bil'adama ka
169
TASKARNOVELS.COM.NG
shigo lambu na babu sallama ka tsinki tuffata ka
cinye. sa'adda hantaru yaji wannan sai kunya ta
kamashi domin yasan baiyi da'a ba kuma bai
nuna shi dane mai tarbiyya ba, cikin sanyin
murya ya dubi budurwar yace yake wannan
ma'abociyar kyau ki gafarceni hakika nayi
kuskure amma ki sani kayan marmarin dake
cikin lambun sunada daukan ido. budurwar ta
bushe da dariya sannan ta murtuke fuska tace
hakika kude bil'adama da rashin hakurh kuke to
kasani cewa kaciwa kanka bala'i domin abune
mawuyaci ka tsira da rayuwar ka ina yimaka
albishir cewa ka fado cikin tarkon uwar mayu ta
aljanu koda gama fadin hakan sai budurwar ta
rikide ta dawo wata tsohumaw mummunar
aljana mai matukar ban tsoro hantaru ya
yunkuri da nufin ya kaimata sara sai yaji cikinsa
ya murde ya fara ciwo kafin cikan dakika biu ya
fara aman jini nan take fadi kasa sumamme.
Koda shumailat taga abinda ya faru da hantaru
sai itama ta fadi kasa sumammiya. lokacin da
shumila ta farfado daga dogon suman datayi
saita tsinci kanta acikin wanin irin gida an
daureta da wata katuwar sarka shide wannan
gida an gina shine da zallan duwatsun wuta
kuma babu komai acikinsa face wata katuwar
170
TASKARNOVELS.COM.NG
tukuba wacce aka hada guma guman itatuwa
suna taci da wuta saman wutar an daura wani
gado yayi jawur. kwatsam sai shamilat ta jiyo
hayania daga can bangaren yammacin gidan
sannu a hankali ya ringa karuwa yana cika
dodon kunne daga can saiga dandazon wasu
yayan aljanu sama dasu million 40 sun taho da
gudu suna tsalle a tsakiyar su wannan
mummunar aljanan ne dauke da hantaru su
duka suka tunkaro inda tukubar wuta take koda
ganin haka sai shamilat ta fahimci cewa cikin
wannan gadon wuta aljanar nan zata daura
hantaru shamilat ta kurma ihu tana kuka tana
mai rokon aljanar kadata kona mata danta
aljannar bata dubi shamilat ba saida suka iso
dab da wutar sannan ta tsaya cak tana kyalkyala
daria tace yake wannan bil'adama kiyi sani
cewa idan ban gasa wannan danaki ba na baiwa
yayana sunci duk mutuwa zasuyi ayau. kuma
basu iya haura kwana 40 batareda sunci naman
bil'adama ba kinga kuwa da bai fi ɗa ba.
Kodajin haka sai shumilat ta fashe da kuka,
aljanar ta sake bushewa da dariya a karo na biu
tace ai gara kisha kukanki ki more kafin na
dawo kanki domin idan na gasaki ni kadai zanyi
walimanki domin yayana basa cin nama mace
171
TASKARNOVELS.COM.NG
cikin tsananin fushi shamilat ta dubi aljanar tace
tir dake wannan la'ananniar maiya inda dana
acikin hayyacinsa yake dakin raina kanki domin
baki isa kiyi masa komai ba sa'adda aljannar taji
haka sai ta bushe da daria sannan ta dakawa
shamilat tsawa tace ke bil'adama kiyi sani cewa
agaban sarauniyar mayun aljanun duniya kike
babu wani mahaluki daya isa ya hallakani sa'ar
ki daya mijina baya nan ya tafi farautar
bil'adama dayanzu kema mun gama dake
dolene na hakura sai yadawo domin akwai yajin
dazai tafo mana dashi wanda muke jin dadincin
naman bil'adama dashi.
