Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kusa watse a wurin suka koma cikin parlour,chan bash ya tashi ya cewa kamal kazo muje gidan su maryam yatsina fuska yayi yace dga dawo wata zaka wani jani zuwa zance hajiya tayi charab ta chafke zancen da cewa yoo ai gwara shi yanada wacce zaiyi zancen da ita Kai kuma fah?tashi yayi yace wa bash mu tafi kaji kar wannan matar ta cinyeni daga dawo wata,daria bash yayi yawa su mum sallama suka fita abinsu zuwa gidan su maryam. WANENE KAMAL??? Kamal Muhammad usman shine cikakken sunan shi asalin iyayen su yan garin zamfara ne.mahaifin kamal babban dan siyasa ne a Nigeria yarike mukamai da dama a Nigeria yayin da kamal kuma babban architecture ne da akeji dashi a Nigeria wani aiki wajeyi a India na 6mnt Wanda dawo warshi kenan!! Kamal shine 1st born a cikin gidan su yanada qanne biyu Jamal sai kuma fa'iza.kamal zaikai akalla shekaru 29 sai kuma qaninin shi dazai kai shekaru 25 sai kuma autar su fa'iza mai shekaru 20.kullum acikin magana daya akeyi akan ya fitar da matar aure yace shi har ynxu bai samu matar aure bah wannan shine takaitatacen tarihin kamal. ✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah Saleehu Dedicated to hauwa Muhammad (slim small) My appreciation to u hadiza sardauna tnx alot 4 ur prayer's to me!!!Allah ya bar xumunchi 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S✍ 1⃣3⃣➖1⃣4⃣ Part din mum dinshi ya fara shiga babu kowa a cikin parlour hakan yasa ya shige cikin bedroom dinta nan maa batanan,fitowa yayi daga dakin suka hadu shida fa'iza murmushi tayi tace brother yaushe ka shigo? ynxu yace Mata a takaice sannan yace mum fah? naga bata dakin ta,fa'iza tace tana part din daddy bata dade da zuwa bah ganin baka dawo bah!daga kafadar shi yayi yace ok toh nina wuce gudnyt,fa'iza tace baza ka shiga bah su ganka? hajiya maa sai mita takeyi wai daga dawo warka ka fita,girgiza kai yayi yace wannan matar rjgimarta bazata taba karewa bah inace daa danace bazan je bah tsiya tafaramin shine yanxu zata ce daga dawowa ta nafita Toh Allah y kyauta mata daga haka ya juya ya nufi hanyar fita zuwa part dinshi,daria fa'iza tayi tace yaya kamal kenan shidai komai nasa daban yake itama ta wuce zuwa dakinta. Yana shiga kayan jikin shi ya cire ya daura towel yashiga toilet yayi wankan shi tsaf sannan yayi alwala ya fito yasaka kayan baccin shi yabi lafiyar gado.kasa baccin yayi duk sanda ya rufe idon shi sai sautin muryar ta yadinga dukan kunnuwan shi,rintse idon shi yayi ya bude yace noo!!meye haka yarinyar daa bantaba gani ba meyasa muryar ta zata dinga min yawo a kwakwalwa ta?oooo Allah ka taimake ni.da haka ya cigaba da tunanin wai miye ke shirin faruwa dani ne?ganin ya kasayin baccin yasa ya tashi ya shiga cikin toilet yasake yin alwala yazo ya hau kan sallayar sa yayi nafila sannan ya zauna yana tasbihi,anan kan sallayar ya kaunta bacci ya dauke shi.kiran sallah ne ya tayar dashi alwala yaje yayi yazo yayi raka'ata nul fijir sannan ya wuce masallachi.Tare suka fito da daddy bayan ya gaishe shi daddy ya amsa sannan dad yace jiya sai yaushe ka dawo? munta jiranka amma shiru,sosa kanshi yayi yace after 9pm na shigo babu kowa parlour sai fa'iza nagani daddy yace owk toh yayi kyau a haka suka shiga cikin gdn kamal ya wuce part dinshi tare da yayi wa dad sallama,yana shiga bedroom ya wuce ya kaunta bai dade da kauncia ba bacci mai nauyi ya dauke shi kasan Cewa baccin da bai samu yayi bah. Karfe 10:15am wayar shi ta fara ringing mika hanun shi yayi ya dauka tare da picking call din,bash yace pls karka cemun wai baka