Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Bude bakinki ki karbi abincin...." Sallamarsa ta sake ji cikin muryar da ta gama ganewa yanzu. Amatullah na ganinsa ta matsa daga kusa da Asmau har allurar da ake yi mata karin ruwa ta soketa ta tsala ihu. Kukanta yaji har ransa ya matsa da sauri ya gyara mata ya bi Asmau da harara, ita kuwa ta matsa gefe rai a bace. Rarrashin Amatullah yayi sannan ya bata abincin kamar ba soja ba ya mayar da kansa yaro a gabanta. Ko sau daya bai yiwa Asmau magana ba har sai da Amatullah tayi bacci sannan ya tashi. Wayarsa ya miko mata fuskarsa babu alamun wasa ta dan ja da baya. "Karbi mana, numbarki zaki saka min" Tayi kicin kicin da fuska "Na bawa Hajiya" "Na sani, ina son karba saboda na kira 'yata anjima". "Da ka barshi ma, saurin mantuwa gareta kana fita zata mantaka" Ya dan daga gira "ke kadai kike son faruwar hakan banda ni da ita. Nasan bazata manta ni ba." Duk da haka Asmau taki karbar wayar tana adduar ya fita kawai. Tunda an biya musu kudin asibitin ba yau ta fara ba, guduwa zatayi idan dare yayi. Ya tsareta da ido "na fa san ba numbar daidai kika bawa Hajiya ba. Kuma nasan baki kira kowa ba dazu. So ki bani numbar tun girma da arziki kafin na fara bincike a kanki." Duk da ta tsorata harararsa tayi tana magana a dan tsorace "A wane dalili zaka yi bincike a kaina? Daga taimako, dole ne na bada number?" Yadda ya kalleta yasa tayi shiru. Wayarta ya dauka daga kusa da Amatullah ya kunna sannan ya saka numbarsa ya kira tasa wayar. Mayar da wayar yayi inda take ya kama hanyar fita "saura kuma kiyi tunanin cire sim din. Na bar sojoji biyu zasuyi min gadin 'yata don kada ki gudu cikin dare". Gabanta sai da ya fadi da ya fadi haka. Ji tayi kamar yana karanta abinda ke ranta. Ba'a fi minti biyar da fitarsa ba taji wayarta na kara. Da sauri ta dauko a tunaninta Zulaiha ce sai ta sake jin muryarsa. "Baban Safina ne, Colonel Ishaq Muhammad Jikamshi. Na bugo ne don na tabbatar baki cire sim din ba." Bai jira tayi magana ba ya kashe wayar yaja motarsa yayi gaba. Asmau ta tsaya tana kallon wayar cike da mamaki. Tsoro ne ya kamata don da gaske ta yarda ya bar masu tsaronta kada ta fita su bindigeta a banza. A hankali ta sake maimaita sunan nasa. Dama a jikin rigarsa ta ga inda aka rubuta I.M Jikamshi. ABINDA AKE GUDU🙆🏽30 Batul Mamman💖 Sau biyu Asmau na leka waje amma bata ga soja ko daya ba. Ga tsoro kada sai ta fita su tsareta. Haka nan ta hakura zata zauna don dole. Dadin dadawa tana so Amatullah ta kara samun sauki. Sallah tayi ta ci abinci itama sannan ta saka kati daya a wayar ta kira Zulaiha ta fada mata inda suke. Sauran ukun kamata yayi ta sayar dasu ta fada a ranta. **** Col. Ishaq gidansa ya wuce dake Tudun yola. Gidan da a yanzu baya son zama cikinsa saboda abubuwa da dama da yake tuna masa dasu. Dakinsa ya shiga ya dauko wasu takardu ya jira akayi har sallar isha sannan ya tafi gidan Hajiyarsa. Babu kowa a falon lokacin da ya shiga shiyasa ya wuce dakin kaninsa wanda yayi aure