Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Abinci da plate sai da ta zuzzuba mai komai sinasir ne miyan agusi badai nama ba kifi amma sai kanshi yakeyi, ta hado mai da sobon da aka hada yaji cucunber ta tsiyaya mai a cup tace my yayancy sauko kaci, To my kanwancy ya sauko ta mikamai dan bowl ta zubamai ruwa ya wanke hannu, yayi bissmillah ya fara debowa yakai bakinta yace haaa my kanwancy, kai nifa na koshi, sai kin ci, uhmm ta bude baki ya zuba mata,aikam ta cije dan yatsan nashi auchhh kai kai kika cijeni, wlh zan rama ne, dariya ta farayi sorry haka suka gama cin Abincin su, ta tattara komai takai kitchen ta dawo tanata bashi lbrn makaranta harda kawanta Raleeyat, da uncle mubarak da irin wahalar dasu dayakeyi😩, tab aiko zan mai magana ya bar wahalar mu da kanwancy da kawarta, yauwa yayancy mun gde, bari in dauko maka ma hoton mu ka gani wlh kawata ta hadu yayancy ni har namaka kamu tunda kaki yin budurwa shiyasa zan maka ni, iyyeh yaushe kanwancy ta girma har ta fara maganar saurayi tab wlh kar in kara ji,nafison kiyi karatu, umar ya gayamun wai yanxu kuna shiri da jafar sosai koh? kai ya umar dinnan ya cika gulma shifa yake shishshigemun fa ko ban kulashi banayi, tom nidai na gayamiki wlh su Alhaji mallam na gani a lakaba miki ace za,a hadaku aure kuma kin san halin mamnshi bata son mu,zasu iya wahalar mun dake,Allah ma ya tsare yayancy Allah ya kyauta shekara biyu fa ya bani 😒, dariya 😆ya Ameen ya fara kinga kanwancyn nan son girman tsiya gareta gaba zaki ce mun kin girmeni😀😀kai yayancy ni bance ba, kai wai gulman me kukeyi ne? kai hajiyan nan munce ne hajiya ta cika fada kwashewa sukayi da dariya gaba dayansu, wai yaushe Alhji mallam zai dawo? sai nan da sati daya, tab har sai na koma school bai dawo baa, yauwa yaya Ameen gobe zaka rakani kasuwan muyo siyayyan provision, ok ba damuwa. wai ke ladi ya maganar gurin mallam me gobe da nisa? zamuje ki bari akawai kudin dinki na danake jiran akawo mun, to ni ina ma da yan kudina da sulemanu ya bani ijiya a ciki zan cire to shikenan, salamu Alaikum wai nanne shashin ladi? eh gani, wai ga kudin dinkin ki na Aska inji danladi, to kace ngd, yauwa hindatu shirya mu tafi yanxu can gaban likoro ne fa, gashi ba Alhji mallam kafin ya dawo, haka suka dauki mayafan su suka tafi ko tsaya tanbayar mazajensu basuyi ba, niko nace Allah ya shiryeku su hindatu, nasan meke tafe daku akan yarinyar gidanku ne yarinyar na tana dunbin baiwa a tare da ita kuma sai ta zama tauraruwa mai haske a kaf dangin ku, to yanxu mallam meye abunyi mu so muke ma kowa ya tsaneta a dangi tazama yar iska, sannan akwai wani yaro keeee!!!! mun san abunda kikeso ki fadi kar yaron ya sota koh? yaso yarki ko na yar uwrki,to gskya bazai taba sonsu ba sai dai zan cusa musu kiyayyar junansu, zan yi kokari inga na shagaltar da ita da ibada domin tana da ibada da addu,oi in har bata rage ibadan ba aikin mu bazai taba kyau ba zata dunga karya