me yasa anayi mana abubuwa rashin mutunci aunty ta hanani d'aukar mataki ? "daidai kenan habib ,abinda aunty tayi shine daidai shine abinda kowace uwa ta gari ya dace tayi idan suna yi muma muna yi to meye bambamci a tsakanin mai ilimi da wanda bai dashi ? kowani irin abu zaka gani a gidan nan ka d'aure ka cije ni yanzu damuwata ba matsalar Aunty hassana bace sanin inda dangin mahaifiyarmu suke shine babban damuwata ."
Ya riko hannunta cikin nashi yana dubanta "ki ciresu aranki abinda muka fi bukata sune dangin mahaifi , ace yau bamu da dangin mahaifi ko ba acikinsu muke rayuwa ba shine babban tashin hankalinmu "suma dangin mahaifiya suna da mahimanci domin zuciyarsu tafi ta dangin uba tausayi , jikina na bani akwai abinda yasa suka nisanci juna dole ina bukatar nasan haka har lokacin aunty tana kallonsu har sanda maryama
ta nufi kofar shiga bangaren umma shi kuma habib ya nufi get din gidan da alamun fita zai yi ta saki labulen tana sauke naunayen ajiyar zuciya ta koma ta zauna cikin zullumi tana tuno rayuwarta ta baya "
Maryama bata iske umma a falo ba dan haka ta samu waje ta zauna akan d'aya daga cikin kujerun falon ta runtse idanunta tana tunani "anya ba wani mummunar abu mahaifiyata ta shuka ba wanda yasa yan'uwanta suka gujeta ita kuma take jin tsoron komawa garesu ba ?"anya ma yan'uwanta su suka d'aura aurenta da mahaifinmu ? anya ma akwai gasky a zamanta da mahaifinmu ? "wad'an nan tambayoyin tayita jerowa kanta wanda bata da mai bata amsa sai mahaifiyarta ko umma ."
shiru ta sake yi tana qoqarin kawar da zarginta akan iyayenta bata san shigowar umma ba sai dai taji an girgizata sannan tayi sauri ta juyo cikin tsoro taga tana kallonta tace "maryama mai kike tunani haka ?na shiga uku ni aseeya kar dai abinda ya faru Kika zauna kina tunani ?" nan da nan ta soma girgiza mata kai alamun "a'a! tana in in nah "amm uhm Allah umma bashi bane ."umma ta girgiza ka fadanta cikin sanyin murya "kin kuwa san lokacin dana dauka ina miki magana baki sani ba ?na jima anan ina kallonki maryama kina tunanin abinda ya faru d'azu still maryama kai ta girgiza mata alamun" a'a!
Cike da nuna kulawa umma ta juya ta qarasa kitchen inda fridge yake ta isa ta bud'e ta dauko kwalin hollandia ta rufe fridge ta matsa kad'an inda d'an qaramin tray da glass cup's Ke kansa ta d'auki d'aya ta dawo inda take zaune ta janyo kujera gaban maryama ta zauna tana kallonta ta zuba mata hollandia ta mika mata tare da cewa "gashi ki sha dan nasan har yanzu baki sakawa cikinki komai ba ta kai cup bakinta tana kallon umma kad'an ta sha ta kawar da bakinta alamun ya isheta."
"karki sake tunanin abinda ya faru d'azu abinda ya rigada ya faru ya faru karki sakashi aranki yazo ya dameki wani ciwo yaje ya kamaki mu shiga uku dan sai nafi kowa shiga damuwa "Allah umma bashi bane wannan ai idan da sabo na rígada na saba "
"Wani kallo umma tabita dashi tare da sanyaya muryarta tace "idan bashi bane maryama sanar dani matsalarki dan bayan mahaifiyarki baki da wanda ya fini ina jinki tmkr ni na haifeki bancin ke kadai uwarki ta haifa da tuni na kwaceki gbdy daga hannunta , wannan soyayyar da nake miki yasa na janyoki jikina sosai karki ji komai sanar dani damuwarki ta fad'a tana kallonta ."