tashi bah!tsaki yayi yace wai menene kuma kai kasan duk a gajiye nake jiya daga dawowa nah ka dauke ni zuwa yawo toh miye inban tashi bah?bash yace toh naji amma yanxu Dan Allah ka tashi ka shirya zanzo sai mu tafi kaji?yatsina fuska yayi yace naji daga haka ya katse kiran sannan ya tashi ya shiga toilet.wanka yayi sannan ya fito, shiryawa yayi cikin wasu qananan kaya sannan ya kwashi wayoyin sa ya fita. Part din mummy ya shiga babu kowa a parlour motsin da yaji a kitchen ne yasa ya shiga kitchen din mum yace ta juyo tayu tana kallon sa matsawa kusa da ita yayi ya hugging dinta sannan yace gud mrng mum.amsawa tayi da mrng ya gajiyan hanya yace babu gajia tace toh yayi kyau jiya nata jiranka baka dawo bah kamal yace eh ai na shigo fa'iza tace kina part din daddy toh shine kawai na wuce! Mum tace toh shekenan muje ayi breakfast nasan yanxu dad dinku ya fito yace toh.suna fitowa suka tarar da daddy a parlour itama fa'iza fitowar ta kenan gaisawa sukayi dukka sannan suka nufi dinning suka fara yin breakfast.sai chan kamal yace wai ina hajiya ne koh bata tashe bane?fa'iza tace ta tashe ai tace ta daina zuwa kan dinning cin abinci wai yana bata wahala jiya ma dan zaka dawo ne yasa ka ganta a nan tabe baki yayi yace kai wannan Mata akwai rigima! Dad ne ya harareshi yace kamal banason wulaqanchi uwar tawa ce mai rigima?dariya kamal yayi yace yi hakuri dad ba ita nake nufi bah,daga haka suka gama suka tashi kamal yace barin je wurin hajiya mu gaisa mum ta bishi da harara dauke idon shi yayi kamar bai ganta bah ya fita yana mamakin miyasa mum din nashi takeyin haka. Part din hajiya ya shiga sai kamshe part din yakeyi sallama yayi ya shiga a parlour ya sameta zama yyi suka gaisa sannan tace ya gajian hanya kuma?yace lafiya lau,wayar shi ya dauko yana dannawa hajiya ce ta katse shirun ta cewa kamalu dago kanshi yayi yace nifah nace miki ba sunana kamalu bah,tabe baki tayi tace toh koh ma dai menene sunan ka kai kasani nidai Dan Allah sonake ka fitar da yarinya yar mutunchi kayi aure Dan naga take-taken wannan mahaifiyar taka so take ta hadaka da ja'irar yarinyar chan wama take?da sauri kamal yace wai Hafsa? Hajiya tace yawwa ita.shiru kamal yayi. sannan yace karki damu nikam babu abunda zanyi da Hafsa Allah ya sawake min auren ta hajiya tayi saurin cewa ameen wlh kaidai Amma Dan Allah kayi kayi ka fito da matar aure kaji?kamal yace naji insha Allah karki damu very soon zan kawo miki kishiya. dariya hajiya tayi tace yawwa koh kaifa!!!wayar shi ce tafara ringing picking Call din yayi daga dayan gefen bash yace ka fito mu tafi Dan Allah!!kamal yace baza ka shigo bane inanan part din hajiya,bash yace aa ka fito mu tafi kawai inmun dawo sai na shigo kamal toh shekenan daga haka ya tashi yawa hajiya sallama ya fita. ✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah Saleehu 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S✍ 1⃣1⃣➖1⃣2⃣ Tana shiga dakin ta cire kayanta ta daura towel sannan tashiga brush ta farayi sannan tayi wanka tayi alwala dan lokacin magrib ya kusa fitowa tayi taje gaban mirror ta shaafawa jikin ta mai sannan ta shaafa humra,gaban wardrobe dinta taje ta bude ta dauki sleeping gown pitch colour tasaka wayarta datake kan gado ne ta fara ringing zuwa tayi ta dauki wayan sunan mas'ud data gani ajikin screen din wayan yasa tayi tsaki ta ajiye wayan tace mutum sai shigen nacin tsiya hularta ta dauka ta saka ta fita daga dakin. A parlour ta tarar dasu a zaune harda abban ta shima lokacin ya dawo wurin shi ta nufa taje ta zauna kusa dashi tace abba sannu da dawowa ai