Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 12
duk hukuncin da ubangi ya zartar a kaina dan haka na rungumi hakan dan ma lokacin Amaan na rarrafensa ko ina lokacin watansa bakwai... Haka akaci gaba da fafatawa ayi ba ayi ba har zuwa sanda na haifi ɗiya ta mace me kama dani sakkk,inda ran suna Hameed ya min wata babbar bazata yana baby'n takwara da sunana wato *A'ISHA* dan haka se ban wani ɓoye mata sunan taba muke ƙiranta da ayshanta kawai. Inda har lokacin ALLAH bai bawa Bilkisu matar yayan mijina Ahmad me bin wanda ya rasu haihuwa ba, dan haka seta fara adawa dani tana nuna min tsana da ƙyashi sedai nakan shareta. Amma kuma ni bana taɓa hana mata yarana domin kuwa hasali ba da kaina nakan zagaya bangarenta na kai mata su tun da itama Yar uwarsu ce ƙanwar ubansu ci da ubanta da ubansu uwa ɗaya uba ɗaya ne ya haifesu Auren zumunta aka musu... Kun kuwa kuwa kenan inma dafa su zatai ta cinye nidai na fita ahammm. Har zuwa sanda mijin yake neman Aure, aikuwa anan hasalin tashin hankalin yake domin kuwa kusan ɗan ƙaramin hauka ta taɓa a lokacin sedai da akace komai me wucewa ne se gashi ya wuce kamar ba'ay ba... Anyi bikin Ahmad da Amaryarsa Sumayya me sunan ƙanwata lafiya akayi aka baje sedai duk wani sha'ani dai an yi shi ne kadaran kada han ata ɓangaren Bilkisu uwar gida. Haka dai zama yaci gaba da luluwa inda ita ma dai Sumayya'n shiru babu cikin dan haka se Bilkisu ta saki ranta harta fara yada wa mutanen gidan magana dama uwar mijin da mijin nata kan cewar ai ganan itama wacce aka auro ɗin dan ta haihu bata haihun ba sedai babu me tankata kasancewar ita Sumayya'n yarinyace me haƙuri amma fa akwai ƙuruciya sosai dangane da yarinyar, domin akwai bishiyar umbrella a gidan haka zata ɗane abinta tayi ta yagar abinta babu abinda ya dameta. Sedai me ni ma sega tawa wata sabuwar kenan... Aysha tana Rarrafe nima Mijina Hameed ya bijiro da maganar kara auren da yake son yi da wata ƴar gidan yayan mahaifiyarsa dake Rano, wacce a da take aure a cikin garin Kanon se suka rabu da mijin. Wanda har rabuwar tasu ma na sani sedai ashe ban sani ba kishin kishin ɗin ma da ake a cikin dangi wai ashe Hameed ɗin shi ne ya kashe mata auren dan ta fito ya aure ta. Ba laifi sama sama mukan gaisa da ita kuma ashe ita ɗin tsohuwar budurwar sace SO a lokacin se iyaye suka hana auren sukace karatu zatay, ashe lokacin dan baya da komai ne su kuma gasu zarmammu abin duniya ke rudarsu, dan haka suka aura mata wani me shayi da buredi a dorayi. Sosai a lokacin na tashi hankali na akan batun domin kuwa nasha jin ƙishin ƙishin cewar ai uwarta ƴar yawon malamai ce ko a gidan mijin itace ke da POWER agun Mijin. Shi kuma a lokacin idanunsa sun rufe ya manta ko da wace yake tare. Ya manta ɗinbin soyayyata gareshi haka har aka bashi ita amma duk wasu a cikin dangin masu so ciki kuwa harda mahaifiyarsa dake Ranon itama tana aure tun da basa tare da mahaifin Hameed ɗin tuni. Kannensa duk maza ne su huɗu Auwal, Ibrahim,Saminu,se autansu a wurinta Abdallah. Tun da Hameed