sunkuyar da kanta kasa tayi tana wasa da yatsun hannunta kusan second goma sannan ta motsa labbanta "daman ba komai bane kawai ina son nasan inda dangin aunty suke, ko sanin labarinta "me yasa bata zuwa wajen yan'uwanta suma kuma me yasa basa zuwa wajenta?" laifin me tayi masu? " me ya faru daita tunda na taso nake ganinta cikin damuwa da raunin zuciya wanda har yasa nima nake jin haka atare dani ."?
Wani dogon ajiyar zuciya umma ta sauke cikin fargaba ta tashi zata wuce har ta juya maryama tayi saurin riko hannunta cikin nata "umma ! ta kira sunanta muryarta na rawa cak umma ta tsaya tare da juyowa fuskarta da tausayawa itama maryama mikewa tayi cikin tsananin tashi hanakali ta rusuna kasa ta daura hannuwanta a saman kafafun umma cikin raunin murya ta fara mgn Kmr zatayi kuka "umma nasan Kinsan komai daya faru da iyayena dan allah karki boye min gskyr dana sanki daita "
umma ta zare hannuta ta sake juyawa "umma Kodai mu din bata hanyar sunah aka haifemu bane ?"
Umma ta juyo da sauri tana dubanta qirjinta na dokawa da karfin gaske "maryama ta gyada mata kai kana ta cigaba da mgn "duk yadda muke da aunty duk shakuwarmu da soyyyar da take nuna mana ta kasa fad'a mana haka kema gashi umma zaki wuce ki barni byn kece kika bukaci kisan damuwata .
"Nasan kinsan komai daya faru ki fada min mu san matsayinmu wata killa ma shine dalilin da yasa muke ganin tasko acikin gidan nan dan girman allah umma karki boye min abinda yafi komai mahimmanci arayuwarmu ki fad'a min na rabu da nauyin dake daskare da qirjina ta qarasa mgnr cike da sheshekar kuka ."
Girgiza kai umma ta shiga yi ta dawo inda take tsaye ta kamota ta zaunar daita akan kujera tana kallonta cike da tausayawa kusan mintuna ashirin sannna ta numfasa tana cewa "ku din ba shegu bane ku din yan halak ne" naunayen ajiyar zuciya maryama ta sauke tana kamo hannu umma cikin nata "kinsan kowani d'an adam da yadda yake kar'bar gaddararsa . wasu mutane basa gane rayuwa duk yadda allah ya rubutawa bawa babu wanda ya isa ya canza maka ita,ita qaddara kuma tana fadawa bawa daidai da yadda allah ya hukunto masa qaddara bata san talaka ba bata san mai kudi ba ,qaddara ce da rabonku ta nisanta mahaifiyarku da yan'uwanta yan'uwanta sun kasa kar'ban qaddarar data fad'a mata amatsayin su na muslimai amman mgn ta gsky ku din yan halak ne sai dai akwai yan'uwanki da'aka samesu bata hanyar aure ba .."
nan take jikin maryama ya kama rawa tmkr mazari ta tsaya tana kallonta tana assessing maganarta umma ta damke mata hannu gam cikin nata tana kallonta tana jin yadda jikinta Ke rawa tamkr mazari , maryama tayi imani bancin a zaune take da ta tabbatarwa kanta kafafuwanta bazasu iya d'aukar ba, da zuwa yanzu ta zube kasa."cikin kyarrrma wasu hawaye masu zafi suka shiga turereniyar zubo mata tana jin wani zafi a qirjinta mara misaltuwa cikin ikon allah allah ya bata ikon furta kalmar "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun shi tayita furtawa tana maimaitawa still jikinta da zuciyarta na rawa ."