kwanakin baya inda yanzu ya mayar nasa. Yayi wanka ya saka kananan kaya sannan ya hau gado ya kwanta. Tunanin Amatullah yake yi yana dan murmushi. Yarinyar ta tsaya masa a rai. Sai kuma ya koma tunanin mamanta. Ji yayi yana son sanin ko ita wace ce. Tunani kala kala ya rinka yi game da ita. Da ya gaji wayarsa ya dauko yana karanta sakonnin da aka turo masa wasu ya share wasu ya bada amsa. Sunan da baiyi tunanin gani bane ya dauki hankalinsa da sauri ya bude sakon. Sallama tayi masa sai hoton baby da ya biyo baya. A kasan hoton ta rubuta _Alhamdulillah mun sami baby boy_. Da kyar Ishaq ya iya hadiyar yawu don tashin hankalin da ya tsinci kansa a ciki. Har wani guntun zazzabi ne ya nemi rufe shi. Ya tashi ya fita zai je wurin Hajiya a daki sai yaji muryarta a falo. Labarai take kallo ita kuma Bilkisu tana zaune a kasa suna hirar sanyin Jos da mai aikin gidan Hinde. Motsinsa yasa Hajiya kallon kofa tace "yaushe ka shigo gidan ban sani ba?" "Dazu ne bayan Isha" Ya zauna akan kujerar kusa da ita tare da mika mata wayar. "Kin gani Badar ta haihu" Hajiya ta kalli su Bilkisu "ku dan bamu wuri" Tashi suka yi Bilkisu sai da ta waiwayo ta kalli Kawunta tana mai tausaya masa. Bayan sun wuce Hajiya ta karbi wayar ta kalli hoton jaririn tayi guntun murmushi "Allah Ya raya" ta gyara zama sosai tana fuskance shi "Mai sunan Alhaji, nasan irin damuwar da kake ciki amma ina so ka sani ba'a yiwa Allah dole. Duk yadda kaso Allah bai nufa zaku kare rayuwarku da Badariyya ba. Duk kuma yadda kuka nemi haihuwa kasan wani baya haifar dan wani." Kansa a kasa yace "na sani Hajiya. Yanzu na tabbatar mun rabu har abada kuma kamar yadda Mami take yawan fada ya tabbata nine bana haihuwa" a yadda yake ji a wannan lokacin gara yayi kuka ko zaiji sauki a ransa. Tausayi ya bata sosai. "A matsayinka na musulmi ka sani cewa babu abinda bawa zai samu a rayuwarsa sai wanda Allah Ya kaddara masa. A bisa tsari da hikimarSa *Yake azurta wasu da 'ya'ya mata, wasu da 'ya'ya maza, wasu Ya hada musu duka biyun, wasu kuma Ya barsu haka* duk inda Allah Ya jarabceka da fadawa kasan babu wayo ko dabararka. Ka zama mai hakuri wata rana zaka ci ribarsa". Ajiyar zuciya yayi ya gamsu da bayananta wanda ya sani dama. "Nagode Hajiya, bari naje na kwanta" "Abinci fa" "Bana jin yunwa. Sai da safe" Tasan halin da zai shiga kenan shiyasa tun tana Jos shekaranjiya da maman Badariyya tayi mata waya ta sanar da ita haihuwar bata fada masa ba. ***** Sake kwanciya yayi yana tuno rayuwarsa ta baya. Auren soyayya suka yi da Badariyya suna zamansu lafiya. Har suka shekara biyu da aure ko batan wata bata taba yi ba. Gashi Allah Yayi shi da son haihuwa tun bata fara damuwa ba ya matsa su je asibiti. An duba su aka tabbatar musu duk lafiyarsu kalau su jira lokaci. A haka har suka yi shekara shida babu labari. Maman Badariyya duk ta damu. Magunguna har da na gargajiya kawo musu take yi amma shiru. Ishaq ya tayar da hankalinsa sosai gashi ko ina suka je sai ace babu matsala. A wani asibitin Jiddah