Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 12
itama me irin shegen kule kulen matan nan ne. *Anan ƴan uwana mata ina son muku gargaɗi da jan hankali ne, akan haka kawai ki ɗauki wata ƴar uwarki ce, ƴar yayar mamankine, ƴar waye ɗin ki ne kice zaki riƙe, to wllh mu kiyayi kanmu. Mazan yanzu basu da amana kunya bata karasa isar su ba. Dan haka bawai nace kar ayi zumunci bana, A ahhh zumunci da mutumci da Alkhairi bawai lallai seka ɗauka ƙanwa ƴar uba. ALLAH yasa ku fahimta inda nake Son kaiwa* To daga nan ne fa tamkar Sumayya'n ta sake ankarar dani ne, sedai nayi danasin hakan yafi sau cikin masaƙi. Don kuwa ƙarara na dinga fuskantar wasu abubuwa masu girma tsakankanin Hameed da baby'n. A cikin wannan taƙin tsakankanin nida sumayya bansan waye yafi wani buƙatar fita daga cikin wannan gurɓatattun ahali. Sedai idan na aunawa irin girman damuwar da nake da se naga nafi Sumayya'n buƙatar hakan..... _Ohhh ALLAH NI kuwa AMMEY LAYLERH na ce uhmm uhmm fa ummih da Bilkisu 🤭 aha dan fa shi kyakkyawan hali aka ce tamkar zanen dutse ne🥰 Amma mudaije zuwa Hameed... _To se ku buyo Ni AMMEY LAYLERH don jin yacce tafiyan zata kaya, kuma kada ku manta nace duk yacce kuke tunani to kuwa tabbas *Ni AMMEY LAYLERH'NKU* nace ba haka tafiyan yake ba🤗_ *BY AMMEY LAYLARH ✍️* 08104493215 🌏𝘿𝙐𝙉𝙄𝙔𝘼𝙍𝙈𝙐🪐 𝙈𝙚 𝙘𝙞𝙠𝙚 𝙙𝑎 𝙩𝑎𝙧𝙞𝙣 ƙ𝑎𝙡𝙪𝙗𝑎𝙡𝙚🤦 ~Na Maryam Naseer Mirrah~ 𝘼𝙈𝙈𝙀𝙔 𝙇𝘼𝙔𝙇𝙀𝙍𝙃 ✍️ Official Mirrah💐 ♡ Page 13&14 https://chat.whatsapp.com/DGIo9iiSjlgJPPqFHNtddH ✯ *🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION💫* (J.W.A) ♡ _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️* Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un 😭😭😭 ³ ALLAH ya ji ƙanki yaya Surayyah mutuniyar kirki ce sosai. 2018 Malam Madori munyi Rashi babba, UBANGIJI ya sadaki da dukkanin Rahamarsa. ALLAH yasa kinje wannan wuri a Sa'a. Muma idan tamu tazo yasa muyi kyakkyawan ƙarshe mu cika da imani da kalmar shuhada Ameen 👏👏. ALLAH ya bama iyaye da mijinki hakuri da juriyar rashinki.... ____________★★★____________ ★★★ ★★★ TESTED AND TRUSTED @queen 𝙍𝘼𝘽𝙄'𝘼 𝙒𝘼𝙆𝙄𝙇𝙄 _skincare 🥰 Is very good with zero side effects👌 Available Glow up your skincare routine with Vaseline Intensive Care.... Shin Ina manyan matan suke ƴan kwalisa masu ji da gayu?🗣️ To maza ku hanzarta kumatso kusa dan kuwa haƙiƙa tabbas duk macen data amsa sunanta mace ya kamaci ace tazo Queen 𝙍𝘼𝘽𝙄'𝘼 𝙒𝘼𝙆𝙄𝙇𝙄, domin kuwa ta zo muku ne da ingantattun haɗadɗun kayan gyaranjiki masu matuƙar gyara fata cikin ƙanƙanin loƙaci ba tare da sunyima fata lahani ba, domin kayan Queen 𝙍𝘼𝘽𝙄'𝘼 𝙒𝘼𝙆𝙄𝙇𝙄 products ne bawai na bleaching ba, zasu gyara ma mutum fata ne ya fiddo mashi da ainihin natural beauty ɗin mutum, haƙiƙa duk wacce batayi anfani da kayan Queen 𝙍𝘼𝘽𝙄'𝘼 𝙒𝘼𝙆𝙄𝙇𝙄 ba to kuwa tabbas anbarta acan ƙarshen bayama kuwa. Yana maganin Pimples, black spot,sunburn, stretchmark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata? Waɗan nan su ne jerin sabulan da muke da... *Super