mana aiki,,,, mun gode me gobe da nisa nawa zamu bayar? bama karban kudi sai aiki yayi kyau ku tashi ku bamu guri shagalallun bayi batattu!!!!! to da baya da baya suka fita, uhmmm ni banjin komawa school dinnan hajiya gabana sai faduwa yakeyi, ki yawaita fadin innalillahi wa inna ilaihirraji´un to hajiyata, haka ummimi ta gama shiri taje sasa sasa ta sallamesu hajiya kaka mahaifiyar ma tayi mata nasiha sosai akan ibada sannan ta sallameta ta tafi, motar baffa shehu yaya Ameen ya ara aka sa mai suka dau hanya✍✍✍✍ please in kin san bazakiyi comment ba karki karanta mun novels.. daga✍✍alkalamin yar mutan zazzau✍✍✍ [6/8, 14:26] 💞FAST CLASS💕: 💗💗💗💗💗💗 *GIDAN GADO* 💗💗💗💗💗💗 *(UNFORGETABLE DAY)* *WRITTING BY ZEEEYTERH YAR MAMA YAR MUTAN ZAZZAU.* ________________________________ *AREWA WRITER'S ASSOCIATION* _________________________________ *💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦* _________________________________ https://www.facebook.com/104534761033461/posts arewawritersassociation@gmail.com بسم الله الر حمن الر حیم امسین و امسا ملک الله *🌹🌹EPISODE TWENTY TWO&TWENTY THREE🌹🌹* *Wannan page din,na sadaukar dashi ga duk wanda ya rasa kakan ninshi.😭😭 Allah ya jikansu, ya gafartamusu,,Ameeen🙏.* *Ku din na daban ne iyayena Allah ya ja kwana,yasa mu gama daku lpy🙏.* *Aunty mu na kan mu Allah ya barmu tare,* Sun Isa gidan Guggo Zuwaira da karfe biyu da rabi, bayan sun Isa Yaya Ameen ya huta' sukayi sallama da Guggon nasu, ya kama hanyar komawa gida, Ummimi ta rakoshi har kofan motan, "to Yayancy sai munyi waya" to kanwancy na zamuyi kewanki sosai, ke dage da karatu kin San nurse nake so ki zama" Insha Allah my Yayancy, kace ma Hajiyata da Guggon Yara Ina kewansu, in Alhji mallam ya dawo tace Mai nace nayi missing dinshi, Kuma na fasa auren tunda yaki dawowa, har na tafi" ayyah ai ance Yana hanya in ya dawo zamu zo tare dashi ya ganki, Kinga sai ya gyara auren nashi" suna cikin hiran su sai ga Yaya Iroh ya zo, tun daga nesa yake mata wani mayen kallo, har sai da Yaya Ameen ya ankare dashi" sai ya tare ta a bayan shi, "a,a Aminullahi idonka kenan badan na dawo ba tafiya fa zakayi? Wlh na tanbayi Guggo tace mun kayi nisa shiyasa, mikamai hannu yayi suka gaisa, " mutuniyar an dawo kenan? Eh Yaya Iro Ina wuni,? Lpy lau, ya shige gida abunshi, sukayi sallama da Yaya Ameeen ya kama hanya Yana kewar kanwar tashi, Inna lillahi wa innah ilaihirraji'un Allahumma ajirni fi musibaty wa aklifni khairan minha,!!!" Yaya Ameen ne ke fadin haka cikin tashin hankali, lokacin da ya iso gidansu ya dubban jama,a anata alwala, "sannu Aminullahi ya mukayi da hakurin Alhji mallam,? Mutumin bai gama rufe baki ba Yaya Ameen ya sume a gurin, da gudu Guggon Yara ta fito ku taimaka Mana Hajiya Yaya ita ma zata bi Alhji!!! Da sauri aka shiga aka fito da ita, sukayi Asibitin Gambo Sawaba, Gida ya rude sai kuka da kuka, Abunka da babban mutum nan da nan rasuwar ya game gari,"Mami!! Mami!! Kinji