ne ma aka ce kwan haihuwarsa bashi da karfi. Ya shiga damuwa sosai sai gashi Badariyya ke bashi baki. Sun sami shekara goma da aure Mamanta taje har gidan Hajiya ta roketa arzikin asa Ishaq ya saketa tunda anfi tunanin matsalar daga gareshi. Hajiya Lubabatu tayi ta rokonta akan tayi hakuri sai tace to nan da wata shida idan ba'a saki canji ba dole ya saketa. A wannan wata shidan Ishaq yaje asibitoci sunkai takwas. Magani kuwa duk wanda aka bashi sha yake yi. Lokaci na cika har gida Mami tazo ta bukaci ya saki 'yarta. Badariyya kanta tace ko waye da matsalar a cikinsu zasu hakura tunda suna son juna. Mami ta dage abu har kunnen manya a danginsu duka. Ganin al'amarin yana neman lalacewa dole ya yi mata saki daya suka rabu ba don suna so ba. Tana gama iddah da wata biyu yaji labarin aurenta, gashi yanzu har ta haihu ko shekara bata cika ba. Ya amince bashi da rabon ganin dansa. Kannensa duka sun haihu hatta autansu matarsa ciki gareta. A haka bacci ya dauke shi zuciyarsa cunkushe da tunani. ***** Da safe likita yazo ya duba Amatullah yace jikin da sauki amma zasu barta sai gobe a sallamesu. Asmau masa tayi godiya sannan ta tashi tayi wanka ta gogewa Amatullah jiki ta canja mata kaya. "Ama zan fita na siyo miki abinci kinji. Duk wanda ya shigo ki ce masa ina bandaki" "Ummi kayya ko, ashe kema kina yi kika ce na dena" Kafin ta iya bata amsa taji tace "yeeey Babana ya dawo" Asmau ta dago kai a kunyace. Karshenta yaji abinda Amatullah ta ce. Yau ma kayan sojan ne a jikinsa sai dai babu fara'a kamar jiya. Duk da haka yayi kyau ga cika ido. Gaishe shi tayi ya wuce bai amsa ba. Wani mutum ne ya shigo da kwandon abinci ya gaisheta ya ajiye a gefe ya fita. Col. Ishaq yana zaune akan kujera yana yiwa Amatullah wasa da tambayar ya jikinta. Asmau duk ta takura ta rasa abin yi. "Ki zuba mata abinci mana idan ke baki jin yunwa." Wai mutumin nan ina ruwansa da ita ne. Me yasa ya kara dawowa ma. Ta danyi tsaki a hankali sannan ta hada abincin ta zauna a daya gefen zata bawa Amatullah ya miko mata hannu alamun ta bashi plate din. "Kema ki zuba kici". Gefe kawai ta ja tana kallon ikon Allah. A baki ya rinka ciyar da Amatullah tana ta yi masa surutu. Asmau tana satar kallonsa. "Abinci nace ki zuba ba kallona ba" Ya Salaam! Ba karamar kunya taji ba ta tashi da sauri ta zuba abincin ta dawo tana tsakura da cokali. Ya tashi saboda ya fuskanci kunyarsa take ji. "Safina bari na je naga likitan da ya dubaki na dawo" Fita yayi ko waige babu. Asmau ta tuttura abincin kada ya dawo ya sameta. ***** Tambayoyi ya yiwa likitan game da ciwon Amatullah. Da ya fito ya tsaya bata lokaci don ya bata damar gama cin abincin. Gara da Allah Yasa yayi tunanin kawo musu abincinsa da yake tafiya office dashi ba don haka ba don ganganci fita zata yi ta bar yarinya ita kadai a daki. Wasu na nema ido rufe ita ta samu bata rike da kyau ba. Kafin ya dawo ta gama ta dauke plates din ta dauraye a toilet. Ya shigo yayi mata alama da ta fito waje. Darajar girmansa da take gani