shekara ashirin kenan ina
maka wahala amma shi danka baisan wahalan
98
TASKARNOVELS.COM.NG
kaba ko guda tabbas ka cuceni kuma kaci
amanata sbd haka nima dole naci amanarka
yanzu take zan kashe ka kuma komai daren
dadewa saina kashe wannan dan naka na cire
kambun nasa, nasa a hanuna na hagu. Kodajin
wannan batu sai mahaifina ya yunkura da sauri
domin ya bude wannan tsohuwar akwatin nasa
amma kafin hannunsa yakai kan akwatin tuni
dumbazu ya zare takobinsa ya fille mishi kai
nan take mahaifina ya sulale kasa matacce.
Batareda bata lokaci ba dumbazu ya dauki
wannan tsohuwar akwatin sihirin mahaifina ya
tafi ya bazama gari nema na amma duk inda
yaje sai ace dashi yanzun nan nabar wajen wato
mukayita sabani kenan lokacin dana koma gida
na iske gawar mahaifina saina sulale kasa
sumamme nan take daya daga cikin almajiran
mahaifina mai suna Kusad ya zuba min ruwa na
farfado kodana bude idanu na nayi arba da
Kusad saina tambaye shi a fusace nace wanene
yayiwa uban nan nawa kisan gilla? nan take
Kusad ya gayamin cewa shide yaga sa'adda
mahaifina ya kira dumbazu cikin turakarsa suka
kadaita kuma daga karshe ya jiyo dumbazu na
daga murya cikin fushi daga can kuma sai yaji
sautin sarar takobi kodajin haka sai kusad ya
99
TASKARNOVELS.COM.NG
la6e a bayan kofar turakar kawai sai yaga
dumbazu ya fito daga cikin turakar da sauri
rikeda akwatin sihirin mahaifina dakuma
takobin sa jini na diga a jikin ta.
*********************
Mazan Jiya Part 14
#Cigaba
Koda gama jin wannan batu saina rushe da
matsanacin kuka domin nasamu tabbacin cewa
dumbazu ne ya kashe min mahaifina babban
abun bakin cikina shine nasan cewa har abada
bazan iya daukar fansa ba akan dumbazu domin
akwai ranar da mahaifina yace dani yakai dana
ko a bayan raina kada ka kuskura kace zakayi
kokarin ganin bayan dumbazu domin bazaka
taba samun nasara a kansa ba saboda yafika
karfin sihiri, kai baka samu komai ba daga cikin
ilmina amma zan baka wata kariya wadda babu
wani mahaluki dazai iya cutar dakai.
100
TASKARNOVELS.COM.NG
Koda naji haka saina dubi mahaifina nace yakai
abbana wai shin meyesa kaki ka koyamin ilmin
ka na tsafi koda mahaifina yaji wannan tambaya
sai idanunsa suka ciko da kwalla har hawaye
suka zubo masa sannan yace kafin mahaifiyarka
ta rasu ta rokeni alfarmar kadana koya maka
tsafi, domin bincike yanuna cewa idan ka
mallaki irin sirrukan tsafina bazaka taba
haihuwa ba a duniya niko saina daukar mata
wannan alkawari kuma na tabbatar dashi najin
haka saina rungume mahaifina muka fashe da
kuka har izuwa lokaci mai tsawo tun daga ranar
da dumbazu ya kashe mahaifina bamu sake
haduwa dashi ba, amma a kullum acikin
farautar nema na yake har yagaji da neman ya
tafi can wata nahiyar inda yadinga amfani da
karfin sihiri yana yakar sarakuna yana mallake
dukiyar su da mulkin su a hakane ya mallaki
kasashe dayawa duk zamo a karkashin kasa
guda mai suna kailus daidai da rana daya sarki
dumbazu bai taba samun nutsuwa da kwanciyar
hankali ba saboda kawai rashin samun daman
hallakani, a kullum a cikin aiko aljanu da
sadaukan bil'adama yake domin suzo su
hallakani yakai hibru kayi sani duk lokacin
dakaga kana samun nasara wajen kare
101
TASKARNOVELS.COM.NG
rayuwata aduk sa'adda aka kawo farmaki ba
takobin ka bane take baka sa'a face kambun
tsafin dake jikin ka na hagu wannan shine asalin
yadda gaba ta kullu tsakani na da sarki
dumbazu ina mai tabbatar muku da cewa babu
yadda za'ayi kuje birnin kailus kuci dumbazu da
yaki face nayi abu guda wannan abu kuwa
bakomai bane saidai nacire kambun tsafina
nabaka kai hibru kasa a hannun ka sannan kaje
ka tari dumbazu tabbas zaka samu nasara akan
sa saidai ni daku munyi bankwana bazaku dawo
ku sameni a raye ba domin ka'idar wannan
kambu shine duk wanda yadaura shi a
hannunsa to duk ranar daya cire shi bazai kara
kwana uku a duniyar nan ba.
