Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
data bata bah!!hasali mah ita take hanata zaman lafiya da hajiya,Kamal ne yayi karfin halin tura kofar parlour'n da suke ciki yana cewa "Ai kun makara,lokaci ya wuce muku da bakuyi wannan shirin tunda wuri bah,Allah ba azzalumin kowa bane!!!ni baku bani mamaki bah saboda nasan zaku iya aikata hakan,saidai nasan waccce ta amince muku ita zatayi mamakin hakan" tsuru-tsuru sukayi da ido dan sunsa yau kam karyar su ta gama karewa,nunasu Mum ta shiga yi da dan yatsar ta "Dama nufin ki kenan akaina?na daukeki a matsayin yar uwata wacce muka fito ciki daya ashe ke ba haka bane a ranki!!!ku ficemin daga gani anan tun kafin na kira muku yan sanda" Ta karashe maganar cikin bacin rai.haka suka dunguma suka fita daga gidan ko waccen su babu gwarin gwaiwa.zama Kamal yayi ya dafa kansa yanajin daci a zuciyar shi,kusa dashi Mum taje ta zauna ta dafa kafadar shi tana cewa "kayi hakuri dana yau na gane kuskure nah wallahi,nayi tunanin zabin dana maka shine daidai ashe ba haka bane,na zalunci yarinyar dabata ji bah bata gani bah.nayi maka izinin kaje ka dawo da matarka ni kuma na nema yafiyar ta" "hmmm!!Mum kenan ta ina kike tunanin zan fara zuwa gidan su Hamdiyya?watan ta daya kenan da barin gida nah amma ban taba zuwa nagan tabah koh in kirata inji a wane hali take ciki saboda kin haram tamin yin hakan,Mum meyasa tun farko baki gane cewa Hamdiyya *itace zabina* bah?sai yau danake ganin wataqila lokaci ya kuremun Gaba daya tausayin danta ya gama saka jikin ta yin sanyi,shaafa kanshi tayi tace "Na fahimce ka son ka yafewa mahaifiyar ka data kasa fahimtar ka,na dage akan cewa Hafsa *itace zabina* ashe ni kuma yadda na dauke su ba haka suka dauke nibah!!amma insha Allah nayi mika alqawarin zanyi iya kokari nah na ganin na dawo maka da farin cikin ka gareka,zan samu Dad dinka muyi magana zamuje mu dawo maka da matar ka insha Allah" Yadanji sanyi a ranshi najin zasu dawo mishi da matar shi.daga haka ta sashi ya hada kayan shi su koma gida. ✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah saleehu Dedicated to hauly hyadar(yar tsohowa) 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S✍ 7⃣7⃣➖7⃣8⃣ Bayan dawowar su gida,Dad suka samu a parlour shida su Jamal,kallon Mum yakeyi itama kallon nashi takeyi dan batasan cewa zai dawo a yau bah Jiki a sanyaye ta karasa cikin parlour'n,shima Kamal karasawa yayi ya gaishe da Dad!!!cikin sakin fuska ya amsa mishi sannan ya juya kan Mum "Daga ina kuke haka?keda dan naki" "Daga gidan shi ta bashi amsa a takaice" Kallonta ya tsayayi dan kana ganin ta kasan bata da gaskia a tattare da ita sannan yace "Ina fata dai bawai kinje kinyi wani abun bane koh?dan yadda naga kinaya kamar wata mara gaskia" Sunkuyar da kai tayi tama rasa ta ina zata fara yimishi bayanin abubuwan da suka faru bayan tafiyan shi,saida ya kara cewa inajinki inma wani abun ne ki fadamin tunda wuri kafin lokaci ya kore mana Bata da wani zabi daya wuce ta fadamishi gaskiar abubuwan dasu faru,dan haka bata boye mishi komai bah