ya aure ni yaran suka koma ƙarƙashina. Wanda ashe ni ban sani ba jin haushi na farko a gidan kenan da matar mahaifinsu Suwaiba fara tsanata domin ada kulawar yaran na a hannunta ne. Wai jin haushin nawa kenan fa, wai daga zuwa na da kissa da kisisina na kwace yara a hannunta, shi ne suka haɗe min kai ita da Bilkisu haka kawai suka huramin wutar tsana a gidan. Sedai bani takan al'amurransu domin basu bane a gabana. Mutum ta farko data fara tausayin min a cikin gidan ba tare da sani naba itace sumayya kishiyar Bilkisu. Wanda ake cewa rashin sani yariga da yafi dare duhu domin kuwa gudun abin magana da gudun abinda ka iya zuwa ya dawo yasa samm banja yarinyar a jiki ba. Wanda ita kuma So take min da zuciya ɗaya ALLAH Sarki kenan, masanin gaubu a haka akayi bikin Hameed da Nafeesa (Ummi).. Sosái iyaye da yan uwa tare da manyan aminai na biyu da a Yanzun sune kan matakai masu girma suka rarrashi zuciyana haɗi da dannar ƙirjina akan nayi haƙuri komai me wucewa ne, haka kuma komai yay farko yana da ƙarshe dan haka sena sake tattare al'amuran su gefe ina Sha re wa. A ranar bikin haka sumayya ta kunna mana doba wanda da ni ban yarda seda ƙawayena da Aunty fa'iza Suka rankwafeni kan cewar kar na hanata ai ko babu komai mutun ya nuna ya damu dakai kaima ka nuna masa ka damu dashi ko yayane ze sama kwarin gwiwa da kuma ci gaba da ƙaunarka... Tabbas bansan kishi bala'i da masifa bane se a daren wannan ranar domin kuwa kusan kwanan zaune nayi tun farkon daren da naji guɗar ƴan kawo amarya ayyiriiiriii!!, Tun daga lokacin da ƙirjina ya wani irin bugamin be koma ba har zuwa washe garin ranar, na shiga tashin hankali fin tunanin me tunani wanda ƙarfin adda'a ne kawai ya danne hakan..... Haka ko a washe garin ranar na tashi da wuri na haɗa musu lafiyayyen girki na ajje a parlour'n sa na sama ina komawana nayi kwanciya tare da yarana bayan mun karya. Haka har suka cinye sati gudan dana basu a bakacin kwana ukun da ake yi. Ranar da ze dawo hannuna tun wuri nake ta aykin gyare-gyare na na ɗan haɗa wasu ƴan sirrikan da bana raba dasu ina dafa na dafawa ina shan na sha da madara.... Amma dake namiji munafukine a wannan daren haka Hameed ya sani gaba har kukansa wai wllh besan abinda ya sashi kara wannan Auren ba, Dana juya masa ƙeya ko ta kansa ban sake bi ba tun ina baccin karya harna gasken ya ɗaukeni. Se wajajen ƙarfe ɗaya na farko na ganshi yana chart Wanda dama na sha kama shi da wannan ɗabi'ar ba tun yau ba amma se yay saurin ɓoye wayar alamun rashin gaskiya. Ba tun na gama lura da cewar Hameed yana da son bata ma domin tsakankanin sa da ƴan mata chatting basu ƙarewa.... Zaune daram na tashi tare da duban shi kana a hankali cikin nutsuwa na furta... "Wai me ke damun kane daddy'n Amaan duk ranar ALLAH bata isheka yin chart ba se dare sosai haka? To ma yau da waye kakeyin chart ɗin domin duk wani mutum na gari na kuma mutumci to kuwa ta tabbas a irin wannan daren yana ɓoye na lulluɓe bayan bacci, kaji tsoron ALLAH aduk abinda kake yi domin kana da yara mata