Koda Sarki hubru yazo nan a zancen sai
hankalin mu ya dugunzuma na dubi sarki hubru
nace ya shugabana ina dalilin salwantar da
rayuwar ka akan yarka.
Kodajin haka sai Sarki hubaru ya zubarda
hawaye sannan yace yakai sadauki dan
sadaukai kayi sani cewa nifa sarki nayi arziki
kuma na haihu duk abinda ake nema a duniya
102
TASKARNOVELS.COM.NG
na same shi haka kuma shekaruna sun tafi yata
fa yanzu ne take ganiyar kuruciyar ta SBD meye
zan bari rayuwarta ta salwanta alhali kadai
gareni idan na mutu itama ta mutu babu wani
wanda za'a kalla a tuna damu idan bakuje kun
ceto rayuwarta ba za ayi biyu babu domin bakin
cikin rashin tane zai kashe ni anan ita kuma
sarki dumbazu ne zai kasheta a can yanzu yanzu
bada bata lokaci ba nakeso kuyi shiri kutafi
izuwa ga bokana domin ya sadaku da hadimin
dazai kaiku fadar sarki dumbazu domin ku yake
shi amma kafun sannan ina mai dada jaddada
muku alkwarin dake tsakanin ku kai hibru
amanar yata na wajen ka domin kaine zaka aure
ta kai kuma maharaz na damka amanar kasata
da jama'ah ta a gurin ka domin kai zaka gaji
sarauta ta gama fadin hakan keda wuya sai sarki
hubru ya cire kambun dake hannunsa na hagu
ya miko min hanuna na karkarwa na karbi
kambun nasa a hanuna ina karba saina saka shi
a hanuna wannan shine babban kuskure danayi
a rayuwa ta domin na manta cewa duk wanda
yadaura wannan kambu toh duk ranar daya
cire shi bazai haura kwanaki hudu ba a duniya
nan take mukayi bankwana da sarki hubaru
yana kuka muna kuka domin munsan cewa mun
103
TASKARNOVELS.COM.NG
rabu har abada bazamu sake ganin juna ba kaico
babu ranar bakin ciki wacce tafi ranar rabuwa
da masoyi tabbas mun shaku da sarki hubru
koma munyi imani cewa yana matukar kaunar
mu kamar yadda muke kaunarsa amma gashi
munaji muna gani zai rasa rayuwar sa bamuda
yadda zamuyi mu kareshi lokocin damuka baro
fadar sarki hubaru muka nufi kofar gidan
shaburus Ibn mukaibar rana ta fadi magariba ta
doso kai muna isa kofar gidan muka iske boka
shabarus a tsaye yana jiran isowar mu koda
mukazo dab dashi sai mukaga idanunsa cike da
hawaye yana kallon mu kawai alamarin daya
karya mana zuciya kenan jikin mu ya karayin
sanyi boka shabarus ya dube mu cikin sanyin
murya yace lale da manyan gobe hakika kun
baro masoyina a cikin mugun hali inda nasan
wannan rana zatazo ta riske ni daban kawo
iyanzu ba kuyi sani cewa a duniya banida
masoyi tamkar sarki hubaru amma gashi an
wayi gari inaji ina gani rayuwarsa zata salwanta
babu abinda zan iyayi don kareshi yanzu bada
bata lokaci ba zan hadaku da babban hadimi na
wadda zai kaiku fadar sarki dumbazu acikin
kwana goma sha daya maimakon tafiyar
kwanaki saba'in da bakwai bisa rakumi ko doki
104
TASKARNOVELS.COM.NG
batare da an yada zango ba koda gama fadin
haka sai boka shabarus ya hade tafin hannunsa
waje guda ya kama karanta wadansu kalmomin
tsafi yana tofawa akan tafin hannun daga can sai
yayi nuni izuwa kan kasa nan take kasa ta dare
saiga wani narkeken aljani ya ratso ta cikin
kasar ya bayyana a samanta aljanin nada suffa
irinta tsuntsaye saidai kansa da wuyansa irin na
biladama ne kuma fukafukansa guda goma sha
takwas ne cikin rusunawa aljanin ya dukar da
kai kasa ga boka shubarus ya kwashi gaisuwa
shabarus ya dube shi yace angaishe ka mara'il
labarus yakai mara'il labarus kasani cewa yaune
ranar karshen aikin ka dani domin abune
mawuyaci kudawo ku riskeni a raye.
