmkr  mai shirin zubar da hawaye sannan yace "wai sweetheart me yasa kike ganin kmr  wannan yarinyar ce kawai zata iya kulawa dake  ? Allah  sweetheart ki daina mata kallon haka  saboda irinsu sune masu bawa dangi kunya  wallahi duk lokacin da naji kince min itace zata san darajarki  bakinciki nake ji kmr na kashe kaina saboda ni duk macen dana kawo miki dolenta ta soki tayi miki biyayya bama Ke ba sweetheart hatta yayyuna biyu din nan dolenta ta bisu  lalacewar mace daga miji ne  ni kuma bazan ta'ba bada wannan damar ba .. " "Sauran kwanaki  goma a daura maka aure da maryam  a lissafina gobe  ko jibi jirginka zai cale zuwa qasar  france  fatana allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya shahida ta  gama shirya komai na aure  fatan alkhairi da dawo da niyyar  angeancewa lafiya and if you do anything  stupidty I will del with you kai ma kasani ina sonka fiyye da tunaninka amman hakan baya hana idan kayi ba daidai ba naki hukuntaka tana qoqarin mikewa hisham ya shigo ya gaishe da mami cike da girmamawa sannan ya zauna kusa da ata  daya   runtse tsumammun idanunsa tun byn da mami ta soma magana "yaakayi mutumina ya karfin jikin hope you are getting better?"numfashi kawai ya sauke wanda Ke nuna masa alamun ya amsa hisham ya cigaba da magana "har yanzu sultan da fahad basu dawo da komai ba fa  Kmr ma sun dauki abun matsayin shiririta tsabgogin gabansu kawai suke." "ina sane da komai kai kasan bana canza maganata ina jiran na dawo daga france ne suna zaune suna hira mb ya shigo haka ma yaya Ibrahim ya shigo duba jikin mr ata tare da aunty abida har da yesmin wacce ta dane jikin mr ata haka ma yammatan gidan d'aya byn daya  suka dinga shigowa suna gaisheshi da kyar yake bude bakinsa   yana amsa musu cikin rashin sakin fuska , cikin wasu  mintuna  aka cika gaban mr ata  da kayan motsa baki , amman babu abinda yaci  illa coffee daya dinga  tsiyaya a  cup yana  kurba ahankali ahankali   shima yana  sha ne kawai saboda  sabon da yayi dashi ." Parlour'n ya dan rage mutane  ya saura daga hisham sai ata   nuzla da diyana  har ma da mrym da nana hauwa'u suka  shigo parlour'n bakinsu  d'auke  da sallama hisham na ganin nuzla ya saki fuskar  ganin masoyi yarsa  gbdy suka hada baki wajen yi ma mr ata ya jiki  banda nuzla  Kmr koda yaushe da kyar ya amsa  masu hisham  yana kallon fuskar nuzla yayinda  nuzla taja ta tsaya daga gefe can ta jingina bayanta da bango ta rungume hannuwanta duka bisa kirjinta tare da tsura ma mr ata  fararen idanunta tana kallonsa cike da matsanancin soyayyarsa  yadda ko kallon mrym da zai aura bai yi ba  abun yayi mata dadi sosai yadda bai son mrym abun na mata dadi har yana bata kwarin gwiwa dan tun daga ranar daaka saka ranar aurenau take jin haushinta sannan take cikin damuwa mai tsanani  ." ahankali ta bud'e bakinta tace "yaya  sannu ya jiki banza yayi mata Kmr bai ji ba nan kuwa yaji sarai hisham yayi qasa da murya  yace "ata ana maka sannu da jiki "naji !ya fad'a