Umma ta kalleta cikin sarewa ta cigaba da magana "wannan qaddara ce maryama km kowani bawa da tashi irin kalar qaddarar bata wuce Kan kowa ba , ki godewa allah da yasa ta hanyar aure aka sameku bilkisu na bani tausayi matuka kullum idan na kalleta sai na zubar mata da hawaye , da gatanta da komai tana rayuwa tmkr bata da kowa ,tana rayuwa cikin kaskanci alhalin bata cancanci haka ba tunda taji an samu wasu babu aure taji komai ya tsaya mata cak hatta shi karan kanshi labarin taji ya fita kanta ."
Mahaifiyarki haifaffiyar wannan gari ce anan aka haifeta aka haifi iyayenta ke hatta kakaninta ana aka haifesu sune asalin yan kasa "Idan mutun ya shigo jahar lagos din nan ya tmbyi family's din alhj rafi'u giwa to babu wanda bai san mahaifinta ba ."mahaifinta ko nace dangin mahaifiyarki gbdy masu arziki ne ."mahaifinta alhj rafi'u giwa yana da mata hud'u kinga kenan suna da yan uba a qalla guda talatin sai dai bazan iya kawo miki sunansu ba ina dai jin Aisha , hauwa wacce suke kira da jiddah abakinta gbdy a gidansu bilkisu ce auta a mata sai kannenta biyu maza dake binta daga kanta mahaifiyarta bata sake haihuwar mace ba haka ma sauran bangaren matan sun daina haihuwa wanda hakan yayi sanadiyar da soyayya mai karfi ya shiga tsakaninta da mahaifinta da yan'uwanta gbdy kowa yana sonta kasancewarta auta a mata "
gabadaya yan'uwan bilkisu masu kudi suka aura daga wanda yake london sai wanda yake Canadá ko American ,mafi yawa daga cikin yan'uwanta suna wata kasa daga maza har mata idan kuma anan ne zaki iske su cikin VI ita kadai ce ta auri talaka marashi ,dan gbdy asalin mahaifinki talakawa ne idan aka cire abban sadam wanda yake da d'an rufin asiri dan yana da gidan bread da kowa ya dogara dashi amman basu da komai ."
"bilkisu ta taso cikin gata da soyayya da kulawar iyaye tun daga tasowarta har zuwa girmanta duk abinda take so shi takeyi ta taso cikin soyayyar iyaye dana yan'uwa kowa yana sonta sannan ta taso da farinjin samari acikin family's dinsu kasancewarta kyakkyawa hasalima kyawun jikinta kika d'auko fuskarki ce ta mahaifinki amman km shi din ma baki dauko farinsa ba dan shi fari ne sol tmkr bature kmr yadda kike ganinsa a hoto ." kowa na sonta da nuna mata soyayya ,acikin masoyanta akwai mubarak dake mutuwar sonta, mubarak cousing dinta ne da ubansa da uwarta uwa daya uba daya kuma shima mahaifinsa mai kudin gaske ne km shi kadai suka haifa ,bilkisu na da shekara shabiyar a duniya alokacin tana ss 1 a secondary school alokacin mahaifiyarta da mahaifin mubarak sukai alkwarin aure a tsakanin yaransu dan mubarak din zai yi tafiya zuwa american qaro karatu , sun bar mgnr atsakaninsu idan ta gama karatunta na secondary sai ayi musu aure ."
mahaifinki ussein adam shima asalin haifaffen garin nan ne haka iyayensa sun kasance su takwas ne a wajen iyayensu mata hud'u maza hud'u umar ,fatima ,gali saadatu ,nazifi fadeela Kmr yadda kikasani , hassana da ussein ne auta ."
yana da shekara ashirin da takwas a duniya ya fara aiki a gidansu bilkisu ta sanadiyyar abokin abban sadam abdulwahab wanda shi gadi yake a makotansu ." mahaifinki ussein ya kasance direban ne gidansu bilkisu wanda Ke kaita school , idan lokacin tashi yayi ya koma ya d'aukota duk inda zata shike kaita hussein ya kasance mutun ne mai tsananin kirki gashi kyakkyawa aji farko illarsa dai shi din ya kasance talaka ne mai son jin dadi arayuwarsa km yana harka da yammata da shaye shaye sai dai bai ta'ba barin gidansu bilkisu sun san da zaman wannan halin nashi ba a boye yake yi saboda tsira da aikinsa ."
