sai imnal
yayi murmushi ya ce indai akana soyaiya ta ga
gimbiya Mulaifa ne a shirye na ke don na kar6i
horo koda kuwa na mutuwa ne, cikin tsananin
takaici hibri ya dube shi a fusace, kawai sai ya
25
TASKARNOVELS.COM.NG
wuce zuwa turakar sa ya bar imnal tsaye a kofar
gida.
Da yammaci kuwa fadar sarki maharaz ta cika
makil da jama.a masu amsa gaiyatar tafiya yaki,
duk da cewa adadin jama.ar da suka taru bai kai
daya bisa goman masu tafiya yaqin ba sai da
fadar ta cika ta batse sai da ya zamana duk inda
ka duba kawunan bil'adama ne rututu.
Tun a farkon yammacin ne sarkin yaqi tare da
dansa suka amsa kiran sarki suka hallara a
fadar, shi kuwa sarki maharaz bai fito ba sai da
kowa ya gama zuwa. Da fitowar sarki kowa ya
miqe tsaye don girmamawa a gare shi har sai da
ya zauna sannan kowa ya zauna.
Sarki ya dubi dubun mutane da suka amsa kiran
sa sai ya cika da farin ciki, da ya duba 6angaren
da su imnal suke tsaye sai ya murtuke fuska ya
6ata rai.
Bayan fadawa sun zube sun kwashi gaisuwa ya
rage sauran sarkin yaki hibru da dansa Imnal,
kawai sarki yayi nuni da hannun sa izuwa ga
wani badakare yana maiyi masa nuni da yazo da
imnal gabansa, nan take badakare ya tasa keyar
sa yazo da imnal gaban sarki.
26
TASKARNOVELS.COM.NG
A wannan lokaci gimbiya Mulaifa na zaune daf
da sarki. Koda taga an tasa keyar Imnal anzo
dashi gaban sarki sai hankalinta ya tashi domin
ta tabbatar da cewa lallai hukunci za'ayi masa.
Gaba daya jama'ar dake fadar kuwa sai suka
cika da mamaki suka zuba ido don su ga irin
hukuncin da za'a yiwa Imnal yaron da ba.a ta6a
ganin yayi wani laifa ba. A kullum shi da
mahaifin sa ba su da wani abin da ya wuce
biyaiya ga sarki, Sarki maharaz ya mike tsaye
daga kan karagar mulkin sa ya dubi jama'a ya ce
ya ku ahalin darul mahabur ku sani cewa
wannan yaro Imnal d'a ga sarkin yakin mu
hibru ya kasance mai ladabi da biyayya a
garemu kamar yadda mahaifin sa ya kasance,
kuma bamu ta6a kamashi da wani laifi ba,
amma sai gashi a jiya ya aikata wani babban laifi
wanda bamu ta6a zaton zai aikata shi ba. Laifin
kuwa shine a jiya sa'adda kowa ya sunkui da
kansa kas a dakin bauta sai shi ya miqe yaje
inda nake zaune ya zauna kusa damu. Wannan
shine karo na farko da wani mahaluki ya karya
dokar maigirma darbuza a cikin kasar nan, don
haka dole ne ayi masa hukunci gwargwadon
laifin sa.
27
TASKARNOVELS.COM.NG
Mai girma darbuza ya ce a daure imnal a sama
jikin katako kuma a cikin rana tun daga
hudowar ta har zuwa faduwar ta ba tare da an
bashi ruwa koda makwarwa daya ba har tsawon
kwana uku. Idan kuma ya sake aikata irin
wannan laifi hukuncinsa zai zamo kisa ne.
Koda sarki maharaz ya zo nan a zancensa sai
idanun Mulaifa suka ciko da qwalla suka fara
zubar da hawaye. Hibru da imnal kuwa ko a
jikin su maimakon ma hankalinsu ya tashi sai
suka kama murmushi domin sun san cewa
wannan horo ba komai bane akan irin horon da
hibru ya bashi tun yana dan karami. Sarki
Maharaz yaci gaba da bayani .. Sai gobe za'a fara
wannan horo ga Imnal, kuma washe garin ranar
da aka gama horon ne zamu dunguma gaba
dayan mu mu tafi izuwa gagarumin yaki da ke
gaban mu. Domin mu riga sarki dujalu dauko
takobin saiful lujara. Ina mai kira ga dukkanin
jama'ar mu da a ci gaba da shirye-shirye babu
sassauci domin tuni dakarun gudunmawa sunzo
da yawan su mu kawai suke jira a tafi...
