Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tayi suka gaisa sannan maryam tace kindai shirya koh?sai a lokacin hamdiyya ta tuna sunyi magana akan zuwan su bash,hamdiyya tace ke wallahi ni nama manta koh Ummee ma ban fadawa bah,tsaki maryam tajaa tace ai nasani shiyasa na kiraki toh sunce bayan sallar jumma'a zasuzo sai ki fadawa Ummee, hamdiyya tace toh shekenan sai anjima daga haka suka kashe wayar.Ummee ce tace me za'a fadamin?hamdiyya tace wai su bashir ne shida abokin shi zasuzo wai akwai maganar da zamuyi,Ummee ta tabe baki tace toh sai kisa hindatu ta gyara part din ajiye baki,hamdiyya tace toh Ummee daga haka ta tashi zuwa fadawa hindatu abunda Ummee tace. ✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah Saleehu Dedicated to hauwa Muhammad (Slim small) 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S✍ 2⃣7⃣➖2⃣8⃣ Bayan ya fita daga part din hajiya ya hadu da Jamal gaishe shi Jamal yayi sannan yace bross ina zuwa ne haka naga kasha kyau haka kamar ba gobe, kodai wurin lucky aunty zaka?harararshi kamal yayi yace ina ruwan ka da inda zanje?Jamal yayi murmushi yace toh inma chan din zakaje ina gaishe ta Allah ya bada sa'a bai jira abunda kamal zaice bah ya tafi yana daria,shima kamal din dariyar yayi ya nufi wurin motar shi.bai tsaya a koh ina bah sai gidan su bash,parking yayi bayan mai gadi yazo ya bude mishi gate sannan ya fito ya shiga cikin gidan kai tsaye saboda gidan ba bakon shi bane,mahaifiyar bash yasamu a parlour tana yiwa mai aikinta magana,karasawa yayi cikin parlour ya nema wuri ya zauna ya gaishe da mahaifiyar bash!!cikin kulawa ta amsa sannan tace idonka kenan kamal?Sosa kai yayi yace ayi hakuri mami,murmushi tayi tace shekenan yasu mum din naka?amsawa yayi da lafiya qalau,sannan tace mishi bashir din yana part dinshi!!Toh yace tare da tashi zuwa part din bash. Fitowar shi daga wanka kenan,koh da kamal ya shiga parlour bayanan saboda haka ya wuce bedroom din nashi,kallon bash ya tsaya yi sannan yace wai dan wulaqanchi sai yanzu kake fitowa daga wanka?dariya bash yayi yace ai kaima dan akwai uzurinka ne shiyasa harka rigani shiryawa amma in badan haka bah da sai nayi zaman jiranka!!!tsaki kamal yajaa yace naji nidai kayi sauri mu tafi kar murasa sallah Dan Allah daga ya fita daga bedroom din ya koma parlour zaman jiran bash. bai wani Dade bah ya fito cikin shadda mai colour din blue cewa kamal yayi toh ka tashi mu tafi sarkin zumudi dan inaga yau in baka hadu da hamdiyya bah kaunan asibiti zakayi,kamal bai kulashi ya mike suka fita saida sukayiwa mami sallama sannan suka tafi.masallachi sukaje sukayi sallar jumma'a sannan suka fito suka kama hanyar zuwa gidan su hamdiyya!!bash ne yace kamal Gaskia inajin tsoron abunda zaije ya dawo kaga mum dinka tace batason auren nan naka da kowa sai da hafsa,toh kar muzo musa yarinyar mutane a cikin damuwa azo ayi aure kuma tazo batajin dadin zaman kaga anyi ba ayiba kenan,ajiyar zuciya kamal ya sauke sannan yace wallahi bash nima inayin wannan tunanin dan koh yau sai da tasake maimaita abun da tace,amma insha Allah babu wani abu marar dadi dazai faru kaga har dad yasan da maganar kuma yace shi dakan shi zai shige mun gaba and then ga hajiya ma tace kar na damu toh shiyasa nadan sake samun hope in mum taga kowa yayi accepting maganar itama zata hakura da maganar hafsa da yardar Allah,bash ya jaa numfashi sannan yace toh Allah ya yarda amma ni inajin tsoro gaskia dan yarinyar nan ta saba kowa a gidan su yana kaunarta kar taje a kaita inda ba'a sonta kaga za'a samu matsala!!kamal yace insha Allah babu matsalar daza'a samu daga haka suka karasa gidan su hamdiyya baba mai gadi