********************
Mazan Jiya Part 17
Labarin Sadauki Hantaru mai takobin saiful
lujara na Mazan Jiya
#Cigaba
172
TASKARNOVELS.COM.NG
Gama fadin hakan keda wuya sai uwar mayu ta
yunkara zata daura hantaru akan gadon wutan
bazato ba tsammani sai sukaga hantaru ya mike
zumbur ya daka tsalle sama daga kan tafin
hannun ta kafin takai masa cafka cikin zafin
nama ya gabza mata naushi a idon ta take
hannun nasa ya burma cikin kwarmin idanun
nata, koda ya zaro hannun nasa saiga kwayan
idanun nata ya fado kasa nanfa jini ya kama
feshi uwar mayu takama kururuwa tana katan
tanwa saboda tsananin zafi da takeji a cikin
idanun ta yayin da yayan uwar mayu sukaga
abunda yafaru da mahaifiyarsu sai sukayi caa
akan hantaru da nufin su yayyaga shi su cinye
shi danye abinda basu saniba sun gamu da
gamon su maimakon sadauki hantaru yayi
amfani da takobin sa wajen yakar su sai yayi
wurgi da takobin sa ya afka musu yadinga
cafkar wuyan su yana gwara kawunan su nanfa
kafun a jima hantaru ya hallaka sama da guda
dubu dari a daidai wannan lokaci ne uwar mayu
tadawo hayyacin ta koda taga mummunar
barnar da hantaru yayi mata saita fusata ta
runtuma sabon ihu da kukan bakin ciki shi
kansa hantaru saida ya razana sakama kon jin
sabon ihun datayi suko sauran yayan nata
173
TASKARNOVELS.COM.NG
dasuka rage sai suka ruga izuwa bayanta suka
tsaitsaya uwar mayu ta tunkari hantaru da
mugun nufi shima sai ya tunkaro ta bada jin
tsoron komai ba koda ya rage baifi taku goma su
gamu sai hantaru ya ruga da gudu yayi tsalle
sama yakai mata wawan naushi da nufin ya fasa
daya idon cikin zafin nama uwar mayu ta kade
shi da hannunta take hantaru ya maku da dirkar
gini ya fado kasa a matukar galabaice koda uwar
mayu taga hantaru a kasa ya kasa tashi saita
rugo da gudu ta daga kafar ta sama ta kawo
masa wawan taku da nufin ta mutsuke shi cikin
zafin nama hantaru ya goce saboda karfin takun
saida kafar uwar mayu ta nutse cikin kasa har
gwuiwan ta uwar mayu ta zare kafar da sauri ta
cigaba da kaiwa hantaru taku yana gocewa
kafun ajima harabar gidan ya cika da ramuka ita
kanta uwar mayu saida ta gaji ainun takama
haki a sannan ne hantaru ya samu ya mike tsaye
aiko sai suka kasa tsere ta dinga binsa tana kai
masa cafka tana wangame baki domin ta hadiye
kansa gabadaya aduk sa'adda ta karta mashi
farata a jikin shi saidai taji kamar ana karta
takobi akan dutse kuma ko korzanewa bayayi
cikin dakika kadan gidan ya hautsine hankalin
kowa ya dugunzuma domin gunguma
174
TASKARNOVELS.COM.NG
gunguman duwatsu ne na wuta ke fadowa kasa
su kansu yayan uwar mayu saida suka firgice
suna neman mafaka itako shamilat tuni dirkar
da'aka daure ta a jiki ta karye ta fadi sannan
wani katon dutse ya fado akan dirkar lokacin da
hantaru ya waigo yaga halin da shamilat ta
shiga sai hankalin sa ya dugunzuma sabona
yasan cewa idan ta dade a kasan wannan katon
dutse na wuta kasa zata iya zaftarewa a wannan
lokaci ne hantaru ya fusata don haka saiya daina
gudun yama tsaya cakk awaje daya yana
sauraron isowar uwar mayu gareshi koda uwar
mayu taga hantaru ya tsaya cak ya daina guje
guje sai murna ta kamata domin tasan cewa
yanzu zata hallakashi bada bata lokaci ba kawai
saita durfafe shi da dukkan karfinta cikin bakin
zafin nama da isowar ta dabb dashi saita kawo
masa wawan cafka da hannayen ta guda biyu
cikin tsananin zafin nama hantaru ya sunkuya
kasa ta kama iska kafun ta sake kai masa hari
tuni daka tsalle ta cikin karkashin kafafun ta ya
zagayo bayanta ya sake daka tsalle kafun ta