atakaice  dan ya fahimci wani abu a attare daita ba tun  yau ba  yana hankalce da irin kallon da take masa a duk sanda zasu hadu tun a office din aunty shahida yaso yaci ubanta allah ya taimaketa "take gabanta ya shiga fad'uwa sbd fargaba dan ganin ko kallon inda take tsaye bai ba illa kur'ban ruwan coffee  daya cigaba dayi kuma taji amsar daya bawa hisham kuma tasan sauran ma sunji abinda ya fad'a  ." ahankali ta juya ta nufi kofar fita cikin bacin rai sannan sauran yanuwanta suka biyo bayanta "amman ai ya kamata ka amsawa gimbiyata ya sake yin mgn can qasa"gsky hisham baka da hankali km kana bani kunya yanzu kai da gaske sonta kake "?sosai ma kuwa ina sonta sai dai ita bata sona ..""what ?" Wallahi haka ta fad'a ai naso bikin a hadashi da naka amman ya zanyi tunda tace bata só na hakura amman nasan sonta ne zai kasheni "amman shine ka kyaleta baka ci ubanta ba? aa babu wannan ai kai ma kasan yadda soyayya take ka duba yadda baka son mrym kake son yarinyar mafarkinka "ka daina kawo wannan misalin ni bana son wannan yarinyar ita ma kuma bata sona kaga akwai matsala wajen namu hadin ko ka fahimceni ."? "Misali ina sonta to ya zama dole dan ubanta ta soni sannan misali da'ace tana sona nima bazan dinga jin tsanarta haka ba duk da nasan nawa rashin son ne babban matsala dan ita prentending ne kawai nasan babu macen da zata kalleni tace wai bata sona dama ne kawai bata samu ba ,ya fad'a yana jan tsaki ka kira min auta  "me zata maka  ?Kai dai kira min ita kawai   yau  yarinyar nan zataci ubanta da me  tafika da zata ce  bata sonka ?shiru hisham yayi yana kallonsa a she haka ata yake sonshi jiki a sanyaye ya dauki wayarsa ya kira nana hauwa'u cikin kankanin lokaci ta bayyana a falon "yaya gani "je kizo min da nuzla yanzu yanzu kafarta kafarki "okay yaya ta juya da sauri ."su kuma suka cigaba da tautaunawa ." Bayan mintuna goma sai gasu sun shigo nana hauwa'u ta  kama  gabanta  ta bar nuzla tsaye cike da fargaba  ta dan saci kallon hisham dake zaune taga ya sakar mata murmushi  ta kalli mr ata taga ya hade rai sai kafarsa daya yake girgizawa har  kusan mintuna  shabiyar tana tsaye sannan tace "yaya gani wai ..."da sauri ya dakata daita ta hanyar daga mata "waye wannan ?ya nuna mata hisham dake zaune "yaya hisham ". "Very good meye a tsakaninku ?nothing ta bashi amsa atakaice ba hisham ba hatta mr ata sai daya dago tsumammun idanunshi ya tsura mata yana kallonta "kika ce nothing kenan baki san yana sonki ba ?nasani but na fad'a masa gaskiya ni bana son shi dan ..."enough ! bana  bukatar  jin  maganarki ko wani abu  kije ki fara shirin aurensa nan da kwanaki  goma  ." cikin firgici da tashin hankali ta shiga d'aga kafafunta zuwa inda yake zaune  "me yasa  yaya ?" dan Allah kayi hakuri karka min haka  wallahi ni bana son shi a matukar tsawace yace "nace karki sake fad'ar wata  magana anan , karki   sake kula kowa  acikin masu sonki shima wanda kike so ki kashe  soyayyarsa  acikin zuciyarki ki so wanda yake sonki  .." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗      MAR'ADAMS      💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.            Page 20 jikinta  na  wani  irin  rawa  ta k'araso ta  durkushe a gabansa har  bata  san  sanda  ta d'aura hannuwanta  duka bisa cinyoyinsa  tana  kallon  cikin   kwayar  idanunsa da  suka  rikid'e  suka  canza   kala   a wulakance  ya   zame   jikinsa  yana  mai  kawar  da   fuskarsa   gefen  hisham  dake  zaune   tmkr   mutun  mutumi  yana   kallonsu   cike  da  matsanancin  tashin   hankali   ,shi   kuwa  mr  ata  alamun  baya  son  kallon  fuskarta  ne   yasa   shi    maida  idanunshi  kan  hisham  ". "dan  allah   dan  Allah !!  yaya  adam  kayi   hakuri    ta  kai  hanuta  tana  qoqarin   juyo  da  fuskarsa  gareta  domin  su  fuskanci  juna , zuciyarta  na  wani  irin    bugawa  da  karfin  gaske  take  kallonsa haka  ma  hisham  zuciyarsa ce take ta bugawa fiyye da   kaida   ya  soma jin  wani sauyi na   daban  a gabadaya  ilahirin   jikinsa   wanda  ke  gauraye da tsantsar   tashin  hankali,  shi  kuwa  mr  ata  mamakinta   yasa   gbdy   ya qasa   magana   duk da maganar   yake  son  yi . Kwayar   idanunta  suka   cicciko  da  ruwan   hawaye muryarta a sarke  tace "dan   Allah  yaya   kayi   hakuri   karka  bari  wannan  auren  ya  kasance  domin   zuciyata   bazata  iya d'aukar wannan  nauyin  ba,   wata razananniyar  tsawa  ya buga  mata  wanda  ya  kamata  ace ta  tsorata   ta dawo da  hankalinta   jikinta   amman   ina  sai  ma  sake  narkewa  tayi  a wajen  zuciyarta  babu  tsoron  komai  acikinta , muryarsa  a kausashe   yace " tashi   ki   bar  nan  ki   kuma  fara  shirinki   kamar  yadda   na  fad'a  miki   oya  leave ." "dan  Allah  ka  saurareni  yaya  "ya  girgiza  mata  kai   yana   cewa "   I don't  want  to listing anything  from   you  just  leave  now "dan   allah  yaya  adam  kayi   hakuri  ka  saurareni    akwai  maganar  da  idan  na  fad'a  maka   nasan   zaka   fahimceni "ata dan  Allah  ka  barta  ta  fad'i  abinda  ke zuciyarta    Hisham  yayi  maganar   yana  qarewa  jikin nuzla  dake  rawa  tmkr   mazari  da   kallo  , yadda  take  cikin   tashin  hankali  haka  shima  ya  tsinci  kanshi  cikin   tashin  hankali  mai  tsanani  har  yana  jin  ma  kamar  ya  cire   mata  nata  damuwar  ya  qarawa   kanshi " Hisham  yayi  tsuru   tsuru  yana  jira  yaji  abinda zata  fad'a  ,yayinda  mr  ata  bai  ce  uffan  ba  ya yunkura  ya  mike  tsaye  ya  kwashi  wayoyinsa  ya  fara   taka  kafafunsa  da   kyar   zai  bar  wajen kasancewar  bai  son  yawon   magiya  bare irin nata dake   hargitsa   kwakwaluwa  nuzla  tayi   saurin  shan   gabansa  tana   fad'in  "yaya  karka  wuce  ka  bar  zuciyata  cikin   maseefa  tayi  maganar  cike  da  tausayawa  ,bai  yi  mata  magana   ba  ya  cigaba  da tafiya  yana  mata  gargadi  da  hannunsa  alamun ta shiga  hankalinta , bata  daddara  ba ta sake  shan   gabansa  dan   gbdy  