da tsoronsa da take ji a yanzu yasa ta fita. Ta tsaya can gefe ta sunkuyar da kanta. "Da ban zo ba sai ki fita ki Safina ita kadai a daki? Kuma shine harda koya mata karya. Allah kadai Yasan me kike koya mata kafin yanzu" Taji haushin maganarsa ta dago kai zata yi masa rashin kunya "ina ruwanka da abinda nake koya mata". Yanayin kallon da yayi mata kadai yasa ta kawar da kanta gefe "Ni kike fadawa haka?" Da wadanda ke karkashinsa zasu ji abinda ta fada kila idan ta fara tsallen kwado sai kafarta ta kumbura. Lallai tana da tsaurin ido. idan kayan jikinsa basu yi mata kwarjini ba ai shekarun da yake jin zai bata shabiyar ko sama da haka ya isa yasa taji kunyar idonsa. Da yake rashin kunyar ba dabi'arta bace sai taji babu dadi "kayi hakuri wallahi nagode da taimakon da kuka yi min. Abinda kaji na fada mata ma don babu wanda zai zauna min da ita ne" "Its ok, zan aiko muku da abinci anjima saboda haka kada ki fita ki barta ita kadai." "Nagode" "Har yanzu baki kira kowa a gidanku ba?" "Uhmmm sun ce zasu zo anjima". "Maman Safina kin iya karya" ya fada yana shafa kansa. Asmau taji kamar ta nutse a wurin. Kai wannan mutumi da bin kwaf yake. "Ance gobe za'a sallameku. Na fadawa likitan kada yayi sallamar sai nazo" Ta dan bata rai "saboda me"? "Saboda na kamaki da kyau. Ina son sanin inda zaki kai min 'ya idan kin fita daga nan" Cikin dakin ya koma ya cewa Amatullah zai je office ya dawo. Har da kukanta ita zata bishi. Asmau ta kalleta bayan ya fita a ranta tace ki gama ganinsa da kyau kafin ki dena ganinsa. Da yamma Haj Lubabatu ta saje dawowa har take tambayar Asmau ina iyayenta. Tace mata yanzu suka tafi za'a kawo musu abincin dare. Hajiya tace "ai mun zama daya nasan zamu hadu ko ba yau ba". A zuciyarta tana kokonton ko da gaske sun zo. Babu wani alamar kayan dubiya ga akwatunansu Asmau a gefe wanda ya kamata ace an tafi dasu gida. Da Ishaq ya koma gida da daddare sai da ta fada masa. Yace shima yana son bincike ne a kanta ko don yarinyar da take tare da ita. ***** Sai wurin karfe tara na safe Col. Ishaq ya dawo washegari amma sau biyu yana aika musu da abinci har da kayan kwalama na yara. A lokacin aka basu takardar sallama da magani. Sauran kudin da ake binsu duk yaje ya biya mutumin da ya kawo musu abinci ya kinkimi akwatunanta. Asmau ta dakatar dashi yace Yallabai ne ya saka shi. Dauka kawai yayi zai fita Ishaq ya shigo yace ya wuce dasu gidan Hajiya zasu biyosu a baya. "Bangane ba" Asmau ta fada a tsorace. "Nima namu gidan zam wuce don Allah kace ya ajiye min kayana" "Kinga ki wuce muje akwai tambayoyin da nake so nayi miki daga nan nayi alkawari zan kaiki gidanku da kaina." "Ni bazan bika ba, haka kawai na sani ko....ko..." Yayi murmushi "karasa mana. Ko satar mutane nake yi. Nima tsoron da nake ji kenan ko sato Safina kika yi". Idonta har ya ciko da hawaye tace "wallahi 'yata ce, don Allah ka barmi mu tafi." Fita taga zaiyi daga dakin tace cikin kuka "zanyi maka ihun barawo" Col. Ishaq yayi dariya ya kalli Amatullah "Safina