Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
wacce bata da kowa acikin duniyar nan ,numfashi ta janyo da kyar ta fesar a hankali kafin ta bude bakinta da kyar "yaushe zamu je wurinsu ?". "karki damu sarauniyata in sha allahu zamu " cike da farinciki maryama ta kai hannunta ta dauki remut tana mai kunna tv tare da maida hankalinta Kan program din daake yi a tashar galaxy tv tana mai jin farinciki da natsuwar zuciya "Aunty zan so naji ranar da zamu na soma lissafa kwanaki "canza fuska tayi batare datai auni ba kafin daga bisani ta kawar da kanta gefe dan karta fahimci damuwarta dan gbdy ta soma neman natsuwarta ta rasa bazata iya zuwa garesu ba ,haka zalika ya'yanta ma bazasuje ga danginta ba most especially mahaifiyarta ta barsu har abada kamar yadda suka barta zata karasa rayuwarta a haka cikin kunci ." a qalla sun dauki mintuna goma zaune suna duban tv babu wanda ya sake yunkurin cewa komai Kafin ahankali cikin sanyi jiki maryama ta mike daga kwanciyar da tai akan cinyar mahaifiyarta ."Aunty lokacin sallah yayi bari naje nayi sallah gashi ina son na danyi zane kafin na kwanata ga bacci da nake jin yana fixgata tamkar zan fadi ni zan shiga ciki sai da safe dan gabadaya yau ko gurin umma bazan shiga ba idan sakina ta shigo kice mata na shiga bacci dan bazan sake fitowa ba allah ya bamu alkhairi ."tana gama fadar haka ta juya ." har tayi taku biyu Aunty ta dakatar daita ta hanyar kiran sunanta "princess! Ta dan tsaya tare da waigowa "abinci fa ? maryama ta dan yatsina face dinta tana ciza gefen lips dinta sannan ta girgiza mata kai alamun "a'a ! "to amman karatun jarabawa ya kamata kiyi ba zane ba ko gobe baku da exam ne ? muna da shi zanyi karatu sannan na d'an yi zanen sai na kwanta " "kiyi karatu da kyau maryama Kinsan a final year kike, ni da son samuna ne da kin bar zanen nan har sai kin gama karatu " karki ji komai Aunty duk zan iya Kiyi min addua da fatan samun nasara ." Aunty ta sauke numfashi tana cewa "allah ya bada saa yayiwa rayuwarki albarka "Ameen sai da safe " "okay to shikenan allah ya bamu alkhairi "Ameen ! ta sake juyawa tana rausaya tamkar zata karye dan rashin jikin da Allah ya bata , har sai da Aunty taga ta shiga cikin d'akinta sannan ta dauke idanunta daga kallon bayanta ." Tana shiga dakin bayi ta shiga tayi wanka hade da dauro alwala ta fito cikin sanyi jiki tana goge gashin kanta da towel tana goge jiki tana mamakin abinda yasa mahaifiyarta bata son zuwa ga danginta alhalin suna gari daya ,"me yasa haka? " zata so tasan dalilin dayasa bata son zuwa garesu da wannan tunanin ta saka doguwar rigar bacci fara sol har kasa ta qarasa inda take ajiye sallaya ta dauka ta shimfida ta kai hannunta ta dauki zumbulelen hijab dinta ta saka ta kalli gabas a natse ta tada sallah ." byn ta idar ta mike ta cire hijab ta ajiye a gefen gadonta ta zauna akan kujera kwaya daya dake dakin wanda gabansa dan qaramin table ne mai dauke da tarin textbook da fararen takardu na zanenta ta janyo textbok daya daga ciki sannan ta zaro farar takarda kwaya daya ta ajiye a gabanta ta soma karatu tana joting kusan mintuna talatin sannan ta