Koda jin wannan sai hankali aljani mara'il
labarus ya dugunzuma ya dubi boka shabarus
cikin damuwa yace ya shugabana ina dalilin ka
na fadan haka boka shabarus yace yakai babban
hadimi na kayi sani cewa zaka dauki sadauki
hibru tare da boka maharaz ka tafida su izuwa
fadar sarki dumbazu domin su yakeshi su kawar
dashi, kodajin haka sai aljani Mara'il labarus
yayi tsalle ya tumu da kasa ya kama kuka yana
mai cewa haba ya shugabana laifin maina maka
kakeso ka hallakani inani ina zuwa fadar
105
TASKARNOVELS.COM.NG
shugaban bokayen duniya domin a yake shi, na
roke ka daka yafemin wannan aikin kanemi
wani yayi shi amma bani ba.
Kodajin haka sai boka shabarus ya dakawa
aljani mara'il labarus tsawa yace dolene kai
zakayi wannan aikin domin kai kadai ne zaka
iya idan kuma kace bazaka yiba yanzu take anan
zan hallakaka kayi sani cewa sadauki hibru na
tareda kambun tsafin sarki hubaru don haka
babu wani tsautsayi dazai sa ku halaka saidai
zaku iya shan bakar wahala, maza ka kwashe su
ku tafi kuma ka tabbatar dacewa kun isa can a
kwanakin dasuka gaza ashirin tabbas bazaku
dawo ku riske niba domin a ranar da masoyina
zai mutu nima zan mutu, koda gama fadin haka
sai boka shabarus ya juya ya shige gidansa, koda
faruwar haka sai aljani mara'il labarus ya
suremu nida maharaz sannan ya bude
fukafukansa yayi sama sannan ya fara tsala
gudu nagaban kwatance muna gifta giza gizai
tambar wucewar tauraruwa mai wutsiya saida
muka shafe kwanaki tamkar wucewar
tauraruwa mai wutsiya, sai da muka kwashe
kwana goma sha takwas muna tafiya bisa aljani
mara'il labarus a sararin samaniya batareda
yasauko kasa ba don ya huta nikam a rayuwata
106
TASKARNOVELS.COM.NG
bantaba ganin aljani mai juriyar wahala ba
tamkar aljani mara'il labarus baisan yunwa ba
baisan ishirwa ba balle lalaci a yammacin
kwana na goma sha takwas dinne muka hango
fadar birnin kailus daga can nesa kadan a gaban
mu.