waigo ya dira akan kafadar ta ya gabza mata
naushi acikin kunnen ta aiko sai hannun nashi
ya lume acikin kunnen ya futo ta cikin daya
kunnen yana zare hannun jini yakama feshi take
175
TASKARNOVELS.COM.NG
uwar mayu ta sulale kasa matacciya a matukar
galabaice hantaru ya durshe kasa bisa
gwuiwoyin sa saboda tsabar wahala a sannan
ne ya lura cewa guma guman duwatsun wuta
dasuka yita fadowa daga saman ginin sun
hallaka gabadaya yayan uwar mayu dayan su
bai tsiraba da rayuwarsa hantaru na durkushe
yana haki sai kawai yajiyo ihun shamilat daga
can kasan wannan katon dutsin daya danne
dirkar ginin da'aka daure ta a jiki cikin zafin
nama hantaru ya yunkura da saurin gaske ya
ruga wajen ya kaimata dauki wani irin takun
sawu mai karfi da hantaru ya jiyo a bayansa
shine tsaida shi ya juya a firgice aiko sai yayi
arba da wata jibgegiyar halitta mai tsananin
kwarjini daban tsoro da muni bakomai ne
wannan halitta ba sai mijin uwar mayu ya dubi
yadda gidan sa ya rugurguje sannan ya hango
gawar uwar mayu a can gefe daya can kuma
saiga gawarwakin yayan sa kota ina kawai saiya
takarkare ya kwarara ihu karar ihun tamkar ana
ruwan kwaran kwatsa daga sama ak'amarin
daya kara razana hantaru kenan musamman
daya karewa mijin uwar mayu kallo sama da
kasa ya tabbatar dacewa ruwa ba sa'an kwando
bane a wannan lokacin ne kuma shamilat ta
176
TASKARNOVELS.COM.NG
cigaba da kwala ihu ashe dutsen daya danne
dirkar da take jiki ne yake kara dannawa kasa
nan fa hankalin hantaru ya rabu gida biyu ya
rasa abinda ya kamata yayi shin mijin uwar
mayu zai fuskanta suyi yaki koko wajen
mahaifiyar sa shamilat zaije ya ceto rayuwarta
harya yunkura zai ruga wajen shamilat sai yaji
an shako wuyan sa ta baya koda ya kama abun
daya shake shi sai yaga ashe wata irin doguwar
bulala ce mijin uwar mayu ya jefa mishi ta shake
shi a wuya kuma ta shake shi ne ainun ya kasa
cire ta mijin uwar mayu yafara janyo bulalar
nan domin ya kawo hantaru gaban sa shiko
hantaru saiya fara cijewa da dukkan karfin sa
domin yasan cewa muddin ya kuskura yaje
gaban sa ya damke shi saidai kuma mahaifiyar
sa ta haifi wani amma shi tasa ta kare hantaru
ya cigaba da cijewa amma saboda mijin uwar
mayu yafi shi karfi nesa ba kusa ba saiya dinga
jansa gabadaya al'amarin daya dugunzuma
hankalin hantaru kenan ya saduda domin yasan
cewa kwanan sa yazo karshe.
******************
Mazan Jiya Part 18
177
TASKARNOVELS.COM.NG
#Cigaba
A lokacin daya rage baifi saura taku biyar ba
mijin uwar mayu ya cafi hantaru da hannun sa
sai wata dabara ta fadowa hantaru ya tuno da
wata wuka dake sakale a bayansa cikin hanzari
ya zaro wukar ya yanke wannan bulala data
shake shi ya fada baya koda mijin uwar mayu
yaga bulalar sa ta yanke sai yayi jifa da ita ya
zare wani katon sungumi dake sakale a cinyar
sa ya ruga izuwa kan hantaru suka kacame da
sabon azababben yaki mai ban tsaro da ban
al'ajabi wohoho!! tashin hankali ba'a saka maka
rana saida hantaru da mijin uwar mayu suka
kwana suka tashi suna fafata yakin bala'i hatta
kasa tasha azaba domin saida mijin uwar mayu
ya ratattaka komai dake cikin gidan nan da
wannan katon makamin dake hannun sa tunda
hantaru yazo duniya bai taba shan bakar wahala
ba irin ta wannan lokaci sau bakwai yana suma
a wannan fafatawa dayayi da mijin uwar mayu
amma kafun mijin uwar mayu ya zaro shi daga
cikin karkashin kasa ya karisa kashe shi saiya
178
TASKARNOVELS.COM.NG
farfado su cigaba da gumurzu saida yazamana
cewa hantaru ya samu karaya tara a jikin sa
amma bai fasa yaki ba.
