Yusuf Daboo🥰
☀️ *First Class Writer Assosciasion* ☀️
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation
MARUBUCIYAR
HALIN RAYUWA
SOYAYYA DA ZUMUNTA
SANYIN IDANIYYA
AIMANAH
YANAYIN RAYUWA
AND NOW RASHIN MAHAIFANA
Episode two2️⃣
*Kirkirarran labari ne in wani ɓangare yai dai dai da wani ko wata ai hakuri arashi ne*
Uwaimeer karfe goma saura minti goma ya sauka a filin jirgin saman malam Aminu kano dake nan garin kano baiyi waya da wani cikin kannansa ba bare yace azo a ɗaukesa ya fito yana gyara zaman jakar dake saɓe a bayansa ya fito daga filin jirgin ya karaso bakin titi ya tsare nape ya hau bayan ya gaya masa inda zai kaisa,
Sandai mai nape ɗin ya tsaya dai dai kofar gidansu ya fito ya sallami mai nape ɗin ya tura kofa ya shiga yana sakin murmushi hakanan ya sami kansa cikin wani farin ciki baya kasa gane na maine, sai dai yaji zuciyarsa sam ba daɗi tunawa da yayi Rubina na school, kai tsaye part ɗin Hajiyarsu ya wuce yasan zuwa yanzu Baffah baya gida ya tafi masallaci tun tara na safe yake tafiya masallacin gidan sarki sai bayan anyi sallar juma'a yake dawowa, bai gayawa hajiya yau zai zo ba shi yasa sanda taga shigowarsa sam bata kawo shi bane zai shigo tadaiji murya anyi sallama kamar ta Uwaimeer amma saita bari a Yusuf ne shine mai murya ɗaya data Uwaimeer, har Uwaimeer yaiwa kansa mazauni a ɗaya daga cikin kujerun falon bataɗago ta kallesa ba hankalinta na kan wayarta
"Hajiya mun sameku lafiya"
"Lafiya kalau Yusuf yasu Amnah?" ɗan zaro idanu yayi yana murmushi
"Amnah kuma Hajiyata" da sauri ta ɗago daga danna wayar datake saura kiris wayar ta faɗi kasa ta zaro idanu tana kallon Uwaimeer dake sanye da black jeans da yellow shart
"Uwaimeer kaine da safiyar nan nifa na zata Yusuf ne"
"Gani kam bakon kano na maku shigar safe, so nake na sami sallar juma'a anan shi yasa na biyo jirgin safe"
"Jirgi kuma waya baka kuɗin jirgi Uwaimeer?"
"Daddy ne ya ce inzan tawo nadaina biyo mota na rinka gaya masa zai rinka samin kuɗin jirgi yafi sauki hanya ba kyau"
"Masha Allah ubangiji ya kara haɗa min kanku"
"Amin" Uwaimeer ya faɗa yana mikewa zai bar wajan nata ya wuce can karshan gidan inda nan ne samarin gidan ke rayuwa, tsit yaji alamar ba kowa kowa ya kama gabansa yasa key ya buɗe ɗakinsa bayan ya shiga babban falon dake ɗauke da ɗakunan nasu, ya shiga ɗakinsa da sallama ya wurga jakarsa kan karamin bed ɗinsa kafin yafara rage kayan jikinsa ya shiga wanka, sha ɗaya da rabi na safe ya fito daga ɗakin sanye cikin shaddar maganta colour kalar data matukar dacewa da fatarsa ta haska sa ya kafa hula zannah bukar ya fito yana ɗaura agogon hannu baya kallon gabansa kum yaji yai karo da mutum da sauri ya dafe goshinsa kafin ya ɗago ya kankance idanu zaiyi masifa saiya ga Amjad ne yai saurin rungumesa yana murmushi "Nai missing naka Amjad, mai kake a gida yanzu? ko dai Baffah bai fita masjid ba?"