ina babanki?" Ta sake lafewa a jikinsa "ga ka" "To kinji, idan kina son 'yarki ki biyoni. Taimakonki nake son yi albarkacin wannan yarinyar" "Bana son taimakon ka bani 'yata...." tafiyarsa taga yayi dole tabi bayansa tana dan gudu gudu saboda yadda ya soma yi mata nisa. Gaban wata mota mai kyau suka tsaya baka ya bude gaba ya ajiye Amatullah wanda dadi ya isheta sannan ya zagaya ya zauna a wurin dreba. Babu yadda Asmau ta iya dole ta bude baya ta shiga. Suna hada ido ta mudubi ya kashe ido yana murmushi ita kuwa ta murguda masa baki. Shi da Amatullah suke ta hira tana bashi labarin gidansu Umma Zulaiha. Gidan Hajiya ya wuce dasu zuciyar Asmau tana ta daridari. Duk kunya ta dameta haka tabi bayansa suka shiga gidan. Haj Lubabatu ta tarbeta cikin fara'a aka kawo musu abinci. Col. Ishaq yace Bilkisu taje ta yiwa Amatullah wanka. Asmau tabi bayansu da ido yarinya sai murna takeyi ta sake dasu. Hannunsa ya dan kada a gabanta ta dawo daga tunanin da take yi. Yace "Malama Asmau ina ganin ya kamata ki sanar damu ko ke wace ce. Hajiya ma ta fahimci akwai abinda kike boyewa shiyasa na kawoki nan ki fada mana a gabanta." Asmau ta soma hawaye "naso ace yadda muka hadu cikin mutumci mun rabu a haka batare da na tonawa kaina asiri a duk inda na tsinci kaina ba" Hajiya tace "kada kiga kamar mun takuraki, rayuwar Safinatu muke dubawa shiyasa. Idan har baki da wurin zuwa ga yarinya mai lalura lallai kina bukatar taimako" "Ina da iyaye da 'yan uwa. Kuma a garin nan muke" Col Ishaq yace "to me ya rabaki da gida har kika kasa fada musu kuna asibiti"? Asmau tayi ajiyar zuciya sannan ta basu labarin rayuwarta. Tun Haj Lubabatu tana kada kai ha[truncated by WhatsApp] ABINDA AKE GUDU🙆🏽33 Batul Mamman💖 Gidan suna dai ya koma wurin zuwa kallon Asmau da 'yarta. Bayan anyi sallar la'asar ne ta tuna da Col. Ishaq da ya kawo su. Dafe kai tayi saboda tasan bata kyauta ba. Ganin su Umma yasa ta manta da kowa. Shema'u ta fadawa cewa dan matar da suka zo tare shi ya kawosu kuma yana waje. Haj Lubabatu tana jinsu sai dai kunya ta dan fari ta sanya taki tuna mata dashi. Kuma tasan yau rana ce mai matukar mahimmanci a wurin Asmau. Ta hadu da iyayenta da 'yan uwa bayan tsahon lokaci. Shema'u ta sanar da Umma. Nan da nan aka samu food flasks aka hada masa duk wani na'uin abinci na gidan sunan. Jafar aka kira akan su wuce gidansa domin bako ya samu yaci abinci ya huta. Jafar da Sabira suka fito dauke da kayan abincin tare da Asmau dake binsu a baya rike da hannun Amatullah. Zaune yake a gaba ya kwantar da kansa a saman kujera yana sauraron karatun Al'Qur'ani kira'ar Shiek Mishary Rashid. Tausayinsa Asmau taji saboda kunyar abinda tayi masa. Babban mutum kamarsa sun shanya shi a kofar gida. Kuma ta tabbatar baici abinci ba kafin su taho. Yana dawowa daga masallaci ko zama baiyi ba yace su taho kawai. Amatullah ta tafi da gudu ta fada jikinsa. Hakan yasa shi saurin bude ido yana murmushi. Jafar ya karasa gaban motar ya mika masa hannu suka gaisa. "Kayi hakuri don