Ko da gama wannan jawabi sai sarki Maharaz da
Mulaifa suka shiga gida sannan jama'a kowa ya
kama gabansa.
28
TASKARNOVELS.COM.NG
Lokacin da imnal da hibru suka isa gida sai
hibru ya aika imnal kasuwa don ya sayo masa
zugazugi na wutar Qira sabo da nasa ya lalace.
Imnal ya hau doki ya tafi kasuwa tun kafin ya isa
kasuwar sai yaga duk inda ya ratsa jama'a na
kallonsa suna magana akan hukuncin da sarki
zai yimasa.
Kafin ya isa kasuwar ne ya hadu da wadansu
kuyangin gidan sarki suna tafe suna hira. Koda
suka ganshi sai suka sha gabansa suka shiga yi
masa kirari suna kodashi. Al'amarin da ya
matukar bashi mamaki kenan ya dubesu ya ce
ya ku wadannan kuyangi ku kuwa mai yasa
kuke kodani haka alhali kuwa banyi wani abin
al'ajabi ba? Suka ce ai kuwa kai ne kayi babban
abin al'ajabi tunda har ka siye zuciyar gimbiya
Mulaifa a halin bata ta6a nuna tana son wani da
namiji ba face kai. A yanzu haka tana can gida
tana kuka sabo da jin za'ayi maka horo na
kwana uku bisa laifin da ka aikata.
Babu irin rokon da gimbiya ba tayi wa sarki ba
akan ya janye wannan horo amma yaki, saboda
bakin ciki ne shi yasa ta kasa ci ta kasa sha
kuma ga dukkan alamu haka zata kwana a
wannan hali yau.
29
TASKARNOVELS.COM.NG
Sa'adda kuyanga ta zo nan a zancenta sai
hankalin Imnal ya dugunzuma ainun ya rasa
abin da ke masa dadi a duniya, sai kawai ya dubi
kuyangin ya ce da su idan kun koma gida ku
shaidawa gimbiya cewa wanda take kuka
dominsa yana bakin ciki bisa zubar hawayenta
da kuma rashin ci da shanta.. Lallai shi ma ba zai
ci kuma ba zai sha ba a yau har sai yazo ya ganta
ta kowane hali...
Jin wannan batu sai kuyangin suka zazzaro
idanu cikin tsananin mamaki wacce tayi magana
dashi tace taya zaka iya shiga gidan sarauta har
ka ganta ahalin akwai tsananin doka da tsaro?
Imnal yai murmushi ya ce ko mutuwa ke tsaro a
yau sai na ga gimbiya Mulaifa kuje ku gaya mata
cewa komai dare ina nan tafe a yau. Koda gama
fadin haka sai imnal ya kada linzamin dokin sa
ya wuce izuwa kasuwa ya siyo zugazugin ya
koma gida sannan ya ci gaba da taya hibru kera
wasu sababbin makaman yaki tamkar babu
wani abu da ke sosa zuciyarsa.
Nima zan so ganin yadda Jarumi Imnal zai iya
ratsawa ta cikin wannan tsaro na gidan sarautar
30
TASKARNOVELS.COM.NG
birnin darul mahabur har yaje ya sadu da
Gimbiya Mulaifa, masu karatu ko zan samu dan
rakiya kuwa?
Da fatan kuna hutun karshen mako lafiya,
sannan duk wanda yake son complete na
Littattafan yaki harma da na soyayya zai iya
tuntubata ta wannan number 08138873799
whatsapp kadai pls banda kira
MAZAN JIYA
Littafi Na Daya (1)
Part C
Marubuci: Abdulaziz Sani M/Gini
Typing: Abubakar Saleh AlQuyraemey
Da tsakar dare lokacin da gari yayi tsit ba kajin
komai face kukan gyare. Da daidaikun sautin
31
TASKARNOVELS.COM.NG
tsuntsaye, imnal ya miqe tsaye dama ko runtse
ido bai yi ba bare yayi barci. Cikin sanda ya debo
wadansu bakaken kaya ya sanya sannan ya rufe
fuskar sa da bakin rawani, takalmin da ya sa
kuwa na fata ne kasansa gashi ne yadda duk
abin da ya taka ba za.aji sautin komai ba.