rufe ta maidashi inda yake ta sake zaro wata takarda ta ciro pencil da kayan aikinta ta fara zane wanda ya kasance abinci ruhinta a duk lokacin da zaka ga maryama a natse zaka ganta kuma akan aiki idan bata makaranta boko tana islamiyya idan bata islamiyya tana Kan aikinta na Architect wanda dashi take samu take taimakawa mahaifiyarta batayi karatu akanshi ba kawai baiwa ce daga allah ya bata babu abinda bata iya zanawa tun tana qarama take Zane dashi ta girma ." cikin kankanin lokaci ta fara zana wasu hadaddun mutane sanye da kaya na maaurata guda biyu macen sanye da wedding gwan yayinda nmj kuma ke sanye da suit sunyi matukar kyau kamar a kirasu su amsa tayi shiru tare da tura pencil cikin bakinta tana taunawa tana kallon zanen ahankali ahankali tana lumshe idanunta alamun bacci "bari na bar aikin nan haka tunda ba urgent bane zuwa gobe na qarasa idan na dawo daga school ta tattara ta bude durowar table dinta ta tura ta mike tsaye ta sake daukar hijab ta sanya ta tada sallah ishai tayi addua ga mahaifinta da alummar muslimai ta mike ta nade dadduma ta maida inda yake ta hau gado ta kwanta ko cikakken minti uku batayi ba bacci ya dauketa ." A can falo kuwa Aunty zaune kawai take duk hirar da habib da sakina ke zubawa da idanu kawai take binsu hankalinta na wani waje karfe goma daidai sakina tayi masu sallama ta wuce tana fita Aunty ta mike tsaye tana cewa habib "ka rufe koina ni zan shiga ciki allah ya tashemu lfy ta nufi hanyar dakinta har zata shiga ta hango haske a dakin maryama dan haka ta dawo ahankali ta shiga dakin ." tana kwance ta dungule waje daya a tsakiyar katifa ta cusa kanta cikin jikinta kwanciya mai tattare da damuwa duk wanda kaga yayi irin wannan kwanciya tabbas yana cikin damuwa ko maraici kuma a duk sanda taga tayi irin wannan kwanciyar ba komai take tunawa ba illa kanta take tunawa alokacin baya irin kwanciyarta kenan wanda damuwa ne silar nata kuma tasan damuwar ce ta janyo mata itama ta qarasa shigowa d'akin har inda take kwance ta kai hannu ta gyara mata kwanciya ta janyo abun rufa ta lullube mata jiki ta shafa gefen fuskarta tana sake jin soyayyarta acikin ranta ya'ya sune farinciki iyaye amman ita ta rasa wannan gatan daga nata most especially mahaifiyarta ." "abinda mahaifiyarta tayi mata abu ne da mutun zai iya yafewa amman bazai ta'ba iya mantawa ba kuma abu ne da bazata ta'ba yiwa ya'yanta ba zata so ya'yanta tamkar rayuwarta bazata iya kuntata masu ba bazata iya azabtar dasu ba sannan bazata iya hanasu cikar burinsu ba zata basu farinciki duk abinda suke so zata basu matukar bai sabawa shari'a ba, fatanta dai allah ya raya matasu cikin aminci "ta mike tsam har lokacin idanunta na Kan maryama dake qoqarin sake dunkulewa waje daya ta kashe mata hasken d'akin sannan ta fito tana mai janyo mata kofar dakin ta shiga dakinta " Ahankali ta zauna a bakin gado zuciyarta cike da zullumi har kusan shabiyu na dare tana zaune sai dai zuwa wannan lokaci tayi rigingine tana kallon saman dakin daya byn daya maganar maryama Ke dawo mata "me yasa bakya son zuwa inda danginki suke ?" mahaifi mahaifiya yan'uwa suna da matukar