bansan ka dawo bah!shaafa kanta yayi yace nima yanxu nadawo na tambaya Ummee tace kina wanka,murmushi tayi tace eh nima yanxu na fito.Ummee ce tace idan kun gama gaisuwar ki wuce kici abincin ki kallon Ummee tayi tace Dan Allah Ummee ki bari in kowa yazoci sai nima naci kinsan banason cin abincin ni kadai pls!!!harararta Ummee tayi tace amma dai kinsan bakici Komai bah dai koh? Abba ne yace toh abari in munzo ci saita ci pls,rungeme abba tayi tace shiyasa nake qara sonka Abba nah!!harara Mubarak ya galla mata yace ai zakiga so idan ulcer ta tashi miki.Abba ne ya dakatar dashi da cewa kaga Mubarak banason mugun baki babu wata ulcer dazata tashi insha Allah!! Yaya Sadeeq ne yace ai inbai tsokane taba baya jin dadi sai tayi magana yace ta raina shi,Mubarak ya tashi yace ai dama nasan bayanta zaku goya, abba ne yace toh ina kuma zaka?yace masallachi daga haka ya fice dariya Ummee tayi tace gaskia na kusa fara goyon bayan Mubarak tunda dai dukkan Ku bayan ta kukebi.Abba yayi dariya yacewa Sadeeq tashi mu tafi muma kar lokaci ya kure daga haka suma suka tafi zuwa masallachi suma tashi sukayi zuwa yin sallar. Bata tashi akan sallayar taba saida akayi sallan isha'i itama tayi haka ma su Abba basu dawo bah saida akayi isha'i sannan suka dawo dama wannan itace aladar gdn.kuda ta fito tasamu su abba sun dawo dinning sukaje suka zauna sukaci abincin su mai rai da lafiya towon shinkafa ne miyan kubewa danya da man shanu, hamdiyya ce ta tattara wurin sannan tazo itama ta zauna a cikin parlour. Yaya Sadeeq ne yace wai lil sis yau ina kikaje ne?hamdiyya tace mun kaiwa wasu frnds dinmu IV din bikin Maryam kasan next weak ne bikin,Abba ne yace Allah sarki har lokacin maa yazo Ashe? Hamdiyya tace eh abba yaxo zuwa Thursday ma zaa fara yin event's insha Allah!!Ummee ce tace toh Allah y kaimu suka amsa da ameen.Mubarak ne yace ke kuma yaushe ne auren naki tunda twins dinki next dis Saturday ne daurin auren ta Dan gaskia mun gaji dake duk Wanda yace yana sonki sai kice aa,shagwabe fuska tayi zatayi magana yaya Sadeeq yace kee Dan Allah kyaleshi mu bamu gaji dake bah shidai ne muka gaji dashi dariya tayi tace yawwa yaya nah fadamishi dai tayiwa Mubarak gwalo,Ummee ce tace ayi dai mugani kowa yayi daria haka dai suka cigaba da hirar su cikin soo da kaunar juna har sai zuwa 9pm sannan kowa ya tashi ya tafi zuwa kwanciya. Tana shiga dakinta taji wayarta nata faman ringing a fusace ta nufi wurin wayar a zatunta mas'ud ne ke kiranta still saida ta dauki wayan taga Maryam ce kafin ta picking call din kiran ya katse missed call's guda biyar tagani uku na mas'ud biyu kuma na maryam.kiran Maryam din tayi Maryam na dauka tafara masifa wai ina kika shiga ne anata kiran ki? Hamdiyya tace yi hakuri Ummee wannan irin fada haka kamar wata uwata nabar wayan a daki ne kiyi hakuri,meya faru? Maryam tace dama bashir ne yazo wai gobe mu shirya zai kaimu muga inda zaayi dinner koh wurin ya mana shine yace nakira ki ya fadamiki amma baki dauka bah kuma har yama tafi!!hamdiyya tace oooo sorry zan kirashi Allah y kaimu goben zan fadawa Ummee sai muje din koh?Maryam tace toh shekenan Allah y kaimu amma ki kirashi ki fada mishi munyi magana, hamdiyya tace toh Zan kira shi yanxu daga haka suka kashe wayar. Number bashir ta nemu ta fara kira saida ta kusa yankewa sannan akayi picking call din sallama tayi acikin nutsuwa! kasa amsa sallamar yayi jin wani irin yanayi acikin zuciyaar shi,jin anyi shiru yasa tasake yin sallama dakyar ya iya amsawa ita kuma jin ba muryar bashir bane yasa tace pls bashir nake nema koh yana kusa?nan