Wohoho!! tabbas fadar ta isa da akirawota da
matsayin aljannar duniya domin gavadaya ginin
ta da gilashin lu'u-lu'u akayi shi babu abinda
zaibawa mutum mamaki face ganin yadda aka
gina gabadaya birnin na kailus a tsakiyar wani
kogi abinda bamu saniba shine aljanu ne suka
zuba tubalin ginin harya fito saman kogin nan
duk inda zaka taka jauhar ne da zabar amma
indaga sama ka taho kana iya ganin yadda
ruwan kogin ya zagaye birnin gabadaya, aljani
mara'il labarus bai sauko kasa ba saida muka
iso dabda birnin sannan ya dira a bakin kofar
garin babu kowa a bakin kofar balle muyi
artabu damasu gadi kuma sai muka iske kofar a
bude wanwar sannan mukaji garin yayi tsit
tamkar babu wani abu mai rai acikin sa,
alamarin dayayi matukar bamu mamaki kenan
batareda fargabar komai ba muka sauko kasa
daga kan aljani mara'il labarus na wuce gaba ina
mai yafuo maharaz da aljani mara'il labarus da
107
TASKARNOVELS.COM.NG
hanuna ina mai cewa kubiyo ni a baya, a lokacin
ne na zare takobi na, na cigaba da tafiya ina mai
duba kowace kusurwa kuma ina kasa kunne
kozanji motsin wani abu daka iya kawo mana
farmaki sumame saida muka shafe sa'a shida
muna tafiya a cikin birnin kailus ko bera bamu
ganiba rayayye duk mutanen garin da dabbobin
su sun kame sun zamo gumaka babu abunda ke
motsi hatta kasuwa damuka ratsa ta cikin ta
mukaga mutane sunata harkoki amma kowa a
kame yake yazamo gunki, wasu suna musayar
kudi da kaya wasu kuma bakunan su a bude
alamar cewa magana sukeyi hakadai muka
cigaba da tafiya har muka iso kofar fadar birnin
anan bamuga komai ba ko gunkin dakaru babu
ma balle muji tsoron cewa zasu iya tashi akoda
yaushe su farmana, kai tsaye muka kunna kai
izuwa fadar har muka isa inda karagar sarki
take amma bamuga kowa ba bamuga wani abu
mai rai ba, kuma duk kofofin fadar nan a bude
suke bamu riski guda daya a kulle ba dazuwan
mu gaban karagar mulki sai muka dubi junan
mu mukayi ajiyar zuciya a tare na dubi maharaz
da aljani mara'il labarus nace yaku abokan
tafiya kuyi sani cewa ruwa baya tsami banza
duk yadda akayi an sanda zuwan mu kuma an yi
108
TASKARNOVELS.COM.NG
mana tanadi, nikam ina ganin cewa wani tuggun
aka shirya mana shiyasa bamuga komai da
kowa ba kafun nagama rufe bakina sai kawai
mukaji kofofin fadar na rufe kansu daya bayan
daya sannan sai mukaji an bushe da
mahaukaciyar dariya amma bama iya ganin mai
dariyar nan nan fa maharaz yafara amfani da
karfin sihirin sa domin yaga mai yin dariyar
amma sai abu ya gagara nan take cikin mu ya
duri ruwa duk da na tuna cewa ina tareda
kambun tsafi wanda sarki hubru yabani amman
sai naji banida nutsuwa da yadda dakai
kwatsam sai mukaga wadansu dakarun aljanu
ma'abota kwarjini daban tsoro sun bayyana
dayawa ba adadi sunyi mana kawanya suna
rikeda muggan makamai wadanda ko a labari
bamu tabajin irinsu ba sbd razanar damukayi
bamu san sa'adda muka kankame juna ba mu
ukun, abin mamakin ma shine aljani mara'il
labarus yafimu firgicewa domin duk ilahirin
gabban jikinsa karkarwa sukeyi kamar wadda
ake zukar jinin jikinsa, bazato ba tsammani sai
mukaga sarki dumbazu ya bayyana tsulum akan
karagar mulkin sa yana kyakyata dariyar
mugunta sannan saiga sauran dakaru na
bil'adama da duk fadawan sa sun bayyana suma
109
TASKARNOVELS.COM.NG
sunayi mana dariya, al'amarin kashe mana jiki
kenan mukaji nadama tazo mana bisa kawo
kanmu izuwa wannan birni domin mun san
cewa mun sayi ajalin mune da kudinmu, lokaci
guda sarki dumbazu ya tsuke bakinsa yabar
dariyar fadar tasa keyin tsit sarki dumbazu ya
dube mu, mu ukun yace yanzu ku uku kacal aka
turo ku yakeni wani haukane yasa kuke tunanin
zaku iya karawa dani hakika yaro baisan wuta
ba, yakai hibru kayi sannin cewa nayi nisa a
halwar tsafi sanina ya wuce na maigidana
mahaifin sarki hubru don haka wannan kambun
tsafi daya baka ka daura a hannun ka bazai
maka tasirin komai ba domin ka gamsu da