Allah an barka a waje tun dazu. Duk laifin Idon kuka ne da bata fada mana tare kuke ba" Col. Ishaq yace "Idon kuka kuma?" Dariya Jafar yayi kana ganinsa kasan yana cikin farinciki, ya nuna Asmau "ai sunanta kenan." Kyakkyawan murmushi Col. Ishaq yayi yana kada kai "sunan ya dace da ita" Duk akayi dariya sannan Jafar ya fada masa yana son ya biyo shi gidansa domin yaci abinci. Da farko Ishaq ya nuna baya jin yunwa sai da Asmau ta bashi hakuri tare da rokonsa. Yayi yar dariya "Haba Idon kuka, bayan ko introducing dina a wurin yayanki baki ba?" Asmau ta sunkuyar da kanta tana murmushi. Jafar ya sake mika masa hannu murmushinsa yana kara fadada "nima da laifina, sunana Jafar ni Asmau take bi,wannan matata ce Sabira. Idan kaci abinci zamu shiga ciki ka gaisa da duk 'yan uwa." Col. Ishaq ya dafa kan Amatullah "ni kuma sunana Baban Safina" Sabira ta kalli Asmau "kice kawai biki zamu sha kwanan nan" Da sauri Asmau ta daga hannuwa "ba haka bane, Ama ce kawai take kiransa babanta. Sunansa...." Shiru tayi duk suka zuba mata ido. Kunya taji ta kasa fadin sunan sai ta wayance tace ya kamata su tafi saboda kada abincin ya huce. Col. Ishaq ya nuna su shiga motarsa. Jafar ya shiga gaba, Sabira na baya sai Amatullah da ta dage zata bi babanta. Asmau tana tsaye suka ja mota suka tafi ta koma ciki. Hira aka dora daga inda aka tsaya. Shema'u tana goye da Abid din Sabira sai jijjiga shi take kafin Sabirar ta dawo. ***** Mata kamar kara turo su akeyi gidan ana ta zuwa kallon Asmau. Hajjo duk ta matsu su firfita don su samu ayi hira yadda ya kamata da Asmau. Duk dakin da ta shiga mata ne harda wadanda ma basu zo ba da farko. Su Umma ma dai kara kawai suke yi amma duk a matse suke da a basu fili suyi hira da 'yarsu. Da suka ga abu yaki karewa Hajjo da kanta ta shiga falo rai a bace tana mita yadda masu hankali zasu fahimta "Kai jama'a ace anzo taron suna anci tatsotse dinnan anci salak, anci tuwo anci wannan anci wancan amma mata sai tururuwa suke yi. Fisabilillahi ko irin karar nan ta a fita a bamu waje da jikarmu muyi hirar yaushe gamo ya gagara". Wasu nan suka fara jin kunya suka fara hada kayansu suna fita. Sauran da suka yi biris kuwa Hajjo ta rufe idonta ta sallamesu. Umma da Mama dai sunji kunya to amma halinmu na mata wurin saka ido da bin kwaf ya janyo musu. Basu samu gidan yayi daidai ba sai bayan karfe tara. A falo suka zazzauna. Duk 'yan uwan Asmau makusanta suna wurin har da Kawu Garzali ga kuma Haj Lubabatu da danta. A nan aka shiga bada labarin abubuwan da suka gabata. Kowa jikinsa yayi sanyi musamman da suka ga Asmau tana ta kuka da rokon a yafe mata. Suka yi ta kukan wannan kaddara da ta riga fata. Mama Yalwa tace "ai wannan bala'i na waya sai an dage da addua sosai. Akwai alkhairi tattare da ita amma sharrinta a bayyane yake. Kuma kullum kara samar da sabuwa akeyi mai saurin hada mutane da barna." "Haka ne" Haj Lubabatu ta amsa mata. " Sai kiga yara kanana sun yini da waya a hannu ki rasa me suke tattaunawa. Wani lokacin a haka