ta fadamishi duk irin wulaqanchin data dinga yiwa Hamdiyya har kawo yau Mamaki gaba daya ya gama kamashi saida ta gama fadan komai da kusan mintina biyar amma baice komai "Kun kyauta sosai daga ke har dan naki,sau nawa zan fadamiki cewa hajiya Maimunah ba mutuniyar kirki bace?amma kika dauke ni bansan abun danakeyi bah,toh ai yau kin gane gaskia koh?da sun kashe muki dan naki sainaga yadda zakiyi kuma,yanzu sai ku fadamin me kukeso naje nacewa iyayen yarinyar?wata daya a gidan su babu wanda yaje yayi magana da iyayen ta,sam bazasu san cewa bana kasar bah Shiru yayi nawani lokaci yana tunanin ta ina zai fara,matsalolin matar shi sunyi mishi yawa "Wato kai kuma gaka mai uwa koh?duk cin mutuncin da mahaifiyar ka tama yariyar mutane baka gane bah,saidai kawai ka cire hannunka ka sharara mata mari bayan nan kuma baka taba kirana a waya ka fadamin halin da ake ciki bah!!!yanxu ai sai kuje ku basu hakuri in kunga dama,ni kuma har yanzu ban dawowa bah balle inje gidan su dan bansan me zance musu bah!!!idan sunga zasu iya sake baku ita toh,in kuma bazasu bada ita bah duk ku kukasani, bazan taba saka bakina bah akan cewa suyi hakuri su barta ta dawo gidan ka bah sai dai in basu hakurin rashin zuwa nah" Daga haka ya tashi ya fuce daga parlour'n.da sauri Mum ta tashi tabi bayan shi danta dade bataga yayi irin bacin rai haka bah Dafa kansa yayi jin yadda kan nasa yake sarawa ya rasa me yake mishi dadi a yanzu,Dad shine kusan mutum na karshe dayake ganin zai iyayi mishi jagora wurin dawowar matar shi amm kuma shima yace babu ruwan *Cigaban labari* Kasa baccin tayi gaba daya tarasa meyake mata dadi a duniyar nan,tunanin zubar da cikin takeyi dan batajin zata haifawa Kamal yaro saboda yadda yayi banza da al-amarin ta Da sallama suka shigo cikin parlour'n babu kowa a ciki sai karar TV,karayin sallamar sukayi jin an amsa yasasu tsayawa Ummee ce ta sauko daga sama,kallon su takeyi da mamaki ganin Kamal da Mum dinshi,daure wa tayi ta karaso cikin parlour'n sannan tace musu " bismillah!!!ku zauna mana sannun ku da zuwa" Sunji matukar mamakin yadda suka ga Ummee ta tarbe su kamar babu wani abu daya faru,bayan sun gaisa!!!hakuri Mum ta fara bawa Ummee akan abubuwan da suka faru Girgiza kai Ummee tayi tace "Mu bamu kukayi wa laifi bah idan Hamdiyya taga zata iya zama daku a yanzu mu baza mu hanata bah!!!tinda ai ita da kanta ta kawo Kamal tace shi takeso" "Toh dan Allah zamu iya ganinta yanzu?" jin murya daga sama sukayi ana cewa "Baza ku iya bah har abada bazaku sake ganin tabah saboda haka karma ku batawa kanka lokaci" Yaya mubarak ne yake fadan haka yana saukowa daga sama "Mubarak menene haka kuma?kai aka tambaya koh me ina ruwan ka?har yanzu a matsayin matar shi take dan haka baka da dalilin dazai sa kace bazai ga matar shi bah" Wannan kuma Abba ne yake maganar dan tun shigowar su Kamal shima ya shigo yanajin duk abinda ya faru Zama shima yayi suka gaisa da su Mum,sannan Mum ta sake bashi hakuri akan laifin tane "Kamar yadda mahaifiyarta ta fada muku cewa bamu kukayi wa laifi bah