mahimanci arayuwar mutun ahlinki suna da hakki akanki most especially iyaye yana da kyau a dinga basu hakinsu domin hakan zai samarwa mai yi kwanciyar hankali,meye acikin duniyar da babu albarka iyaye acikinta ?nan take taji wasu hawaye masu zafi ya ganganro gefen idanunta." "tabbas gaskiy diyar cikinta ta fad'a mata amamn ai sune sukace babu ita babusu har abada me zataje tayi masu a yanzu da take cikin damuwa da bata da komai tasan ko taje garesu wulakanci ne zai biyo baya gara ta cigaba da zamanta hk babu dangi har karshen rayuwarta ,maryama da habib sun isheta komai , sheshekar kuka take sosai wanda batasan tanayi ba maraici sosai take ji alhalin ita din ba marainiya bace ta daura hannunta daya a saman kanta ko zataji saukin zafin da zuciyarta take mata ." tana cikin wannan halin taji an turo kofar dakinta da sauri ta dago tare dawowa haiyacinta tana mai goge hawayen idanunta da hannuwanta duka habib ne ya shigo wanda sakamakon sheshekan kukanta ya shigo dashi sai daya mata kallon tsanake sannan yace "me ye damuwarki male? dake shi kuma haka yake kiranta dashi ta sake sanyawa jikinta jarumta tana girgiza masa kai " alamun babu komai." "karki fad'a min haka byn kukanki ne ya shigo dani ya fad'a yana kafeta da fararen idanunshi qara maimaita tmbyrta yayi tayi kasa da kanta sakamakon hawayen daya sake cika mata ido domin kwalkwaluwarta ta toshe ta kasa fad'a masa dalili "ya sake matsota sosai male ki fad'a min damuwarki domin bazan bar dakin nan ba muddin baki fad'a min ba domin dai damuwa Ke saka mutun kuka irin wannna kuma tunda nake ban ta'ba ganin kukanki irin haka ba kuka mai fitowa daga kasan zuciya ." Ya kai hannu ya dago habarta yana kallon hawayenta dake zuba yabi hawayen da kallon hankalinsa na sake tashi cikin tsananin tashin hankali yace "wanene ya bata miki ranki haka? ta girgiza masa kai kawai "wai meye haka ne male kina son zuciyata ta kasa sukuni ne ko me ?ta sake girgiza masa kai ya juya a fusace zai bar dakin "bari naje na taso heartbeat.." ta riko hannusa da sauri "karka tashe ta bacci dan baccinta yayi nisa gashi gobe tana da exam's "to ki fad'a min damuwarki kamoshi tayi ta zaunar dashi a gefenta ya zauna yana sauraronta kusan second goma sannan ta zayyane masa komai sai daya numfasa kana ya soma mgn "male duk abinda heartbeat ta fad'a is right and it good dan daman nima ina neman hanyar da zan miki wannan tmbyr domin abu ne daya dade cikin kwakwaluwata har ya Kan hanani kwanciyar hankali Kiyi tunani male gsky heartbeat ta fad'a miki ya kamata kije ga danginki ko mu ki fad'a mana inda suke muje domin muna bukatarsu " Jin haka yasa ta barke da wani sabon kuka "baku san me suka min ba baku san irin wahalar dana sha a hannunsu ba ,na sha wahala kuma duk akan mahaifinku ne bana tunanin zasu qaunaceku shiru yayi yana dubanta cike da mamaki "me dady yayi masu haka ?sannan wani irin wahala kika sha a hannunsu ?yayi mata tmbyr a jere cikin tsananin tashin hankali kafin a hankali ya kai hannu yana goge mata hawaye shiru tayi ita kanta tana son ta basu labarinta amman bata san yadda zata dauki abun ba "tana son mahaifiyarta