"Ya fita fa yau lauyewa nai irin banda lafiya ɗin nan harga Allah inason hutu shi Baffa kullum yana tafe daga ya tashi fita kuma sai dai kaji yana kwala min kira Amjad kai Amjad kana ina fito mu tafi, shi yasa tun jiya muka haɗa plan da Mutuniyarka ta faɗawa Baffah bana jin daɗi, shine fa na samu yau ya fita da yaya Mahmud yanzu nasan yana masallaci yana zikiri" kwashewa Amjad da Uwaimeer sukai da dariya kafin Uwaimeer ya yi gaba ya faɗin "Bafa zaka tsare ni da abin dariyar nan naka ba kana nan yanda kake sauri nake yau so nake na ɗakko mutuniyar daga school na kashe bakin mita kullum korafin aikin nan nawa take wai yasa nai nisa ko school na daina kaita bare na ɗakko ta"
"Kunfi kusa ai" Amjad ya faɗa yana kokarin shigewa ɗakinsa, Uwaimeer yai dariya yana fitowa daga falon nasu
RUBINA
Da sauri sauri na haɗo books ɗina na saka su a jaka ganin an kaɗa kararrawar tashi tuni wasu ma sun fita daga class ɗin sai yan tsiraru irina waɗanda bamu gama kwafar home work ba daga allo na saɓa jakata na fito da sauri ina fitowa daga cikin aji kai tsaye na nufo bakin get ɗin makaranta, sai dai turus naja na tsaya ganin motar gidanmu tai kwana cak na tsaya wani takaici ya kume min zuciya, ba yau su Sulaiman suka fara tafiya suna barina ba amma na yau yamin zafi sosai sabida ban da ko naira goma a jakata gaba ɗaya na gama kashe kuɗina da muka fito break hawaye suka zubo min nasa hannu na goge ina tina irin uban tafiyar da zanci da kafata nai kamar na tare nape in gaya masa in munje gida zan karɓo masa na tare guda ɗaya ina gaya masa yai gaba abinsa baima tsaya ya gama jin abinda zance ba, na fara tafiya ina gabda barin layin makarantar naga mota tai parking gefena har tsorata nayi, na raɓa ta gefan kotar nai gaba aka kuma bina ana min horn na tsaya ina hararar motar ya sauke glass ɗin motar ya ɗan leko yana murmushi
"Yaya Meer" na faɗa da wani shauki na irin kai mamakin ganin abin da baka zata ba nai saurin buɗe motar na shiga jikina har rawa yake na rungume jakata ina kallonsa sai kuma kawai na fashe masa da kuka
"Kefa Rubie rigimarki yawa gareta maimakon ki murnar ganina saiki wani zo ki fashe min da kuka"
"To ai kukan na murnar ganinka ne nidai dana sani da banyi addu'ar samun nasararka ba dakayita saka ni a gaba kana min daɗin bakin na tayaka addu'a ka cinye jarabawa gashi nan yanzu an maida ka can nesa inda zamuna watanni bamuga juna ba, da lokacin kana kaduna ai duk weekend kake zuwa yaufa sati bakwai kenan ban ganka ba" ta karashe faɗa tana shashshekar kuka
"To ai naga ma wataran aure zakiyi ma gaba ɗaya kilama ki yi nesa da kano sannan ma saimu fi wata biyu bamuga juna ba"
"Ni bazanyi aura inda bazan rinka ganinka ba, ko kuma ka samo min wani abokinka na aura mu zauna gida ɗaya" Uwaimeer yai dariya "Har yanzu bakida hankali Rubie" yafaɗa yana tashin motar suka fara tafiya "Waima ko ki tambaye ni ya hanya"
"To ai sai munje gida" kai Uwaimeer ya gyaɗa yana murmushi yaci gaba da tukinsa, akan idanun Hajiya Umma Uwaimeer suka shigo gida shida Rubina haka nan taji bata son wannan alakar mai karfi da take tsakanin Uwaimeer da Rubina alakat da tuntuni ta kafa mata ayar tambaya saidai zancan auransa da Raihana ya goge mata duk wani zargi dake ranta amma duk da hakan bazatai sanya ba taje garin kallon ruwa kwaɗo yai mata kafa
"Assagafurullah" ta faɗa a fili jin zuciyarta na kawo mata wani tunani na daban, da sauri ta kirasa a waya lokacin yana kokarin shiga part ɗin su Rubina kiran Hajiyar ya shigo wayarsa, ya tsaya ya ɗaga kiran da sauri hanin Hajiyarsu ke kira "To" kawai yace banji abinda aka gaya masa a wayar ba ya kalleni tareda bani school bag ɗita dake hannunsa ya ce