wacce kukayi wa laifi ita take da zabin hakura taje ta cigaba da zama daku,dan haka inta yarda toh,in kuma bata yarda bah babu wani abu da zamu iyayi akai" Cewa Ummee yayi data kaisu dakin Hamdiyya tunda bata jin dadi!!ba musu ta tashi su kuma suka bita a baya zuwa dakin Hamdiyya. ✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah saleehu Dedicated dis page to u cwt mmn khalipha!!!Allah ya raya mana khalipha, tnx 4 d luv nd d prayer. *Ina godia a gareku masoya,ina matukar jin dadin addu'arku Allah y barmu tare* 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S 8⃣3⃣➖8⃣4⃣ Ganin babu kowa a dakin ne yasa sukayi tunanin koh an chanza musu wani dakin ne, wata nurse ce datazo wucewa ya tsayar da ita yana tambayan ta ina aka maida yan dakin nan? Bayan ta fadamishi an discharging dinsu mamaki ne ya kamashi ya wuce office din doctor dan ya kara tabbatar da maganar Bayan yayi knocking doctor ya bashi izinin Shiga,wuri ya nuna mishi amma yayi kamar bai gane bah sai cewa dayayi "Pls patient din damu ka kawo ne? naga basa dakin kuma wata nurse tace wai anyi discharging dinsu" "Eh munyi discharging dinsu saboda su suka bukaci hakan kuma munga babu wata matatsala shiyasa" Shiru yayi sannan yayi wa doctor godia ya fito suka kama hanyan zuwa gidan su Hamdiyya A kwance take akan kujera dan taqi ta Shiga cikin dakin ta,Abba ne ya sauko yana cewa "Mama nah maimakon kiyi hakuri ki zauna a asibitin koh da zuwa gobe ne akara ganin yanayin jikin naki amma kikaqi" "Abba ai Naji sauki babu inda yake min ciwo shiyasa,kuma banason zaman asibitin nan wallahi" Tabe baki Ummee tayi sannan tace "Ai duk Sadeeq ne yake biyewa shirman tannan,amma ai dayaci ace koh kwana daya ne tayi" Suna cikin hakan su Mum sukayi sallama tare da shigowa cikin parlour'n,amsa musu sukayi Ummee tace su zauna Wuri suka samu suka zauna sun kasa cewa komai,sai chan Mum tayi qarfin halin cewa "Munje asibitin aka ce wai anyi discharging dinku shine muka biyo nan,Allah ya kara lafiya" Da Amen suka amsa,takaici duk ya gama kama Hamdiyya ganin yadda iyayen nata sukeyi kamar babu abinda ya faru,hakan yasa ta tashi ta fara nufar hanyan dakin ta Da sauri mum ta kira sunan ta "Hamdiyya" Tsayawa tayi batare data jiyo bah,tashi Mum tayi taje kusa da ita "Hamdiyya na rokeki da Allah da kiyi hakuri da abubuwan dasuka faru,nasan ban kyauta bah amma yanzu na gane kuskuren danayi,cikin dayake jikin ki baisan komai bah ina rokan ki dakar ki cire shi" Ummee ce ta kalli Abba shima ya kalle ta dan basu gane inda maganar Mum ta dosa bah,itama Ummee matsowa kusa dasu tayi tace "Meya faru kuma?ai batace zata cire cikin bah,shi miye laifin shi da zakuyi tunanin zata cire?" "Ummee nah cire shi zanyi,bazan haife shi bah" Hawayen dake kokarin gangaru mata ta share sannan ta kalli Mum tace "Babu wata wacce zata so ace surukar ta karuwa ce,kuma zata haifawa danta baby,hakan nan kema nasan bazaki so hakan bah!!!in jika kikeso ai akwai matar dakika aura masa kije wurinta zata baki,ita nasan bah karuwa bace,amma nikam babu abinda zai hanani