bayani na a yanxu zan nuna maka wani abu,
koda gama fadin haka sai sarki dumbazu ya
bude damtsen sa na dama saiga irin wannan
kambun tsafi wadda sarki hubru yabaiwa hibru
nan take sarki dumbazu ya cire kambun ya jefa
shi a cikin wani kasko take kambun nan ya kone
kurmus, sarki dumbazu yasake kyalkyalewa da
dariyar mugunta a karo sannan yace to kaga
yadda nayi da irin kambun nan na hannunka ko
dan haka wannan kambun darajar su daya da
takarda banza a wajena amma idan baka yadda
ba zakaga zahiri a yanzu, kafin na bude baki
110
TASKARNOVELS.COM.NG
nace wani abu tuni sarki dumbazu ya dubi
waddan nan zakakuran aljanu nasa yace ku afka
musu naga iyakar jarumtakar su, nan take
aljanun nan sukayi mana rubdugu nan fa
aljanun nan suka haumu da sara da suka
maharaz ya tare su da karfin sihirinsa yana kare
harin su shima aljani mara'il labarus niko da
karfin damtsena na taresu amma sai akayi min
kwab daya na zube a kasa sumamme ko dakika
arba'in ba'ayi ba aljanun sarki dumbazu sukayi
fatafata da jikin aljani mara'il labaru, aljani
mara'il labarus ya fadi kasa magashiyam ko ina
a jikinsa yazamo kofar fitar da jini kawai
maharaz ne yadan tabuka wani abu domin
yasamu dakika kusan dari uku da tamanin yana
fafatawa da aljanun nan sannan suka karya
karfin sihirin sa sukayi masa sara tamanin ya
baje a kasa ko shurawa bayayi.
Lokacin dana farfado idanuna suka bude saina
tsinci kaina a wata fadar a daure a jikin dirkar
gini wata irin sarkar tsafice ta daureni koyaya
na motsa sai naji sarkar ta kara matseni bisa
dole na hakura na daina motsi bisa mamaki sai
naga abokina maharaz a daure kusa dani yana
numfashi sama sama kaida gani kasan cewa
akan gangarar mutuwa yake, raunukan jikinsa
111
TASKARNOVELS.COM.NG
guda tamanin na digar da jini shiko aljani
mara'il labarus babu shima a wajen alamarin
daya tabbatar min da cewa aljani mara'il
labarus ya mutu kenan, bazato ba tsammani sai
naga sarki dumbazu ya riko hannun gimbiya
sahira yar sarky hubru sun tafo gareni sunata
hira da dariya cikin nishadi nan fa na cika da
tsananin mamaki nace a zuciyata saboda me
sahira zata saki jiki da babban makiyin ubanta
wadda a halin yanzu ya rabata da ubanta kuma
yazamo sanadin ajalin sa sarki dumbazu yakai
gimbiya sahira izuwa kan wata kujera ta
alfarma ya zaunar da ita sannan ya tafo gareni
saida yazo dab dani yadda muna iya jin
numfashin juna sannan yace dani ga masoyiyar
ka can tazamo tawa a yau zan sadaku da ita
sannan na cika alkawari na wato na kasheta a
gaban idanun ka tunda mahaifinta ya saba
ka'ida ta bai baku kansa kun kawomun ba, bisa
mamaki sarki dumbazu yaga na dubeshi nayi
murmushi sannan nace matukar bil'adama na
numfashi a doron kasa ako yaushe to baya
yanke kauna da kubuta daga kowani irin bala'i,
ya kai wannan azzalumin sarki maci amana kayi
sani cewa lallai karshen lalacewa kuma har
abada burinka bazai cika ba idan har amana da
112
TASKARNOVELS.COM.NG
soyayya sun kasance ababen gaskiya lallai
bazaka samu nasara akan gimbiya sahira ba.
Kodajin wannan batu sai sarki dumbazu ya
kyalkyale da dariyar mugunta yace yanzu kai a
tunanin ka har akwai wani tsautsayi dazai sa
nakasa samun nasaran abinda nasa a gaba duk
duniya fa babu sadauki mai karfin damtse na
babu matsafi mai karfin sihiri na wanene ya isa
yaja dani nan take dumbazu ya shiga yiwa kansa
kirari yana ihu da kururuwa a gabana yana cikin
yin hakan ne na lura da wani guru dake kugunsa
wadda ke dauke da layun tsafi akalla guda dubu,
alkyabbar dake jikin sane ta rufe gurun amma
saboda yana juyi da daga hannaye a gaban idona
sai idanuna suka hango wannan gurun, cikin
shammaci da zafin nama na sunkuya na kaiwa
gurun nan chafka da bakina aiko sai nayi sa'a na
chafke laya guda da hakorana na gatsa layar ta
fashe take gurun nan ya bace bat itama sarkar
tsafin da aka daure mu ta bace bat itama.