sanar wan da,ake a radio kuwa? Kai Ummimi wannan Kira haka Mami ji fa nake kaman Ana sanarwa Alhaji Mallam ya rasu, "Kai haba dai ka gamun ja,irar yarinya kosawa kikai ya rasun ko kuwa,? Wlh da gske nakeyi fa,! Basu rufe baki ba suka karajin sanarwan a radio, ai tuni Ummimi ta sume a gurin Mami tayi kanta a sukwane,!! Sai ga Iro ya shigo a birkice Mami!! Mami!! Kinji rasuwa? Yauwa Iro debomun ruwa don Allah mun shiga uku!! Da gudu ya shige kitchen ya debo ruwa ya kawo ma Mami suka zuba mata, da ihunta ta farfado "wlh Mami bai mutu ba dazu fa Yaya Ameen yace mun suna hanya, ita kuka Mami kuka,sai ga Alhaji ya shigo, " ku tashi ku shirya mu tafi ance bayan sallah Asuba za,ai jana,izan shi, don Allah daddy kucemun ba Alhaji mallam ne ya rasu ba, Kuyi hkr da wannan yau sai a hankali. Daga alkalamin Yar MUTAN ZAZZAU✍✍✍ [6/8, 14:26] 💞FAST CLASS💕: 💗💗💗💗💗💗 *GIDAN GADO* 💗💗💗💗💗💗 *(UNFORGETABLE DAY 2)* *WRITTING BY ZEEEYTERH YAR MAMA YAR MUTAN ZAZZAU.* بسم الله الرحمن الرحیم فاذ اصابت من موصیبت قالو انالله و انا الیه راجعون۔ *🌹🌹EPISODE TWENTY FOUR&TWEANTY FIVE🌹🌹* *Wannan page din naku yan Arewa writters.* ________________________________ *AREWA WRITER'S ASSOCIATION* _________________________________ *💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦* _________________________________ https://www.facebook.com/104534761033461/posts arewawritersassociation@gmail.com *1.babban aunty, Aunty Hauwa (maman uswan)💖* *2.ummu Affan💕* *3.ummu intissar🌷* *4.babban doctor ina yinki doctor maryam🌺* *5.takwarata zainab ga gaisuwanki.🌻* *6.sister Laurat m bello ban mance ki ba🌸* *7 .tab na kusa in mance da maman khaleel sorry😜😜* *8.mai sunan yan gayu Sa,amlad da fatan na fada dai dai😂* *9.ga wata Mai sunan Yan gayun Hafscall nayi dai dai koh😂* *da duk wanda ban samu daman anbato su ba kuyi hkr kunsan sabon shiga ban gama haddace yan gidan gaba daya ba, ina yinku ga page nan na baku kuyi yanda kukeso💞💞* Sun iso zaria ana sallah isha,i sai da Mami ta rirrike Ummimi suka karaso kofar gida, suka ga jama,a da yawa a kofar gidan, ihu Ummimi ta kara sakawa, "shikenan Mami Ashe da gske ne Mallam Dina ya rasu !! Ta karishe maganar tana innalillahi wa'innah ilaihirraji'un shikenan dama bazan Kara ganinshi ba shiyasa ya zauna ya dunga mun nasiha" Suna shiga gida tayi dakin Hajiya yayah da gudu, "Hajiyata!! Hajiyata!! Tana shiga dakin sai mutane Yan gaisuwa kawai ta gani bedroom din Hajiyan ta shige,sai ganin Hajiya tayi a kan gado an samata drips, Guggon Yara ta gani zaune kusa da Hajiyan taci kuka har ta gaji,da gudu ta karasa ta fada jikin Guggon Yara tasaki wani kuka Mai cin Rai, daurewa kawai Guggon Yara takeyi, ta rungumeta ta fara lallashinta" Ummimin Hajiya kiyi hkr Allah ya fimu son Alhaji mallam, shiyasa ya dauke shi yanzu addu,a yake bukata a garemu ba kuka ba kinji Yar albarka,? Mallam dake ya rasu, har ya rasu Yana bada Amanarki, wasiyyan shi duk akanki ne, bai tuna da