zubar da ciki......" Bata kai ga karasa maganar bah Ummee ta dauke ta da wani irin mari har saida ta daina gani sosai,sannan tace "Idan nasake jin kin furta irin maganganun nan wallahi zakiga bacin rai wanda baki taba ganin irinshi a rayuwar ki bah!!!shi cikin uban meya miki dazaki ce zaki zubar?" Dafe gefen marin da ummee tayi mata tayi,hawaye na zuba daga idon ta cikin muryar kuka tace "Ummee tunda nayi wayo na tashi dake a cikin gidan nan baki taba cire hannun ki kin dake ni bah sai yau!!!yau din mah akan mutanen dasuka cutar dani a rayuwata...." Kuka ne yaci karfin ta hakan yasa tadanyi shiru,sannan ta goge hawayenta ta matsa kusa da Kamal tace "Kunji dadi ynxu?babu wata kaunciyar hankali dana samu a cikin gidan ka sai tashin hankali,yanzu nazo inda hankali nah ya fara kwanciya amma kuma kun sake dawo kun rushe shi,meyasa kuke da son kanku da yawa ne?Naji zan Haifa maka danka na baka shi dan nasan shi kuke da bukata amma bani bah" Daga haka ta wuce ta barsu a haka duk jikin su a sanyaye,bama kamar Ummee!!!hakuri Mum ta soma basu kamar zatayi kuka "Bakomai hajiya koma kuyi hakuri da abinda ya faru yarinta na damunta,sannan kuma da abubuwan da suka faru,amma nasan mama nah insha Allah komai zai wuce zata gane" Shidai Kamal kamar an dasashi a wurin ji yakeyi kafar shi bazata iya daukan sa bah!!saida Mum ta taba shi sannan tace yazo su tafi Haka suka yi sallama dasu Ummee, Ummee mah ta kara basu hakuri sannan suka tafi Kuka takeyi sosai kamar ranta zai fita,Abba ne ya shigo cikin dakin yaje ya zauna kusa da ita tare da cewa "Mama nah zaman duniya hakuri akeyi,duk wanda kika gani a duniyar nan toh hakuri yakeyi,ba akanki aka fara irin haka bah!!saboda haka inaso kiyi hakuri da yadda rayuwa tazo miki,kinga yau har Ummee dinki tayi fushi dake" Rungume shi tayi sosai sannan tace " Naji Abbanah na gode,dan Allah kabawa Ummee hakuri bazan sake bah wallahi". "Na hakura Hamdiyya kamar yadda Abban ki ya fadamiki akan ki kara hakuri ai dai kinga suda kansu sungane kuskuren su" Haka suka cigaba dayi mata nasiha akan rayuwa harsai da tasamu nutsuwa sannan Ummee ta hada mata ruwan wanka tace taje tayi. ✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah saleehu It's 4 u again dear, khadija Abba(yar rigima)tnx 4 d luv!!!I hrt u alot 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S✍ 8⃣1⃣➖8⃣2⃣ Kamar ya hadiye zuciyar shi yakeji jin takera cikin dake jikinta da bashi da uba,yasan cewa bakin cikin sune yasa ta fadan haka!!!babban abinda yasake tayar musu da hankali shine datace zata zubar da cikin Mubarak yayi saurin samata hannun shi abakin ta,nan take shima jikin sa yayi sanyi dan yasan halin qanwar shi idan tace zatayi abu toh sai tayi shi saidai kuma wani ikon Allah Cigaba tayi da kukan ta kamar cewa akeyi ta kara volume Tare da yaya Sadeeq Ummee suka dawo,da sallama suka shiga dakin Sannan suka ajiye kayan dayake hannun su!!! Yaya Sadeeq suka gaisa dasu Kamal,Ummee ce tace "Wai ke meye nayiwa mutane kuka ne haka?sai wani ciwon yasake kamaki sannan zakiji dadi kohmai