tana tausaya mata tana gudun bacin ranta ,bata son ganinta cikin damuwa amman a karshe itace abar kyama itace abar wulakantawa, itace mara mutunci a idanunta har tana cewa allah yasa mijinta ya wulakantata Allah ya hanata haihuwa Allah yasa ya saketa mijin da take tsananin so duk akan ta zabeshi a matsayin jikin aurenta ." Kuka sosai take tmkr ranta zai fita tana furta "na yafesu har abada zan zauna na qarasa rayuwata ni kadai "yayinda habib Ke share mata hawaye yana kuka yana bata hakuri domin yasa duk abinda yasata kuka irin haka mai girma ne muryarsa a sanyaye yace "kiyi hakuri male ki daina kuka kukanki na balain daga min hankali na hakura da son jin komai domin jinsa bazai zame min alkhairi ba amman kema kiyi qoqarin ki manta abinda ya rigada ya wuce amman iyaye da yanuwa duk abinda sukayi baa yafesu ."yana gama fadar haka ya juya har ya fita ya rufe mata kofar dakin hawaye ne yake fita dga idanunta "yaya suke son tayi da rayuwarta duk abinda suka fad'a mata tasan gsky ne amamn har yanzu zuciyarta ta saka mantuwa akwai wani abu da yake tsaye acikin zuciyarta ta rufe idanunta ta sake jingina jikinta da pillow daya saka mata a bayanta tana jujjuya maganganun yaranta tana yin filla filla dasu tana son kawar da bukatarsu amman tasan gsky suka fad'a mata bata taba daukar ya'yanta zasu girma da son danginta irin haka ba kasancewar suna cikin dangin mahaifinsu." ***** mrym zaune a d'akin hjy zulaiheart tana shirya mata  kayanta  da mai gugansu  ya kawo  tana tsaka da aikin aunty shahida  ta shigo bakinta d'auke da sallama ta amsa tana gaisheta fuskarta d'auke da murmushi  "aiki kike yi ne haka  amaryar  ATA tayi mgnr cike da zolaya " sannu da zuwa auntynmu me kika zo mana dashi ta fadi haka dan kawar da maganarta ,cikin dariya aunty shahida ta zauna akan sofa tana cewa "kayan dadi da bazasu fad'u ba maryam tayi murmushi yasu madina kwana biyu shiru  kmr anyi ruwa an dauke "ke dai bari madina exam ne ya sakata gaba Amman Ina ganin ma zuwa wani sati zasu kammala ". "okay to Allah Bada sa'a "Ameen ta amsa tana cewa "wata shawara nazo miki dashi a tsakaninki da ATA jin haka yasa ta dan tsaya ta kasa cigaba da abinda take hankalinta gbdy ta tattara shi kan aunty shahida " Ina sauraron shawara daga bakin aunty nah maganin kukana " Marym please ki sanya kunnen baseera akan abinda zan fada miki "ta sake mika mata hankalinta sosai " kin dai san halin wanda zaki aura  yana da kyau ki dan rage wasu abubuwa sannan ki koyi wasu abubuwa nasan kin fahimci abinda nake nufi ki zamo mai kwantar da kai da iya girke girke dan bazance girki ba ,daga ke har nana na fuskanci Kuna da matsala ta wannan bangaren dan haka ki dage ki koyi kowani irin girki da tsafta duk Inda zaki kasance acikin gidanki  the next thing shine kamshi domin shi din ma'aboci son dadd'adan girki ne da son kamshi ki zamo mai hakuri da lallabashi domin ta haka zaki yi saurin dakusar da duk wani taurin Kansa abubuwan social media Shima ki rage "dan kinsan bazai yarda dashi ba wasu daukar hoto kullum ana d'aurawa a duniya Shima bazai yarda ba  ". "shikenan naji aunty inshallahu Kuma duk zan