kowa ba sai ke, Kinga Koh addu'a shine yafi bukata agareki, shine karshen soyayyan dazaki nuna Mai," inshallah Guggon Yara zanbi shi da addu'a,motsi Hajiya ta fara duka suka tashi suka karasa wajenta, Washe gari anyi jana'izan Alhaji Muhammad Fulani sai muce Allah ya ji kanshi ya kyautata makwancin shi, Mutuwar data girgiza kannin Mallam da ya'yanshi da jikoki da Matanshi,da sauran Yan uwa da abokan arziki, Hajiya Yaya ta warware sai dai gaba daya ta canza daga kuka sai dai ka ganta Tana Jan tasbaha, kwanci tashi ba wuya yau har anyi addu'a bakwai inda kowa ya watse, aka bar Wanda mutuwan ya shafa da jimamin Rashi, "Yauwa boka so muke yarinyar nan ta bar gida kar a Kara ganinta, Kuma kowa ya manta da ita a gidan, an gama shagalallu" kowa zai mance ta Amma Banda mutane hudu kakanta na gurin uba, sai mahaifiyarta, sai Yayanta, sai kakanta na gurin uwa,"Amman Zan kulle bakin su bazasu taba magana akan haka ba,, "Yauwa boka mun gode, Kai ba,amun gdya Anan, ladan aikin ku sai Kun dawo hahahaha,!!! "Kuje da garin maganin na matukar ta taka garin maganin shikenan, ku tashi gafalallu marasu raban rahma kutashi ku tafi boka ya baku sa,a" da baya da baya suka fito suka kamo hanyar gida, "Ummimi kizo inji maman jafar, to kice ganinan xuwa bayan ta gama hada kayanta, lkcn Kuma Hajiya na toilet, ta fita zuwa sashin su Yaya Jafar, Tana Isa ta taka kofar gabanta yayi wani mummunan faduwa,kawai sai ta juya ta kama hanyar kofar gida, dama su Maman Jafar suna make suna ganinta "hhhh yarinya keda gidan nan har Abada basai ayi karatun bokon mu gani ba, suka Kara kwashewa da dariya, Lokacin da Ummimi zata fita ba Wanda ya ganta,,,,,,,✍✍✍ Allah sarki Ummimi na tausayamik. in kin san bazakiyi comment ba karki karanta mun novel zeeeyterh ce yar mutan zazzau✍✍✍ [6/8, 14:26] 💞FAST CLASS💕: 💗💗💗💗💗💗 GIDAN GADO 💗💗💗💗💗💗 (LOOSING MEMORY) WRITTING BY ZEEYTERH YAR MAMA YAR MUTAN ZAZZAU. ________________________________ *AREWA WRITES ASSOCIATION* _________________________________ *💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦* _________________________________ https://www.facebook.com/104534761033461/posts/119016616251942/?app=fbl بسمالله الرحمن الرحیم و من یتوکل عل الله فهو حسبه۔ 🌹🌹EPISODE TWENTY SIX&SEVEN🌹🌹 Wannan paje din kyautace ga duk masoyin littafin GIDAN GADO. kuna sani nishadi yan AREWA WRITERS ina yinku irin sosai din nan luv u buhu buhu, amma banda kanawa da sakwatawa lolz 🤣 just for tsokana ce @⁨💞🖊💞ǟʊTǟʀ ǟʀɛաǟ💞🖊💞⁩ nadai yi shiru, Tafiya takeyi sosai tun Tana da karfin tafiyan, har ta fara yi tana daga kafanta da kyar, ga gari ya fara duhu jikin wata bishiya ta samu ta zauna, ta fara tunanin wai ita wace ce,a Ina take, Kuma Ina zata tanbayoyin data dunga ma kanta kenan, wasu Yan Fulani ce suka zo wucewa, ta kusa da inda take gaba ta kasa ko motsi saboda tsaban wahalan da Tasha, ga yunwa ga kishin ruwa datake ji, Har sun gota kusa da ita sai yarinyar tace" Baffa niko sai