ya bude musu gate suka shiga. Parking sukayi sannan bash ya kira Maryam yace tacewa hamdiyya sunzo,Maryam tace ka kirata dear kasan halin bestyn tawa yanzu sai tace meyasa baka kirata da kanka bah!!dariya yayi yace ai wannan bestyn naki sai ke barin kirata maryam tace toh Allah yasa ayi a sa'a murmushi bash yayi yace ameen sannan ya kashe wayar,number hamdiyya yayi dialing bata dade tana ringing bah ta picking call din tare dayin sallama,amsa sallamar yayi suka dan gaisa sannan yace mata gasunan sunzo suna waje,da mamaki tace bada maryam kuka zo bane?bash yayi daria yace eh bada ita bane!!hamdiyya tace toh shekenan ganinan zuwa bash yace toh madam sannan ya kashe wayar, saukowa tayi da hijab dinta purple colour ta same Ummee a kitchen tace Ummee wai sunzo nina zata da maryam fah zasuzo ashe wai su kadai ne,kallon ta Ummee tayi tace toh hajiya ai bani zan baki amsan nan bah kije ki shigar dasu karki barsu a waje sai kizo ki daukan musu ruwan shaa,hamdiyya tace toh Ummee daga haka ta fita zuwa shigar dasu part din sauke baki. Cikin nutsuwa take tafiyar ta,tunda ta fito yake kallon yadda take tafia cike da nutsuwa har ta karasu wurin su!!cikin fara'a ta gaishe su suka amsa sannan tayi musu iso zuwa part din baki,bayan sun zauna tace tana zuwa,ginger mai sanyi ta zuba a cikin jug sannan ta dura akan tray ta saka cups tare da saka snacks akan wani tray daban hindatu ce ta temaka mata ta kai musu itama gaishe su tayi suka amsa sannan ta fita. Wuri ta samu ta zauna sannan ta kalli bash tace ango ai nazata da Amarya zakuzo ashe ku kadai ne ta kareshe maganar tana murmushin ta mai kyau. tunda ta fara maganar kamal ke kallon ta yanajin wani irin sonta yana kara shigar shi.murmushi bash yayi yace ai zuwan namu ne da abokina shiyasa batazo bah!!zaro ido tayi ta kalle bash sannan ta kalli kamal taga ita yake kallo sannan ta juyo kan bash tace toh Allah yasa dai lafiya,bash yace zai dai zama lafiya in har kika aminche wa aboki nah.DA mamaki tasake kallon bash irin tana neman karin bayani sannan tace aminche wa kuma wani irin aminche wa?bash yayi dariya sannan yace hamdiyya tun jiya da aboki nah ya ganki yaji yana sonki so kuma da aure toh shine muka zo muji koh zaki aminche mai?tun daga kanta har kafar ta taji wani abu ya tsirga mata ta kasa cewa komai,saida bash yace hamdiyya re u there?dagowa tayi sannan da kyar tace yeah!!yanzu me kakeso nace?murmushi bash yayi yace sonaki naji aminche warki eh koh a'a amma zan so naji kince eh!!ajiyar zuciya hamdiyya tayi tace toh bash zan danyi tunani,da sauri kamal yace no pls hamdiyya daga jiya zuwa yau ma da kyar nakai saboda son jin mai zaki fada,so pls don't prolonged the chapter just answer me pls and I beg u don't say noo!!ya karasa maganar cikin wata irin murya,kallon shi kawai bash yakeyi yana mamakin daama akwai wacce kamal zai iya roka akan soyayya?duk kansu jira suke taji mai zatace,da kyar ta iya cewa toh Allah ya zaba mana abunda yafi zama alkhairi, dan ita kanta tasan tunda ta ganshi taji ya mata.wata irin ajiyar zuciya kamal ya sauke saida ta dago ta kalle shi,dariya bash yayi sannan yace toh bestyn mu mun gode sosai Allah yasa ayi damu ya kuma tabbatar da alkhairi.saukowa tayi ta zuba musu ginger data kawo musu!! Sosai kamal yasha ginger Dan bah karamin dadi ya mishi bah sannan bash yace toh Mr's man yanzu na sauke nauyin koh?kallon shi kamal yayi yace nadai sauke,dariya bash yayi yace oooo haka ma zakace?kamal yayi daria yace ehmn, bash yace toh yayi kyau sai ka tashi mu tafi inba kauna zakayi bah.kamal yace ai da zan samu na kaunan inaso daga haka shima ya tashi,sallama sukayi da hamdiyya suka nufi kofar