duk abinda kama ɗan wani faɗin Manzon ALLAH ne kaima se anma naka...... Daga haka na meda kai na ina kwanciyata duk kuwa da yanda yake tamin magana amma haka na sha re shi har zuwa sanda ya fara lalubata da niyar maimaici amma na hana hakan domin sammm ko ɗaya bana ƙaunar wannan sabbin halayensa da ahar kullum wasu sabbi yake fiddo min dasu... ★ A washe garin ranar ma da wuri na tashi nayi aiki na kasancewar weekend ce se ban tashe shi ba har seda na kammala duk ayyukana kana na dawo dakin. A tsaye na same shi yana cire rigarsa na ƙara sa taya shi cirewar tare da gaida shi bayan wacce na may da subhi... Fuskar nan haɗe ya amsa ni domin shi ma idan yaso badai tsare gida barin ma duk lokacin da zan wani ɗan gyara daga cikin rayuwarsa... Kallona yake kamar yanda nima nake kallonsa fuskata ɗauke da gajeran murmushi ina basarwa na furta.. "Uhmmmm dama sau da tari me faɗin gaskiya shike tashi a tutar munafiki, haka zalika kuma baya taɓa farin jini wa al'umma!, Sedai ka sani kai miji ne kuma jigo da goben yarana dan me zanga kana ƙoƙarin kauce hanya kana kuma naja baki na nai shiru kenan ba so na tsakani da ALLAH nake baka ma? In har zanka kana aikata ba daidai ba na ƙyaleka kaci gaba da aikatawar kuwa daddy'n Amaan!" ban damu da yanda ya sha re ni ba hakan kuma be sa na fasa daga taya shi cire kayan jikin saba, ƙara sa cire masa nayi ina kama hannunsa na kaishi har ƙofar mashigar bathroom ɗin. Na juya kenan da niyar barin wurin naji ya ja hannuna ina faɗa wa saman jikinsa da babu riga ya manne ni da jikinsa yana zu ba min idanuwansa masu azabtar da ni a koda yaushe... Na zata ma wani abin kirki zaiyi min amma sai jin sauƙar kalamansa nayi yana me furta.... "Ƙarya kike A'isha duk wannan abin kina min ne domin zafin kishi! Yara kuma ai ba ke bace ALLAH kenan ma ke da kanki kike ma yaranki bakin wata ƙaddara ta rufta musu?" Yay maganar yana ture ni daga jikinsa yana yin baya tagal tagal zan faɗi amma ban faɗin na na tsaya kan ƙafafuwana....Nan da nan naji raina ya ɓaci da irin wannan cin mutuncin da yay min ban da Wanda yake kan min gaban kishiyata na wannan banzar ɗabi'ar na zagina kattt kansa tsaye.... Se dai sammm ko kaɗan banyi yunƙurin tanka shi ba don ganin hanyar cikin mutumci kawai yake neman, Directly ɗakin yarana na shige can na tarar da su suma sun tashi shirya su nay kana muka nufin upstairs na daddy'n su. Zaunar dasu nayi bayan nace Amaan yaje ya ƙira aunty'n sa Amaryar daddy'n sa. Zunɓura baki yaron yayi wanda seda na dawo na tallari ƙeyarsa domin In Sha ALLAH bazan taɓa barin yarana su raina matar mahaifinsu ba. Lokacin dana shiga ya kammala shiryawa cikin shaddarsa ruwan zuma wacce tamay kyau sosai ƙibar daya ɗan sake tamay chass ɗagwas abinsa... Da sallama ɗauke a bakina na shiga sedai na haɗe face nawa tare da furta masa muje muyi dinner.. Bin lallausan lips nawa ya shiga bi da wani mayen kallo da fitinannun idanuwansa wanda basu rabo da jaraba ko haƙuri akan mace, Sosai na masa wani irin kyaun da duk ɗazun be lura da hakan ba na