nake ga kaman nishin mutum karkashin bishiyan can, " Anya kuwa Shatu? Muje mu duba to,suna zuwa suka ga ummimi ce kwance rai hannun Allah da sauri Shatu ta dauko Goran ruwan su ta mika ma Baffa. Suka samu suka dagata suka bata ruwan, tana gama Sha ta dunga Amai, sbda ba komai a cikin ta tun safe don ko break fast batayi ba, Bayan ta gama ne, Shatu ta bata ruwa ta wanke baki ta kamata suka tashi, suka dorata akan jakin dasu tafe dasu,suka kada sauran dabbobin nasu sukayi gaba, Hajiya Yaya ce ta fito daga toilet, fitowan daza tayi sai dataji gabanta ya Fadi, kallon Akwatin kayan dake kan gadon tayi, ga Kuma wasu tarkace a kasa, ta fara tunanin waya hargitsamata daki oho, Akwatin dake kan gadon ta dauka ta Dora Daman drawer ta kwashe sauran tarkacen kayan dake wurin duk tasa a drawer, "Kwanci tashi yau sati biyu da batan Ummimi Amma ba Wanda yayi mgna, ba Wanda ya Kara tunawa da anyi wata Ummimi a gidan Fulani, "Maman Jafar Ashe haka maganin mutumin nan yake kaman yankan wuka'? Wlh abun ya ban mamaki harfa ita kakan nata ta manta da ita,balle ita uwar tata, balle wannan kodaddiyar tsohuwan 🤔, hhhh wai Hajiya innah kike magana? Dallah wake sa wannan a lissafi, dariya 😃 suka kwashe da shi,"yanzu saura wannan yaron na yola, "Ina so yanzu ya dawo ya nemi Baby tunda Kinga Bili yanxu take tasowa sai in anyi auren ta dauki bilin su tafi can Kinga itama sai ta samu nata mijin a can, "Ahayyye wlh kuwa Maman kin iya shiri shiyasa nake sonki, "Baiwar Allah mene sunarki ne? Wlh Baffa ban sani ba, ban San wacece ni ba, Ikon Allah Baffa dama haka na faruwa? "Sosai ma kuwa Shatu, walau ta samu hadari walau Kuma an mata Asirin dazai sa ta mance komai ne, "to yanxu mu Baffa ya zamuyi da ita, gashi mu matafiyane, Kuma ga halin da kasar mu take ciki ba gskya da Amana,shiyasa muka samu shuwagabanni dai dai damu,ga rashin tsaro sanadiyar haka na rasa Yan uwana, da mahaifiyata,Kuma muka bar garin mu gashi muna garari a daji bamu San inda, muka dosa ba,taya zamu iya taimaka mata Baffah,? "Karki damu shatu duk Wanda ya dogara da Allah Kuma ya taimaki wasu Allah zai taimakeshi,zamu cigaba da tafiya da wannan baiwar Allah har Allah ya bata lpy mu maidata ga iyayenta, Zubewa Ummimi tayi a kan gwiwanta hawaye na zuba a idonta, "na gode Baffa Allah ya saka maka da alheri,ya bamu ikon cin jarabawar Ameen suka amsa, Cigaba da tafiya sukayi suna tafe suna hira, kaman dama sun saba, dama Shatu akwai surutu, Dare ne yayi Baffa ya basu izinin su tsaya suyi sallah sai su Sha Madara su kwanta kafin gobe a cigaba da tafiya, Haka ko sukayi bayan sun Dan kafa bukka kusa da Dan korama sbda suyi sallah da wanka,bayan sun gama komai suka zauna Shatu ta dauko littafan islamiyanta, taje gurin Baffanta don yi bita inda Ummimi Wanda yanzu Baffa ke cemata Hajjo tunda basu San sunanta ba,itama ta Isa kusa dasu don itama ayi karatun da ita, "Hajiya Yaya lpy inata sallama kinyi shiru kin zabga uban tagumi,; "ke