fita,har sunkai kofar kamal ya dawo gaban hamdiyya yace nagode sosai da aminchewar ki a gareni inda baki aminche min bah da bansan ya zanyi bah murmushi tayi tace nima na gode,kamal yace gobe zakuje lallen koh?daga kai tayi tare da cewa eh,kamal yace toh sai goben zanzo na kaiki dariya tayi tace a'a zamuje da kanmu.maqe kafada yayi yace a'a ban yarda bah,sosai ya bata dariya sannan tace toh Allah y kaimu shima dariyar yayi yace Ameen!! Yau babu murguda baki koh?kafin ta bashi amsa bash ya shigo yace kaga Mallam in baza ka tafi bah ni kabani key din na tafi,dariya yayi yace Allah ya baka hakuri,sannan suka sakeyin sallama da hamdiyya suka fita zuwa wurin motar su suka shiga suka tafi. ✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah Saleehu Dedicated to hauwa Muhammad (slim small) 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S✍ 2⃣9⃣➖3⃣0⃣ Tattare kayan wurin tayi sannan ta koma cikin part din nasu,Ummee ta tarar a zaune tamata sannu sannan ta wuce kitchen da tray's din ta dawo parlour ta zauna,Ummee tace har sun tafi kenan? Hamdiyya tace eh sun tafi,Ummee tace lafiya dai koh?murmushi hamdiyya tayi tace lafiya lau Ummee!!Ummee ta tabe baki bata sake cewa komai bah.sai chan hamdiyya tace Ummee meza'a dafa ne yau?Ummee tace abban ku yace yau fried rice yakeso sai ayishi kawai da pepper soup na kayan ciki,tashi hamdiyya tayi tace toh barin je nayi la'asar sai nazo na fara daga haka ta wuce zuwa yin sallar.tana shiga wayarta ta fara ringing maryam ta gani picking call din tayi kafin tayi magana maryam tace besty I'm so happy gaskia da kika aminche wa kamal duk da bansan shi sosai bah amma inajin labarin shi a wurin bash yana cewa mutumin kirki ne sosai gaski naji dadi,hamdiyya tace ikon Allah har an kiraki an fadamiki na aminche?Toh niba cewa nayi na aminche bah addua nayi nace Allah zaba mana abunda yafi zama alkhairi, dariya maryam tayi tace ai aminche war kenan kedai Allah ya tabbatar mana da alkhairi hamdiyya tace Ameen,maryam tace gobe kinsan da wuri mai lalle tace muje koh?hamdiyya tace eh nasani dazu zainab ma ta kirani tace wai kawai mu hadu a wurin mai lalle basai mun biya mata bah zataje kawai.maryam tace yawwa hakan ma yayi Allah ya kaimu goben bye!!!! Ajiye wayar tayi ta shiga toilet tayi alwala tazo tayi salla sannan ta sauko kasa,yaya Sadeeq tagani a zaune karasuwa tayi tace bross har ka dawo?dago kanshi yayi yace har ne ma?anfayi la'asar koh danke kina zaune a gida,dariya tayi tace ba haka bane anyway sannu da dawo wa yace yawwa sannu,tashi tayi zata shiga kitchen yace sis!!!dawowa tayi tace gani, ajiyar zuciya ya sauke sannan yace kauna biyu banga Zainab bah koh lafiya?dariya ta farayi ya Sadeeq yace meye kuma abun dariya daga tambaya?tsagaita dariyar tayi ta zauna sannan tace bross yanxu in nace kanason Zainab sai kacemun ba haka bane koh?Sosa kanshi yayi yace yau kam bazan cemiki ba haka bane dan hakan ne,cikin jin dadi tace yawwa koh kaifa yaya ni nasan kana sonta tun tuni ai,kallon ta yayi yace toh naji yanzu ya za'ayi?hamdiyya tace karka damu ni nasan yadda za'ayi zan maka campaign!!dariya yayi yace dats my lil sis nagode miki sosai kinji?shagwabe fuska tayi tace ai dai kasan babu godia tsakanin mu koh?kunnen shi ya kama yace sorry na manta ne,murmushi tayi tace toh barin shiga kitchen yau abba nah yace fried rice yakeso!!ya Sadeeq yace toh yar abba Allah yasa yayi dadi, turo baki tayi tace ai kaima kasan zaiyi dadi dan nafi zainab iya girki bata jira mai zaice bah ta gudu kitchen abun ta. Kana ganin shi kasan yana cikin jin dadi suna tafe suna hira shida bash, bash yace toh frnd ynxu angama da wannan saura kuma