ma da kyar ya iya cewa aa baya kusa yadan fita Sayan Abu ne Amma in yadawo zan fada mishi hamdiyya tace toh nagode bata tsaya jin mai zaice bah ta katse wayar ta ajiye.kasa cire wayar yayi a kunen shi har bash ya shigomotar yace mr man mekakeyi da waya a kunne kuma? A firgice kamal yace kiranka wata tayi shine na dauka nace ba kanan karbar wayar bash yyi yace oooo hamdiyya kenan!!jin sunan da kamal yayi yasa ya dago kanshi da sauri yace who is she?kallon sa bash yayi da mamaki kasan cewar yasan baya shiga irin abubawan nan sai kuma yace frnd din Maryam ce da muka ta kira dazu bata picking bah any problem? Kafada kamal y daga yace aa.tabe baki bash yyi ya kunna motar suka tafi ya sauke shi a gida akan gobe tare zasu fita sukayi sallama bash shima ya kama hanyar gida. ✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah Saleehu Dedicated to hauwa Muhammad (slim small) 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S✍ 1⃣5⃣➖1⃣6⃣ Sauko wa tayi ta tarar da su Ummee a dinning itama dinning din ta karasa ta gaishe dasu abba da brother's din nata sannan itama ta zauna suka fara'a yin breakfast yaya Sadeeq ne ya fara tashi yace shi ya wuce asibiti yanada operation daxai yi a asibiti kasan cewar shi Dr.sallama yayi musu ya fice!!Ummee ce tace toh kai kuma fah oga naka kajaa ka zauna bazaka fita bah ne?Mubarak yayi murmushi yace yau ina gida Ummee tare zamuyi komai harda girki maa!!daria hamdiyya tasa tace chabdi ashe yau abincin gidan nan bazai ciyo bah gaba daya,A hasalce yace wai yarinyar nan meyasa kika rainani ne?murmushi Abba yayi yace mama nah aida kinyi shiru abinki muga yadda abincin zaiyi koh?Ummee tace mubarak kyalesu kaji yau zaka basu mamaki ai,Mubarak yace yawwa Ummee nah!! Abba ma tashi yayi yace toh muna jiran muga Abun mamakin koh mama nah?hamdiyya tace eh Abba zamu jira mugani,daga hka abba shima yace zai wuce office hamdiyya ce ta daukan masa brief case dinshi suka fita har bakin motar shi ta bude sit din baya tasaka mishi brief case din shima bayan ya shiga daga haka hamdiyya tawa abban nata sallama tare da mishi Allah ya kiyaye hanya ya kuma bada sa'a!! da ameen ya amsa yace Allah y miki albarka mama nah itama ameen din tace ta wuce ta koma cikin gidan, driver ne yaja motar baba Haruna mai gadi ya bude musu suka fita. Sanda ta shiga parlour Mubarak ta tarar a zaune kusa dashi taje ta zauna tace Ummee ta shiga ciki ne?Mubarak yace eh tana dakin ta!!hira sukeyi sama-sama wayar tace ta fara ringing ganin Maryam ce ta dauka tana cewa Amarya a gdn bash ya akayi ne?Maryam tace toooh fah yau kuma sunana kenan?hamdiyya tace dama sunanki kenan, Maryam tace hope dai kin shirya dan bash yace suna hanya amma Zainab tace wai bazata samu zuwa bah Umma zata aike ta wurin kanwar ta.hamdiyya tace owk toh sai kunzo kinga fah banma fadawa Ummee bah amma barin fadamata ynxu Maryam tace toh daga haka suka katse!!hamdiyya ta tashi zuwa dakin Ummee dan fadamata Mubarak yace sai kace akanku aka Fara yin aure kullum sai kun fita, murguda mishi baki hamdiyya tayi tace ina ruwan ka toh wai?tashi yayi ya bita ai da gudu ta kwasa shima kuma bai fasa binnata bah a haka suka shiga cikin dakin Ummee!hamdiyya ta fada kan Ummee data gama sallar walha tana kan sallayar ta Ummee tace wai nikam miye haka kukeyi ne kamar jarirai?kai dama shiyasa kace baza ka aiki bah yau koh?Mubarak yace wallahi Ummee yarinyar nan ta rainani daga Mata magana saita Fara murgudamin bakiUmmee tace ai kai kaja ta rainaka cewa yayi ai dama nasan haka zakice Ummee Amma babu damuwa ke koma zamu hadu daga haka ya