lightening soap* *Organic lightening soap* *Baby soap* *Lightening dilka soap* *Attractive soap* *Morocco soap* _A kwai wanda yake saka haske akwai wanda yake maintaining na skin ba tare da ya saka maki haske ba_ Call or chat us on whatsAp to place ur order +2347048742957 business only🥰🙏🏻 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡ This destiny got me feeling all the feels, I can't control my emotions akansa, Tabbas nayi dana sani mara iyaka a lokacin da baya da amfani. Na shiga halin rayuwa sosái me wuyar a misalta, ni kaɗai na. Nayi kuka nayi kuka nayi kukan nada sau babu adadi. Ni AYSHA to da me ne zanji? Matsin da nake ciki na kishiyar data jefani a ciki ta rabani da mijina?... Ko kuwa takurar Uwar mijin da shekara ɗaya baya mijin da take aure a Rano ya rasu babansu ya dawo da ita aka sake bi ta kanta aka mallake. Bana da wani kataɓus a gidan aure na sai ya zama laifi!, Ƙiri da ƙiri ake nunama yarana tsana da tsangwama. Idan bana da lafiya babu me dubani a cikin gidan domin bana da wannan matsayin. Ko yau da nake kwance ina ta kaina se da naji shigowar Maman Hameed ɗakin Ummih, duk zato na ma ko dubani tazo takanas amma se naji saɓanin haka. Inajin sanda ta fi ce a ƙofar ba tare da ta leƙo inda nake ba. Haka zanga yaranta manya da dama sauran yaran gidan sun zo amma babu me iya buɗar baki ya duba, wanda ko ban faɗi ba kallo ɗaya mutum zai yi min ya fahimta cewar lallai bana da cikakkiyar lafiya, domin kuwa na sake ramewa fiye da baya Sosái. Dan sosai wannan cikin yazo min da laulayi bana wasa ba. Idan naji na tsani rayuwar dama kaina gaba ɗaya, idan kuma na tuna cewar duk karfin ikon mutum bai isa kokawa da ƙaddarar da Ubangiji ya rigada ya jarabta masa se naji kuma nadamar hakan take, domin kuwa tun kafin zuwan mu duniya ALLAH ya rigada ya Kaɗɗara mana hakan cikin littafin nan da baya taɓa goge kaifi ko tsinin kaɗɗarorinmu....... A washe garin ranar dake adaren Hameed ya komo ɗakina wanda ma ni ko shigowarsa ban sani ba. Haka da safe Ummih ta ƙi min girki wanda na fito kenan naji Maman Hameed tana cewa ummin gobe kona langwaɓe kar ta daddara ta ce zata ɗora min girki, Bayan fitar ƴan gidanmu da suka zo dubani wanda seda suka biya ma nata ɓangaren suka gaisheta. Amma tsabar wutar ƙiyayyar da take min sannu bata ƙara so ta min ba, wanda tana fitowa a ɗakin ummin muka haɗu har ma na gaida ta Ina tsugunnawa har ƙasa, amma kawai ta buɗe baki ta ce min yaya jikin shi ne taƙe ƙyashin hakan. ALLAH Sarki Rayuwa kenan, idan na zauna ni kaɗai nakanyi mamakin ire iren mutanen nan, se kace su ma ba ƴaƴa matan gare su ba, shin minene ribar uwar mijin da kawai zata ɗauka karan tsana ta ɗorawa matar ɗan ta? Babu? Su kansu basu da amsoshin ire-iren waɗannan tambayoyin. A ta yaya ne ma rayuwar mu zata ci gaba? kuma wai dan tsabar wani rashin gaskiya irin na ɗan Adam ke ƴar ki na aure itama a wani gidan amma ki ce ita ba za'a takura mata ba, ai hangen nesa ma name hankalin