"Hajiya na kirana bari naje na dawo"
"Tam maizan dafa maka"
"A'a kibari sai anjima in mundawo daga masallaci ki shirya muje tare" da murna ta shiga wajan Ummi dake ta yiwa Khalipha masifa danme zasu tawo su bar Rubina
"Ummi kiyi hakuri ai gani nazo ma, kuma na tabbata ba laifin khalipha bane"
"Allah Anty Rubina baba driver ma saida yayi magana yace baki fito ba shine Yaya Sulaiman yace mu tafi kawai da Baban ma yaki tada motar bakiga zagin dayai masa ba harda cewa saiya saka an koresa an kawo wani driver ɗin"
"Ke maiya zaunar dake a class ɗin har Sulaiman ya rigaki fitowa"
"Na tsaya kwafar homework ne Ummi kiyi hakuri" Ummi ta wuce bedroom ɗinta rai ɓace, ni kuma na shige ɗakina nafara cire Uniform ɗina na nufi loundry na wanke Uniform ɗina dana su Khalipha a washing machine sannan na shiga wanka, bayan na zagaya baya na shanya mana su
HAJIYA UMMA Bayan ta kira Uwaimeer a waya ta sakko daga benanta ta tsaya a a falonta na kasan tana jiran shigowar Uwaimeer ɗin
Rai ɓace ta kalli Uwaimeer daya shigo yanzu "Uwaimeer ban gane ba ban san inda kasa gaba ba akan yarinyar nan wai mai kake nufi ne nace mai kake nufi ne" da mamaki Uwaimeer ya kalli mahaifiyar tasa yana kokarin danne abin dake ransa ya basar yana faɗin
"Bana nufin komai Hajiya kin sani tun Rubina na yarinya nake kulawa da ita, kawai Allah ya sani biyayyarta a gareni yasa nake jinta ta daban a cikin kanne na,"
"Uwaimeer karnaji kar kuma na gani karka kuskura naji wata magana ba kalar wannan daka faɗa min yanzu ba"
"Hajiyata ba wata magana a yanzu ko a gaba bayan wacce na gaya maki yanzu ki rigada kin sani Rubie kanwata ce uba ɗaya kuma ba ita kaɗai ba komai naiwa Rubina ina yiwa Rahma kawai Rahama batada kunya ne shi yasa na sallamata, Rubina nada hankali sosai"
"Hmmm munafuncin banza matsa ka bani waje" yana fitowa daga part ɗin hajiya ya jingina da bango yana sauke numfashi ya ɗora hannunsa ɗaya a kirji ɗayan kuma ya soma goge hawayan daya fara zuba daga cikin idanunsa na tsananin tausayin Rubina da bakin cikin bazai iya cika burin zuciyarsa ba, xuciyarsa tai wani irin rauni raunin daya saka gaba ɗaya jikinsa yin sanyi kalau, jiki ba kwari ya wuce ɓangaransu ya buɗe dakinsa ya shiga ya cire rigarsa ya sakale ya faɗa gado, ya ɗauki wayarsa ya shiga callary ahankali yake bin hotunansa da Rubina da kallo yanayi yana goge hawayan da suka kasa daina zuba daga cikin idanunsa ya ɗakko diary ɗinsa yai rubutu ya maida inda ya ɗakko ya adana ya shiga bayi yai alwala sannan ya fito ya maida rigarsa ya feshe jikinsa da turare ya fito,
na gama shiryawa na saka babban hijab na shiga bedroom ɗin Ummi inda zan ɗakko dadduma, Ummi na gani zaune a gefan gado taja tagumi har batasan da shugowar tawa ba na zaune gefan gadon ta janye hanjunta daga tagumin da tayi ina binta da kallo
"Ummi maine?" na tambayeta
"Ba komai Rubina kaina ke ciwo" Ummi ta bani amsa tana kokarin mikewa ta shiga bayi na ce "Zamuje masallaci da Yaya Uwerr"
"Allah ya kiyaye sai kun dawo ku tafi tareda Usham Allah ya tsare" da to na amsa na fita daga ɗakin bayan na ɗauki dadduma na feshe ta da turare yana kokarin shigowa nima zan fito hannuna rikeda hannun Usham, fuskar Yaya Uweer nagani ba kalar ta ɗazu da muka rabu da shi ba, jikina nima naga yai sanyi kamar yanda nagansa a sanyaye sai da muka ɗau hanyar masjid naji Yayi shuru a motar baya cewa komai sai karatun suratul juma'a daya kunna a motar yana bi a hankali
"Yah Meer" na faɗa ina gyara zama na fuskance shi sosai shi kuma bai amsa kiran danai masa ba sai ɗagowa da yayi ya kalleni sau ɗaya ya maida ganinsa ga tuki nai rau rau kamar zanyi kuka na ce
"Wai Yah Meer maiya sameka bayan mun rabu?"