kike nufi?kin tsare mutane sai faman rusa kuka kikeyi kamar anyi miki mutuwa" Murmushi yaya Sadeeq yayi yaje ya zauna kusa da ita "Yar gidan Abba meye kuma ya faru?kiyi shiru da kukan haka ba kyau kar kanki yayi miki ciwo,koh akwai inda yake miki ciwo ne?" Kai ta girgiza alamun A'a sannan ta juya musu baya ta cigaba da kukan ta mara sauti Mum ce tace musu zasuje gida zuwa anjima zasu dawo,sannan sukayi sallama suka fita itada Kamal!!!tanajin sun fita ta juyu tacewa yaya Sadeeq "Yaya dan Allah kacewa doctor ya sallame mu wallahi banason zaman wurin, ni babu inda yake min ciwo" Dariya yayi yace "Toh barinje insami doctor din,amma sai kinmun alqawarin kin daina yin kukan nan haka" "Na daina Allah,nidai mutafi" Ummee da Mubarak ne suka tabe baki,shi kuma ya tashi ya tafi wurin doctor!!!hada mata tea Ummee ta farayi batare data tambaye ta bah dan tasan cewa zatace ta koshi "Ki tashi kishanyi tea din nan kafin doctor din yazo" "Ummee ni banajin yunwa wallahi banaso" "Kinsan Allah inbaki tashi kinsha tea din nan bah koh doctor yace mu tafi bazamu tafi bah" Ai da sauri ta fara kokarin tashi,Mubarak yayi murmushi ya taimaka mata ta tashi tasha tea sannan ta koma ta kaunta Doctor ne suka shigo shida yaya Sadeeq,dubata yayi ganin babu wata matsala yasa yayi discharging dinsu,suka kama hanya suka wuce gida Bayan sun koma gida Mum tacewa masu aiki dasuyi mata pepper soup na kayan ciki,dama angama launch!!! babu yadda Mum batayi akan Kamal yazo yaci bah yace shi bayajin yunwa daga karshe mah tashi yayi ya tafi part dinshi Duk Dad na kallon su baice musu komai bah balle ya tambaye su ya sukayi sai chan fa'iza take cewa " Mum taqi yadda ta biyo ku koh?shiyasa brother yaqi cin abinci koh? "Bakin biyo mu tayi bah anyi admitting dinta a asibiti ne" A fusace Dad yake kallon ta irin yana neman karin bayani tagane meyake nufi, hakan yasa tace "Bafa wani abun bane doctor yace tanada ciki ne shiyasa" Tsalle fa'iza ta daka tana murna,dan sake fuskar shi Dad yayi yana maijin farin ciki a ransa amma bai nuna musu hakan bah,ita kuwa fa'iza inbanda murna babu abinda takeyi sannan tace "Mum dan Allah inzaku koma zanje nima na ganta" Mum bata kulata bah!!!ta tashi ta nufi part din Kamal A kwance yake akan Kujera ya rasa mai yake mishi dadi.jin an taba shine yasa ya tashi ya zauna yana kallon Mum "Karka damu son nasan Hamdiyya tana cikin bacen rai ne shiyasa ta fadamana haka, amma babu abinda zatayi wa cikin nan da yaddan Allah" "Mum meyasa zata kira mun dana da bashi da uba?ni nasan cikin nan nawa ne,meyasa zata shegan tamin dana?kuma tace saita zubar dashi,laifin meya mata?shifah bai san komai bah" Shafa kanshi Mum tayi tace "Kar kaga laifin Hamdiyya son,duk laifi nah ne da ban kirata da suna karuwa bah da bazatace haka bah!!! yanzu ka tashi kayi wanka sai mu koma asibitin" Baiyi mata musu bah ya tashi ya shiga daki danyin wanka,ita kuma ta koma part dinta ta hada abubuwan da zata kai musu asibitin Dad duk yana kallon ta ya gane cewa akwai wata matsalar hakan yasa ya kirata yace "Kince Hamdiyya