ɗaukar hankali. Wanda ni kuma kallon da yake bina da shi ya sanya tsigar jikina tashi, ina jin wani zirr a duka ilahirin jikina, Amma ina shanye hakan nayi kamar ban fahimci me yake so ba. Ina wani basar da shi yaji in da daɗi tare da sake gimtse fuska ta. Jin sauƙar hannuwansa kawai nayi kan saman fuskana yana shafawa tare da faɗin."pls Ashsha Just 20 minutes plssss 👏" ya wani faɗi yana haɗe min hannayensa biyu wuri guda. Sosai nasan cewa Hameed samm baya da kunya akan duk abinda ya shafa mace, dan haka bazai iyu gacan yarana parlour'n suna jiran fitowa na kuma In tsaya nace zanyi wani abu da shi na dan haka na furta. "Me akayi da zan baka 20 minute ɗin ko dai haƙuri zaka bani? To in haƙurin ma zaka bani ai na se na baka har mintuna ashirin ba, bayan ga yara can da auntynsu na jiran mu a parlour'n ba....nayi maganar ina ƙoƙarin tafiya na. Ido kawai ya bini dashi dan yasan cewar tas na fahimci ko me yake nufi, nasan cewa sex yake nufin yi dani kawai dai wulaƙanci ne. Zuwa lokacin tuni na jima da bar masa ɗakin... A hankali ya fara taka ƙafafuwansa yana barin cikin bedroom ɗin har zuwa cikin ainihin parlour'n. Fitinannun Idanuwan nan nasa na sauƙa a kaina kai tsaye. Wanda ni kuma daidai lokacin dana ɗago kaina jin ƙamshinsa aikuwa aka gaman Katar idanuna suka faɗa cikin nasa inda ya watso min wani shegen kallonsa wanda iyaka ni kaɗai daya yima nasan fassarar kayana. Haka yaci gaba da tako parlour'n ƙafafuwansa sanye da lallausan slippers na Versace kamshinsa na mamaye parlour'n wanda ya ankarar da yaransa isowarsa parlour'n... Yaran ne suka shiga rige rigen gaishesa yana amsasu cikin zallar farin ciki yana shafa kawunansu tare da musu albarka. Nan. Madam Ummih Amaryar da akaci kunu itama ta gaida shi ya amsa mata yana sakar mata da wani lallausan murmushin da seda ya sani jin faɗuwar gaba abincin nayi saving namu kowa kana muka far ci natse daga nan bayan an kammala aka ɗana fira kana yaran suka fice zuwa ɓangaren kakanninsu ni kuma Boss ɗin na jana ta ƙarfin tsiya muka koma ɗaki... Daga nan dai rayuwar ta fara cillawa har yau 2 Months kenan da min kishiya inda nake kallon Ikon ALLAH muraratan... Yau tun sassafe suka shirya suka fita wai zazzaɓin dare take yi zai kaita asibiti, adda'an samun sauƙin na mata yana ɗaukar ta a mota suka nufi Hospital ɗin..... Ina zaune a inda nake ban kai ga tashi bama naji sowar wayana wanda kai tsaye na gane shi ne me ƙiran kasancewar ringtone na daban na saka mishi. Wayar na ɗauka tare da ƙara ta a kunnena kai......"Ashsha Albishirin ki" Ina ɗaukan wayan abin da ya fara ce dani kenan duk da ban san cewar ko akan mene yake min albishir ɗin ba. Amma hakan be hanani ce masa "Goro fari ƙal ma kuwa daddy'n Amaan" ina jiwo sautin murmushinsa ta cikin wayar kafin ya wani ce dani. "Ummih Is pregnant" ya faɗi cikin wani irin zumuɗin da hakan ya kusan bani mamaki. Amma sena danna abin da ke taso min na washe baki ina faɗin. "Kai Ma sha ALLAH ALHAMDULILLH barka da na tayaku murna sosái ALLAH ya raba lafiya." Cikin