amincewar mum!!kallon shi kamal yayi yace yadda aka gama da wannan nasan insha Allah mum ma zata aminche, bash yace toh Allah yasa!!!a haka suka isa gidan su bash, bash yace bazaka shiga bane?a'a yace na matso naje naa fadawa hajiya hamdiyya ta aminche tabe baki bash yayi yace lalle kam!!toh sai munyi magana daga haka ya wuce shima kamal ya wuce gida. A parking space yayi parking,part din hajiya ya wuce kai tsaye cikin jin dadi a parlour ya sameta ita da dad din shi karasawa yayi ya zauna ya gaishe su suka amsa.hajiya ta kalle shi tace kamalu daga ganinka kayi nasara koh?murmushi yayi ya daga kanshi,dad ya kalle su yace nasara kan me?hajiya tayi dariya tace zance yaje daa wai ya tafi da tsoron karta ce bata sonshi amma ni nasan koh hauka takeyi zata aminche.dariya ta basu duk Kansu sannan dad yace toh alhmdll tunda kun shirya kanku in kuma da gaske kukeyi banason maganar nan tajaa wani lokaci sai muje muyi magana da iyayen ta dan banason wata matsala ka daiji abunda mahaifiyar ka take cewa,kamal yace toh dad zan fadamata insha Allah!!hajiya tace toh yadai fi hakan Allah ya tabbatar da alkhairi yasa ayi damu suka amsa da ameen,kamal shida dad dinsa suka tashi suka yiwa hajiya sallama akan zasuje masallachi daga haka suka fita. ✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah Saleehu Dedicated to sadeeyarh chamo (dota)luv u so much dear.... 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S✍ 3⃣1⃣➖3⃣2⃣ Bayan sallar isha'i ya shiga part din mum dinning sukaje cin abinci fa'iza ce tayi serving din su,saida suka gama mum tacewa dad tanason magana dashi,dad yace toh inajinki.gyara zama tayi tace so nakeyi kaje ka nemawa kamal auren Hafsa!!!A zabure kamal ya juyo yana kallon mum din nashi sannan ya kalli dad dinshi yana jira yaji mai zaice,dad yayi murmushi sannan yace haba madam bayan yaro yace ga wacce yakeso amma kuma kice a nema mishi auren wata?cikin bacen rai mum tace oooo wato ni ban isa na zaba mishi matar aure bah kenan?dad yace niba haka nake nufi bah amma kamata yayi a barshi ya aure wacce yakeso tunda dai shi zai zauna da abun shi saboda haka ni na yanke shawarar wacce yakeso ita zai aura.tashe tsaye mum tayi tace koh ya aura wacce yakeso sai ya aura hafsa indai nina haifi shi,kamal da gaba hankalin shi ya gama tashi yace mum Dan Allah kiyi hakuri bani da burin auren Hafsa karki sakani auren ta dole koh na aure ta bazan mata adalci bah!!!harara mum ta watsa mishi tace inka aure ta ka kashe ta bah rashin adalci bah kaji koh daga nan ta wuce abinta ta barsu a zaune. Dad ma tashi yayi ya wuce baice komai bah,Jamal ne ya matso kusa da kamal yace brother pls karka damu kanka akan wannan maganar beside baka ga dad yana bayan ka bah?kama hanun jamal din yayi yace meyasa mum bazata fahimchi cewa hamdiyya ITACE ZABINA bah?fa'iza tace woow wat a nyc name bross gaskia har naji na matso in ganta wallahi,Jamal ne yace yaya wai wacece ita a ina take?ajiyar zuciya kamal ya sauke sannan yace qawar wacce bash zai aura ce.a haka dai qannen nashi suka dinga yi mishi hira fa'iza na cewa Dan Allah ya kaita ta ganta,kamal yace karki damu zaki ganta koh da a bikin bash ne,sai chan kamal ya tashi yace musu shi zaije ya kaunta sallama suka mishi sannan ya fita. Yana zuwa part dinshi ya shiga wanka sannan yazo ya kaunta amma bacci yace bazai yiwu bah,muryar hamdiyya yakeso yaji koh zai dan samu kaunciyar hankali!!wayar shi ya dauko da niyar zai Kira ta sai kuma ya tuna Ashe koh number ta baida shi bai ansa a wurin bash bah, number bash ya shiga kira bata dade tana ringing bah bash ya picking call din yana cewa na hamdiyya me kuma ya faru? nifah ka saka ni a