Maryama ta runtse idanunta tana jin wani tuttukin bakinciki a zuciyarta. ta d'aura kanta akan cinyar umma ko zata samu sausaucin zugin da zuciyarta take ,dan tun baaje koina ba ta fara datasanin jin labarin iyayenta , mahaifinta manemin mata ne ga shaye shaye a iyan nan ma kad'ai ta raina kanta ta sake yarda su din marasa gata ne ."
" tun farkon ganin bilkisu da ussein taji ya burgeta daman shi Allah yayi masa farinjin mata dan atarihinsa bai ta'ba cewa yana son mace ba dan har prouding yake , wannan yasa ya qara samun kusanci daita sosai , duk abinda taci sai ta rage masa idan zai kaita school ta bashi tun abun yana bashi mamaki har yazo ya daina bashi mamaki ya ajiye abun amatsayin ita din mai alkhairi ce , shima kma yana kulawa daita sosai dan hatta murfin mota kafin ta fito ya fito ya bude mata sannan idan sun iske an gama assembly zai tabbatar da ta shiga class akan idanunshi sannan zai juya ya koma gida ,ga iya bada labari, ussein ya iya bada labarin da zai saka mutun nishadi amman fa ga wanda yake da mahimanci a wajensa duk wannan yana cikin abinda yasa bilkisu ta sake sakewa dashi , shiyasa kullum bata da magana sai na fadar kirkinsa a wajen iyayenta wanda har hakan yasa iyayenta suke son batunsa tana sa ayi masa alkhairi na mussaman kullum da irin kyautar da take sa ayi masa ."
haka rayuwa tai ta tafiya mubarak na kiranta a waya amman sam bata bashi lokacinta yayinda wata irin shakuwa mai karfin gaske ta shiga tsakanin ussein da bilkisu lokacin da ta kai shekaru sha bakwai ta fahimci ba shakuwa bace kawai a tsakaninsu soyayya ce mai karfi wanda shima zuwa lokacin ya kamu da matsanancin soyayyarta ta yadda ya kasa hakuri sai daya zaunar dani ya fad'a min ciwon dake zuciyarsa yace zai yi qoqarin ya boye nashi domin itama bilkisu ya fahimci irin son da take masa bazai ta'ba barin wannan soyayya ya tabbata a tsananinsu ba domin dai yasan tafi karfinsa tafi karfin aurensa ita din ba sa'ar
aurensa bace babu ta yadda zai sameta arayuwarsa ."
"Nima na karfafa masa gwiwa ya danne abinda yake ji akan bilkisu na nuna masa bambamci dake tsakaninsu daita samun auren irinsu akwai wahala duk da babu yadda allah baya al'amarinsa shi yayi talaka kum shi yay mai kudi nace yayi addua sai allah ya kawo masa sauki da mafuta , amman alokacin ya sheida min zai ajiye aiki ya nemi wani still dai nice na hana na bashi kwarin gwiwa ya cigaba da aikinsa ya dai rage sakar mata fuska da kusanci daita ."
yana cikin wannan halin kwatsam bilkisu ta bayyana masa soyayyata da fari yaki amincewa hakan yasa ta shiga damuwa mai tsanani har rashin lfy ta kwanta batare da iyayena sun san akanshi take ciwon ba wanda ta kai har dakin daaka bashi a gidan take biyosa tana kukan ya amshi soyayyarta "ya zaunar daita ya fad'a mata gsky soyayya atsakaninsu ba abu ne mai yuwu wa ba duba da matsayinta da nashi , kuka take tana nuna masa babu wani bambamci a tsakaninsu dashi duk abu daya ne a wajen Allah da kalamai masu sanyaya zuciya da soyayya tasa ussein ya amince tunda daman shima yana sonta ranar daya amince aranar yan gidansu suka ga ikon allah domin dai bilkisu ta warke daga rashin lfy da take suka fara gudanar da soyayya ."