"Ya isa Rubina dan Allah ki kyale ni karki daɗa min damuwa da wannan ɗan karan surutun naki" baya na ɗanyi na jingina da seat sosai har sannan idanuna na kansa harya juyo muka haɗa idanu yaɗan saki fuska kaɗan ya ce "Yi hakuri kece zaki karamin damuwa raina a ɓace yake wallahi"
"Na sani na fahimci hakan shi yasa ma nai magana koma dai maine kayi hakuri kawai"
"Hmm Rubina bazaki gane ba na daɗe ina hakuri da abin dake damuna a zuciya saina hakurar da zuciyata sai kuma na kasa jurewa kimin addu'a dan Allah ubangiji ya warkar min mikin dake cikin zuciyata, bana zuciya tayi raunin da mikin nan zai fashe fashewarsa tamkar ɗakko dala ba gwammo nai tsakani na da hajiyata"
"To Yayana kaje hospital mana ai anayin hoton heart agani muje kawai hospital inmun dawo daga masjid saisu duba ka," Kai Uwaimeer ya girgiza yana dariya kafin ya ce "Yanzu idan nace bakida hankali sai kiji haushina ce maki akai ciwon da likita zai iya gani ne"
"Yayana wallahi fa ana hoton zuciya zasuga komai duka zasu ga mikin sai su ɗoraka akan magani" dariya sosai Uwaimir yayi harda kwarewa yana cigaba da tukinsa idan ya juyo ya kalle ni saiya kuma kwashewa da dariya zuciyata ta cika fam da bakin ciki na takure waje ɗaya har muka karasa masjid ɗin ban sake kula saba
UMMI
Bayan fitar Rubina daga ɗakin binta kawai tayi da kallo na tsananin tausayin yarinyar harta gujewa ganinta idanun Ummi nakan Rubina fashewa Ummi tayi da kuka sosai ta ɗaga hannu sama tana addu'a cikin kuka ganin lokacin sallah yayi tana nan zaune yasa ta mike tai alwala ta shimfiɗa dadduma ta kabbara sallah, tana nan zaune kan daddumar Aliyu da ɗansa suka shigo ɗakin Aliyu da ɗansa Fauzan suna sanye cikin shadda kala ɗaya hannun Fauzan na rikeda karamim carbi yana ganin Ummi ya karasa wajanta da gudu "Oyoyo mai sunan Baffah ina ka baro Ni'ima ka mata wayo ko ka biyo Abbah kunje masallaci"
"Ummi ina yini" Fauzan ya faɗa bayan ya tsugunna har kasa "Lafiya kalau masoyina ya momynku"
"Tana nan kalau tace na zauna anan zata zo da yamma inta dawo daga wajan saloon"
"To Allah ya kawota lafiya" Ummi ta faɗa tana maida ganinta ga Aliyu daya zauna kan sofa ya dafe kansa da hannu biyu "Kai fa kana lafiya kuwa naganka kamar wanda kwai yafashewa a ciki"
"Ummi tundai kan maganar da na maki jiya ne, zuciyata taki aminda da abinda kika gayamin dan Allah kimin alfarma Ummi dan Allah" yafaɗa yana sakkowa daga kan sofa ya tsugunna a gabanta ya haɗe hannuwa alamar roko Ummi ta ɓata fuska tambar bata taɓa dariya ba ta kankance idanu ta ce
"Aliyu matukar na kuma jin makamancin maganar nan ta jiya daga bakinka zan matukar saɓa maka kuma ta yaya zaka tono asirin dayake rufe taya zaka tone wannan sirrin"
"Ummi kusan kowa na gidan nan yasan da maganar nan yasan ta yanda aka sami yarinyar nan ɗai ɗaikun cikine basu sani ba yara kamar su Khalipha su Rahma amma inaga ko su Twince sun san wannan maganar,"