nada ciki!!!amma kuma naga kina cikin damuwa,koh baki yadda da cikin bane?saboda ga sunan da kika kirata dashi Da sauri ta girgiza mishi kai sannan tace "Nasan cewa ita bah karuwa bace,bansan meya zo kaina bah na ambace ta da haka.cewa tayi zata zubar da cikin wai dan baida uba" Murmushin takaici Dad yayi yace "Nasan za'ayi haka ai,amma dai kinsan duk meya faru ke kika ja haka koh?toh yanzu sai kije ki san yadda zakiyi ai" Daga haka ya tashi ya barta a zaune a wurin,har Kamal ya shigo yace mata tazo suje asibitin!!! Haka ta tashi tasa aka kai kayan cikin mota sannan suka tafi duk jikin su a sanyaye. ✍✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah saleehu Dedicated dis page to u halima(ummu fadeel) I miss u alot dear,thank God u re back again. 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S✍ 7⃣9⃣➖8⃣0⃣ Bayan shigan ta daki bakin gado taje ta zauna ta fara dirzar kuka kamar babu gobe, idon nan ya kada yayi jawur duk ya kunbura Suna kaiwa kofan dakin Hamdiyya Ummee ta tsaya tace musu su shiga cikin dakin,sannan ta juya Tsayawa sukayi a kofar dakin kamar bazasu Shiga bah,kowa a cikin su da abinda yake tunani!!Mum ce tayi karfin halin tura kofan ta shiga ciki,ganin Mum ta shiga yasa shima ya shiga ciki Tanajin an bude kofar dakin ta fara goge fuskar ta,dagowar daza tayi sukayi ido hudu da Kamal!!! Kallon ta yakeyi kamar bai taba ganin ta bah,haka mah Mum tabita da kallo ganin yadda idon ta suka kumbura A hankali ya fara takowa kusa da ita,kafin ya gama karasuwa Hamdiyya tayi zumbur ta tashi tana cewa "Karka sake ka matso inda nake,cin mutuncin ne baku gama min bah kuka biyoni nan ku karasa?koh kuma me kukeso?" Chak ya tsaya yana kallon ta yadda take maganar kamar ta sanda da zuwan su ta tsara mezata fada Hade hannun ta tayi wuri daya tana cewa "Dan Allah Ku tafi banason ganinku anan ku fitan mun a dakina" Ganin basu da niyyan fita yasa ta nufi kofar fita daga dakin Bata gani sosai saboda jirin datake gani,hakan yasa ta fara dafa bango dan tasamu ta fita daga dakin!!!Amma hakan bai yiwu bah jin numfashin ta na neman daukewa yasa ta tsaya a wurin Sulalewa tayi a wurin a sume,da gudu shida mum suka iso wurinta,jijjigata Kamal ya farayi yana kiran sunan ta amma bata koh motsi,haka ya dauko ta da sauri kamar wata jaririya Da Mubarak sukaci karo wurin fitowa "Me kuma kukayi mata?duk abinda kuka mata bai ishe kubah said a kuka biyo ta har gidan su kuka kara cutar da ita?......" Bai tsaya sauraron karashen maganar Mubarak bah yayi hanyar waje ita,haka suma suka rufa mishi baya suka wuce asibiti Emergency direct aka wuce da ita,su kuma suna tsaye babu wanda a cikin su ya iya zama!!!Mubarak ne ya matso kusa da Kamal yana cewa "Kasani duk wani abu daya sameta kune kuka jamata,kuma kayi adduan babu abinda ya faru da ita inba haka bah,u will pay for it I promise!!!" Abba ne yazo yana bin Mubarak da wani irin kallo na ya tashi daga wurin Haka ya koma ya zauna,shi kuma Abba ya bawa Kamal hakauri!!!haka suka cigaba da jiran fitowar ta Bayan kusan 45 minute da shigar da