da nutsuwa ne, ta ya ya? Ta ya hakan zata taɓa faruwa? Alhalin ne nan kin zo kin takura ƴar wasu kuma ke kice ƴarki ta zauna ƙalau ƙarya ma kenan. Domin duk abubuwan da suke faruwa damu a zahiri ya zamana ne tamkar zubin zubeben kwaryar koman koma ne, domin kuwa abinda kama ɗan wani shi za'a ma naki, shi yasa ganan ƴaƴansu kullum suke yawo a haukace, ni a hakan ma tawa me sauƙi ce su kuwa fa? Ganan Mai Jiddah a gabanta tun kafin tay shinshinan dawowa gidan mijin ta ya sake ta bayan kishiyarta ta lakaɗa mata na jaki ta ci ubanta. Yau kimanin shekaru biyar kenan, Wllh tun da ta fito ko kare bai taɓa leƙowa da sunan wai yana son mai jiddan ba, kun ga kuwa kenan tarin alhaki da zunuban dake kan ta yake bibiyar yarin yar nata. Wacce itama ba ƙaramar baƙar muna fuka bace ta bugawa a gidan jarida ma kuwa, tana yawo tsakanin nan da can kuɗiy kuɗiy... Amma dake ba masu ganewa da fahimta bane kullum su cikin nemo hanyar musguna min suke.......... Haka ban yi ƙasa a gwiwa ba na ɗora girki na tun wuri nayi na gama. Ina gamawa kamar ko yaushe ita na fara zuwa ba seda na cika mata kular da na wa re kawai dan zuba mata abincin. Shimar nawa na ɗauka saman window na na zira bayan na miƙa na ummih nima na ɗauka nawa dana Hameed na nufi ɓangaren su don kai mata. Da sallama a bakina na shiga har ɗakinta, ina tsugunnawa tare da ajiye kulan dana soya doya da ƙwai gabanta, ina gaishe ta amsa ba yabo ba fallasa kai nifa rayuwar nan ta gidan duniya ban san abinda ya shiga tsakanina da matar nan sama ta ka ba. Dan kuwa da Sosái take mutum tani, dawowarta ne duk waɗan nan ƙalubai ɗin suka soma. Daga ace na bada abinci kaɗan, se ace be dahu ba. Idan aka gadama ma kuwa ina kaiwa za'a biyo bayana wai na bada nashi wanda nakai bazai ishe su. Haka zan ɗauka na bayar duk yaranta sun dena girmamani, an gama sukana da zubar min mutumci a wurinsu. Kallo ɗaya tama kular tsabar bala'i da masifa ba tare ma data ko buɗe ba tace na kawo mata na Hameed. Tsammm na miki domin zuwa na kawo mata har nakai bakin ƙofar fita ta sake cewa. "Ki haɗo da shayi da madarar da akace anga kina dafawa da baki kawo min ba, Ni da gumin ɗana amma har a dafa abu a gidan sa a hanani" haka na tsinkayi muryan ta cikin ƙaushi² da fushi²..... Saurin barin wurin nayi jikina na wani irin kakkarwa bakina nason furta salati da ambaton sunan ALLAH amma na gaza, cikin tsantsar mamaki nake ta jujjuya maganar shayin da akace na dafa, Kofi ɗayan ruwan zafi fa na ɗiba a pkast ɗina na ruwan zafi na haɗawa yara zasu tafi school, wanda madarar ma tun jiya na bama Amaan ya sayomin ta dubu ɗaya a bayan layi. "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un ³" na shiga maimaitawa zuciyana na wani kalan yunƙuromin da ƙirjina, a daffe na isa ga ɗakina na ɗauka ƙarin jug Ina jefa Lipton da shugar tare da madarar dana zuba guda biyu na juya su, kana na juya ina fita na koma dakin ina kai mata. Wannan karon kammm kai tsaye da harara ta bini tana me