gaba,tsaki kamal yayi yace bash banason iskanci number ta kawai nakeso ka sending mun inaso na kirata, bash yace toh zan turo maka amma daga wannan ka barni na huta tunda dai ba'a kanka aka fara soyayya bah!!!kamal yace kadai ji dashi ina jira pls daga haka ya kashe wayar yana mai sauke numfashi. Kamar yadda suka saba bayan ta gama abincin ta jera akan dinning su abba sun dawo daga nan sukaje masallachi suma sukaje sukayi sallar.bayan sun dawo suka ci abinci sannan suka danyi hira sai kuma bayan after 9pm kowa ya tashi ya tafi ya kaunta,harta shiga dakinta sai kuma ta fito taje dakin Ummee tace mata Ummee gobe fah zamuje lalle insha Allah na manta na sake tuna miki,Ummee tace toh hamdiyya Allah ya kaimu!!!hamdiyya tace ameen saida safe.har ta juya zata fita Ummee ta kira sunan ta dawowa tayi tace gani Ummee,Ummee tace dazu mai su bashir suka zoyi shida abokin shi?sunkuyar da kai tayi ta fara kame-kame,murmushi Ummee tayi mara sauti sannan tace toh tunda bazaki fada bah shekenan amma nidai a kullum ina kara fadamiki ki zama mai kare mutunchin kanki,kizama mai tsoron Allah a duk inda kike, komai dinki kiyi shi tsakaninki da mahaliccin ki dan yana kallon ki bawai ina fada miki haka bane dan baki sani bah a'a inada tunasar dake ne kawai kije Allah ya miki albarka ya kuma kareki.Ameen tace sannan tace insha Allah Ummee bazan taba bari in sabawa ubangija nah bah alhalin ina sane nagode matuqa da addu'arki a gareni da kuma nasihar ki daga haka ta tashi tamata sallama ta fita tana maijin dadin samun uwa ta gari. Bayan ta shiga dakin ta chanxa kayanta zuwa na bacci ta shiga toilet tayi alwala sannan tazo tayi addua ta kaunta, harta Fara yin bacci taji wayarta na ringing ganin batasan number bah yasa batayi picking call din bah har ya tsinke.text ne ya shigo wayar dauka tayi ta fara karantawa!!plss hamdiyya kiyi picking call dina bazan iyayin bacci bah idan banji muryar ki bah kamal ne.tana gama krntw tayi murmushi kamin tayi dialing number har yasake kira,picking call din tayi sannan tayi sallama, wata irin ajiyar zuciya ya sauke har saida taji,cewa yayi nagode sosai da kika picking da bazan iyayin bacci bah kuma inaso nayi,murmushi tayi tace toh ba damuwa dama dan bansan number bane yasa ban dauka bah.shima murmushin yayi yace toh yanxu kinsani Koh?hamdiyya tace eh nasani,hira suka danyi kamar sun dan dade da sanin juna.sannan kamal yace hamdiyya inaso iyayen nah suzo ayi magana akan auren mu,zare ido tayi kamar yana ganinta tace da wuri haka?dariya yayi yace ehmn Koh bakya so nane koh kuma kinaso wani yamin shigar wuri?itama dariyar tayi tace ni bance bah kabari zan fadawa Ummee nah duk abunda tace sai na fadamaka.cewa yayi toh nagode sosai yar gidan Ummee nasan za'a aminche mun ai,murmushi tayi tace toh zan kwanta,shagwabe muryar shi yayi yace har kin gaji dani koh?hamdiyya tace nifah bance haka bah kasan gobe zamu fita kuma da wuri toh shiyasa nakeso na kwanta, kamal yace toh ba damuwa Allah ya kaimu goben sai munzo daukan ku by wat tym?hamdiyya tace around 10am to 10:30am tunda tace muje da wuri,cewa yayi toh Allah y kaimu tace ameen dga haka sukayi sallama kuwa ya kaunta cikin farin ciki. ✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah Saleehu Dedicated dis page to hakuri da juriya online writer's luv u all guy's Allah ya bar zumunchi.. 