Itako shamilat tuntuni ta suma ta nutse a cikin
karkashin kasa batama san abunda dake faruwa
ba ana cikin wannan gumurzun ne mijin uwar
mayu ya samu nasarar yiwa hantaru wani irin
wawan naushi a fuska nan take numfashin
hantaru ya dauke ya baje kasa ko motsi bai sake
yiba mijin uwar mayu ya tsaya cakk yana haki
kuma ya kurawa hantaru idanu domin yagani ko
zai motsa a wannan lokaci shima mijin uwar
mayu duk jikin sa raunuka ne jini na zuba har
jiri na diban sa yana layi tsawon dakika dari
shida da sittin hantaru bai motsa ba. don haka
sai mijin uwar mayu ya tabbatar dacewa ya
mutu amma duk da haka hankalin sa bai kwanta
ba saboda bai taba ganin bil'adama hatsabibi
mai tsananin jarumtaka da naci da taurin rai
tamkar hantaru ba, nan take mijin uwar mayu
ya nufi kan hantaru kai tsaye da nufin ya cizge
kansa da karfin tsiya ya cinye, koda yazo dabb
dashi ya raba kafafun sa akan hantaru kuma ya
sunkuyo da nufin ya kama kansa sai kawai yaji
hantaru gabza masa naushi a ido, take hannun
hantaru ya burma ta kwarmin ido ya fito ta keya
179
TASKARNOVELS.COM.NG
take mijin uwar mayu ya fadi ta baya tamkar
giwa uku sun fadi a kasa, lokaci guda.
Da kyar da jan jiki hantaru ya isa inda dutsen
nan ya danne shamilat hantaru yayi amfani da
dukkan karfin damtsen sa ya dago dutsen
sannan kuma ya shiga zaro wannan dirkar gini
wadda ta nutse cikin karkashin kasa kuma
shamilat take daure a jiki saida yasake shan
bakar wahala sannan yasamu ya dago dirkar
yana gama zaro dirkar yaga shamilat a
mimmike babu abinda ke motsi a jikin ta nan
hantaru ya kurma ihu kuma ya fashe da kuka
domin a zaton sa ta mutu, wani iko na Allah sai
hadari ya gangamo adaidai wannan lokaci nan
da nan aka kece da ruwa, koda ruwa ya daki
shamilat saita farfado a wannan lokaci kan
hantaru na sunkuye yanata rusa kuka, kwatsam
sai yaji shamilat tayi tari cikin zafin nama
yadago kai koda yaganta a raye ya matsa gareta
ya rungumeta duk su biyun suka fashe da kukan
farin ciki.
Saida su hantaru suka kwana arba'in a cikin
wannan busashen gida na uwar mayu suna
jinyar cikin su sannan sukayi shiri suka cigaba
da tafiya, sannu sannu bata hana zuwa sai dai a
180
TASKARNOVELS.COM.NG
dade ba je ba tunda su hantaru suka bar
wannan daji dayayi mugun yaki dasu uwar
mayu basu sake gamuwa da wani abu ba daya
wahalar dasu har suka iso birnin darul habur da
la'asar su shamilat suka shigo cikin birnin darul
habur tundaga bakin kofar birnin shamilat ta
cika da tsananin mamaki domin komai na garin
yana nan kamar yadda tasan shi shamilat da
hantaru suka yita kalle kalle suma suka zamo
abun kallo a matsayin su na baki lokacin dasuka
ratsa ta cikin kasuwa da makera sai hantaru
yadinga ganin zaratan jarumai masu kirar karfi
sunata kera makamai iri-iri wasu kuma sunata
baiwa kansu horon kokuwa da gudu, daganin
wadannan zaratan jarumai sai hantaru yasha
jinin jikinsa yasan cewa lallai ya shigo nahiyar
sadaukai inda sai yayi da gaske jarumtakar sa
zata kwace shi, domin bai taba ganin samari
masu girma da tarin kwanji irinsu ba abunda
yafara fadowa hantaru a rai shine batun gasar
nan na gudun kamo barewa nanfa ya shiga
tunanin al'amarin a cikin zuciyar sa.