fita. Ummee tace Dalla ni daga ni wallahi babu ruwa nah inya rike ki jikin ki zai fadamiki kindai ji nafada miki koh?turo baki tayi tace Ummee nifah nazo na fadamiki su bashir da Maryam zasu zo zamuje ya nuna mana inda za'ayi dinner in wurin ya mana.Ummee ta harareta tace Dan samun wuri harsai wurin ya muku?nidai ayi ayi bikin nan kuwa ma ya huta,hamdiyya tayi dariya tace Ummee ai ankusa Ummee tace toh Allah y kaimu ameen hamdiyya tace sannan ta mike tace barinje na shirya Kansu zo Ummee ta tabe tace toh daga haka hamdiyya ta fita daga dakin. Yana fitowa daga part din hajiya wata mota ta shigo cikin mansion din nasu koh gama parking wacce take motar batayi bah ta bude kofar ta fito da saure ta nufu inda kamal yake,yi yayi kamar bai ganta bah ya cigaba da tafia wurin da bash yyi parking itama nan din tasake nufa ganin baida niyyar tsayawa gashi ya dan mata raata yasa tace kamal!!jiyowa yayi yana mata wani iri kallo.shigar riga da wando tayi dasuka kama mata jikinta sosai karasawa tayi kusa dashi da murmushin ta tace ashe ka dawo kamal shine koh ka fadamin saiji nayi ana cewa ka dawo!wani irin kallo ya mata sannan yace dama kin aiki nine da har zan fadamiki na dawo?shiru tayi kamal yace kinga hafsa ni inada abunyi as u can see daga haka ya wuce ya barta a wajen ya karasa Inda bash ke jiranshi.gaban motar ya bude ya shiga ya zauna bash ne ya kalle shi yace kamal wallahi ba kyau wulaqanchi nasan Hafsa ba irin matan daya dace ace mutum ya aura ba kenan amma at least ka respecting feelings dinta pls koh da bazaka so taba!!hararar shi kamal yayi yace miye amfanin relationship din baza ayi aure bah kai kaga Mallam inzaka jaa motar nan mu tafi kaja mu tafi in kuma bazaka tafi bah in fita in koma ciki,girgiza kai bash yayi yace toh Allah ya kyauta maka daga haka ya jaa motar suka tafi. A kofar gidan su maryam sukayi horn mai gadi ya bude musu suka shiga ciki bash yayi parking a wurin parking space.wayar shi ya dauka ya kira maryam yace mata sunzo tace toh gatanan zuwa daga haka suka katse wayar!! Bayan 10min sai gata tafito wurin motar karasa ta bude baya ta shiga gaishe da kamal tayi ya amsa da cewa laifi lau Amaryar mu ya kike?lafiya lau tace bash ne yace ni bazaki gaishe ni bah koh?hararar shi tayi tace eh din...murmushi yayi yace ba damuwa ai ya jaa motar suka nufa gidan su hamdiyya. Sai chan bash yace kai kuma tun wuri ka nema amaryar ka dan wannan tawa ce ni kadai dan naji kana cewa amaryar Ku,murmushi kamal yayi yace abun gori ne kuma?bash yace ehmn inka ji haushi ka fito da mata yanxu basai anjima bah!!nan ma dariya Kamal yayi yace mai kake ci na baka na zuba kai dai ka tsaya kayi kallo kawai bash yace toh na tsaya Maryam dai dariya kawai take musu a haka suka karasa gidan su hamdiyya.baba haruna ne ya bude musu gate suka shiga Maryam ce tace barinje mu fito bash yace toh!A parlour ta tarar da Ummee da Mubarak a zaune gaishe su tayi Mubarak yace kaga Amarya sai kyali kikeyi daria tayi tace kai yaya Mubarak Ummee tace ke kyale shi kinji hamdiyya na dakin ta maryam tace toh ummee ta tashi ta nufi dakin hamdiyya tana shiga tace I hope dai kin gama?hamdiyya tace eh nagama mutafi ina bashir din?Maryam tace yana waje hamdiyya tace bazai shigo ba su gaisa da Ummee bah?maryam tace hmm kinsan halin shi ai saidai ke kije kice ya shigo wataqila ya shigo din hamdiyya tace toh Bari na gwada dga haka suka saukko parlour hamdiyya tace Ummee zanje na shigo da bashir ku gaisa,Ummee tace toh ki shigo dashi daga haka hamdiyya ta fita. A nutse take tafia a cikin hijab dinta daya kaimata kusan