wannan dai farin cikin ya sake ce dani. "Ke na fara ƙira na sanarmawa, sosái naji daɗin hakan nace a mata sannu idan ta tashi, kafin su dawo gida na mata lafiyayyen girki Sosái me rai da lafiya. Koda suka dawo da murnata da farin ciki na tare su tare da mata sannu amma seta wani yatsine fuska tana amsawa da ƙyar ita gamai ciki... sauce ɗin icefish na musu da lemon kwawa na buɗe da niyar saving nasu ita da Hameed ɗin ta wani irin toshe hanci wai ƙamshin girkin be mata ba. Cilakk na tashi na bar wurin domin nima babu wanda yasan ina ɗauke da nawa cikin a lokacin.. Cikin shegen kissar ta da kisisisnarta abinda naki yi tun wuri wato jan sumayya a jiki na a cikin ƙanƙanin loƙaci ta janyeta jikinta. Ehhhhhh lallai anan ni Aysha nace kowacce mace ta duniya idan takai goshinta ƙasa ta gaida Ubangijinta to tayi adda'a haɗi da roƙonsa karya haɗa mata zafi biyu wato kishiya me shegen iya kissa da kisisina da kuma yawon bin malamai a lokaci ɗaya. Don kuwa naga sharrin hakan akan kaina... Wai masu iya magana sukance gaida me gaisheka koda baze amsa ba, haka kuma dai inji masu azancin magana suna sukan ce *ZUCIYA NASON ME KYAUTATA MATA* domin kuwa kyautatawar da sumayya take buƙata tun farkon fari na bata ban bata ba haka sama taka wata tazo ta bata ita.... Sun zo sun zama manyan abokai sosai da sumayya sedai ita babu komai a zuciyarta game dani se wannan soyayyar da take min har cikin zuciyarta, haka Ummi tazo ta yaudara duk wani mutum dake Family'n nan da lumbu lumbunta. Takan kame yarana Amaan da Aysha ta wanke tama Aysha kitso kasancewar ta iya sosai... Idan zani kitso gidan Aunty fa'iza se take bi na bansan a wacce tsiyar a wacce kwanar ba kawai naga ta dena bina, wai ashe Suwaiba ce ta jata ɗaki ta ce da yanzun baya taɓa yarda da kishiya yanda nake ɗin nan da baƙar zuciya tsaff zamu haɗa máta wani asirin a cikin man kitsonta ba tare da ta sani ba... ALLAH Sarki ohooooo ni banma san anai ba kuma se duk kulawar da take bama yarana ta dawo ta fara denawa kaɗan da kaɗan. Har komai ya watse, abinci wannan da muke ci tare seda muka dawo kowa ya ware kwanonsa. Ana haka sati biyu da sanin ta na da ciki ta fara laulayin cikin. Shi kuwa zo kaga rawar kai wurin Hameed tamkar wanda ba'a taɓa haifa masa yaran ba. Haka zata lanƙwashe a ɗaki taki fitowa tayi aiki ita nan me ciki amma duk na shareta ina mata uziri. Kai se ta kai ta kawo abincin gidan ma ta dena ci sedai yawon wuraren cin abinci... Wanda se a lokacin nima nawa cikin ya bayyana amma kowa seyay kamar besan ina da ba ciki kuwa har dashi uban gayyar... Tun farkon shigowar Ummih cikin Rayuwar AURENA da HAMEED USMAN DATTI jarabawa ce domin tun daga lokacin abubuwa soka soma sauyamin daga yanda na sansu gata irin matan nan da masa rufa sirrin aurensu duk inda taje se ta bada labarin mijinta karshe ne wajen sarrafa mace a bed. Nidai duk nakan toshe kunnuwana daga munanan kalamanta mara ɗa'a da alfanu. Kasancewar cikina ya fi nata girma se kowa ni yake bama haihuwar sedai kuma cikin Iko na Ubangiji ta rigani