ita doctor ya fito daga dakin da aka kaita,da sauri suka karasa wurin suna jiran suji mai zaice!!!ganin gaba daya hankalin su a tashe yake yasa yace suje cikin office dinshi Ai gaba dayan su haka suka dunguma zuwa office din,bayan sun zauna Kamal ya kasa hakuri doctor yayi magana dan gani yakeyi kamar doctor bazai ce komai "Doctor meke damunta dan Allah?" Gyara zama doctor yayi sannan yace "Ba wani abu bane ciki ne da ita,sai kuma tana yawan yin tunani wanda zai ita shafan cikin dayake jikin ta inba'a bata kulawa sosai" Murna ce kwance a fuskar ko wanne daga cikin su,Mum tafi nuna murnan ta akan kowa!!!A zuciyar ta tana cewa insha Allah kodan cikin nan Hamdiyya zata hakura ta koma dakin mijinta Godiya sosai sukawa doctor sannan suka fita zuwa wurinta,sanda sukaje bacci takeyi haka suka tsaya suna jiran farka warta Ganin su Mum basu da niyyan tafiya yasa Abba yacewa Ummee tazo suje gida ta kwaso abinda zasu bukata Bataso hakan bah dan taso ace tananan Hamdiyya zata tashi amma bata mishi musun hakan bah tayi musu sallama akan tananan dawowa,shi kuwa guga Mubarak yace yananan har saita tashi A hankali ta fara bude idonta sukayi ido hudu da Kamal,da sauri ta maidasu ta rufe kamar taga wani abun tsoro Yana ganin ta bude ido yayi saurin karasawa kusa da ita yana mata sannu,haka suma Mum da Mubarak,jin muryar Mubarak datayi ne yasa ta bude idonta tace "Yaya Mubarak ina Ummee nah da Abba nah suke?meyasa kabarsu sukazo nan?Dan Allah kace musu su tafi" Hakauri yafara bata akan tayi shiru zasu tafi amma ta kasa tsayar da kukan datake yi,haushin su takeji ba dan kadan bah Shirun data danyi ne yasa Mum ta matso tana cewa "Hamdiyya dan Allah kiyi hakuri da abubuwan dasuka faru ki yafimin,kinga har kina dauke da cikin Kamal kodan wannan ki yafemun ki koma gidan ki dan Allah" Hmmm!!!waya cemiki cikin Kamal ne?koh kin manta cewa ni karuwa ce?bakya tunanin a karuwan cina nasamu wannan cikin?nasan cewa inada ciki amma kuma bazan haife shi bah zubar dashi zanyi dan baida uba!!! ✍✍✍ [1/22, 10:55 PM] ‪+234 813 539 4575‬: ❣❣❣ITACE ZABINA❣❣❣ NA Khadeejah Saleehu Dedicated to hauwa Muhammad (slim small) 🌐HAJOW🌐 🌐HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S✍ 8⃣7⃣➖8⃣8⃣ Bayan sun gama parking a cikin harabar gidan,dukkan su suka fito daga cikin motar sannan suka kama hanyar Shiga cikin gidan!!!Hajiya ce ta tsaya tace "Hamdiyya ga part din mijin ki chan yananan a ciki,ki wuce chan dan nasan yanzu dawowar mu kawai yake jira" Gyada kanta tayi batare data ce komai bah sannan ta wuce wurin da Hajiya ta nuna mata Sallama tayi amma bataji an amsa mata bah!!!hakan yasa ta shiga ciki,baya parlour sai ta nema wuri ta zauna a tunaninta zai fito Takai kusan 15min a zaune a wurin amma bataji alamun motsin shi bah!!!hakan yasa ta tashi ta nufi cikin dakin A kwance yake yana bacci,amma kana ganin baccin kasan banajin dadi bane, karasawa tayi ta zauna a kasa sannan ta dora kanta a gefen gadon ta gefen dayake baccin Kallon shi takeyi sosai kamar yau tafara ganin shi,gaba daya ya

Chapter 10 of 12