zuciyarta  ta  rigada  ta bushe  babu  abinda  take  qoqarin  aikatawa  face  ta  bayyana    masa  ciwon  dake  cikin  zuciyarta ." Ya  tsaya   kawai   yana   mata   wani  mugun   kallo yana  furzar  da  iska   mai   zafi   daga  bakinsa muryarta  cike  da  rauni  da  buqatar  atausaya  mata  ta  fara  magana  "bazan  iya  jure  ciwon  rabuwa  da  wanda  nake  só  na  auri  wanda  kake  só  ba ta  karasa  mgnr   tana   rungumeshi  ajikita   tana  kuka a matukar   zuciye  ya  fixgeta  daga   jikinsa   yana  sake  furzar da  iske  "are you out of  your sense ?ni sa'anki   ne  da  kike  shiga  gabana? "  ko  ina  wasa dake   ne  da  ina   magana  kina   magana ? ya fad'a yana   kawar  da  fuskarsa   akanta  domin  dai zuciyarsa  ta  fara  tausaya  mata  tausayawar  da  bata  da   wani  amfani  dan  bazai  ta'ba  iya  mata taimakon  da  take  nema  daga   garesa  ba ." Hisham  ya  rasa   meke   faruwa   atsakaninsu  babu  abinda  zuciyarsa  bata  kissa  masa  ba  a zaune  da  yake  tmkr an  dasashi  irin  kallon da take  ata  da  rungumar da  tayi  masa  ya  fara  gasgata  zuciyarsa  akan  abinda  bai  niyyar  yarda  dashi  ba  yaso ya  mike  ya  qarasa  zuwa inda  suke  tsaye  yasan ko akan  me  take  masa  magiya   har  da  runguma amman  hakan  nan  yaji  gara  ya  cigaba  da  zama a  inda  yake  zai  fiyye  masa  alkhairi   kuma  bugu da qari    yayi  imani  ata  bazai  ta'ba  aikata  komai  ba face  abinda  yasan  zai  zamewa  rayuwarsa  farinciki   he really  trust  him  mutun  ne  shi  mai  kyakkyawar zuciya   akanshi ." Hawaye  na  gangaro  mata  bisa  kuncinta  yayinda  magana  ya  fara  fitowa   daga  bakinta  "ina qaunar ka  yaya  ? bai  yi  mamakin    jin  fitowar  hakan  daga  bakinta  ba  domin  ya  rigada  ya  gama karantata  tsab  "na sani  sai  akayi  yaya  ?ya  fad'a yana   kallonta  yana  jin  kamar  ya  soma  yar yarfa mata  maruka  ta  dawo haiyacinta  "dan  Allah  yaya karka  ce  min  a'a !   a kowani  hali  zan kasance  tare  da  kai "  ta  maimaita  hkn  a fili   yafi  sau   goma tana  mai kai  hannu ta shafa  kasumbar  dake   kwance a  fuskarsa  ji  yayi  kamar  ta  shafa  masa garwashin  wuta ,shi  fa  duk  duniya  babu  macen da  yake  jin  zata  ta'ba  shi   yaji  wani  abu  ajikinsa sai princess  ita ma  din   yanzu  ya  soma  gogeta a zuciyarsa  da  rayuwarsa ."cikin  fita  haiyacinta   ta riko  fuskarsa  sosai  ta  sanya  kwayar  idanunta  dake  tsiyaya  ruwan  hawaye  acikin nasa " ban  san  hka  soyayyarka  tayi  tasiri  acikin  zuciyata ba  sai  dana  qasa  amsar  soyayyar  kowa ." "Ban  san  tasirin  soyayyarka  ta  kai  mizanin  da  zan  iya  rasa  rayuwata  ba  sai  da  naji   zaka  min  nisa  , yaya   kaine  duniyata ruhina  yana  tare  da  kai  ako   da  yaushe , nayi  yunkurin   bayyana  maka soyayyata a tun  lokacin  da  mubina Ke mutuwar  sonka   amman  na  gaza  aikata  hakan  ina  ganin  cewar   zan  iya   cire   soyayyarka  na cigaba  da  rayuwata  