Ko allura bai dauka ba a matsayin makami, ya
bude kofar dakin sa ya fita ba tare da hibru ya ji
motsin sa ba, maimakon ya bude kofar gidan sai
kawai ya daka tsalle kamar dan biri ya dira akan
katangar gidan, duk da cewa tsawon katangar
ya kai kamu sittin. Kafin ya tafi ya tanadi kayam
da ya cire daga jikinsa a cikin 'yar qaramar jaka
kuma shifidar da ya kwanta sai yatara
tsummokarara yai musu siffar mutum ya
lullu6esu tamkar mutum ne a kwance.
Dama tuni ya daure dokinsa a kofar gida bai
shiga da shi ciki ba saboda dama yasan cewa zai
yi amfani da shi yayin da dare ya raba. Koda
imnal ya dirgo daka kasa daga kan katangar sai
yaje ya kwance dokin ya haye kansa ya
zabureshi ya nufi hanyar da zata kai shi gidan
sarki tuni ya aiyana a ransa ba zai wuce rabin
sa.a ba zaije ya dawo.
32
TASKARNOVELS.COM.NG
Cikin matsanancin gudu imnal ya ci gaba da
tunkarar gidan sarautar sai ya sauya hanya
domin ya 6ullo ta bayan katangar gidan, cikin
kakanin lokaci ya hango katangar gidan da sauri
ya sauko daga kan dokinsa ya daureshi a cikin
bishiyoyi masu duhuwa sannan ya 6uya a cikin
duhuwar, ya kurawa katangar idanu yana kallon
dakaru kuma yana nazarin hanyar da zai bi ya
shiga gidan ba tare da wani ya ganshi ba.
Al'amarin da ya qara tayar da hankalinsa kenan
domin bai ga ta yadda hakan zata iya faruwa ba.
Sai imnal ya dan jima yana nazari sannan
dabara ta fado masa.
Nan take ya hau kan bishiya ya karyo itatuwa
sannan ya sauko ya daddaure itatuwan da
6awon bishiya yayi siffar mutum mutumi ya
dora shi kan dokin sa ya kora shi, dokin ya fita
da gudu ya wuce ta gaban wadannan dakaru
dake tsaitsaye a bayan katangar.
Ko da suka ga mutum a sukwane ya wuce ta
gaban su sai suka bi shi gaba daya da gudu
domin su kure masa gudu, damar da imnal ya
samu kenan ya fito da gudu daga cikin duhuwar
da ya 6uya.. Ko da ya rage saura taku uku ya
33
TASKARNOVELS.COM.NG
riski katangar sai ya daga tsalle yai sama tamkar
tsuntsu ya kama karshen katangar, yana kama
katangar sai ya ji ta da tsananin santsi har
hannun sa ya su6uce zai fado sai ya sake jefa
daya hannun nasa ya kamo katangar ya dafa
kafafun sa sama ya dirga akan katangar, koda ya
leqa qasan katangar izuwa cikin gidan sai ya ga
akwai tsawo sosai in yace zai fada zai iya
karyewa.
A dai dai wannan lokacin ne ya jiyo dawowar
dakarun da suka bi dokin sa sun dawo da gudun
tsiya. Nan fa zuciyar imnal ta buga da karfi
domin ya san cewa babu mamaki sun bi dokin
ba su ga kowa a kan sa ba sai itatuwa, sai baban
su ya ce lallai ma ko waye mai dokin nan ya
raina mana wayo, sai ya daka ma sauran
dakarun tsawa ya ce kowa ya koma malafar sa
ya ci gaba da aiki don akwai alamar zuwan baki
gidan nan.
Imnal ya ringa bin katangar har ya hango wani
tafki a jikin katangar daga cikin gidan sai yayi
sauri zuwa wajen keda wuya sai yaga bakin
tafkin 12dakaru ne suke kaiwa da komowa,
amma sai yayi ta maza ya daka wawan tsalle sai
ya fada cikin tafkin nan ji kake Zundum..
