exam,ok barin Abban iro ya shigo zan fada mai, to ngd mami.
zan shiga makota barka ki karasa girkin can,sai kin dawo.
yankan albasa takeyi tana bin karatun kur,ani datasa a wayanta kawai jin mutum tayi ya rungumota ta baya, ihu tayi iya karfinta tana kiran mami,ke matse mata baki yayi, ke nice fa baby zaro ido tayi hadi tureshi cikin masifa da takaici ta fara fadin haba yaya iro kasan ba kyau hakan, please karka karamun irin haka haba ummi zan dan gaisa da ajiya nane kullum sai sun tsokalemun ido yana fadan haka yana kara matso ta, tana kara matsawa nifa yar uwarka ce yaya iro karka batamun rayuwa ni yarinyace karama please yaya iro haka rungumota yana kokarin daukanta zuwa dakin shi,tana dukanshi da yakushin ship, amma bai sauketa ba ya fito falo dauke da ita, dai dai lokacin mami tayi sallama cikin falo,,!!daskarewa mami tayi a tsaye me idanunta suke gane mata iron ta ke shirin lalata mata yar dan uwa a cikin gidanta,sauketa yayi da gudu ummimi taje ta rungume mami tana kuka kaman ranta zai fita,zuwa yayi zai wuce ta gabanta wani lafiyayyun mari mami ta sauke mishi, cikin fushi take nuna shi nayi danasanin haihuwanka iro kanwarka,!! akuyan cin naka har ya kai haka iroohh bar gidan kafin inkusa kashe wlh!!!
Kiyi shiru ummimi na don Allah wannan mgnar ya zama sirri a tsakin mu ni dake please umimi karki fadama hajiya yaya na miki alkwarin hakan bazai kara faruwa ba kinji yata? eh naji guggo insha Allah.
washe gari ummimi ta gama hada duk abunda zata bukata ta fito sai ga mami ma ta fito da mayafi a hannu, muje ko, to mami suna isa school raleeyat na zuwa taryan su, gaida mami tayi, mami ta ansa tana kallon raleeyat tayaba da hankalin yarinyar hakan yasa ta kara amincewa da zaman ummimi tare da ita, har hostel din sai da taje ta ga inda yar ta ta zata zauna sannan ta kara musu nasiha su kula da kansu, suyi abunda ya kawo su, insha Allah mami sai na dawo haka mami ta tafi tana kewar yarta,
fita sukayi domin su debo ruwa, uncle mubarak da uncle Aliyu suka gani sun shigo school din a motan uncle mubarak din shi yake driving din,har su sun wuce sai yayi revers ya dawo ke ku kawomun ruwa a gida banda ruwa,,!!!raleeyat ne jikin ta na rawa ta ansa da to,ita ko ummimi banza tayi dashi ke i am talking to you kinyi shiru,sir na amsa ai tana murguda mai baki ta juya,kawai samun kanshi yayi da murmushi😊 kawai uncle Aliyu sakin baki yayi yana kallon shi imaging abunda zai sa mubarak dariya, anya yarinyar nan uhmmm tafiya sukayi sukuma su ummimi sukayi gaba diban ruwansu,sai da suka yi guri sahu biyar gidan uncle mubarak,sannan su ka wanke mai toilet suka gyara mai gida sannan suka debo nasu,ranar ba karamin gajiya sukayi ba,gashi duk aikin nan dasuke mai yana zaune a falo yaki fita,haka suka koma hostel a galabaice ranar ko iya zuwa karban abinci basuyi coonflex suka shabbier,
besty besty ki tashi muyi karatu,uhmmm kai besty ki bari sai asuba,no kin san dai gobe karbe takwas muke da exam, kuma kin san baki iya calculation din physic dinnan ba kuma zai iya fito mana a exam,haka ta tashi suka dunga karatu har saida ta tabbatar sun gane sosai sannan suka kwanta,asuba nayi sun dauki bucket zuwa masallaci daga nan su debo ruwa,sun ajiye buckets din ruwansu a bakin fanpo suka shige masallaci,bayan idar da sallah sukayi azkar suka danyi karatun kur,ani, bayan gari yayi haske suka zo fanpo don su debi ruwa su Afra suka tarar a gurin suna diba sai suka koma gefe suna jiran su gama, bayan sun gama suka dauki ruwan su zuwa hostel duk da su afra sun takalesu amma basu kulasu ba,sbda raleeyat tayi iya kokarinta na ganin kawanta bata kulasu ba,
Exam hole bakajin karar komai sai na fanka da paper can na hango ummimi a can karshe inda kawanta take farkon hole, uncle mubarak shine invigilators nasu yana ta kai kawo a hole din,sir i need extra bucklet, ok,mika mata yayi ta cigaba, sir i am pinish, are sure? yes sir, check it dai, nifa na gama ok kawo tayi submitt ta fice can sai ga besty ta tafito,