Cikin zafin nama na zare takobina, haka kuma
sai aba daya dakarun aljanun nan sarku
Dumbazu sai naga suna narkewa kamar ana
narka man shanu a kasko, kafin kiftawar ido
duk sun zama ruwa a kasa. Su kuwa fadawan
113
TASKARNOVELS.COM.NG
sarki Dumbazu sai duk suka firgice suka
mimmike tsaye jiki na kyarma. Sarki Dumbazu
ya tsaya kyam a waje daya ko motsi bai yi ba.
Kawai sai ya suddar da kansa kasa yana mai
zubar da hawaye, ni dai har wannan lokacin ina
rike da takobina banyi yunkurin yin komai ba,
daga can sai Sarki Dumbazu ya dago da kai ya
dubeni cikin tsananin fushi fuskar nan tasa a
murtuke, a wannan lokacin ne naga gimbiya
Sahira ta mike tsaye zumbur tana kalle kalle a
cikin fadar kuma tana kallon jikinta, ga dukkan
alamu ta dawo cikin hayyacinta na ce a cikin
zuciyata. Wato a da an juyar mata da tunaninta
ta manta da kanta da kuma komai nata.
Sarki Dumbazu ya kura mata idanu har wannan
lokacin hawaye bai daina zub daga cikin
idanunsa ba, kawai sai ya bude baki da kyar ya
ce "Ya kai yaro hakika ka cuceni, ka ruguza Mani
tsafin dana kwashe sjekaru da dama ina shirya
shi, yanzu bani da suran sirrin tsafi a tare da ni,
lallai sai na yi maka kisan gilla irin wanda ba'a
taba yi ma wani a wannan duniyar ba, kayi sani
cewa ko bani da sirrin tsafi ai in da na karfin
damtse wanda babu kmaarsa a kaf nahiyar nan,
dan haka maza bisa kanka yi kokari ka cice
rayuwarka na gani. Cikin wani irin azababben
114
TASKARNOVELS.COM.NG
zafin nama sarki Dumbazu ya zare takobinsa,
takubbanma guda biyu ne ya kawo mani wasu
tagwayen mugayen sara, duk da nayi sauri na
kauce amman sai da takubban nan suka zarge
rigar dake jikina, kuma suk yi mani dogon yanka
akan kirjina har jini yana tsartuwa. Kawai sai na
tafi da baya taga-taga zan fadi kasa ana layi.
Koda Dumbazu yaga ya samu wannan
gagarumar nasara sai ya sake dako tsalle domin
ya dura a kaina da nufin ya gididdiba sassan
jikina, amman sai na yunkura cikin karfin hali
da matukar juriya na yi tsalle can gefe guda
yayinda takubban nasa suka sari wata kujera
take ta ragargaje.
Nan fa muka ci gaba da azababben yaki yayi ta
kokarin ya gididdibani ni kuma na himmatu ina
mai kare hare-harensa, ina zuluyewa gami da
kaucewa amman ko kadan na saka mayar da
martani ko da sau daya ne kuwa. Domin zafin
namansa da karfin saransa sun wuce misalin ta
yadda bazan iya taresu ba har na mayar masa
da martani.
Sai da muka shafe sa'a tara muna wannan bakin
Artabu Dumbazu ya kasa samun nasara a kain
115
TASKARNOVELS.COM.NG
ni ma na kasa maida mashi da martani koda sau
daya ne kuwa, hakika duk wanda ya fika
jarumta to fa ya fika har abada, domin baka isa
ka kamoshi ba.