34
TASKARNOVELS.COM.NG
Al'amarin da ya juyo da hankalin kwamandan
dakarun nan sai ya umarce su da su shiga cikin
tafkin su lalubo abin da ya fada su fito da shi.
Nan take suka bi umarninsa suka shiga tafkin
nan.. Koda imnal ya ji dakarun nan sun shigo
cikin ruwan, cikin zafin nama ya samu guda
daga cikin dakarun nan ya suburbudeshi ya
bishi da mazga, nan take ya suma sai ya cire
kayan jikin sa ya sanya masa shi kuma ya sanya
nasa, sakamakon dakarun duk kayan su iri daya
ne. Can sai gaba daya suka yo sama su shaida
ma sugaban ba su ga kowa ba, sai ya ce kowa ya
koma ma6uyar sa imnal ne na karshe ya fito
daga cikin tafkin ya ruga izuwa cikin wani
sashen gidan sarautar. A lokacin da imnal ya fito
daga ruwan ne ya ruga akayi akasi shugaban
dakarun ya waigo kawai sai ya hango imnal ya
ganshi dan karami kamar wada. Al'amarin da ya
ba shi mamaki kenan domin ya san cewa duk
cikin
yaran sa babu gajere ko wada. To ya ya akayi
aka samu wannan? .
A gigice shugaban dakarun ya ruga izuwa bakin
tafkin kawai sai yaga nasa badakaren a saman
35
TASKARNOVELS.COM.NG
ruwa a sume.Shugaban dakarun yayi sauri ya
kwala wa yaransa kira suka firfito daga malafar
su a guje suka taru a gaban tafkin. Ya dubesu
yace lallai muna da baqo a cikin gidan nan ku
bazama neman sa.
Nan take dakarun suka bazu izuwa kowanne
sashe na gidan sunan dube dube.
Lokacin da imnal ya ruga cikin gidan sarautar
yana la6e la6e sai ya rasa hanyar da ya kamata
ya bi saboda bai san 6angaren turakar gimbiya
mulaifa ba. Kawai sai ya bi kan wata
matattakalar bene da gudu. Da zuwa ya ga
dakaru za su gan shi sai ya nemi wuri ya 6uya. A
haka ne yayi ta wuce dakuna barkatar yane leke
leke ta cikin tagoginsu. Wani lokacin sai kaga
saura kiris a ganshi sai kuma ya duka kasa ko ya
shige cikin wani lokon ya 6uya.
Yana cikin haka ne ya hango wani daki kofar sa
a bude kuma fitila a kunne. Koda ya leqa tagar
dakin sai ya hango kuyangin nan guda biyu a
zaune cikin tararrabi idanun su a bushe babu
alamar sunyi barci ko suna jin sa, cikin zafin
nama imnal ya fada dakin ya rufo kofa. Koda
kuyangin nan biyu suka ganshi sai sukayi sauri
36
TASKARNOVELS.COM.NG
su kashe fitilar dakin, cikin rada daya daga cikin
su ta matso dab da shi ta ce hakika ka cika mai
sa.a yaya akayi ka shigo cikin gidan nan ka
tsallake duk tsaron waje da na ciki?
Imnal yayi ajiyar zuciya ya ce ni dai yanzu bani
da lokacin amsa tambaya ,abin da nakeso da ku
kawai kuyi mini jagora izuwa inda turakar
gimbiya take.
Cikin hadin baki suka ce"ta6dijan ka rufa mana
asiri indai ba so kake a hallakamu ba shin ba ka
jin guje gujen dakarun tsaro ne? Nan din nan ma
da kake ciki hadari ne ga rayuwar mu idan aka
shigo aka ganka. Abin da zamu iya yi maka
kawai shine mu baka zanen taswirar gidan nan
mai dauke da nunin inda gimbiya take" Imnal ya
ce na gode da hakan ma maza ku bani.