Lokacin da hantaru yake ta wannan tunani itako
shamilat farin ciki ne ya lullube ta sabona
tsintar kanta a cikin mahaifarta in banda
murmushi da kalle-kalle babu abunda shamilat
181
TASKARNOVELS.COM.NG
takeyi hakadai suka cigaba da tafiya bisa
dawakan su rakuman su na gaba, kwatsam sai
daya daga cikin rakuman su hantaru yaje yana
shinshina wata katuwar randa dake cike da
ruwa yana kokarin ture marfin ta, dama
rakuman na fama da kishirwa sunfi kwana
talatin rabon su da shan ruwa domin sun dade a
cikin sahara suna tafiya, ruwan dasu hantaru
sukayi guzuri bashida yawa, a garin ture marfin
randar ne rakumin ya bangaje randar gabadaya
ta fashe karar fashewar randar ce tasa mai
randar ya fito a fusace daga cikin rumfarsa
rikeda takobi, koda yaga rakumin daya masa
wannan barna sai yayi kansa zai sare shi cikin
zafin nama hantaru ya zare takobin sa ya daka
tsalle daga kan dokinsa ya dirka a gaban mai
randar ya tare wannan sara takubban su suka
hadu suka fitar da kara gami da tartsatsin wuta,
nan fa aka tsaya ana kalon kallo tsakanin
hantaru damai randar a iya rayuwar hantaru bai
taba ganin saurayi mai tsawo da kauri da
murdewar jiki kamar wannan saurayi ba,
sannan yanada matukar kwarjini koda sauran
jama'ar dake cikin kasuwa sukaga abinda ke
shirin faruwa sai hankalin su ya dugunzuma
kowa ya baro wajen sana'ar sa aka rugo inda su
182
TASKARNOVELS.COM.NG
hantaru ke tsaye aka tsaitsaya ana kallo cikin
tsananin fushi wannan saurayi ya dubi hantaru
yace shin kazabi karasa rayuwar kane akan na
rakumin ka hantaru yayi murmushi yace inason
rayuwa ta, kuma inason rayuwar rakumi na
idan saboda akan randar ka kakeso kadauki ran
rakumi na toh gaskiya ka fadi kudin randar ka
ko nawane zan biya kodajin haka sai saurayin
yadakawa hantaru tsawa yace kai bako waye
Kaine harda zaka nuna min gadara a cikin birnin
mu lallai yau zakasan cewa ka tabo zaki uban
dawa kuma dodon maza dakai da rakumin
nakan duk yanzun nan takobi na zata sha jinin
ku, kafun hantaru yace wani abu sai saurayin ya
daga takobin sa cikin zafin nama ya kaiwa
hantaru wawan sara a ciki da nufin ya tsarga shi
biyu hantaru ya jada baya takobin ta sari iska
nanfa suka kacame da azababben yaki,
al'amarin dayayi matukar firgita shamilat kenan
ta fara kuka tana rokon jama'ah dasu raba
wannan fada amma babu wanda ya saurare ta
face gudu da jama'ah suka ringayi domin wuri
ya hautsine tsautsayi na neman afkawa kan
kowa.
Koda ganin haka sai Shamilat ta zaburi dokinta
ta nufi gidan mahaifinta sarkin makera Shuraim
183
TASKARNOVELS.COM.NG
ibn Alkasim domin tq sanar da shi abinda ke
faruwa.
Wohoho! Jarumtaka ta hadu da jarumtaka dole
ne fafatawar ta zama abar tsoro, nan take
Hantaru da saurayi suka hargitsa kowa da
komai dake cikin kasuwar, suka rinka rushe
rumfunan suna dagargaza dukiyar jama'a, nan
fa jama''a suka dinga guje-guje da iface-iface,
kafin a juma labari ya cika gari, Hantaru da
wannan saurayi suka rinka kaiwa junansu sara
da suka cikin tsananin zafin nama juriya da
bajinta ba kakkautawa, sai da suka shafe kusan
rabin sa'a amman dayansu bai samu nasarar
koda kwarzanar jikin dan uwansa ba, har
takubbansu suka dakushe. Al'amarin daya
fusatasu kenan suka zubar da makamansu suka
sake ruguntsumewa da azabben gumurzu da
bugun juna da hannu da kafa, nan take kuwa
kowa ya hada wa kowa jini da majina.