ake haduwa da mutane babu sanayya idan kika yi rashin sa'a ba nagari bane sai su bata maka tarbiya ba tare da ka lura ba. Kwanakin baya jikata dake karatu a nan wurina Bilkisu na fuskanci ta soma nacewa waya fiye da yadda ta saba. Kullum suna hira da wata yarinya da suka hadu a irin group dinnan na waya. Kunsan yanzu tsakanin mace da mace ko maza ma babu abinda ba'ayi. Na kula kawancen ya soma yawa bata da zance sai nata. Abun ya fara bani tsoro. Shabiyun dare sai kiji suna waya sai da nayi mata tas akan hakan." Hajjo tace "ni idan babu hali ba sai a hakura da wayar ba. An fara abu da gaisuwa da sada zumunci a hankali waya ta zama tamkar kana dauke da duniya a tafin hannu. Idan kaki bawa danka waya ma zai fita ya gani a ta wasu." Tattaunawa suka yi ta yi a game da tasirin waya ga al'umma yanzu. Babu babba babu yaro kowa yana da ita kuma ya iya amfani da ita. Jankunne sosai manyan suka yi garesu akan su dubi yadda rayuwar Asmau ta kasance su kula da kawunansu da na yaransu. Kasancewarsu masu aure duk bashi bane domin yanzu hatta mata da mazan aure suna fadawa tarkon waya. Daga group sai kaga matar aure tana mu'amala da 'yar uwarta mace ko namiji mai aure ko mara shi wanda a da ba halinta bane. Sun jima suna hira har shadayan dare tayi basu kula ba sannan Haj Lubabatu da Col. Ishaq suka tashi tafiya. Sun sha godiya a wajen dangin Asmau sosai tare da neman a cigaba da zumunci don yanzu sun zama daya. Fitowa suka yi har bakin mota rakiya Amatullah na makale jikin Col. Ishaq tana bacci. Tashin da yayi zasu fito yasa ta farka ta soma rigimar binsa. Shi kan shi baya son rabuwa da ita. Ana ta lallabata taki yin shiru sai da Asmau ta karbeta ta karfi tana mata fada. Hakura tayi amma bata dena kukan ba. Col. Ishaq ya bata rai sosai saboda fadan da tayiwa Amatullah. Kallon da yake mata ya nuna rashin jindadinsa sai kawai ta sunkuyar da kanta. Bayan tafiyarsu Umar ya tafi kai Mama Yalwa gida shi kuma Abdulhalim ya dauki matarsa da yara suka wuce. Dakin Umma suka koma Amatullah tana ta kuka har sai da Asmau ta goyata duk girmanta don taki yarda da kowa. Daga nan aka soma wata sabuwar hirar har aka zo kan Kawu Rabe Asmau tace shi kadai ne bata gani ba . Shema'u tace "hmmm Asmau mutum babu kyau. Ashe duk tsahon lokacin nan Kawu Rabe wurin wani malami yake zuwa ana rufe bakin Hajjo da su Yaya Abu. Bayan tafiyarki Hajjo tazo ta nemi gafarar Umma har ta bukaci lallai ta dawo gidannan dasu Aina'u idan har ta yafe mata. Shi kuma tace ya soma gyara musu gidan kofar mazugal su koma. A nan aka ji ashe ya dade da siyar da gidan. Ya kuma dage wannan nasa ne. Sai ga ainihin takardun gida Hajjo ta fito dasu, ke magana har za'a shiga kotu don duk su Kawu Garzali sun ce sai ya biyasu kudin gidansu da ya sayar. Wurin aikinsu ma suka kore shi yaci kudin kamfani bai biya ba. Sai da yaga abu ya kure masa ya roki gafarar Umma suka tashi. Yanzu haka yana kauyen Dakasoye can ainihin kauyen babansu Anti Sagira. A nan baban nata ya bashi gona da gida suka