Cikin rawar jiki daya daga cikin kuyangin ta
dauko taswirar wadda ke zane akan wata
busasshiyar fata ta miqa masa ta ce "Wannan ita
ce gudummawar mu a cikin soyaiyarku kai da
gimbiya"
Koda jin haka sai murna ta kama imnal yace "Ni
kuwa nayi muku alqawari duk ranar da burin
mu ya cika ni da gimbiya sai na 'yantaku na ba
37
TASKARNOVELS.COM.NG
ku kyautar dukiya irin wacce ba.a ta6a baiwa
wani ba"
Gama fadin hakan keda wuya sai suka ji ana
kwankwasa kofar dakin da qarfi ana yi musu
tsawar su bude.
Kafin kuyangin suyi wani yi wani yunkuri sai
suka ga imnal ya daka tsalle sama kamar dan
biri ya naushi saman rufin dakin wanda akayi
shi da katako mai kaurin gaske. Take saman ya
6urma ya fice fit ta cikin sa. Koda imnal ya tsinci
kan sa a saman rufi sai ya ci gaba da gudu akan
dakuna. Ba zato sai yaji ana harbo masa kibiyoyi
cul cul cul ! In ba don karfin gudun sa ba da tuni
an sameshi, sai da yayi tafiya mai tsayi a sama
sannan ya hango wani tafkeken tafkin wanka
mai dauke da ruwa garai garai gunin ban
sha.awa.kwatsam sai ya hango gimbiya Mulaifa
a tsaye a gaban tafkinkwatsam sai ya hango
gimbiya mulaifa a tsaye a gaban tafkin ta daga
kai sama tana duba madubi.
Koda imnal yaga babu kowa a kusada ita sai ya
yadako tsalle ya fado cikin tafkin kafin ya fito
daga tafkin tuni itama ta daka tsalle ta biyoshi
ciki kawai saita danna shi izuwa kasan tafkin
38
TASKARNOVELS.COM.NG
sukayi nutso ta wuce gaba yana biye da ita sai
gasu sun biyo wani kwararo sun fito saman
wani sabon tafkin wadda yake tsakiyar cikin
turakarta babu kowa awajen face kuyangi
fitowar keda wuya daga cikin tafkin sai kuyangi
2 suka rugo suka yafa musu mayafan goge jiki
har izuwa wannan lokaci mulaifa bata dubi
fuskar imnal ba balle tace dashi wani abu kuma
fuskarta a murtuke take tamkar wadda aka
aikowa sakon mutuwa.
Al'amarin daya jefa imnal cikin mamaki kenan
amma sai yayi shiru baice komai ba bayan an
gama tsame lemar dake cikinsu sai Mulaifa ta
sake kama hannun imnal zuwa dakin baccinta
da zuwa sai dukkanin kuyangin da suke ciki
suka fito waje suka rufo kofa nan take Mulaifa ta
sharawa imnal mari ta fashe da kuka ta
rungumeshi tana mai cewa saboda mai zaka
saida rayuwarka kace sai kazo ka ganni a
wannan dare, shin mun rabune har abada
baxamu sake saduwa ba inda tsautsayi yasa ka
hallaka da tuni nima na kashe kaina.
Sa'adda imnal yaji wannan batu na mulaifa sai
gabadaya jikin shi yayi sanyi nan take yaji
kaunar mulaifa ta kara mamaye zuciyarsa kawai
39
TASKARNOVELS.COM.NG
saiya janye jikinsa suna masu fuskantar juna
yace yake abin begena kiyi sani cewa sa'adda na
samu labarin halin da kika shiga sbd hukuncin
da aka yanke min sai hankalina ya dugunzuma,
naji bazan iya yin komai ba sai nazo na ganki
burina na ganki da idanuna koda kibiyoyi dubu
zasu nutse a cikin gangar jikina, sa'adda imnal
yazo nan a zancen sai mulaifa ta sake
rungumeshi cikin tsananin farin ciki tana mai
cewa tabbas kaine zaka zamo abokin rayuwata
gama fadin hakan keda wuya sai sukaji Sarki
Maharaz na kwankwasa kofa yana cewa a bude
alamarin daya dugunzuma hankalin imnal da
kuyangun ita kuwa mulaifa ko a jikin ta kawai
saita dafa imnal da dan yatsanta guda na hagu
take imnal ya rikide yazamo kofin zinare irin
wadda ake saka furanyi aciki faruwar hakan
keda wuya sai mulaifa ta umarci kuyangin nata
su bude kofar. Sarki maharaz ya shigo a fusace
yana haki nan take ya kama kalle-kalle yana
nazarin ko wace kusurwa batareda yace komai
ba. daga can sai Mulaifa ta duci sarki tace babu
wani bako daya shigo wajena koda jin haka sai
sarki maharaz yayi murmushi ya matsa dab da
Mulaifa ya dafa kafadunta yace yake yata a iya
sanina baki taba min karya ba ashe za'a wayi
40
TASKARNOVELS.COM.NG
garin ranar da zaki min karya saboda soyayya
inaso kisani cewa na fahimci akwai soyayya
tsakanin ki da imnal dan sarkin yaki tabbas
shina nake zargi da shigowa gidan nan ahalin
yanzu na tura dakaru zuwa gidan sarkin yaki
idan sukaje suka iske baya nan tabbas toh shine
yazo... hukuncin kisane zai tabbata akan shi
maimakon horo.