d'auki shawararki ki dai tayani da addua biyyaya zanyi a aurena da ya Adam Allah yasa ya zamemin alkhairi "Ameen byn biyyaya har da soyayya sai kunyi aure zaki fahimci hk "Kai aunty babu wata soyayya "  ki rubuta ki ajiye a Inda bazai goge ba ko na mutu sai kin fada "Kai aunty shahida bana tunanin yaya zai soni a yadda yake nunawa ni dai zanyi iya yina kawai "karki tsaya iya yinki kiyi kokari ki canzasa gbdy ta yadda zai manta  da mafar.." "wannan Kuma  impossible aunty bazata iya ba  " suka ji sautin muryarsa acikin dodon kunnensu a tare suka juyo a firgice  suka  Kalli Inda yake tsaye sanye da farar jallabiyya mai gajeren hannu ajikinsa gashi kan nan nashi sai sheki yake zubawa  tamkar balarabe kallon second biyar mrym  tayi masa tayi saurin  d'auke kanta sakamakon mugun kallo da yake jifanta dashi  .matsowa kusa da aunty shahida yayi sosai  fuskarsa a hade babu alamun murmushi "babu abinda za'a ta iyayi wanda zai dakusa wannan soyayyar dake dawainiyya da zuciyata da gangar jikina   Ina son princess so mai girma sannan gara ki fad'a mata babu iskanci da sakarci a gidana  dan bazan dauka ba ." Take kwakwaluwar  mrym  ya shiga ceculating abinda mgnrsa take nufi  kenan akwai  wacce yake so  aka takura masa aurenta ?take jikinta ya kama kyarma ya ware hannuwansa duka cikin jin dadi  "okay a she fa bata san da wannan zance ba fa ?"gsky ya kama ta san cewar  akwai wata acikin zuciyar Adamcy Kuma ko ba dade ko bajima muddin na ganta zata kasance cikin rayuwata bukatata na ganta domin nafi bukatarta fiyye da komai  ." gbdy mrym dake zaune taji babu dadi acikin ranta "tabbas wannan shine dalilin dayasa bai maraba da aurenta  wani bakinci ya ziyarci qirjinta ta mike tsam zuciyarta cunkushe ta nufi kofar fita tana fita aunty shahida ta soma magana cikin fushi "wai me yasa kake yin hk ne sam bai dace ba?  "me Kuma nayi byn gskyr dake cikin Raina na fada gara tasani ?  ''idan kana yiwa mrym hakan bazamu ji dadi ba , rainmu  zai dinga  baci fiye da bacin ran daka gani yanzu acikin kwayar idanuna ,dan bazamu  yarda ka fifita wata banza can akanta ba banzar ma da ba gskiya bace  . "duk son da nake   maka zan   iya ajjiyeshi gefe   na hukuntaka hukunci mai tsanani akan mryam ,kada  ka sake makamancin wannan maganar a gabanta  wannan ya zamo Karo na karshe  ya jiyo sautin mahaifiyarsa wacce ta shigo byn fitar mrym nunfashi ya fesar yana cewa ''relax  sweetheart  insha Allahu  an gama ya fice ya barsu   "Allah ka shirya Adamcy na rasa meke damunsa "  meke damunsa kuwa ban da iskanci aunty shahida ta katse hjy zulaiheart , nifa wani lokacin sai naji kmr Abar had'in nan kar yazo ya bata zumunci   ."babu wani zumunci da zai bata wannan auren Allah ya rigada ya hadashi tunda gashi har ya amince ayi ,da yarda Allah rayuwar gaba zatai dadi "Allah yasa inji cewar aunty shahida. Da fari  baba qarami hjy zulaiheart taso ta kira ta sanarwa hukuncin data yanke kasancewar shi yana bangaren baya inda mallakinsa yake sai dai tayi tunanin ta fara sanarwa baba Babba kasancewarsa babba a tsakaninsu a yanzu   saji  daga bakinsa tayi murmushin Jin dadi dan tasan baba qarami