" tun tana boyewa har tazo ta fara bayyanawa zuwa lokacin a family's duk wanda yasan bilkisu yasan ussein idan har kana son kaga kyautar bilkisu ko yalwataccen fararta to kayi mata mgnr ussein family's dinta babu wanda bai san ussein direba ba idan ya dauko ta daga school zasu samu waje su parka su sha soyayyarsu ussein yana da yammata masu son shi amman soyayyar bilkisu tayi karfin da bazai iya cigaba da soyayya dasu ba ,wata irin soyayyar ussein Ke nuna mata mai karfi wanda har ta kai yana iya ta 'bata batare data hanashi ba nasan wannan ne saboda ussein na kawota gidan nan wajen mahaifiyarsa akwai lokacin dana shiga bangaren hajiya bata nan na iske su a dakin tana kwance ajikinsa sanye da kayan makaranta ajikinta suna romance ."hajiya mahaifiyar ussein ba ƙaramin jin daɗin haɗuwar bilkisu da ussein tayi ba ganin yadda yaron nata ya fara natsuwa ba kamar daba ba yanzu duk wani harkar mata ya jinginar da ita, haka zalika shaye shayensa yayi sauki sai wanda ba'a rasa ba."
Bayan bilkisu ta kammala karatunta na secondary akace ta fito da miji saboda masoya sunyi mata yawa kowa na sonta da aure km mafi yawansu cikin yanuwa ne sai kawai ta gabatar da ussein amatsayin mijin da zata aura hajiya rahma na gama jin abinda bilkisu ta fad'a ta mike tsaye tana dubanta abun ya mugun girgizata a matukar firgice tace "bilkisu banji abinda kika fad'a da kyau ba ina son ki sake maimaita min ,fad'a min naji da kyau tayi magana a tsawace batare da wata fargaba ba ta sake maimaita abinda ke ranta ai nan take mahaifiyarta da yan'uwanta da suka fito ciki d'aya suka nuna rashin amincewarsu mamakinta ne ya kamasu daman shakuwarsu ba iya nan ta tsaya ba ,har ta kai matakin soyayya juyin duniya akayi daita tace ussein take so har da ikirarin muddin zatayi aure to shi zata aura ,nan fa suka fara raba jaha da mahaifiyarta yan'uwanta kowa zaginta ya shiga yi me zatayi dashi ta rasa wanda zatayi soyayya sai direba common direba zata aura ? ita dai jinsu kawai take amman ita aranta ta kudurta komai zai faru sai dai ya faru amman ita ussein take so km har lokacin mahaifinki na shaye shayensa sai dai ba kowa ke iya fahimtar hk ba km nasan yawon tsaftansa da amfani da turaruka masu kamshi yasa baa ganewa amman mu dake rayuwa a gidan nan mun sani tunda idan yana gida yana shan kayansa a bayan dakin salma lokacin baa gina ba ."
Tashin farko mahaifiyarta tasa akayi kiransa cike
da matsanancin fargaba da tashin hankali ya nufi part dinta bakinsa dauke da sallama ya shiga falon tana zaune akan kujera na alfarma bata amsa sallamar da yayi ba haka zalika bata dubeshi ba tun kafin ayi masa gurin zama yayiwa kanshi yana mai yi sunkuyar da kanshi a kasa agabanta tmkr mai neman gafara ahankali ya furta" hjy barka da dare ta dago kai daga Kan tv ta maida kanshi tana qare masa kallon tsab tana nazarinsa ko kayan kirki ma babu ajikinsa kana kallonsa kasan mataiyaci ne mai yaci bare ya bawa bilkisu shi kuwa kallo daya zaka masa ka tabbatar da cewar ba cikin natsuwa da kwanciyar hankali yake ba tunda ya samu kiran gaugauwa daga hajiya rahma bai sake samun kwanciyar hankali ba har zuwa yanzu da yake durkushe agabanta sai data gama qare masa kallo sannan ta numfasa ta fara magana a kausashe "meke tsakaninka da bilkisu ?da sauri ya girgiza mata kanshi alamun babu komai ."