furta. "Indai baƙar zuciya ce aikin mutum to wllh ze gani a Akansa". Idanuna har wani rufe min suke ina ganin kowanne abu bibbiyu da haka na laluba hanya ina komawa ɗakina.... Jikina wani kalan rawan tashin hankali yake take komai dake faruwa dani suka shiga min zeroying maind nawa, wani irin kuka na fashe dashi cikin tsananin ɗacin dana jima tarawa na shiga furta... "_Indai Haka uwar miji da dangin miji suke to kuwa nawa dangin miji da uwar mijin Ubangiji ALLAH ya haɗasu da Masifa,Bala'i, jafa'i da dukkan wasu almasifun da suke tattare cikin wannan duniyar!. Ya ALLAH cikin kuka ina mai zub da hawayen da babu matararsu ko me iya tsayar min dasu se ƙarfin Ikon ka, Ya ALLAH to ina roƙonƙa da kyawawan sunayen ka ɗari ba ɗaya indai bana da Haƙƙi akan waɗan nan mutanen, to kabi min kadina da haƙƙi na akansu!!!. Kayi gusti gutsi da duk wasu sassa na jikinsu, ya ALLAH inda haka ko wacce MACEN AURE ke fama da matsalan Uwar Miji da dangin miji to kuwa lallai tabbas ko wacce MACEN dake cikin wannan duniyar na jinjina ma ƙoƙarin ta!, kuma dole ne Ayaba mata a kuma jinjina mata kai harma a ƙirata da JARUMA💪 Ehhhhhh lallai Tabbas JARUMA 💪 Saboda ba zaka taɓa sanin hakan ba se loƙacin da ƙaddarar hakan ta afka maka na Rashin dace da UWAR Miji da kuma dangin miji na gari. Ya Arrahamanu, ya zal'arsheem azeem kaci gaba da bani ƙarfin gwiwa da kuma ƙarfin zuciyar da zan ci gaba da fuskantar Wannan Babban ƘALUBALEN,Don tabbas a yadda jinin jikina ke tafasa ina jin ina dab da kashe nawa AUREN ata sanadiyyar UWAR MIJINA da kuma DANGIN MIJINA, tun da ta zama tamkar kishiyata koma nace fiye da kishiyan. Kayi haƙuri Hameed duk duniyar nan idan za'a haɗeta da abinda yake cikinta ina ganin babu wanda ya kaini S0NKA!, Koda kuwa wacce ta Haifekata ɗin. Saboda kaine mutum farko da zuciyata ta fara aminta da kai, sedai kaci amanar yardar da wannan zuciyar ta maka kai da butulun danginka.......... Daga inda nake zube dirshan ina kuka tamkar raina ze fita naji kaina na wani kalan bala'in mugun sara min, Se kuma naji tamkar ana jana i zuwa baya, daga haka ban sake sanin abinda ke faruwa ba ama cikin duniyar baki ɗaya. Se buɗar ido nayi na ganni kwance a gadon asibiti. Wanda na farka ne bayan sallar magrib, akan yaya ta fa'iza kuma idon nawa suka fara sauƙa. Dan haka ina ganin itace na sake fashe mata da kuka ina ce wa da ita dan ALLAH kar a maidani gidan Hameed na gaji wllh na gaji... Jin irin kukan da nake mata ne ya karya mata zuciya harta roƙi Bappa'n mu kan dan ALLAH idan nayi koɗan kwana biyu ne a gidan na koma daga baya. Be ƙi ba haka aka sallameni yaya khaleel da Bappa ya turo yay gidanmu dani. Alhamdulillh cikin kwana biyun nan har na fara dawowa hayyacins. Kuma koda meƙe ummih bata leƙo ba amma dake uwar su Hameed ɗin almakiratu ce lamba ɗaya kullum sassafe dake zuwa dubani. Idan na fito tsakar gida shan iska haka Baba me gadinmu yakan bani wasu ƴan adda'o'i yace na riƙe naka yi, In sha ALLAH