Koda mulaifa taji haka sai hankalinta ya
dugunzuma amma saita dubi sarki maharaz
batare da nuna wani damuwa ba tace ina mai
tabbatarka imnal na gida a kwance, sarki
maharaz yayi murmushi har ya juya zai fita sai
idanunsa suka kai kan wannan kofin zinaren
sarki maharaz ya kura kofin kurawa kofin idanu
yana nazarinsa, a lokaci ne zuciyar Mulaifa ta
fara bugawa.
Lokacin da sarki maharaz ya kurawa kofin
zinaren nan idanu yana nazarin sa a lokacin
zuciyar Mulaifa ta fara bugawa da karfi bayan
sarki maharaz ya gama nazarin wannan kofin
saiya juyo ya dubi mulaifa yace yaushe kika
samu wannan kofin? Nide asanina bantaba sayo
irinsa ba mulaifa tayi murmushi tace ai
musamman na aika birnin shamrun aka kera
41
TASKARNOVELS.COM.NG
mini shi koda jin haka sai sarki maharaz ya
karisa inda kofin yake ya daukeshi yana mai
jujjuya shi a hanun shi yace amma fah ya bani
sha'awa sosai shin zaki iya bani kyautarsa
mulaifa tayi murmushi tace ya abbana ai komai
kake so daga gareni basai ka tambaya ba dauka
yakamata kayi kawai amma akwai wanda zaifi
dacewa dakai nasa akera maka shi zaizo nan da
kwana Bakwai, yayin da sarki maharaz yaji
wannan magana sai jikinsa yayi sanyi kuma ya
kasayin gardama kawai saiya ajiye kofin sannan
ya sumbaci goshin gimbiya mulaifa ya fice daga
cikin turakar. Fitarsa keda wuya sai kuyangi
suka rufe kofar turakar. ita kuma mulaifa saita
ruga ta dauko wannan kofin zinare nan take ta
karanta wadansu dalamisan tsafi ta tofa akan
kofin faruwar hakan keda wuya sai kofin ya
tarwatse kamar an watsa hoda, sannu a hankali
hodar ta dinga disashewa ta bace bat kawai sai
gimbia mulaifa ta tafi izuwa kan gadonta ta
kwanta domin sai a sannan ne hankalinta ya
kwanta.
Al'amarin imnal kuwa shide kawai ya tsinci
kansa ne kan gadon cikin dakinsa kawai sai yaji
ana magana da mahaifinsa hibru a kofar dakin
ga dukkan alamu ran hibru a bace yake domin
42
TASKARNOVELS.COM.NG
yana magana ne cikin daga murya da fushi
maganar da imnal ya fara ji daga mahaifinsa
itace, yanzu niza ayiwa haka to kusani cewa tun
safe ina tareda dana kuma yanxu haka yana
cikin dakinsa yana barci wata kakkausar murya
tace "Ya shugabana kayi hakuri mu yan aiken
sarki ne dan haka bai kamata kaga laifin mu ba
saboda bin umarni ne, yanzu dolene ka bude
mana mugani idan yana ciki musan amsar daza
muje mugayawa sarki, idan kuma bazaka bude
ba dolene mu bude da kanmu".
Koda jin haka sai hibru yayi ajiyar zuciya yace ai
bama sai takai haka ba.