har kasa mai hannu ne hijab din wurin dasu kayi parking ta nufa kamar ance ya dago kanshi bai sauke idon shi a ko ina bah sai akanta Ya salam!!! ya furta a zuciyar shi.harta karaso baisan ta karaso bah gefen bash taje tayi knocking a window bash ya sauke window murmushin ta mai kyau tayi tace ango kasha kamshi shima dariyar yayi yace kai hamdiyya gaisawa sukayi kamal kowa ya kasa dauke Idon shi akanta itama kallon shi tayi ganin yadda yake kallon ta kamar ya samu TV yasa ta murguda mishi baki sannan ta gaishe shi.dariya ce taso ta kufce mishi ganin yadda ta murguda mishi baki sannan a lokaci daya kuma ta gaishe shi,amsawa Yayi sannan tace wa bash ka shigo Ku gaisa da Ummee sannan mu tafi murmushi yayi yace toh bestyn mu yadda kikace itama murmushin tayi tace toh ango.kallon kamal yayi yace Mr's man kazo muje mu gaisa da Ummee shima kamal din Kallon shi yayi tare da cewa kaji tace ni in shiga ne?cewa fah tayi ka shiga ku gaisa da Ummee. Dariya bash yayi yace toh kinji fah hamdiyya wai baki ce ya shiga bah?hamdiyya tace toh ai tare kuke inzaka shiga shima ai zai koh?bash yace toh kazo muje daga haka suka fita a motar hamdiyya na gaba suna binta a baya har suka shiga cikin parlour. A kasa suka zauna suka gaida Ummee amsawa Ummee tayi da fara'a tace ya shirye shirye kuma?bash yace alhmdll!!Ummee tace toh Allah yasan ya alkhairi suka amsa da ameen anan suka gaisa da Mubarak dake zaune shima.hamdiyya ce ta fito daga kitchen da zubo a jug akan tray ta ajiye musu Ummee ta tashi ta haura sama,shima Mubarak ya fita bash ne yace hamdiyya muda zamu tafi miye na kawo mana wani abu?hamdiyya tace ai inbaku shaaa bah babu inda zamuje dariya bash yayi yace ai bata kai nan bah madam tayi daria tazo ta zuba musu suka shaa sannan suka tashi kamal yace toh mun sha ai sai mu tafi koh?hamdiyya tace toh barin kira Ummee kuyi sallama.tare suka sauko da Ummee sannan sukayi sallama suka fita!!suma su maryam din sallama suka mata suka tafi a mota suka tarar dasu shiga sukayi bash yajaa motar suka tafi. ✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah Saleehu Dedicated to hauwa Muhammad (slim small) 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S✍ 1⃣7⃣➖1⃣8⃣ Tunda ya tafi ya barta a wajen ta kasa motsawa saboda tsabar takaici sai chan ta nufi wurin motar ta datayi parking budewa tayi ta shiga ta kunna motar mai gadi ya bude mata gate a guje ta fige motar ta fita daga gidan.da gudun tsiya take tafia zuciyar ta namata zafi ta rasa dalilin da zaisa kamal yana wulaqan tata a rayuwa,itadai tasan tana da kyaun ta dai dai misali kuma tana da dirin jiki shima dai dai misali toh wai meyasa kamal ke mata haka neh wai?wannan tambayan data kewa kanta a halin ynxu babu mai bata amsa!!a haka ta karasa gida cikin bacin rai horn takeyi kamar wata mahaukaciya mai gadi da sauri yazo ya bude mata ta shige nan dinma koh parking mai kyau batayi bah ta kashe motar ta ta bude ta fito, cikin gidan nasu ta shige a parlour ta tarar da mahaifiyar tata Amma koh kallon ta batayi bah ta wuce dakinta kai tsaye. Tunda mahaifiyar tata taga haka tasan akwai abunda ya faru dan tasan tace mata za taje gidan su kamal.tashi tayi tabita dakin nata!akan gado ta sameta a kwance karasawa tayi taje kusa da ita ta zauna tace hafsa meya faru ne haka?koh dai bakiga kamal din bane? Hafsa ta tashi zaune tace ai mummy dama ban ganshi bane da duk da sauqi amma in kinga yadda ya wulaqanta gani wallahi mummy kare ma bazai ci bah.shiru mummy tayi sai chan Hafsa tace nifah mummy ina ganin mu hakura kawai da Kamal dinnan dan

Chapter 2 of 12