dai bari Hajiya Innah na rasa Mai ke damuna kwana 2, wlh kuwa Nima hakan take a gareni, wai nikuwa Hajiya Yaya ina, Koda bari inje inyi walha kar lokaci ya kure, to Nima yanzu na idar, tashi tayi ta fice Saida ta koma daki ta tuna Ummimi zafa ta tanbaya to wai Ina tayine? Niko nace Allah ya kyauta dai, Barci sukeyi cikin bukkan da Baffa ya hada musu, shi Kuma Yana bakin Bukkan ya shin fida tabarma Yana kawai jiyai an haskoshi da tochlight da sauri ya tashi wani mutum ya gani a kanshi, A,a Kaine a gidan namu? Eh Yayan mu, to mu shiga ku gaisa dasu Hajiyan,"to Allah yaji kan Alhji mallam da yanan gurin shi Zan fara zuwa, Kai dai bari ai munyi Rashi, Sun shiga sun fito gaba daya hankalinshi nakan ya tanbayi Ummimi Amma bakin shi yamai nauyi ya kasa tanbaya Kuma kullum da ita yake kwana yake tashi, Sai yanzu ya gane sonta yakeyi, To meya hanata komawa school,kodai aure aka mata, Kai Ina bazai yuwu ba Nusaibat tashi ce, Zaune take abun duniya ya isheta, school din ma ba dadi saboda bata, ita Kuma Bata San gidansu ba, ko gidan Guggonta datake zaune bata sani ba, Wai Raleeyat tunanin me kukeyi ne, kawai tsinta kanta tayi da cewa ba komai, Tofah masu karatu kutaya Ummimi addu'a domin tana cikin wani hali, kowa ya hasko Baffa, kudai cigaba da bin YAR MUTAN ZAZZAU uwar gidan kanawa, Dan uwa light bada Kai fa nakeyi ba lolz 🤪 🤪✍✍✍✍ [6/8, 14:26] 💞FAST CLASS💕: 💗💗💗💗💗💗 GIDAN GADO 💗💗💗💗💗💗 (BAFFAH) ________________________________ *AREWA WRITER'S ASSOCIATION* _________________________________ *💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦* _________________________________ https://www.facebook.com/104534761033461/posts arewawritersassociation@gmail.com WRITING BY ZEEYTERH YAR MAMA YAR MUTAN ZAZZAU بسم الله الر حمن الر حیم ا تقل الله حیس ما کنت 🌹🌹EPISODE TWENTY EIGHT&NINE 🌹🌹 Sakon taya murnan sallah ga dukkan yan group din (AREWA WRITTERS ASSOCIATION) da fatan munyi sallah lpy Allah ya Amshi ibadun mu 🙏🙏🙏 GIDAN GADO FANS kuma ina muku Barka da sallah Aunty Hauwa Sakon brka da sallah tare da fatan alheri Sai nazo yawon sallah Kawan aunty kayan sallah na na hannunki (Ummu Affan) Sai nazo amsa🙈🙈🙈 Aunty na ki shirya sokoto nake bida inyi sallah wanga sallah, Awo ki tanajeni da kayan dadi😋😋😋(Ummu Inteesar) Ina masu sunan yan gayu kawaye biyu (Hafscall da Sa,amlad) da fatan na fada dai dai 😜😜 Sai nazo yawan cin nama😋😋 Aunty Laurat da aunty Zainab Sai nazo karban cin cin din sallah😋😋 Tab ina Doctor Maryama Autar Arewa ki tana dan mun metronidazole sabo da tsaro ko da naci nama yamun yawa😂😂😂 Brothers Aliyu da Aliyu da dan uwa Muhammad kutama ku tanaji goron sallah ban san tsoffin kudi nafi san sabbi yan 2020 🙈🙈🙈 "Kai mallam tashi da Sauri Baffah ya mike lafiya bayin Allah Mai na muku?!! Me kuke bukata? Bai gama rufe baki ba yaji sauka bindiga a kafarsa, karan da Baffah ya saki ne ta tashi Shatu da Hajjo daga barcin da sukeyi, a firgice su Mike,!! Kuka Shatu ta fashe