Nan take ya bude kofar dakin aiko saiga imnal
yanata sharar barci abunsa kamar ma baisan
abinda akeyiba sai jikin dakarun sarki yayi
sanyi babban cikinsu mai kakkausar murya ya
dubi hibru yace ka huta lafiya ya shugabana
kawai saiya juya ya fita daga cikin dakin sauran
dakarun kuma suka rufa masa baya, cikin
hanzari hibru yaje ya kullo kofar gidan sannan
yadawo cikin dakin imnal ya dubi imnal yace
yakai dana tashi muyi magana nasan idanunka
biu kuma tabbas ka fita daga cikin gidan nan
cikin dare.
43
TASKARNOVELS.COM.NG
Koda jin haka sai imnal ya mike zumbur ya
kurawa hibru idanu cikin mamaki sannan ya
sunkuyar da kanshi kasa cikin alamun kunya da
rashin gaskiya.
Koda ganin haka sai hibru yace yakai dana kayi
sani cewa duk wanda ya rigaka kwana dolene ya
rigaka tashi a ka'idar rayuwata duk tsakar dare
nakan farka na duba ko'ina na gidan nan kuma
na fita kofar gida na kwanta, tun kafin a haifeka
nake wannan al'ada kuma mahaifiyar ka
batasan inayi ba, yauma kamar kullum hakan
tafaru kuma dana duba cikin dakinka sai naga
baka nan kuma dana duba waje sai naga babu
dokinka, hakan ya tabbatar min dacewa ka fita
cikin daren nan abinda bansani ba ina katafi?
yanzu na samu amsar inda kaje tunda dakarun
sarki sunzo don su tabbatar da cewa ko kaine
kaje gidan sarki yakai dana mai yasa kake jefa
kanka cikin rigima da tashin hankali mai kajeyi
gidan sarki shin kamanta ne cewa kanada
babban kaifi kuma a gobene za'ayi maka
hukuncinsa.
Sa'adda hibru yazo nan a zancensa sai jikin
imnal yayi sanyi, daga can sai yadago kai cikin
alamun nadama yace yakai abbana ka gafarceni
44
TASKARNOVELS.COM.NG
kayi sani wannan kuskuren danayi bayin kaina
bane zuciya ce ta ribance ni ina mai tabbatar
maka ayanzu nida gimbiya mulaifa bazamu iya
rayuwa ba idan bama tare da juna.
Koda jin wannan batu sai hankalin hibru ya
dugunzuma ya mike tsaye ya juyawa imnal baya
lokacin da idanunsa suka ciko da kwalla, imnal
ya mike tsaye ya zagayo gaban hibru ya tsaya
kawai saiya durkusa bisa gwuiwoyinsa ya kama
tuba da neman gafara hibru kuma kama kafadan
imnal yayi suka fuskanci juna a lokacin da
hawaye ke zuba da idanunsu hibru yace yakai
dana bakayi min laifin komai ba kayi sani cewa
in bah soyayya ba da nine sarkin wannan birni
namu, amma saboda na zabi soyayya nayi watsi
da mulki in badan soyayya ba da maxan jiya
guda uku wato jarumi hulkas mai hular
Lamsara, Kaura Shaddadu na birnin Kufa mai
mashin galilul haras da sadauki Hantaru mai
takobin Saiful Lujara da basu mutu a banza ba
tabbas soyayya tushen wahala ce sai mai sa'a da
rabo ke tsallake shaukin cikinta ina tsoron kada
rayuwar ka ta kare irin yadda tawa takare da
kuma yadda ta mazan jiya takare, ya kai dana
kayi sani cewa na ziyarci bokaye da dama kuma
sun tabbatar min dacewa zaka samu daukaka
45
TASKARNOVELS.COM.NG
anan gaba. Da wannan furuci nake maka
sallama sai ka je ka kwanta ka rintsa muga
abinda zai faru dakai gobe, gama fadin hakan
keda wuya sai hibru yaja kofar dakin ya rufe
Imnal ya koma kan gadonsa ya kwanta.
Tab! Gaskiya nima fa na fara tsorata da sha'anin
soyayya dan haka zan ajiye dukkan wasu
kalamaina na soyayya a wajen guda tunda ga
jarumai ma masu dakakkiyar zuciya sun mutu a
banza saboda tafarkin soyayya ballantana mu
, amman dai wace irin shawara zaku bani
shin na cigaba da soyayya ko kuma na hakura
da ita gudun kada abinda ya faru da mazan jiya
ya faru da ni.