"To naji kowa ma ya sani amma wanne sharaɗi Baffa ya kafa akai maiya ce duka gaba ɗaya ƴaƴan kowacce a gidan nan ba wanda ya ɗaga maganar sai ta nan sai ta wajena haba Aliyu kamin adalci mana" Aliyu bai sake magana ba ya mike ya fice daga ɗakin Ummi tai tsai tanaji a zuciyarta inama inama inama ace abinda Aliyu yazo da shi zai tabbata da tabbas saita fi kowa farin ciki to amma Baffah fa da wacce fuska zai karɓi maganar Aliyun....
07039793439
[7/24, 4:18 PM] maman sauban: 🌹 *RASHIN MAHAIFANA* 🌹
Story and Writting by
Mamie Yusuf Daboo🥰
☀️ *First Class Writer Assosciasion* ☀️
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation
MARUBUCIYAR
HALIN RAYUWA
SOYAYYA DA ZUMUNTA
SANYIN IDANIYYA
AIMANAH
YANAYIN RAYUWA
AND NOW RASHIN MAHAIFANA
Episode Three3️⃣
*Kirkirarran labari ne in wani Ɗangare yai dai dai da wani ko wata ayi hakuri arashi ne*
Afusace Aliyu ya shiga motarsa ya mata key yabar gidan ko inda Fauzan yake bai sake bi ba, Hannah da kallo ta bisa lokacin daya shigo gida a fusace bata ce masa komai ba saima taɓe baki da tayi taci haba da sabgoginta na gida a kokarinta na ganin ta gama da wuri uku takson fita zataje Zooread wajan kitso, a fusace yakai hannu ya ɗauki wayarsa yana dannawa Daddy babban yayansu kira sau uku yana kira kiran baya tafiya sai hakura yayi ya kwanta jiki duk ba kwari,
Yau ba kamar yanda muka saba zuwa masallaci ba ada nida Yayana in muka tawo daga masallaci bayan an sakko muna ziyartar yan uwa, sosai muke zaga gidajan yayunmu amma yau ko gida ɗaya bamuje ba kai tsaye gida mukayo, tunda muka rabu a wajan adana motoci na gidan ban sake saka yayana a idona ba sai da ya aiko Khalipha da babbar leda da bansan maine a ciki ba yace na kaiwa Anty Raihana, Raihana budurwar Yaya Uwaimir ce sosai suke zuba soyayya kamar baza'a matu ba, ba yau na fara zuwa gidansu Raihana ba kusan ko yaushe in yayi zuwa irin haka ko kuma zai'a kai mata wani abu ni yake aika nake kai mata Raihana ƴar kawar Hajiya Ummah ce kawa kuma aminiya sai dai sam Hajiya da Maman Raihana ba halinsu ɗaya ba Raihana da Mamanta nada mutumci sosai da sosai hannu bibbiyu suke karɓata aduk sanda naje gidan yauma haka suka karɓe ni cikin fara a
"A'a lale da zuwanki kanwarmu Rubie" Raihana ta faɗa sanda nai sallama a gidan, Mama dake zaune kasan bishiya tana shan iska itama murmishin tayi tana amsa gaisuwar danake mata na zaune gefan Maman dake zaune kan karamin carfet ɗin data shimfiɗa
"Wai anan zaki zauna kizo mu shiga ciki"
"A'a Anty Raiha ki barni na zauna nan kusada Mama" Anty Raiha ta zauna itama kusa dani na mika mata ledar da Yayana yace na kawo mata " ta karɓa tana min godiya ta mikawa mamanta mun jima a gidan muna hira nida Anty Raihana dan tanada kirki sosai, dana tashi tafiya 1k Maman Raihana ta bani ta ce nahau nape danaki karɓa Raihana ta karɓo min ta min rakiya har bakin titin ubguwarsu nahau abin hawa ta bawa mai nape ɗin 1k ɗin tace yaban canjin mai nape yaja tana ɗagamin hannu
🔯🔯🔯🔯🔯