dashi "tana fadin shikenan sun kashemun Baffa na, toshe bakinta Hajjo tayi "kiyi shiru kar su jimu" Tattara gaba daya dabbobin sukayi, su kai gaba dasu yayin da suka kara Harbin Baffah a karo na biyu, Nan ya zube a gurin ba rai ba Alamanshi, bayan tafiyan sune su Shatu suka fito daga bukkan da gudu suka nufi Baffah "don Allah Baffah Karka mutu ka barni kai kadai ka ragemun a duniya" Shatu keta fadin haka tana gigiza Baffa, da kyar ya dago ya kamo hannun Shatu dana Hajjo ya hada da kyar ya bude baki "Yace ma Hajjo duk randa kika warke, kika tuna Asalinki ka yar uwanki nan ki taimaketa kamar yadda muka taimakeki bata da kowa yanzu a duniya Sai ke, ku kiyaye mutuncinku duk runtsi karku rabu da juna Allah ya tsaremun ku ya albarkaci rayuwarku,,,,!!! Maganar da bai karisu ba ke Baffah ya rasu😭😭. Haske sun da akayi da toch light ne yasasu mikewa da Sauri dama akwai wata jaka rataye a wuyan Shatu, aikam suka rike hannu juna su ranta a na kare, aikuwa barayin nan suka rufa musu baya,,!! "Wai Hajiya Yaya meke damunki kwana biyu duk kin rame ko duk mutuwar Alhaji Mallam din ne yake kara dukan ki"? Ke dai bari ni na rasa meke damuna Aishatu, to Allah ya yaye mana damuwa, "bari inje in Dora girki Abban su Umar ya kusa dawo wa, " to yar albrka. "Maman jafar wai ya maganar rabon gadon Alhaji Mallam ne? "Ke dai bari ni gidan nan nakeso a raba kowa yaja katan ganshi in dai na ganin makiyan nan namu, 😀😀😀 dariya sukayi, suka tafa, "yauwa wai ya maganar komawa gurin bokan nan ne? Ki bari gobe zamu Sai a turaro shi yaron yazo kawai ayi ayi a wuce gurin wlh kuwa mu kwashi arziki,,,,!!! Dariya suka karayi "kinji inje in Dora sanwa kin san Billy bazata taba yin aikin nan ba, "wlh yaran yanzu san jiki ya musu yawa aje gidan miji ba,a iya komai ba, "Ai da sauki ma ya dauko mata yar aiki, Tofa readers kunji tun ba,ayi auren ba ake maganar yar aiki😀 Allah ya shiryi masu hali irin nasu Ameen🙏🙏 Ku cigaba da bin YAR MUTAN ZAZZAU don sanbado muku lbr✍️✍️✍️✍️ [6/8, 14:26] 💞FAST CLASS💕: 💗💗💗💗💗💗 GIDAN GADO 💗💗💗💗💗💗 (SHATU&HAJJO UMMIMI) WRITTEN BY ZEEYTERH YAR MAMA YAR MUTAN ZAZZAU. ________________________________ *AREWA WRITER'S ASSOCIATION* _________________________________ *💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦* _________________________________ https://www.facebook.com/104534761033461/posts arewawritersassociation@gmail.com BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM 🌹🌹EPISODE THIRTY&THIRTY ONE🌹🌹 Kanawa yaran zazzagawa ina muku brka da sallah sai kun kawomun naman sallah don kusamu albrka na😜😜😜 Gudu sukayi na ceton rai inda Shatu ta fadi, "Don Allah yar uwa ki tashi gasunan zuwa fa, "Hajjo ki Gudu ni karfina ya gama karewa, ki Gudu ki ceto ranki ki barni su kasheni in bi Baffa, ki Gudu nace gasunan fa, "ni bazan Gudu ba sai dai su kashemu tare, "don Allah ki gudu,!! Badan Ummimi taso ba ta tashi tana hawaye tanajan Shatu, Shatu ta fisge hannunta ta turata, haka