A daidai lokacin ne Shamilat da mahaifinta
Shuraim tare da wasu jama'arsu suka iso wajen
a guje bisa dawakansu, aikuwa sai ga wata
jama'ar da ban bisa dawakai a sukwane, ba
kowa bane yake jagorantar su ba face sarkin
mafarauta na birnin wanda ake kira zaharu ibn
184
TASKARNOVELS.COM.NG
Dauwal, nan fa rundunonin nan suka ja tunga
suna masu fuskantar junansu ga dukkanin
alamu so suke su yaki junansu, abinda ya
hanasu shine kallon fafatawar da su Hantaru ke
yi.
Zaharu ibn Dauwar shine mahaifin wannan
saurayi dake fafatawa da Hantaru, kuma
tsakaninsa da Shuraim gaba ce mai tsanani tun
iyaye da kakanni, kuma ba komai bane ya
haddasa wannan gaba ba face wannan gasa da
ake gudanarwa duk karshen shekara ta tseren
gudun kamo barewa, domin auren budurwar da
babu kamarta a birnin, duk shekara idan aka yi
gasar zuri'ar mafarauta ce take cinye gasar,
zuri'ar makera basu taba cinye gasar ba, saboda
an fisu zakwakurarun jarumai masu
sadaukartaka.
Shuraim n da wani da guda daya mai suna
Hurais, a duk fadin birnin babu kyakkyawan
saurayi kamarsa, kuma ya kasance mai matukar
kwarjini a cikin al'umma, Hurais kanin Shamilat
ne, dan Lokacin da aka yi mata aure bai wuce
shekaru bakwai ba.
185
TASKARNOVELS.COM.NG
Lokacin da Hurais ya girma ya zama saurayi sai
soyayya mai zafi ta kulli tsakaninsa da wata
kyakkyawar budurwa mai suna Marilat, wacce
ta kasance kanwa ga wannan saurayi da ke yaki
da Hantaru.
Shi dai wannan saurayi ana kiransa da suna
Rabbasu, ma'anar sunan shine mai karfin zaki.
Bayan soyayya ta yi karfi tsakanin Hurais da
Marilat sai iyayensu suka farga, nan fa iyayen
kowanne daga cikinsu suka taka masu burki,
aka hanasu ganin juna domin babu yadda za'a yi
a bari suyi aure tunda akwai gabar asali a
tsakanin dangin nasu.
A asirce Hurais da Marilat ke haduwa a daji
suna tattauna yadda zasu bullo wa wannan
al'amari kan soyayyarsu, a karshe dai sai suka
yanke shawarar cikin dare su sulale su gudu
zuwa wani garin suyi aurensu. Aikuwa cikin
tsakiyar dare suka sullae suka bar garin, koda
gari ya waye sai aka nemi Hurais da Marilat aka
rasa, nan fa rigima mai karfi ta kacame tsakanin
dangin mafarauta da kuma dangin makera har
ta kaisu ga yakar juna, wanda sai da takai cewa
anyi asarar daruruwan rayuka, da kyar sarkin
garin ya raba wannan rigima.
186
TASKARNOVELS.COM.NG
A karon banza aka kamo Hurais da Marilat acan
wani kauye waishi Gabril, a lokacin da suke daf
da daura wa kansu aure.
Daga wannan rana Hurais da Marilat basu sake
ganin juna ba, a dalilin aka ne duk su biyun suka
shiga mugun hali suka kwanta cuta, a karshe dai
ciwo yakai ciwo rai yayi halinsa duk su biyun
suka mutu a kuma rana guda. Marilat ce ta fara
mutuwa, aikuwa Hurais na samun labarin
mutuwarta sai shima ya hadiyi zuciya ya mutu.
Bakin ciki a wurin dangin makera dana
mafarauta ba sai an fada ba domin sai da
kowannne bangare suka shafe kwanaki talatin
suna kuka da bakin ciki na wannan abu daya
afku, wannan shine sanadin daya kara zafafa
kiyayya da gaba a tsakanin dangin guda biyu.
Lokacin da rundunar biyun ta tsaya ana kallon
ffaatawar da akeyi tsakanin Hantaru da
Rabbasu sai kowa ya cika da tsananin mamaki,
domin ba'a taba ganin jarumin da yayi gaba da
gaba da Rabbasu ba har ya iya yakatsa ba sai
yau, saboda tsananin jarumtakarsa da iya
yakinsa.