Koda sa'a tara ta cika muna wannan gumurzu
sai gajiya ta riskeni har ya zamana cewa da kyar
nake iya daga takobina na kare saran da
Dumbazu yake kawo mani, shikuwa ko kadan
bai gajiba domin kmar ma a sannan ne ya fara
gumurzun. Yayi da yaga na fara sarewa sai ya
cika da murna ya ci gaba da kawo mani hari a
sannu yana murmushin mugunta, sai da ya kaini
jikin bango ya tareni sannan ya buge takobina ta
fadi kasa sannan ya labta mani wawan sara a
cinya, ban san sa'ar da na kwarara uban ihu ba
tare da durkushewa a kasa ba cinyata na zubar
da jini.
Dumbazu ya sake dankara mani wani saran a
dayar cinyar tawa na zube kasa wanwar a
matukar galabaice nan fa idanuna suka fara gani
dishi-dishi. Dumbazu ya sake dag takobinsa da
nufin ya fille mani kai, amman kawai sai naga
hannun nashi ya sandare ya kasa labta mani
saran, da kyar da sidin goshi na juya baya kawai
sai naga wuka ta nutse a tsakiyar gdon bayansa
116
TASKARNOVELS.COM.NG
jini na burbulowa ta tsakiyar girjinsa, tsaye a
gaban Dumbazu gimbiya Sahira ce jikinta na
karkarwa, a sannna ne na gane cewa ita ce tayi
ta maza ta rugo ta caka wa Dumbazu uka a
gadon bayansa. Nan take Dumbazu ya sullae
kasa matacce ko shurawa bai yi ba, a sannan ne
nima idanuna suka rufe na sume a wajen.
Lokacin dana farfaɗo sai nayi arba da gimbiya
Sahira tsugunne a gabana ta rusar kuka,
raunikan dake jikin cinyoyina an saka masu
magani, a gefe daya kusa da ni kuma Maharaz
ne a kwance har wannan lokaci yana numfashi
da yar duk da cewa an sa masa magank a jikin
raunikan nasa.
Koda na daga kina na dubi gabas da yamma,
kudu da arewa sai naga ashe gaba daya
mutanen birnin Karlus ne suka rufemu sun
tsura mana idanu suna kallonmu kawai, a gefe
daya kuma fadawan Sarki Dumbazu ne a
tsaitsaye sunyi tsuru-tsuru kamar ace kyet su
fice da gudu. Ashe duk mamakinmu suke yi
yadda akayi har muka iya ffaatawa da sarkinsu,
har ma kuma muka samu nasarar hallaka shi.
117
TASKARNOVELS.COM.NG
Saida muka yi kwana arba'in muna jiyyar
raunikan mu a birnin Karlus ni da Maharaz
sannan muka warware, amman duk da haka
bamu warke sumul ba, sai a sannan
hankulanmu suka dawo jikinmu har na samu
damar baiwa gimbiya Sahira llabarin dukkan
abinda ya faru tsaninmu da mahaifinta gami da
wasiyar da ya bamu mu shaida mata.
Koda gimbiya Sahira ta gama jin bayanina sai ta
fashe da matsanancin kuka kuma ta rungumeni
tana mai ci gana da kuka. Da kyar na lallasheta
daga can sai ta dubeni ta ce da ni tana so tayi
wata magana ta sirri da Maharaz.
Cikin matukar mamaki na dubeta nace da ita
"Ke kuwa wace irin magana ce wannan da zaki
yi da abokina wacce bakya so na ji?
Koda taji wannan tambaya ai hawaye ya zubo
mata ta ce ka yi hakuri ya kai mijina na gobe,
wannan magana da zanyi da maharaz sakone
daga mahaifina zuwa gareshi, kuma ya
gargadeni da cewa komai rintsi da tsanani kada
na kuskura na sanar d kai.
Koda gama fadin haka sai gimbiya Sahira ta tafi
wajen maharaz tayi masa rada a kunnensa,
118
TASKARNOVELS.COM.NG
gabadaya jama'ar dake wajen babu wanda yaji
abinda ta ce masa, faruwar hakan keda wuya sai
kawai muka ga Aljani Mara'il Labarus ya sakko
daga sama tare da tsirga a gabanmu, al'amarin
da yayi matukar bamu mamaki kenan domin mu
a zatonmu ya dade da mutuwa, hakan yasa ko
neman inda gawarsa take ba muyi ba.