Ummimi taci gaba da gudu, barin gurin nata yayi dai dai da isowan su, "Oga ita kadai fa ta rage kuma da,alama nunan rana ce fa za,a shana, hhhh "kai jj baka da kyaufa amma wannan yar shilan meza,a ci a jikinta, "kai Oga irinsu fa sunfi dadi fa, "kai damisa aikata inda muka aika ubanta Kaji, ita ma dayar a shiga dajin a nemo min ita, "a,a Oga kar a kashe yarinyar nan zatayi mana Amfani fa, "dob Allah ku kashe in bi mahaifina yafimun ku taimaka mun ta karasa maganar tana fashewa da kuka!!!, "Kuma JJ ya kawo shawara tsula dauketa ka kaimun gida akwai Amfaninta, haka tanaji tana gani kato ya sabata a wuya, Wasu suka bi bayan Ummimi. Iya gudu tasha don kwana tayi ta gudun ceton rai, Ankira sallah Asuba yayi daidai da zuwanta bakin titi, ta zube a gurin, dai dai wani Mota ya kwasu a guje har ya wuce ya dawo baya, wani matashin saurayine ya fito a Motan bazai wuce shekara Ashirin da takwas fa daga ganin shi kasan hutu ya zauna a tare dashi, black beauty ne ga wani zagayayyen saje da ya tsagaye dogon fuskan shi yana da manyan idanuwa, da dogon hanci wanda yai dai dai da karamin bakinshi, yana da fadin kirji kana ganin shi kaga irin sadaukan mazan nan masu motsa jiki, Da sauri ya kariso gurin sai da gaban shi ya fadi ganin ta da yayi, tattaren hannun riganshi yayi ya dauketa sai yaji kaman ya daga takarda saboda tsaban Rashin nauyinta, Mota ya kaita ya shimfideta gidan baya ya rufe Motar ya zaga ya shiga, ya figi Motan da gudunshi, "Yaro kasan yau Abokinka zai dawo daga jos, ya kamata ku fitar da matan Aure kai dashi gaba daya kunki Aure, Asibitin naka ma ka dena zuwa, can Makarantar ma da kake dan zuwa can zaria shima ka bari, gaba daya baka da walwala na rasa meke damunka,? Iye ka fadamun mana, "wlh Momy ni kaina ban san meke damuna ba, kawai dai jikina yana bani na rasa wani Abu mai muhimmaci a rayuwata kuma na kasa tunawa," "To Allah ya yayemaka damuwan yarona kayi ta Addu,a Amma nidai na kosa kuyi aure, "inshaallah Momy zamuyi, Allah yasa inga lokacin "Ameeen Momy" Horn ya keyi a wani Kofan gate na Asibiti ba tsayawa me gadine ya zo da gudu ya bude mai gate, "Barka da zuwa maigida Ashe kazo garin ne Eh kawai yace mai figi Motan shi, tun kafin ya iso yake kiran shi bai dauka ina ya ajiye wayan ne. Ko gyara parking baiyi ba ya fito da sauri yana kiran Nurse, Nurse!! Nurse!! Da gudu suka kariso da gadon daukan marasa lafiya, don sun san halin Oga Ammar ba hakuri, gungurata sukayi suka shiga da ita emergency, ya rufama musu baya, ba kuma wanda ya isa ya hanashi shiga yanxu ka jama kanka kora, "Al'ameen hankalina yana tashi kwana nan na rasa meke damuna, "ki bari kawai Ummah wlh duk haka muke, ni ina tunanin rikice rikecen gidan nan da rasuwan Alhaji Mallam duk shi ke damun mu, hayaniyar dasu kajine yasa su fitowa da sauri Ashe fada akeyi da Baban su billy da matar kaninshi, "kai Umma Allah ya hore mana mu tashi a gidan na, Rigimar Gidan Gado

Chapter 3 of 12