187
TASKARNOVELS.COM.NG
Koda yake shi kansa Hantaru ya raina
jarumtakarsa domin bai taba haduwa da jarumi
bil'adama kamar Rabbasu ba, kai ko yakinsa da
mijin uwar mayu bai bashi tsoro ba kamar
wannan gumurzu da yake yi da Rabbasu, domin
ya tabbatar da cewa indai aka kara sa'a guda
nan gaba sai dai cikin biyi ayi daya, kodai suyi
ragas ko kuma daya ya kashe daya.
Babban abinda ya tayar wa da Rabbasu hankali
shine aduk sa'ar da ya sari jikin Hantaru sai dai
yaji kara kal! Takobin nan bata tasiri a jikinsa
sai dai wajen daya sara din ya dan kunbura.
Shiko Hantaru abinda ya dugunzuma hankalinsa
shine ko sau daya ya kasa samun nasarar
yankar jikin Rabbasu.
Ana cikin wannan hali ne kwatsam sai aka
hango wani mahayi bisa wani farin doki ya
durfafo wajen, tun kafin ya karaso wata irin iska
mai karfi ta dinga tarwatsa mutane ba shiri aka
buda masa hanya domin an gane kowane ne. Da
isowar mahayin wanda ke rike da wata farar
sanda sai yayi nuni da sandarsa izuwa ga
hantaru da kuma Rabbasu, nan take duk su biyu
188
TASKARNOVELS.COM.NG
suka zube kasa sumammu, wato suka yi
rabuwar dole ga barin yakar junansu.
MAZAN JIYA
Littafi Na Daya (1)
Part N
Marubuci: Abdulaziz Sani M/Gini
Typing: Abubakar Saleh AlQuyraemey
A sannan ne mahayin dokin ya tsaida dokinsa ya
dubi rundunar su Zuhairu da kuma ta su
Shuraim yace kowa ya dauki nasa ku tafi gida,
na raba wannan rigima a yanzu amman fa bata
kare ba, domin za'a yi babbar fafatawa ta karshe
nan gaba tsakanin Rabbasu da wannan bakon
jarumi a ranar gasar tseren gudu, ta neman
auren Gimbiya Larziyya, to nan ne za a yi
wannan fafatawar ta karshe.
Ko da gama fadin hakan sai mahayin yayi
girgiza ya bace bat! Shi da dokinsa, b wani bane
189
TASKARNOVELS.COM.NG
wannan mahayin sai kakan Shamilat wato boka
Sulbaini ibn Hukaish. Bacewar boka Sulbaini ke
da wuya sai ko wanne bangare suka dauke nasu,
wato su Shuraim suka dauki Hantaru suka tafi,
su kuma Zuhairu suka dauki Rabbasu suka tafi
da shi.
Lokacin da hantaru ya farfado yana bude
idanunsa sai ya tsinci kansa bisa cinyar Shamilat
ta zuba mashi idanu tana zubar da hawaye, a
gefe daya kuma sai yaga wani dattijo dogo siriri
kuma kyakkya a tsaye a kusa da shi kuma wata
dattijuwar mace ce sun kura masa idanu suna
murmushi gami da zubar da hawaye.
Hantaru ya dubi ko wacce kusurwa yaga a cikin
wani kyakkyawan daki yake, cikin matukar
mamaki ya mike zaune zumbur! Ya dubi
Shamilat ya ce yaya aka yi nazo nan, sannan
wadannna mutanen su waye?
Koda jin wannan tambaya sai Shamilat ta share
hawayenta ta ce ya kai dana kayi sani cewa
kakana boka Sulbaini ibn Hukaish hine ya zo ya
raba yakin da kuke yi da wannan sadaukin
saurayin, nan dai Shamilat ta baiwa Hantaru
labarin Rabbasu da mahaifinsa Zuhairu da kuma
190
TASKARNOVELS.COM.NG
irin gabar dake tsakanin zuri'arsu da ta su
Rabbasu. A karshe ta shaida masa cewa boka
Sulbaini yayi bayanin cewa za a sake fafatawa
da Rabbasu ta hanyar tseren gudun kamo
barewa, bisa takarar neman auren Gimbiya
Larziyya.
Sa'adda da Shamilat ta zo nan a jawabinta sai
hantaru ya kuma cika da mamaki ya ce wace
kuma gimbiya Larziyya?