kwanci tashi ba wuya a gurin Allah gashi yau su umimi sun gama exam kowa ka gani ranar farin ciki yakeyi,ummimi har wani rama tayi sbda exam dama ita ba auki ba a lkcn kuma ummimi ta cika shekara sha shida ta kara girma duk wani abu na cikan budurwa ya bayyana ga ummimi kyace ta kai shekara ashirin ne sbda Allah ya hore ma ummimi dirin jiki doguwa ce ummimi ga hips da Allah ya wadata ta dashi, fara ce ita sosai tana da manyan idanu tare da tsara tsaran gashin ido pink lips gareta gami da dogon hanci,ga kwantaccen gashin kanta tun daga goshinta har gadan bayanta nannadeshi takeyi tayi kaman acuci maza, dama kuma ita bata cika son kitso ba,
yau ya kama zasuyi hutu,an taru gurin assembly don karban hutu, malamai duk sun taru principal ake jira bayan an bude taro da addu,a a ka gabatar da kyaututtuka ga dalibai ciki har da su nusaibat da kawanta bayan bada hutu kowa ya kama gaban shi students na ta tafiya gida jensu, wasu kuma ana ta zuwa daukan su,inda yayan raleeyat yazo daukanta, da gudu taje ta rungumeshi irin su daya da yayanta kasan cewansu black beuty oyo yo sweet bross oyo yo autan Ammah shine Ammah bata biyoka ba sorry Ammah tana can tana hada ma autan ta deliseous food, uhmmm wato besty tunda yayanki yaxo kin ma shareni kin manta muna tare,ayyah sorry besty na my bross meet my best freandy besty meet my sweet bross, ina yini yayan mu ya hanya, shikam yaya gaidashi akeyi amma gaba daya ta tafi da imaninshi,sai da tace bross ya dai besty na nata gaidaka, da sauri ya dawo hayacin shi yana amsawa sannu kawan mu ya exam i hope kunyi kokari duk da nasan kannina masu kokarine,sunkuyar da kai tayi sbda kallon dayake mata,yaya dama zamu je gidan guggonta tayi mata sallama sai mu sauketa a zaria to shikenan ba matsala kanwancy duk yadda kikace haka za,ayi yauwa dats y i love u yayana suna shirin shiga mota sai ga uncle mubarak yazo ga dukkan alama su yake nema, lah besty ga mutumin ki can,sai gashi ya iso gun su hannu ya mika ma muhammad suka gaisa are you raleeyat ya,u brother yes dats naga kunyi kama am i want see nusaibat please🙏 ok nusaiba ur uncle talk to u nan da nan ta daure fuska ta fito munyi waya da guggonki tace mun yayanki Ala,ameen zai zo daukanki ya kusa isowa, sbda haka muje office dina ki jirashi, ita mamaki ne ya kashe nusaibat ta ina yasan guggonta balle ya Ameen, inda haushi ya isa mohammad da sister shi, ba haka suka so ba haka suka tafi muhammad yana jin wani haushi mubarak yayi da ya sanin tsayawa da yayi, bayan sun tafi ne ya juya ya koma office dinshi yace inkin ga dama ki biyoni ko kuma kita tsayuwa a gurin,kawai hawaye taji yana biyo mata fuska haka ta bishi tana zuwa ta motan shi a bakin office din bude mata yayi yace shiga muje,inje ina dama ba yayana dazaizo daukata kace za,a daukata tsawan daya daka matane yasa ta shiga da gudu, ya bude but ya zuba mata kayanta a buta ya rufe ya fito ya shiga mota suka kama hanya,,,,✍✍✍
freands an samu mistake dana ce muku jss one suke ss one zance, ngd i hope kuna biye da yar mutan zazzau, bazan daina yinku ba Arewa Writters Association one love🥰🥰
[6/8, 14:26] 💞FAST CLASS💕: 💗💗💗💗💗💗
*GIDAN GADO*
💗💗💗💗💗💗
*(NEW LIFE)*
*WRITING BY ZEEEYTERH YAR MAMA YAR MUTAN ZAZZAU.*
________________________________
*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com
_*ASTAG FIRILLAH WA'ATUBU ILAIH.*_
_*🌹🌹 EPISODE FOURTEEN & FIVETEEN 🌹🌹*_
*Innalillahi wa'innah ilaihirraji'un,Allahumma ajirni fi musibaty wa aklifni khairan minha,ya Allah muna tawassilli da sunayenka kyawawa ka kawo Mana karshen wannan masifa ta Corona virus, don wannan cuta ta zama musifa garemu, Allah kabama Wanda suka kamu lpy, mukuma ka karemu ka nisantamu da ita da dukkan musulmai duniya baki daya 🙏🙏🙏*