Yayin da Aljani mara'il labarus yaga muna
mamaki da ganinsa a raye sai ya bmau labarin
cewar ai dama dogon suma yayi, lokacin daya
farfado sai yaga babu kowa a wannan fada ta
farko da muka fara shiga, dan haka sai ya tashi
da yar ya tafi can bayan birnin Karlus ya boye
knsa a cikin daji yayita jinya har saida ya warke.
Koda jin wannan labari sai muka cika da farin
ciki, a daidai wannan lokaci ne wazirin sarki
Dumbazu ya zo gaba ya tsaya tare da cewa ya
kai wannan sadauki mai abun mamaki, tunda
har ka samu nasarar kashe sarkinmu, yanzu
abinda ya kamata kayi shine ka maye mana
girbinsa. Da jin wannan batu sai nayi murmushi
n ce ai ni bnai da bukatar mulki ko dukiya,
abinda nazo nema na samu, kuma ba komai
bane face masoyiyata kawai, sai nayi nuni izuwa
ga gimbiya Sahira, ita kuwa sai ta rugo gareni
119
TASKARNOVELS.COM.NG
cikin farin ciki gami da murna ta rungume ni.
Daga nan sai na dubi wazirin Dumbazu nace da
shi mukam yanzu mun kammala aikin da aka
turomu yi a birninku, saboda haka muna yi
maku sallama sai ku zabi shugabanku a
tsakaninku.
Gama fadin hakan keda wuya sai Aljani mara'il
labarus ya rankwafa bayansa muka hau mu uku
muka zauna, sannan ya bude fuka fukansa guda
18 yayi sama da mu, kafin kiftawar idanu mun
bace bat a cikin gajimare. Tun daga wannan
rana sai naga abokina Maharaz ya daina sakin
jiki da ni, ya daina yin hira da ni, hatta abinci
baya yarda muci tare, al'amarin daya
dugunzuma hankalina kenan na rasa binda ke
mani dadi a duniya, a duk sa'ar dana
tambayeshi shin ko nayi masa wani laifi ne? Sai
yayi murmushi ya ce sam banyi masa laifin
komai ba.
Tsawon kwanaki 17 da muka shafe muna tafiya
a sararin samaniya daga birnin Karlus zuwa
birninmu na darul mahabur bamu yi hirar rabin
sa'a ba nida Maharaz. Muna isa birnin darul
mahabur muka iske sarki Hubaru da boka
karlus sun mutu an binne su, muna kuka muka
120
TASKARNOVELS.COM.NG
isa inda kabarinsu yake, sai da muka shafe sa'a
uku cur muna a gaban karin muna kuka sannan
da kyar aka kawar damu daga bakin kabarin aka
tafi da mu izuwa fada.
Kashegari da safe aka dora Maharaz akan
karagar sarki Hubaru kuma aka daura aurensa
da Husuna yar sarki Hubaru, bayan an gama
bikin nadin Sarki Maharaz ne aka daura aurena
da gimbiya Sahira sannan ya bani sarautar
sarkin yakinsa, na cigaba da yin bauta gami da
biyayya ga sarki Maharaz tsawon shekaru,
kuma duk bukatar da ya zo mani da ita ina binta
ga dukkan iyakar karfina ban taba nuna masa
cewa na gajiya ba, na sha bakar wahala akan
biyan bukatunsa musamman a lokacin da suka
rasa haihuwa shida matarsa Husuna, domin sai
da na kusa rasa rayuwata a kakarina na nemo
masu maganin haihuwa. Duk wannan iyayya da
bauta da nake yiwa sarki Maharaz bai taba yi
mnai godiya ko sau daya ba, kuma gabadaya
abotarmu da kusancinmu sai ya yanke su, ko
magana bana samun damar yi da shi face in
mun zauna dakin gani tare da sauran fadawa
idan bukatar hakan ta taso. Har yau har gobe
ban san dalilin da yasa sarki Maharaz ya nisanta
da ni ba. Yake gimbiya Mulaifa wannan shine
121
TASKARNOVELS.COM.NG
tarihin rayuwata data mahaifinki da kuma
dangantakar dake tsakanina da shi. Masu iya
magana suna cewa ranar wanka ba'a boyon cibi,
yanzu dai gani ga shi kuma yace zai fada mani
wani sirri wanda
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 13