zanga sanji sosai,na kuwa ji daɗin hakan rana ta uku ya sake ƙirana ya bani ruwan rubutu yace naka sha nida yarana In Sha ALLAHU duk wasu abubuwan dake jikinmu se warware, se kuma tsare mu sosai wani aiki dai ba zai taɓa samun mu da Ikon ALLAH, haka kuwa akai duk da da ban so har seda Ummah tace nayi kawai ai taimako ne kuma ALLAH yaga zuciyana ba da mugun nufi na nufi kowa ba, na tsarin kaina da yarana ne, hakan kuwa akayi muka fara sha muna wanka har sedai mukai kwana bakwai. Inda a daren ranar Bappa yace na shirya ze mayar dani gidan Hameed, harda kuka na a lokacin domin wllh na gaji da Auren ma baki ɗaya, amma Bappah ba mutumin da zai faɗi umarni bane naƙi bi dan haka muka shirya ya sake meƙa mu *BAƘIN GIDA* Haka dai al'amari sukaci gaba da lulawa cikin ikon Ubangiji kuma se komai ya fara sauƙaƙa a gareni rayuwata ta soma kyau da gyaruwa.... Sedai kashhh a daidai lokacin ne kuma wani tashin rabon ya sake ɗibar ummih ta sake bazama gun malamanta ganin komai ya fara sukurkuce mata, domin kuwa yanzu kai tsaye Hameed ya fara cin ubanta. Dama ALLAH yace dama biyu sau biyu takk yake ba mutum, na farko idan ka kauce a hanya ze duniya na ɗibarka kana aikata abinda kake so, se yace To idan yaso wannan bawan da rahamar sa ne ze kwace komai a hannunsa farar ɗaya. Idan mutumin yana da hankali da hangen nesa ze tsaya yay tunani me kyau dan nemawa kansa mafita, sedai idan kuma dama can baka da rabon shiryar nan a sanda ya kwace komai ɗin a hannunka zaka sake fantsamena domin dawo da wannan abinda ya kwace ɗin daga gareka, wanda dama bata ALLAH aka bi ba aka sama abin ba. A lokacin ne kuma ALLAH ya sake bata nasarar da dake kallar kamar isarta da malamanta ne suka bata, Nan fa na sake dawowa ruwa tsundum², sedai ko kaɗan bana taɓa wasa da tarin adda'o'i na. Haka Hameed ze min cin mutumci na jure,Ummansa tamin na jure, kishiya tamin duka na taru na shanye hakan, ga danginsa agains wanda ƙiri da muzu suka juyamin baya zuwa ga ƴar uwarsu. A lokacin cikina yana watan haihuwarsa ne, Ina cikin wannan tsanani wata ƙaddarar ta sake kusanto kanta gare ni, sedai bata faru ba amma ta gitta min tsakanin Jalila da kuma ƙanin mahaifinsu, Ranar juma'ar da bazan taɓa mantawa da ita ba a cikin rayuwata Kamaal ƙaninsa ba wanda suke uwa ɗaya ba uba ɗaya yazo yace na shirya jalilan zasuje gidan Anty Ummah yayarsu. Na shiryata gaba na nata faɗuwa haka kawai, kuma a ranar ne yarinyar ta ta min surutai barkatai tace min. "Mummy da kin sani da baki aifeni ba ko?" Saurin kallonta nai tare da rungumo kanta jikina, jikin nawa na rawa na furta. "Banyi dana sanin haihuwarki ba jalila!, Kuma In Sha ALLAHU bazan taɓa danasanin haihuwar ɗaya daga cikin ku ba, Ina Sonku kune *DUNIYATA* gaba da baya ALLAH ya muku albarka ya albarci rayuwar ku dukanku ya raya min ku, ya kare min daga sharrin me sharri, Ubangiji kar ya jarrabeku da laifin da ba kune kuka aikata ba, sanda ake aikatawar kuna bacci wasu kuwa tun kamin kuzo