zai ji dadi sosai  idan labarin auren adamcy dan kusan kullum sai yayi mata maganar ." ***** a natse ta fara  neman   layin qanwarta    hjy nuriyya   wacce ta kasance abokiyar wasanta iyayensu uwa d'aya Uba d'aya Kuma akwai shakuwa  sosai a tsakaninsu tana  zaune  a kasar  london  tun aurenta har zuwa wannan lokacin acan ta haifi yaranta duka iyakarta da naija ziyara ko wani sha'ani mai mahimmam. suka gaisa cike da farinciki  Inda hjy zulaiheart take sanar mata batun hada Adamcy aure da maryam  " Kai  alhamdulillah masha Allah gsky abu yayi kyau  sosai Allah ya sanya alkhairi ya  nuna mana lokaci ,wannan karon zanyi k'okari na shigo kasar  kafin lokacin  domin ayi biki dani ". Hjy zulaiheart tace "gsky kam anyi  bukukuwa duk baki  samu  damar shigowa  naija ba "haka ne kam  amman inshallahu  zan shigo wannan bikin nayi ne no any excuse ta k'arasa maganar tana murmushi suna cikin hirar hjy zulaiheart  tace "nuriyya wai kuwa  kina jin  labarin bilkisu  ?dip hjy nuriyya  tai tmkr an d'auke wuta nepa tana jin  wani irin daci acikin ranta sai data yi kusan minti biyar sannan tace  "bana Jin labarinta Kuma bana son na  ji labarin Inda take ,  kuma  Ina son ku shareta ku cireta acikin zuciyarku har abada  Kmr yadda mukayi yarinyar data nuna mana bamu Isa daita  ba ,sannan  bata  sonmu  ta zabi rayuwa ko babu mu me yasa zamu damu daita ? "ni dai duk wanda zai nemata acikinku yaje amman  ni nuriyya bana ciki kuma babu hannuna  babu kafa ta ciki  "naunayen ajiyar zuciya hjy  zulaiheart  ta sauke tana cewa " dan Allah nuriyya kiyi hakuri ko babu komai rayuwarta qaddara ce Allah ne ya d'aura mata wannan rayuwar babu yadda zata gujewa qaddararta ,wallahi  duk sanda ta fado min sai na zubar da hawayen tausayinta , da nasan Inda zanganta  wallahi zan nemota  . "Kune fa kuka damu daita ko nace ke dan duk  cikinmu babu me zanceta wallahi sai ke ,bata ga wuya bane shiyasa bata dawo ba, wallahi nafi son rayuwa ta juya mata baya ta dawo tana kuka  tana  rokonmu  kullum mummunar adduar da nake mata kenan sannan Ina adduar duk tsanani karta dawo mana da zuria Kmr yadda hhyrmu take addua ." "wannan addua ta rashin haihuwa a tsakaninsu batayi ba ku daina mata mummunar addua gskiya "ai babu abinda ya kamaceta da wuce mummanar addua " yanzu dai kiyi hakuri  muyita mata addua da fatan alkhairi a duk Inda take lokaci nata tafiya a lisafinsa shekaru ashirin kenan rabonmu  daita , kiyi hakuri dan mu barwa Allah komai sannan muyi mata adduar Allah yasa ta waiwayo mu cikin koshin lafiya naunayen  ajiyar  zuciya hjy nuriyya tayi  sannan tace  "shikenan big sister ai abinda  kikace shi zamuyi  cike da qauna yar'uwarta hjy zulaiheart sukayi  sallama da yaruwanta suna gama wayar uncle Umar ta kira ta sheida masa tana son ganinsa  ." Ranar asabar   da misalin karfe hud'u na yammaci  baba bAbba   yazo   bisa Kiran da hjy zulaiheart tayi masa , byn sun  gaisa   hjy  zulaiheart ta karanto  masa hukumcinta   akan ATA cike  da farinciki uncle Umar yace "masha Allah wannan hukuncin yayi  Kuma mun gamsu dari bisa dari dan burin mu bai wuce muga adam ya ajiye iyali ba  ,bugu da