Kafin Shamilat ta bude bakinta ta bashi amsa sai
Shuraim ya riga da cewa ya kai jikana Hantaru
ka yi sani cewa ba wata bace Gimbiya Larziyya
face yar sarkin garin nan namu Uhairu ibn
Sabus, kuma a halin yanzu a gaba daya nahiyar
nan babu wata mace mai kyawunta, ya kai
jikana kayi sani cewa mahaifiyarka Shamilat ta
bamu labarin jarumtakarka data gani da
idanunta a yayin tafiyarku tsakanin birnin sarki
kusaidu zuwa nan. Hakika kayi gagarumar
bajinta irin wacce wani bai taba yi ba, domin
fiye da shekaru hamsin baya, babu mai iya
ratsawa ta wadannan dazuzzuka ya fita lafiya
face ayarin dakaru masu yawa kuma masu
karfin sihiri, amman kai gashi kai baka da
sihirin komai face na kariya irin wanda muka
191
TASKARNOVELS.COM.NG
shayar da mahaifiyarka tun tana karama, shi
wannan kariyar kawai kake da shi.
Haka dai aka cigaba da fira tsakanin Shuraim da
Hantaru suna cikin tsananin farin ciki, daga
karshe sai Hantaru ya dubi Shuraim ya ce ya kai
kakana yanzu ya ya za a yi naga gimbiya
Larziyya?
Shuraim yayi murmushi yace wai shin me kake
ci ne na baka na zuba? Ka kwantar da
hankalinka zaka ga gimbiya Larziyya da
idanunka amman sai bayan mun dawo daga
gidan mahaifina boka Sulbaini, domin yace da ni
lallai mu kaika gidan shi gobe da safe.
Koda jin haka sai murna ta kama Shamilat dan
dama bata da burin daya wuce ta sadu da boka
Sulbaini, ba tre da bata lokaci ba Shuraim da
matarsa Shaulat suka shiga hidimar shirya
walima ta musamman dan murnar dawowar
Shamilat da jikansu Hantaru. Nan take aka
yanka rakumi da raguna guda uku, Sannan
Shuraim ya aika wasu kuyanginsa kasuwa, suka
je suka yi cefane. Nan fa aka shiga dafe dafe da
soye-soye, daman tuni an aika da sakon gayyata
192
TASKARNOVELS.COM.NG
ga yan uwa da abokan arziki da kuma
makwabta.
Tun kafin a gama shirye-shiryen jama'a suka
fara hallara a gidan Shuraim, nan da nan kuwa
gidan ya cika da jama'a, wasu abokan ma na
Shuraim rabonsu da zuwa gidan an fi shekara
goma, sai da kowa ya zauna a inda aka tanada
sai kuyangi suka fara fito da abinci da na sha
aka fara walimar, bangaren maza da ban haka
na mata da ban.
Sai da aka fara walimar annan Shamilat, Shaulat,
Shuraim da Hantaru suka fito daga cikin daki
suka fara gaisawa da jama'a, Shuraim na
gabatar da Shamilat da danta Hantaru ga
wadanda basu sansu ba, kuma suma bakin ana
gabatar d su ga su Hantaru, ana gaggaisawa.
Ana cikin wannan gaggaisawar ne sai Hantaru
ya hango wata mace can tsaye, wacce ta rufe
fuskarta da mayafi, idanunta kadai ke iya gani,
ita dai wannan macen ita kadai ce, bata ci kuma
bata shan komai, kuma ya lura da ita cewa
Shuraim take satar kallo. Yayi tunani a zuciyarsa
ya ce to shin wace ce wannan? Kuma me ya
193
TASKARNOVELS.COM.NG
kawota wannan taro, tunda bata damu da komai
ba na walima? Hantaru ya tambayi kansa.
Bayan gama gaisheshe ne sai Hantaru ya saki
wuri shima ya zauna ya fara cin abincin, a
lokacin ne sai gaba daya samarin dake wajen
suk zo suka lullubeshi suna masu yi masa jinjina
bisa gagarumar bajintar da yayi ayau, na
fafatawa yaki da Rabbasu.
Al'amarin da ya baiwa Hantaru mamaki kenan
ya ce wai shin shi wannan Rabbasu har shayinsa
ake yi a garin nan?
Wani saurayi mai suna Kumais ya ce ai a tarihin
jarumtakar Rabbasu a nan grin ba a taba samun
gwarzon daya taba tararshi ba, balle har su
fafata yaki ba sai kai kadai, kai a takaicema
gabadaya nahiyar nan babu kamarsa a
sadaukantaka, sannan kuma bashi da
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 13