DUNIYAR, ALLAH In sha ALLAHU bazai jarrabe mu da wannan ba ko dan halin Rayuwar da muke ciki na tsanan. Zeji tausayinmu, yay riƙo da Hannayenmu da tsarkin mulkinsa..." A ranar haka na wuni cikin wani irin sanyi da mutuwar jiki, A kaf duniyar idan da abinda yafi faɗar min da gaba to shi ne laifin Mahaifin ya faɗa kansu wata rana ko na yanzu ba. Wanda Ummih har habaicin take min ita yaranta maza ne, babu na ɓatawa, bata da fargabar komai tun da yaranta ita maza ne, duk inda ta zaune wannan zancen shi ne farkon furucinta, dan haka take sake ruguza duk wani kwarin gwiwa nawa..... Ko da yamma da kamaal ya dawo min da jalilah se tace min. "Mummy nan ɗi na zafi" tay min maganar tana nuna min ƙasanta,wanda dama kullum cikin check out náshi nake saboda tsananin fargaba. Saurin buɗe wurin nayi, se naga duk fatar wurin haka ta ɗan tattare ba da yawa. Dan haka na zare mata Ido tare da furta. "Dan ubanki wa yake buɗe nan?" Nai mata maganar ina zare mata ido, sai tace min, "Bappa kamaal ne daya ɗauke ni a keke shi ne ya fito da cijinsa yake nuna min ya sa min a nan, shi ne na ture" tay min maganar tana buɗe min gabanta, ƙalau gurin yake babu alamar ya mata komi amma sosái hankali na ya tashi, kawai dai tace zafi wurin ke mata dan haka na tashi na haɗa ruwan ɗumi na mata tsarki na wanke mata wurin. Bayan mun dawo parlour'n na zaunar da ita kan kujera na kamo kafaɗunta kana cikin lumana nace. "Duk sanda Bappa'n yace kizo, karki yarda kije, idan ya miki magana karki yarda ki amsa Indai ba'a gaba na kike ba zanci gaba da adda'ar ALLAH ya tseratar min da mutumcinku....... Haka na shanye wannan ɓakin cikin ni kaɗai abuna, da dare kuwa dake babu ALLAH a wasu zukatan se gashi yazo amsar abinci, raina a haɗe sosai na ɗauko na bashi ina jinsa yana ta mata magana tayi shiru ta ƙyale shi, ina bashi nace "Jalilah ta maza tashi muyi sallah dan kai kukanmu ga ALLAH da addu'ar yaƙar azzalumai da masu mana zamba cikin aminci" a take kuwa jikinsa ya bashi sim sim ya ɗauka kulan abincinsa ya fice yana bar min ɗakin. Ko washe garin ranar ma se naji kamar in sanarma Hameed Amma kuwa wata zuciyar na tankwarata kan kawai na ƙyaleshi. Hakan kuwa akayi na bar abin iyaka ni ba tare da kowa nawa na faɗa mishi ba, na bar shi iyaka sirrin ciki se hanji kodan goben yarana.... Chart kamm da Baby tun idan na ritsa shi yana saurin ɓoye min waya har ma ya dawo dena ɓoyemin ɗin. In yaso zuciyana in ma bugawa zatayi ta buga, amma baya bari in kalla sedai ya koma wani fannin tun da yasan dai wannan yawan messages nasu da Baby na sani, sedai be zata na san komai ba. ★ *Mabuɗin ƙaddarar* _Kuma baƙar rana_ Akan yima juma'a laƙabi da juma'a tu Babbar rana sedai ni a gareni ba hakan take ba, domin kuwa duk wani iftila'in da zai sameni yafi samu na a juma'a tu. Ranar na tashi da wani irin mutuwar jiki sosai, ga shi kuma ni ce da girki, dan haka na lallaɓa na ɗora girki dan ina cikin satin haihuwa ne kamar yanda likitoci suka