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S✍ 3⃣3⃣➖3⃣4⃣ Bayan ta tashi tayi sallar asuba bata koma bacci bah karatun Qur'an tayi sanan tayi su azkar.karfe 7:15am ta sauko kitchen ta shiga ta fara hada musu breakfast arish potatoes ita da hindatu suka hadu suka fere sannan suka soya shi da kwai,sannan ta dura tea mai hade da kayan kamshi ta juye shi a flask taje dining ta shirya komai,8:56am sun gama hada komai na breakfast sannan tacewa hindatu zataje tayi wanka kafin su Ummee su fito hindatu tace toh sai kin fito daga haka ta wuce zuwa yin wanka. Wanka tayi tsaf abinta sannan ta fito ta shaafa mai ta shaafa humra kamar yadda takeyi ko yaushe,wardrobe dinta taje ta bude ta ciro wata bakar doguwar riga ta saka sannan ta daura dankwalin rigar,wayarta ta fara ringing dauka tayi zainab tace I hope dai kin tashi?dan nasan halinki!!hamdiyya tace haba aunty nah na tashi,nama rigaki tashi ai.zainab tayi dariya tace toooh fah yau kuma da abinda kika tashi kenan nice auntyn ki?itama dariyar tayi tace eh ai daga yanxu kin zama aunty nah amma ki bari in mun hadu zamuyi maganar,,zainab tace toh naji dan Allah dai ki fito da wuri daga haka suka kashe wayar. Yana taso yake kira bash yaji koh ya shirya amma kuma yana jin tsoron sharrin bash yanzu zai fara cemishi saboda yanason ganin hamdiyya ne yasa ya tashi da wuri.yana cikin tunanin yaji kiran bash ya shigo da sauri ya picking call din daga dayan bangaren bash yace ai dole kayi saurin picking saboda nace kazo mu tafi, toh sunce sun fasa zuwa!!dafe kanshi yyi yace bash kaifa dan iska ne tun dazu nakeso na kiraka amma na hakura saboda banason wannan Sharrin naka,bash yace ai ba sharri bane yanxu dai ka gama shiryawa zanzo na dauke ka,kamal yace toh sai kazo daga haka ya tashe zuwa part din mum. Sanda ya shiga dad dinshi ya samu shida Jamal karasawa yayi shima ya zauna ya gaishe da dad sannan Jamal ma ya gaishe shi,dad yace son ina fatan dai ka fadawa yarinyar maganar da nace da ka fadamata? daga kanshi yayi yace na fadamata dad tace zatayi wa maman ta magana zata fadamin yadda sukayi!!dad yace toh shekenan Allah ya tabbatar da alkhairi Jamal yayi saurin cewa ameen.tashi dad din yayi yace shi zai fita daga haka sukayi sallama ya fita, fa'iza ce ta shigo parlour ta gaishe da kamal ya amsa sannan yace ta hada mishi coffee bayan ya shaa ya cewa fa'iza mum na daki ne?eh tace sannan ya tashi ya nufa dakin mum din nashi,bayan ya gaishe ta amsawa tayi ba tare data kalle shi bah,tashi yayi yace mata zai fita nanma bata koh amsa bah haka ya fita a dakin ya wuce part din hajiya. Gaisawa sukayi sannan tace sai ina kuma?kamal yace sai wurin hamdiyya bude baki hajiya tayi tace lalle ka iya zumudi kamalu da sassafen nan zaka tafi gidan mutane?bata rai yayi yace hajiya wai sau nawa zan fadamiki ba sunana kamalu bane?hajiya tace yau kujimin ja'irin yaro ta haka naga daman fada kuma babu wanda ya isa ya hanani fadan haka eheeee......kafin yayi magana wayar bash ta shigo cikin wayan shi picking call din yayi bash yace kana ina? nazo part din mum tace ka fita,kamal yace ina part din hajiya kazo ku gaisa sai mu tafi bash yace toh ganinan zuwa. Sallama yayi wa mum ya shiga part din hajiya suka gaisa sannan hajiya tace shekenan bashiru dan zakayi aure an daina ganinka toh inkayi auren kuma shekenan koh?dariya yayi yace kai hajiya shekenan kuma fah kikace? abubuwan ne da yawa shiyasa,tabe baki tayi tace toh Allah ya sanya alkhairi.tashi kamal yayi yace ke kowa sai kin bata mishi suna wai bashiru.....hajiya tace eh nace bashiru sai a dakeni.dariya bash yayi yace wa yaisa ya dakeki hajjajo?hajiya tace shi kamalu mana baka ga yadda ya raina ni bah musamman kauna biyun nan dan yaga yyi budurwa.kamal yace kai dalla ka tashi mu tafi kaji inka biye ta wannan tsohowar babu inda zamu,dariya bash yayi ya tashi yace hajiya sai mun dawo!?hajiya tace toh a dawo lafiya kai kuma zaka dawo ka sameni, baice mata komai bah ya kama hanya

Chapter 4 of 12