Shiru tayi tana cigaba da kallonsa kafin daga bisani ta cigaba da magana cikin bacin rai "kace babu komai ?da sauri ya girgiza mata kai alamun Eh !
"ni nasan akwai komai amman tunda kai da kanka kace babu komai to ya tsaya a babu komai din domin idan ya zamo akwai komai zaka hadu da mummunar bacin raina zan maka abinda har ka matu bazaka manta dani ba sannan daga wannan lokacin aikinka ya qare acikin gidan nan ya dago da sauri yana kallonta a tsorace "haka nake nufi ko kana bin mu bashi ne da ka wani tsareni da ido .?"
ya sake girgiza mata kai alamun a'a ! "to maza ka tashi yanzu yanzu ka tattara komai naka ka bar mana gidan matsiyaci banza kawai ,kaga yarinya qarama shine kake son kayi mata wayo, guda nawa bilkisun take da zata auri me shekarunka ? Idan km kwadayin kudin ubanta kake kayi kad'an kaci . matsayinka bai kai nan ba, ka bari ya'yan manya ya'yan masu arziki irinta su more ba kai matsiyaci ba , matsiyacin ma wanda ko rigar kirki baka dashi tana zuba ruwan bala'i ya zabura ya mike da sauri zai wuce tace " ba estate din nan ba ko a bakin get din estate din nan aka gaya min anganka wallahi wallahi sai nasa an daure min kai ko nasa a 'batar min da kai idan ma ba son abun duniya da son zuciya irin naka ba ina kai ina bilkisu? kai yanzu kaga dacewarku daita ?da sauri ya girgiza kai "a she kasan gsky maza tashi ka bani guri matsiyaci banza kawai ko maza sun qare a duniya mai bilkisu zatayi da kai da sauri ya qarasa barin falon bai tsaya jin sauran karashen zancen ba yana fita daga falon bilkisu ta fito daga d'akinta daman km hayaniyar mahaifiyarta ce ta fito da daita ta tmbyeta ita da wa ye ."
"Nida wannan matsiyacin ne dake neman cutar da rayuwarki "ta bata amsa atakaice tana dauke kanta bilkisu tayi shiru tana nazarinta idan har ta fahimceta da ussein take ? da sauri ta nufi kofar fita ta dakatar daita "idan kika sake kika bar falon nan sai na tsine miki albarka cak ta tsaya tana kallon mahaifiyarta " shasha shar banza da bata san ciwon kanta ba duk cikin yanuwanki wani dan iskan kika ga ya kawo miji Kmr wannan tsukakken da ko kayan kirki babu ajikinsa kullum yana yawo cikin kodaddun kaya ,kisani ko zaki mutu bazaki auresa ba na haramta miki aurensa ke intakaice miki baki da miji sai mubarak dan albarka in sha allahu
a ranar useein ya tattara ya bar gidan ya dawo dakinsa dake nan byn makaranta faidiyya ."
Tun daga ranar lamari ya sake lalacewa domin tunda bilkisu tasan ya bar gidan hankalinta ya tashi ta shiga damuwa sosai ta kauracewa kowa numfashi kawai take acikin gidansu amman rayuwarta da komai nata yana wajen ussein ta kirasa yafi sau babu adadi bai daukar kiranta da kyar da ban hakuri da turo sakonin ya sauko sannan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 43