Salima tai juyi a gado juyo kukan Amira da tayi a bakin kofa yasa ta duro daga kan ɗan karamin gadon nasu ta zo bakin kofar tana kallon Amira dake kuka, damuwa karara ta bayyana akan Fuskar Salima ta ɗauki yarinyar mai shekaru huɗu ta shiga da ita ɗaki ta zaunar da ita kan katifa tana kallon ta ta ce
"Maine kike kuka da safan nan"
"Mama mama har yanzu bata dawo ba kuma yunwa nakeji" Salima damuwa ta kuma mamaye fuskarta ta figi hijabinta dake ajje jikin kofar ɗakinsu ta fita, gida gida nan makotansu take shiga tana tambayar dan Allah su san mata abinci zata bawa Amira ko wanne gida ta shiga amsa ɗaya wallahi bamu da sauran abinci ranta a ɓace ta dawo gidan ta zauna tana aikawa Mamansu kira a wayarta amma bata shiga ta kuma ɗaukar hijab ta fita ta zaga baya inda matasan unguwarsu ke zama kan dakalin wani gida taji daɗi data hango Ameer zaune cikinsu ana musu daga nesa da mazan kaɗan ta yafito Ameer da hannu alamar yazo tsam ya mike ya karaso inda take tsaye tana wasa da gefan hijab ɗinta tai kasa da kanta
"Salima gani muɗan matsa daga nan gayun can nasan yanzu duk idanunsu na kanmu" batace masa komai ta juya ta soma tafiya yabi bayanta suka zagaya kofar gidansu
"Ameer dan Allah ɗari biyar zaka ranta min mamanmu bata nan har yanzu bata dawo ba inata kiran wayanta a kashe ga Ameerah nata mana kuka" baice komai ba yasa hannu a aljihu ya zaro kuɗi masu yawa daga aljihun nasa ya zaro dubu ɗaya ya mika mata ta karɓa
"Ameer ɗari biyar fa nace"
"Ki karɓi dubu ɗayan kawai kuci ko indomie ce zaku rage kafin Maman ta dawo, kyauta na baki ba rance ba a tsakanina dake ba rance" yana gama faɗar haka ya juya bai koma wajan samarin ba yai hanyar gidansu, itama juyawa tayi tai kamar zata shiga gida amma saita fasa ta nufi kanti tsayawa tai a kofar kantin tana tinanin ta inda zata sai indomie duka kuɗin indomie biyu zai sai mata bazata ishe su ba itada kannanta guda biyu ta juyo tabar kantin ta karasa gidan mai abinci tasiyowa Amira na ɗari biyar ta siyo dankali soyayye na ɗari biyu awara ma ta ɗari biyu ta dawo gida, sanda ta dawo ta tarar kanwarta mai binta Marwa ta tashi ledan abinci ta mikawa Ameerah itada Marwa sukaci dankalin da awaran sukai shuru na tsawon lokaci kafin Marwa ta katse shirun da faɗin
"Yaya Salimah wai ina Mama ta shiga ta manta da mu numberta tun jiya bata shiga yau kwana biyu fa bata nan ta barmu bata damu da halin da muke ciki ba haba dan Allah ko kaji MAMA Ta bari aita binciki lafiyarsu"
"Hakane Marwa muyiwa Mama uzuri da fatan Allah yasa tana lafiya shurunta jiya zuwa yau ya daman duk wannan faɗi tashin da Mama keyi sabida mune kina kallo babanmu ba abinda ya damesa da mu, baisan cinmu da shan mu ba baima damu da yaya muke rayuwa ba mama ce dai itace kullum ke faɗi tashin yanda zamuci muyi rayuwa walahi Marwa nima na fara gajiya da wannan rayuwar tunda muka taso haka baba yake yaki ya canza haka kamar ba ubanmu ba" Marwa shuru tayi tana bin yayartata da kallo tsawon lokaci ba wanda yace komai har sanda sukaji sallamar kaninsu Sani da ya shigo yanzu