Qari zaa sake  karfafa zumunci a tsakanin   inshallahu  zan sheidawa sauran yan'uwana sai mu saka ranar da zamu ga alhj saidu  dan  zamu so a daura auren nan  kusa". "wannan  maganar tayi Kuma naji  dadinta  sosai dan  haka a fara sheidawa  baba qarami dan  nasan murnarsa sai tafi  ta kowa domin duk yafi  mu d'auki son ganin  Adamcy  yayi aure ta k'arasa maganar tana murmushin jin dadi  "ai kuwa daga nan ma bangarensa zan shiga na fara sheida masa  Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana lokaci "Ameen ya Allah,Allah  kadai yasan murnar da zaiyi  idan yaji  ya sha lemu da kayan snaks din da'aka jera masa suka zarce da  tautaunawa  kafin daga bisani sukayi  sallama ." Baba qarami   na zaune akan  kujera me zaman mutun uku  sai ga baba Babba   wanda ya kasance yaya  garesa Kuma Kani ga   mahaifin ATA yana ganinsa ya saki fuska tare da farincikin ganinsa  ya d'an  mike tsaye cike da girmamawa ya bashi hannu  suka gaisa sannan ya nuna masa mazauni atare suka zauna "sannu da zuwa yaya ! "ya gida da iyalin  fatan  suna lfy?"alhamdulillah kowa Lafiya yake ya naka iyalin  ?"Suna lfy ya bashi amsa yana murmshi ya mike ya  dauko masa abun sha "bazan sha komai ba daga bangaren hjy zulaiheart nake na sha "  . suka yi shiru na second biyu sannan baba babba ya fara magana a tsanake " kamar yadda na fad'a mk  daga bangaren hjy zulaiheart nake tayi decide ta had'a Adam aure da diyar kaninta abdulrauf " what ?"when ?ya fada a matukar rude yana Jin wani  irin abu ya  caki kahon zuciyarsa , yayi saurin runtse idanuwanshi "zulaiheart na bukatar wannan labarin ya zamo Kaine ka fara jinsa   bisa kokarinka na son ganin adam ya ajiye iyali dan haka nan da sati me zuwa zamu gana da yayan mahaifin yarinya alhj  saidu  ." shiru  baba qarami yayi har sanda yayansa ya dasa aya  ya mike tsaye"to ni zan wuce duk abinda ake ciki zan kiraka a waya a fusace baba qarami   ya mike Shima  yana cewa "yaya wannan wace irin maganar banza ce kazo min dashi  sannan kana k'okarin sa kai ka wuce ka barni  ? yayi mgnr  a fusace yana sa hannu ya daki center table din dake tsakiyar falonsa wanda ke d'auki da ruwan lemu kala dabam  dabam ,nan take wasu glas cup  suka  tarwatse yana huci yake kallonsu "yanzu ni dana cin burin ya zabi daya daga cikin ya'yana ya aura shine dan munafurci zata hadashi da diyar kaninta saboda son Kai irin nata ? "ya'yana  yafi  dacewa Adam  ya aura ba wannan yarinyar ba ya sake dukan table wanda hakan yasa gbdy ahlin da ke numfashi a part din suka bayyana" burina bai wuce ya'yana ko jikokina su had'a  iri da dashi ba yayi mgnr yana kallon cikin kwayar Idanu dan uwansa  ."me yasa zaka fadi haka idris?  "eh na fad'a yayi mgnr yana cakunar wuyan dan'uwansa da iyakacin karfinsa  yana maxurai  abinda bai taba faruwa ba a tsakankanisu ,hindatu wacce suke kira da hindu     ta samu guri ta zauna tana kallonsu zuciyarta na rawa dan ta dade a tafkin qaunar ATA mahaifinta ne ya hana a fito da soyayyar a cewarsa yana jiran lokaci yau ga lokaci ya zo masu a wani iri . sauran kuwa hankalinsu ne yayi kololuwar tashi ganin yadda mahaifinsu

Chapter 14 of 43