zauna tunda bashi da wurin zama. Yanzu da wuya yazo cikin Kano. Zahra dai tayi aure tana Jigawa" Asmau tace "har ya bani tausayi. Da ma Umma ta barshu kawai a nan din" Aina'u tace "tabdi, ko yanzu fa ba wani rissina yayi ba. Tsoron hukuma yaji don da gaske su Yaya Abu sunso a kama shi sai ya biyasu kudin shiyasa ya bada hakuri ya tattara yayi gaba" "To Allah Ya kyauta" duk suka ce Amin. Kan katon gadon Umma suka kwanta su uku sannan aka shimfide yaran akan bargunan banda baby Asmau wadda suke kira Husna. Sai wurin daya da rabi na dare Umma ta baro dakin Hajjo inda su Anti Lami suke. Su ma sum gama tasu hirar. Wani hawaye taji yazo mata da taga 'ya'yanta mata kwance su uku a wuri daya sun takure alamun daya gefen nata ne. Kasa kuma ga yaransu duk sunyi bacci. Maimakon ta kwanta alwala ta dauro tazo tayi sallah tana mai mika godiyarta ga Allah tare da adduar dadin shiriya ga zuri'arta da sauran musulmi. ***** Col. Ishaq yana kwance amma ya kasa bacci. Ya rasa abinda yasa yake ta tunanin Asmau. Can kasan zuciyarsa yace tausayinta ne kawai da kuma son Amatullah. Sai dai kuma ko rufe ido yayi murmushin da tayi bayan komawarta gida yake tunawa sai kawai ya tsinci kansa da yin murmushin shima. ***** Washegari karfe takwas na safe sai ga Jafar da Sabira dauke da kwanunkan abinci. Dankali ta suya da plantain da kwai. Duk da tasan dai a gidan ma za'ayi. Umma ta nuna jindadinta sosai. Shiyasa take son Sabira, barta dai da surutu amma mace ce mai ladabi da sanin ya kamata. Sauran matan masu jini a jika irin su Shemau da Rashida suna kitchen ana ta soye soye. Aina'u ma ta tashi duk da hanata aikin komai ita da Zubaida mai ciki. Asmau kuwa kamar wadda aka saukarwa bacci tana yin sallar asuba ta koma. Ji takeyi rabonta da bacci mai dadi cikim kwanciyar hankali har ta manta. Amatullah ce ta tasheta tana kiran Babanta. Cikin bacci Asmau ta janyota jikinta ta soma rarrashi "Ama nan ne gidanmu fa, na rasa inda kika koyi rigima. Amma idan kika cigaba zan mayar dake wurin Zinaru" Shiru tayi ta kwanta a jikin Asmau daga baya tace "Ummi to zaki kaini naga Babana sai mu dawo?" Asmau ta shafa kanta tana murmushi "in sha Allah zan kaiki kinji. Tashi muje muyi brush a gaishe da su Hajjo" Suna fitowa falo suka tarar da kowa a zaune har su Jafar. Rike take da hannun Amatullah sai suka basu sha'awa. Ita kuwa kallon da suke mata yasa taji kunya ta saki hannunta. Yanzu tunda anzi gida sai ta koyi kara kada ace bata da kunya. Suna zama suka gaishe da kowa Anti Bintu ta cikawa kowannensu plate da abinci. Amatullah ta ware ido sai ta tashi taje tayiwa Asmau rada a kunne. Duk ana kallonta sai suka ga tana share hawaye. Hankalinsu ya tashi Umma tace me ya faru. Kunya tasa Asmau ta kasa fada da wayo Umma tace "Safina zo ki fada min abinda kika fadawa Ummi. Kinga gashi har kin sakata kuka" Duk aka zuba mata ido ita kuwa tace "Ummi in fada?" Murmushi kawai Asmau tayi tace "tambayata tayi taci ko kuwa" Amatullah ta cafe "idan naci Ummi zata ce nayi

Chapter 12 of 23