"Yane ya mai zan samu ne nifa yunwa nake ji, e yane kun gane ko" Salima ta watsa mashi wani banzan kallo batace komai ba ta mike ta fita yabita da harara ya kai hannunsa mai rike da hankaci baki yaɗan zuka kana ya maida ganinsa ga Marwa
"Ya Anty Marwa mai zan samu ta wajanki ita daman Yaya Salima ba wani mutumchi ta cika ba"
"Sani mai kuwa zaka samu mai zan maka ba rayuwar daka zaɓa kenan ba kullum kana wajan abokai kwana a gidama ka daina ka lalata rayuwarka da shaye shaye haba Sani dan Allah kaiwa kanka faɗa mana kana ɗan karamin yaronka dakai duka duka shekarunka nawa"
"To faɗan me zanwa kaina Yaya Marwa nifa bana shan komai kawai dai ina ɗan zukar wiwi ne ya kin gane ko itama sai naji kaina ya ɗau caji to saina ɗan zuka nayi fresh kin gane kuma ai su jakob ke bani idan nace su ban nacin abinci sai su ce saina ɗan zuka, kin gane ina zuƙa naji fresh to abinci sai wanda nace inaso zasu sai min"
"Hmm Allah ya shiryeka Sani ya ganar dakai gaskiyya ni ba abinda zaka samu yanzu a wajena banda ma ko sisi yau haka na tashi yanzuma sai Yaya Salima ce tasai mana dankali da awara muka ɗan ci muka rage, in zaka je ka nemi sana'a kaje tun wuri ka nema ka daina zuwa makaranta gaba ɗaya kana son ka cuci kanka"
"Kai wai Anty faɗa ma kike min, kai wallahi dan de kece amma da ace wani ne kemin faɗan nan da tuni nakai masa naushi" Sani yafaɗi haka yana wani rangaji irin na bugaggu yasa kai yafita daga gidan Marwa ta goge hawayan dake zubowa daga cikin idanunta.
🔯🔯🔯
Sanda na koma gida daga gidansu Anty Raiha na tambayi Ummi ko yaya Uweer ya shigo tace min bai shigo ba nai shuru ina tunani can dai nacewa Ummi bari na shiga wajan Ummu ta ce "To" na mike na fita kai tsaye part ɗin samarin gidanmu na nufa dake can karshe gidan wajan tsib ba alamar motsi sai bishiyu dake kaɗawa kasancewar yamma tayi sanyin la'asar yafara kaɗawa, na tura kofar babban falon a hankali nabi kofofin ɗakunan nasu da kallo idanuna suka tsaya kan kofar Yaya Uwaimeer na karasa a hankali nai kamar nai knocking na kofar sai kuma dai kurum nasa kai na murɗa handling na kofar na shiga da sallama, saurin ɗagowa yayi yana kallona ya maida kansa ya ɗora kan diary ɗinsa na karasa bakin gadon nasa na zauna ban damu da a yanayin da yake ba, na sake binsa da kallo yana kwance daga shi sai gajeran wando na kakin soji ko singlate babu a jikinsa ganin bai kalli inda nake ba yasa na ce
"Yaya Meer wai dai ko bakada lafiya ne najika shuru baka fito ba"
"Ke fita falo ki jirani na fito" yafaɗa rai ɓace yana aika min da kallon gargaɗi, tsam na mike na fito falon nasu na zauna a ɗaya daga cikin kujerun falon minti biyu tsakani ya fito yana sanye da bakar jallabiya fuskarsa ba walwala ya zauna a kujerar danake kai yakai hannu ya kama kunnena ya ce
"Daga yau karki sake shigo min ɗaki kai tsaye Rubie ki rinka tsayawa iya falon nan ko kuma ki fara neman izinin shiga" na ɗaga kaina ina