haihuwa da sati biyu ciffff inda ta haifa yaronta namiji yaci sunan mahaifinta Ameenuh. Ni kuma na haifa mace dan haka na roƙi Hameed alfarmar inason a sanya min sunan ƴaƴata Aunty fa'iza. Hakan kuwa akai se kuma wasu ɓoyayyun halaye game da ummin marasa kyau da ɗa'a suka fara fitowa fili. Gaban yarana da suka fara tasawa zata ringa abubuwan rashin ɗa'arta, Se nake killace kaina tare da yarana a ɗaki mu wuni duk weekend ko idan an musu hutun makaranta..... _Shin anan mi ne ne laifina dan na killace kaina da yarana daga gudun abinda nasan bazai mana kyau?, Kenan se hakan ya zama laifi_ Aifa se hakan ya zamana na magana dake babban gidane sosai matan ƙannei yayyai duk ana tare da iyayen Mijin. Gata da shegen kwashe kwashen ƙawaye kamar me haka zatayi ta jajuɓosu suna zuwa kuma dake ba abu bane na hankali haka zasu zo suyi zaman dirshan a gidan se kace na ubansu. Abu na farko da ya fara girgiza duniyata tare da ɗauke farin ciki da walwalana shi ne Ranar da nasan cewa Hameed mazinacine..... _Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un 😭😭😭😭😭_ a ranar kuka idan da abinda ya fishi ciwo da ɗaci to nayi a wannan lokacin domin kai tsaye rayuwar yarana na far dubawa ba me gobensu zata haifar? Babu ban sani ba, dan haka ƙunci da shiru shiru sune suka zame min manyan abokan da bana da kamar su a cikin WANNAN DUNIYAR tamu... Duk wani guntun hope nawa ya karasa guduwa ina rasa duk wasu qualities nawa Akan mafarkin gobe na. ★ Ranar ina zaune ina wankin kayan datti dana fitsarin lil fa'iza muna ɗan taɓa fira sama sama da ummi kishiyata ta dube ni tare da cewa dani.... "Aunty A'ISHA kin san kuwa me na gani jiya?" Ta tambayeni wanda ya sanya gabana wani kalan mugun buguwa da ƙarfin bala'in da seda na kusan kwarewa amma ban kai ga kwarewar na. "Jiya da dare Yaya Hameed yana bacci na ɗauka wayarsa dake nasan password nashi da besan na sani ba na cire kai tsaye ina fara shiga shiga cikin pisc nashi, Wllh wllh Wllh Videos da pisc nashi na dinga gani tare da yan mata barkatai. Ke In dai takaice miki wllh harda wanda sukayi video da wata suna sex da ita har yana tambayar ta wai ya cire Inplanning ɗin daya saka mata?.. Wllh a daren kasa bacci nayi har na komo daki na Ni kaɗai na dinga sintiri zuciyaata kamar ta fito ashe dama Hameed ɗan iska ne?" Duba ɗaya na mata ina ɗauke idona daga gareta tare da furta mata "Na sa ni!" Dake haka ban sake bi ta kanta ba naja bakina nayi shiru ina kammala wankina na koma ɗakina nayi kwanciyata,zuciyata na wani kalan kunburowa tun daga lokacin na fara ciki da shi kansa Hameed ɗin dan ni yarana sune abu na farko da nake fara tunawa da tausaya. A ranar ne kalaman ASAAD JUNERD MAJEED suka dinga min amsa kuwwa cikin kunnuwana suna karaɗe ilahirin duniyata baki ɗaya.... Wasu hawaye masu ɗaci na ɗauke ina me furta. *"TABBAS BAN CANCANTA ZAMA ƘARƘASHIN INUWAR MAZINACIN MUTUM IRIN KABA HAMEED, Haƙika a yau na yadda da zancen ka ASAAD JUNERD tabbas Ita ƙarya fi re take ba iya fidda ɗa take ba...."