_*Wannan page din nakune Yan Arewa writers gaba dai gaba dai Allah ya Kara hada kawunan mu,ya Kara Mana hazaka da fasaha da tsakin hannu,Aunty mu hauwa munayinki irin sosai dinnan Allah ya Raya zuri a Ameen 🙏🙏*_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
I hope kuna ganewa? Yes sir ok akwai Mai tanbaya no sir ok gobe munada text by second period, where is class captain sir ok kiyimin submit na Assignment dina, can't hear me I am taking to you, I say ok sir juyawa yayi ya fice, wow besty wlh teacher nan yayi fa mtsww wlh besty kin cika ban haushi meye abun birgewa a gurin me shegen girman kan tsiyan nan ni haushi yake bani dazu fa danaje Kiran shi a office nashi nafi minti arba'in Ina Mai magana kafin ya dago ma ya kalleni balle ya amsani,ni wlh indai period dinshine sai dai ki dinga zuwa kina kiranshi don bazan Kara zuwa a wulakanta ni ba, yanxu bari nayi submitting assignment din ki Kai mishi, tab wlh besty ni ma tsoron shi nakeji sai dai muje tare, wlh baxani ba,oya class ku hada assignment dinku kowa ya kawo nashi,bayan ta gama hadawa ne ta mikama Raleeyat besty Kai mishi, excuse sister nusaibat farhat da Maryam basu bada nasu ba sun mantoshi a hostel sunje daukowa, Ana maganar sai gashi sun shigo farhat ta mika mata gashinan sai aje a kaimana in anga dama, me kama da aljana yarinya karama wai ita ce shugaban mu don an raina Mana wayyo, ai wlh uncle Abubakar San Kai yayi,ke dakata!!! Tsawan da nusaibat ta daka matane yasa ta tayi shiru Bata karasa maganar ta ba,wlh bari kiji in gayamiki bar ganinki katuwa bazai bani tsoro ba ni nusaibat ba,a mun na kyale Wanda ya fiki ma bai isheni ba balle ke karamar alhaki banxa guxuman banza in kin Isa ki tabani ki gani, ke ni kike gayama haka Maryam ku sake ni inci uban yarinyar nan,ki dai ci ubanki don ubana yafi karfin ki,haba besty don Allah ki rabu da ita Mana in karya na haushi ki barta tai tayi zata gaji ta bari, ke Raleeyat ni kike cema karya ko wlh dukanku dake da kawar taki zaku San Kun taboni janta kawayenta sukayi itama raleeyat taja nusaibat suka fita a class din don zuwa office din uncle Mubarak,don tasan in ta barta baza,a kwashe da dadi ba don tasan halin besty nata, haba besty ki dunga hkr Mana ki daina biyema su farhat kin San halin su fa, su basa son zaman lpy, besty bazaki gane bane nifa ba yarinyar data Isa ta takani in kyaleta ai sai suga kaman tsoron su akeji,to in banda abunki besty inake Ina farha kina jin ki kaman sillen Kara duka nusaibat ta kaima raleeyat ai gunda ni dake,to dame kika fini don dai hips din da kike dashine za,a ga kaman kin fini kiba😏 oho dai nadai fiki Kuma wlh ki kiyaye farhat kar kija ta zanemu fa😃😃 Kuma kin San wani Abu besty wlh nidin ba karfi gareni ba duk cika bakine😂😂, Amma andai ji kunya naji din, daidai sun iso office din uncle Mubarak, nocking raleeyat ta farayi sun Kai minti Sha biyar suna nocking har sun cire rai daza,a bude raleeyat tace besty ko baya nan ne,wlh yananan wulakanci ne zomu tafi, yes come in ajiyar heart sukayi a tare Ashe besty da gskyanki tab lallai kinyi gskya,ok shiga ki Kai Mai don Allah bazan shiga ba,
Bude kofan raleeyat tayi ta shiga hadi da yin sallama it's dai bataji ya amsa ba tadai ga mouth nashi yayi motsi alamun amsawa,well done sir,banza da ita yayi Yana cigaba da rubuce rubucenshi, uhmm dabur cewa tayi duk ta rude,sir dama dama assignment din dakace ama ama submit ne na js 1a, will you shut up my friend!! Tsawan daya mata sai da ta firgita taji kaman ta zubar da littafan ta gudu,are u d one I am asking you to submit my assignment? Am no sir but I am asisstant, she not feeling well,ok out of my office,ta kawomin da kanta ko Tana tafiya tana faduwane ok sir thank you,ta juya har ta Kai kofa yace ma look ta waigo kice na bata five minutes in ganta a office dinnan ok sir.