sanar min. Ranar shinkafa da miya nayi, se na mana kunun Aya me kyau da daɗi wanda ashe bana da rabo a cikin su duka. Ina daga kitchen na jiwo kukan Ashman da jalila, dan haka nayi saurin fitowa tare da tambayarsu menene?, Ummi ce ta fito daga ɗakinta tana wani haki tace Ayman ɗin tane ya daki Ashman shi ne jalila ta rama masa, shi ne itama ta rama masa.... Kallon ta nai da mamaki duk da ba wannan bane karo na farko in yara na faɗa ta shigar musu. Ɗauke kaina nayi ina2 nufar komawa kitchen se na tsinkayi muzryan ta tana me furta. "Aikin banza gayyar tsiya, ai da seki ce kema zaki rama musu, wacce bata iya haihuwar kowa ba se ta ƴaƴa mata gayyar wahala da ƙajaga" A wani irin fusace na juyo yau duk wani haƙuri na da juriyana na guduwa, ina juyowa tare da furta. "Su ƴaƴa mata da kike ji kike gani tamkar tsamiya haka suke, idan suka jiƙu sun ishi kowa, da haihuwar wani namijin sau ɗaya gwanda ka haifi mace sau ɗari, In banda toshewar basira ma akwai abinda yakai haihuwar ƴaƴa mata daɗi da ni'ima ne? Se dai idan akace mutum ya tafi tofa ya tafin ne. Kuma kaɗɗarar da kike ma dariya INS HA ALLAHU wata rana se ta kai ki ga kuka Ummih" daganan na barta tana ta ruwan alkaba'inta iri da kala na Sha re ta, domin sama sama dama yau na tashi ina jin kaina. Ina kammala girkin lokacin an ƙira sallah kenan, amma seda na rarraba na kaima kowa kana na shige ɗaki domin yin Sallah. Ina nan daga ƙofar ɗakina dake anan nai sallar, ina zaman tashiya Hameed ya dawo upstairs náshi ya wuce, ashe ummin ta bishi, ta zayyane masa karya da gaskiya wai ni ce na daki yaran nata, Ina jin sa ya shiga kwalamin ƙira, ban amsa ba tunda Ubangiji na nake gaidawa a loƙacin yafi min kowa da komo muhimmanci.... Dan haka cikin wannan masifar tashi ya ƙalama ummin dake zaune saman brander Yana ce da ita. "Wai ina A'ishah take ne, tsabar wulaƙanci tana jin ina ƙiranta ba zata amsa min ba?" Buɗar bakinta se kuwa ce wa tay. "Gata nan a nan nan ƙofar ɗakinta tana jinka ba nisa tayi ba". Ni kuwa a daidai lokacin na sallame sallata tare da ɗaga hannuwana sama wasu ruwan hawaye na zuwar min bakina na rawa na furta. _YA WADUD!_ _YA ZAL'ARSHIL MAJID_ _YA FU'ALILLUMA YURID_ _AS ALUKA BI'IZZIKALLAZI LA YURAM_ _WA MULKIKALLAZI LA YUDAM_ _WA NURI WAJ HIKALLAZI MALA ALKANA ARSHIM LAJJINI MIN HAZAL MUJIRIM_ *YA WADUD* Ya me cikakken ƙauna wa bayinsa! *YA ZAL'ARSHIL MAJID* Ya ma'abocin al'arshi me girma me ɗaukaka. *YA FU'ALILLUMA YURID* Ya ALLAH me aikata duk abinda yaga dama. *AS ALUKA BI'IZZIKALLAZI LA YURAM* Ina Róƙonƙa da buwayarka wanda wani baya kwaɗayinsa. *WA MULKIKALLAZI LA YUDAM* Ina Roƙonƙa da ƙarfin mulkinka da wani ba ya iya rusushi. *WA NURI WAJ HIKALLAZI MALA ALKANA ARSHIM* Ina Roƙanƙa Saboda Hasken Fuskarka data cike al'arshinka ka tseratar dani daga wannan mutumin...... Kana na Roƙe ka ka rabani da duk abinda yake ba Alkhairi na bane, dan tsarkin mulkinka, ya zal jalalu wal eekram....... Dai dai nan

Chapter 8 of 12