* Wannan damuwar hakan shi ne abu na farko daya fara kassara rayuwata haɗi da ruguza duk wasu farin ciki daya min saura a cikin Rayuwa. Ciwuka ne da yawa da yawa da yawa ke damuna suna cinye zuciya da Ruhina, wanda gaba ɗaya na fara dena kyan gani fata ta me kyau ta fara zama baƙar ƙarfi da yaji. Hakan kuma bazai hana Hameed nemana ba a shimfiɗarsa. Bana hana masa haƙƙinsa amma duk wata tarayraya kamm da nake masa babu tabbas sedai yayi kiɗinsa yayi rawarsa ya gama uffan bance masa. Wannan abu shi ne mataki na biyu da ya sake ruguza min rayuwar da ta minnguntu. Anan Ummih ta zage dantse wajan nuna masa zallar soyayya cikin kissa da uwar mata. Wanda naga wata irin tarairayar da tafi baya ya soma bata. Wanda komai bai da aiki sena ƙiran sunan ta. Komai ban iyaba Ummih itace ta iya matar da ko girkin arziƙi bata iya ba ga satar kayan miji ta sayar... Nidai nawa Ido haka kuma ban sare da dena binsa da adda'ar shiriyaba kodan kasancewar shi uban ƴaƴana... ahaka har muka yaye yaranmu muka kuma samun wani cikin kusan tare sedai wannan karon kamm fikon namu akwai ɗan nisa domin dan wajen wata biyar ɗan ta data sake haifar namiji ya bama yarinta Maryam da muke ƙiranta jalila.... Da ganan komai ya gama lalacemin domin kuwa mijin kansa neman rabani dashi ake, bayan an rabani da duk wani farin ciki da walwala nawa wanda duk wanda yasan asalin cikakkiyar AYSHA MUSTAPHA WAZEER *ROYAL BLUE* ba zai taɓa cewa ni na dawo haka ba. Babu komi ya gudu garinsu yo Ina fargaba da lalurar duniya zata sanya nayi abin arziƙi.... Komai na gidan kafff ya koma hannun Ummih haka yarana sun zama su kamar ba ƴaƴan ba se ƴaƴan Ummih, sau da tari idan na zauna nakanyi kuka na kuma gode wa Ubangiji bisa wannan ƙaddara daya zaɓar min ALLAH yasa itace mafi Alkhairi a gareni ya kuma sa iyaka bakinta kenan. A kullum kwanan duniya adda'ar da nake yi kenan.. *Tushe* _tommmm bara na gudu se a page na gaba In Sha ALLAHU maji maye tushen? Wannan wanda tushe ne kuma kuma dai nasan hakan kuke jimirin jira ai shikenann semu gumtse kawai 🤸 anan haka nan🤗_ *BY AMMEY LAYLERH ✍️* 08104493215 🌏𝘿𝙐𝙉𝙄𝙔𝘼𝙍𝙈𝙐🪐 𝙈𝙚 𝙘𝙞𝙠𝙚 𝙙𝑎 𝙩𝑎𝙧𝙞𝙣 ƙ𝑎𝙡𝙪𝙗𝑎𝙡𝙚🤦 ~Na Maryam Naseer Mirrah~ 𝘼𝙈𝙈𝙀𝙔 𝙇𝘼𝙔𝙇𝙀𝙍𝙃 ✍️ Official Mirrah💐 ♡ Page 11&12 *𝙄 𝘿𝙀𝘿𝙄𝘾𝘼𝙏𝙀𝘿 𝙏𝙊 𝘼𝙇𝙇 𝙂𝙊𝙑𝙀𝙍𝙉𝙈𝙀𝙉𝙏 𝙂𝙄𝙍𝙇 𝙐𝙉𝙄𝙏𝙔 𝙎𝙀𝘾𝙊𝙉𝘿𝘼𝙍𝙔 𝙎𝘾𝙃𝙊𝙊𝙇 𝙈𝘼𝙇𝘼𝙈 𝙈𝘼𝘿𝙊𝙍𝙄 𝙋𝙈𝘽 001* ✯ *🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION💫* (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️* *_𝐌𝐚𝐫𝐲𝐚𝐦_𝐝𝐞𝐥𝐢𝐠𝐡𝐭_* Best kayan kwalam 09025859622 or 09163353050 *END OF DISCUSSION PACKAGE* Now available in- candies package stop in and stock up on a sweet piece of summer! 🍬🍔🧆 𝐌𝐚𝐫𝐲𝐚𝐦_𝐝𝐞𝐥𝐢𝐠𝐡𝐭: ce ta shirya tsafff domin kawo muku. Samosa Spring rolls Filled doughnut Glazed doughnut Puff puff Shawarma Cupcake Birthday cake Bento cake Egg roll Milk cake Candy's Alewar madara Gullisuwa Tsami gaye Coconut laddo Milky gireba Albishir Mandula Sayen daya ko sari muna aikawa ko ina cikin aminci muna karɓar order bikin suna ko aure Location zamfara state ,gusau What's no :-09025859622 or 09163353050 Hajiya karki bari

Chapter 6 of 12