amman   still  na  qasa  domin  kuwa  every  each  second   nake  jin  sonka na  qaruwa a cikin  zuciyata ,  ina  ta  qoqarin  sheida  maka  halin  da  zuciyata  take  ciki  kwatsam  kuma  sai   ga  batun   aurenka  da  marsi  bance  ka bar  marsi  ba  amman dan  allah  ka  had'amu  ka auremu " rokonki bai  kar'bu   ba   bare   wata   alfarmar  ya kamata ku koyi  yadda  ake  iya  control  din  zuciya  "ka taimakeni  ban  san  ya  zanyi  ba  " kar    allah  yasa ki   sani   ya  fad'a  yana  jan   tsaki   ." kuka   take  sosai   tana   kallonsa   tmkr  ranar   ta  fara  ganinsa  shi   kuwa  haushi  ne ya turnikesa  a  wajen  zuciyarsa   banda  tuttukin  bakinciki  babu  abinda  yake , a  ganinsa  ma  ta  balain  rainashi shi  zata  kalla  tace   tana so  alhalin  ga hisham dake  mutuwar  sonta?  "kayi  hakuri  dan  girman Allah  nasan zakayi  tunanin  komai  akaina   wallahi  haka  ne , dan  na rigada na   haukace  akanka  bazan  iya jurar  abinda   nake  ji  akanka   ba  sannan  bazan iya amsar    soyayyar   yaya  hisham  ba  ,dan  kona auresa  gangar  jikina  ya  aura  zuciyata  da  komai nawa  yana  gareka   da  kawai  zan  iya  rayuwa ..." Ta  riko  hannunsa  hawaye  na zuba   daga   idanunta  ta  soma tafiya   dashi  taku  d'aya  biyu  yayi ya  tsaya cak , itama  ta  tsaya  suna fuskantar  hisham naunaye  ajiyar zuciya  ta sauke  tana  goge hawayen  dake  tsiyaya  ,ahankali  ata ya zare hannunsa  dake cikin nata  ya  yarfar   sannna  ya  zura  cikin  aljihun wondonsa  yana  jan  tsaki "ya hisham! ta  kira  sunansa  a kid'eme  "banyi  niyyar  fito  da  sirrin  dake  zuciyata  ba  amamn  ya  zama  dole  na  fad'a  maka  tunda  na  fad'awa  yaya   adam babu  komai  acikin   zuciyata  sai..." karki   kuskura  kiyi  wannan ganganci  dan  kome  zaki  yi  tawa  zuciyar   bazata   amince   ba "to  kuwa  gara    ka  ksheni da hannunka  na  huta   dan  nima  bazan iya  auren  yaya  hisham ba , yana   sona  ni kuma kai nake   so.."you're  very  stupid  Kiyi  maza ki  danna  madannin  gogewa  ki gogeni  arayuwarki  da   zuciyarki  dan ni  mallakin  mafarkina   ce   " yana   gama   fad'ar  haka  ya juya  ya haye  sama  yana  taka  step   yana  magana " hisham  ka manta da shirmen   wannan  yarinyar  ka  soma  naka   shirin   domin   wannan  auren ko   zata  mutu  sai  anyisa  useless  girl  kawai  ga  inda ake  sonku  aka  damu daku   amman ku  dinga  kai  kanku  inda  bazaa  ta'ba  sonku ba nonsense " Hisham  ya  runtse  idanuwanshi "kenan  hasashensa  ya   tabbata ,  zarginsa   ya   zama  gasky   kenan akan ata  yake  shan  wulakanci  da  tsana  da wahala a wajenta ?   ,"ya  kalleta  cike  da  tausayawa yace "daman  ata  Kike so ?jikinta  yayi mugu  mugun sanyi ta rasa  me  zata  cewa  hisham  illa ta  runtse  idanunta  gam  tana  jin  zafi  da  ciwo  mara   iyaka a zuciyarta  ,ta durkushe qasa  tana kuka tana nemawar   kanta  mafuta   dan  dole  tasan  abun  yi  kafin  a had'ata  aure  da  hisham shima  ya durkushe  gabanta  ya  dago  ha'barta  ya  sanya  kwayar  idanunshi  cikin  nata , tai  saurin  buge masa  hannu  tana  kallonsa  cike  da tsantsar  tsana "ka  kyaleni  ni wallahi  bana  sonka  tunda  burinka  kenan  na  soka  , dan  girman   allah  ka  rabu  dani  ka manta  dani,  ka  manta da maganar  ka  ta'ba  sona  arayuwarka , ka  mantani  ta qarasa  fad'ar  haka  tana  fidda huci  mai  zafi ." "Dan  allah  kiyi  hakuri  nasan  irin ciwo da  zafin  da  Kike  ji  acikin zuciyarki  ciwo ne  kwatankwacin wanda  nake ji  acikin  zuciyata  nasan  zafin  ciwo da radadin  kana  son  wani  baya  sonka ,wallahi  na  tausaya  miki  amman  me  yasa nuzla ?"me  yasa  sai  ata  zuciyarki  zata  kamu da so byn ni  ina qaunarki  ya  kai hannunsa  yana  share   mata  hawaye"ata bashi  da  wannan  lokacin   wahalar da kanki da zuciyarki   kawai  zakiyi  babu  wannan  tausayin a zuciyarsa    a karshe  ya  rungumeta  ajikinsa   tsam  yana  shafa  bayanta   ahankali  ahankali  babu yadda ta iya dole ta  kasance  rungume  ajikinsa  domin tana  bukatar  wanda  zai  rarrasheta  kuka  take  sosai   tana  rungume   ajikinsa "ki daina  kuka  nuzla  dan  zuciyata  bazata  iya  ganin  hawayenki  da damuwarki  ina  matukar  sonki  da  zaki  bani  dama da  sannu  zaki  daina  son  ata  ki soni  ya  fad'a  yana  qara rungumeta  gam   ajikinsa   ahankali ya mike tsaye  tare  daita  ya  nufi  kofar  fita  tun kafin mutane su  shigo su  fahimci  halin da suke ciki ." Washegarin  da  misalin  karfe tara na dare   ata ya  shiga d'akin mami  sanye  cikin  fararen kayan bacci wondo da  riga , hannunsa  rike  da black cup dinsa  dake  dauke  da ruwan coffee  ,yayinda  dayan  hannunsa Ke cikin aljihun  wondonsa  ya samu mami  tsaye a gaban wordrobe  dinta tana qoqarin  rufewa  tana ganinsa ta sakar masa murmushi tana cewa "Masha allah   adamcy nan ya karfin jikin ?alhamd sweetheart ya qoqari dani ?kwana  nawa ya saura ai Allah Allah  nike  Kayi tafiyar nan ka dawo mu sha biki  ranar bani da dama zan aurar da d'a daya tilo ya  girgiza  kai kawai yana  ajiye  cup din hannunsa  akan bedside dinta  ya tsura mata tsumammun idanunshi yana kallonta tmkr wani maraya "yaakayi adamcy nan duk sanda kayi haka akwai abinda kake son fad'a  "haka ne sweetheart kin fi kowa sanin halina alfarma nazo nema ." "Alfarmar kuma ?mami ta maimaita abinda ya fad'a "Eh  ina neman wata  alfamar a wajenki   sweetheart "ina sauroronka Allah yasa zan iya ,ya marairaice  murya sosai kafin ya soma mgn  "dan  darajan  Allah sweetheart ki   qara min  lokacin auren nan wallahi wallahi wallahi !!! kinji na rantse   miki zan auri yarinyar nan zabinki , wasu yan kwanakin kawai zaki qara min har naje na dawo dan  zan dauki lokaci a france daga nan ma zan wuce  hollond  yi wasu abubuwa  masu  mahimanci  a  yanzu  na samu sauyin  lokaci amman kuma idan kina ganin zaa iya yin komai ko bana nan  fine na amince a daura auren ayi komai  amman da zaa

Chapter 26 of 43