Shin kana bukatar wani littafi na yaki kawai
tuntubeni ta wannan Number ko kuma kayi
mani magana da profile dina 08138873799.
Zan ci gaba.
46
TASKARNOVELS.COM.NG
MAZAN JIYA
Littafi Na Daya (1)
Part D
Marubuci: Abdulaziz Sani M/Gini
Typing: Abubakar Saleh AlQuyraemey
Al'amarin sarki hibru kuwa tunda duku dukun
safiya ya shirya abincin kalaci ya shiga dakin
imnal sai ya iske shi acikin mafarki har yana
surutai a fili, ba komai yake ambato ba face
sunan gimbiya Mulaifa yana fadan kalamomin
soyayya. Hibru ya daki kafar imnal yana mai
daka mishi tsawa yace mai kakeyi har yanzu
baka tashi ba, to kasani saura kiris mu makara
zuwa fada, kashirya ka sameni a falo muyi
kalaci, gama fadin hakan keda wuya sai hibru ya
juya ya fita, shiko imnal sai yayi sauri ya kimtsa
ya riski hibru a falo sukayi kalace sannan suka
fita kofar gida domin su tafi izuwa fada. Da
fitowarsu sai hibru ya shiga cikin bsuma ya
kamo dokinsa da nufin su hau tunda na imnal
baya nan, har sun yunkara zasu hau sai imnal ya
47
TASKARNOVELS.COM.NG
hango nashi dokin ya tafo da gudu shi kadai,
cikin gaggawa imnal ya rugo ya riske shi kawai
sai yaga wasika a karkashin siddin dokin cikin
zafin nama ya zare wasikar ya boyeta acikin
rigar sa saboda kar hibru ya gani, nan take
imnal ya hau kan dokin shi shima hibru hau kan
nashi suka tafi fada.
Fada ta cika makil babu abunda mutum zai gani
sai kawunan bil'adama lokacin da hibru da
imnal suka shigo cikin fadan kowa ya gama
halatta har sarki kuwa sai da yazo, kuma a
wannnan lokaci shi ake jira a hankali suka
cigaba da tafiya bisa kafafunsu suka durfafi inda
sarki yake. Sarki maharaz da gimbiya Mulaifa na
zanne sun zubawa su hibru idanu shi dai sarki
maharaz fuskar sa acike takeda murmushi
amma na mugunta ita kuwa gimbiya Mulaifa
fuskarta acike take da tsananin damuwa kamar
zata fashe da kuka. Koda hibru da imnal suka zo
dab da karagar sarki sai suka zube kasa suka
kwashi gaisuwa. Sarki maharaz ya amsa
gaisuwan cikin murmushi yana mai kauda kai
ga kallon su kawai saiya dubi wadansu karti
biyu majiya karfi da suke tsaye a gefe daya yayi
musu inkiyar su cika aikin su, nan take kartin
biyu suka kama imnal suka daure shi ajikin
48
TASKARNOVELS.COM.NG
wani murtukeken ice mai gwafa dake kasa
sannan sai suka yayyage rigar jikin imnal da
karfin tsiya suka daga murtukeken icen sama
suka soke shi acikin rami mai zurfi saiga imnal a
sama.
Koda kammala haka sai sarki maharaz ya miki
ya fiskanci gabadayan jama'ar da suke fadan
yace yaku jama'ar darul mahabur, kamar yadda
kuka sani fiye da shekaru talatin da suka gabata
muna bautan mai girma darbuza a kasar nan, ba
ataba samun wanda ya karya doka ba, sai a
wannan karon da imnal dan hibru ya aikata
wannan laifi kusani mai girma darbuza shiya
yanke hukunci dakansa hukuncin kuwa shine za
ayita shara masa bulala har sai fatar jikinsa da
kwoilewa kuma ana zuba mishi gishiri acikin shi
har sai ya suma. Ba za'a kunce shiba sai ya
kwana, kuma babu ci babu sha har na tsawon
kwana uku.
Koda sarki maharaz yazo nan a zancensa sai
gimbiya Mulaifa ta fashe
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 13