A sanyaye raleeyat ta fito ta samu nusaibat a zaune Tana charabkenta hankalin ta kwance, a,a besty ya dai Naga ranki a bace, meya Miki inje in Mai rashin mutunci yanxun nan, a,a bai karbi assignment din bane,to wanne Zan amsa Miki a ciki iye,uhmm to yace ki Kai Mai da kanki tab Allah bazan Kai ba😏, sorry my besty ki taimakeni ki Kai mishi ba don halina ba, ban San wani Abu ya sameki kin San hankali na bazai kwanta ba Kuma wlh zai iya dukanki, kema kin San dukan ki dai dai yake da a watsamun tafasasshen ruwa please besty, uhmmm kawo nasan yanxu sai ki faramun kukan naki na fama komai kuka,is ok Zan Kai shikenan kin ji dadi 😏,eh ngd my sweet besty na,to kiyi dariya Mana😃😃 nayi to yauwa ko kefa,ok na tafi sai kin dawo,ko nocking bata tsaya yi ba, ta bude kofan office din ta shiga,komai bata ce ba taje kan table din office din ta ajiye takardun ta juya, gaba daya mamakin karfin halin yarinyar yakeyi yasa har ya kasa mata magana har Saida ta fita, ya kaima iska naushi oh my God wai meke damunane meyasa ban Bata punishment va har na bari ta tafi,
Babbah yane? wlh zanje dauko Yar shila tace a makaranta hhhhh 😂 wai wannan Yar faran yarinyar danaganta a mashin dinka eh ita fa, Kai wai a Ina kasamota ne? Wlh yarinyar kawu nane na zaria, Mami so take fa ta hadamu aure Kai babbah wlh baku dace da yarinyar nan ba,tafi kar finka,hhhh koh wlh saita soni kuwa tab kana da aiki,
Besty inaga in an kusa fara exam gurinki zan dawo a hostel muji dadin karatu,wlh danaji dadi kuwa besty,Kai ga Dan jagaliyan yayanki can yazo,kefa besty baki da mutunci,har Ina Mai ruko Naga zaku dace🤪,kut Amma besty kin cuceni nama fasa gaisheshi kin jamishi,ta juya ta tafi ita Kuma ta karasa gurin Yaya iro tun daga nesa yake kallonta irin kallon data tsani ya dunga mata,harta karaso bai San ta iso ba,sai da tamai magana Yaya iro muje Mana au wai kin hau ne ? Kaji ka ma,ni mutafi na gaji Jan mashin din yayi suna tafe suna hira har suka Isa gida,
Aslm Mami mun dawo sannu ya'ta ya karatun Alhmdulillah,sannu da hutawa Abba yauwa, iro ne ya shigo ko sallama Babu yauwa Abba yaushe ka dawo Dan Abba yanxun nan na dawo, dama wlh Banda kudi oh no zuwaira wai yaushe iro zakayi hankali, ka shigo ba sallama balle sannunku sai tanbayar kudi to baza,a bada ba,uhmmm Abba kaji Mami Koh zata fara, Kinga dakata zuwaira bansan fa takura,au haka ma xakace Alhaji duk Kai ka gama lalata yaron nan,Ina ruwanki, my iro karbi ATM card dinnan kaje ka Ciro yanda zai maka yauwa Abban Ina yinka over,fita yayi.
Haba Alhaji wannan ba gata bane wlh, to in Banda abunki in ban ma iro ba wazan ma shi kadai fa nahaifa, duk da haka bazai hana mubashi tarbiya ba to n
Kwanci tashi ba wuya a gurin ubangiji gashi su ummimi har sun kusa fara exam,inda fada tsakanin ta dasu farhat yake dada ci gaba,ga uncle Mubarak ya taso ta a gaba duk ummimi ta rame ga karatu, dama ita sai a hankali...✍️✍️✍️
Up UP AREWA WRITER'S ✍️✍️
[6/8, 14:26] 💞FAST CLASS💕: 💗💗💗💗💗💗
*GIDAN GADO*
💗💗💗💗💗💗
*(SWEET MOMENT)*
*WRITTING BY* *ZEEEYTERH YAR MAMA YAR MUTAN ZAZZAU.*
بسم الله الر حمن الرحیم
رضیت با الله رب و بلاسلم دین و با محمد نبیا.🙏🙏
________________________________
*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com
*🌹🌹EPISODE EIGHTEEN&NINETEEN🌹🌹*
bazan gaji da baki page ba aunty hauwa (maman uswan) Allah ya raya zuri,a ina godiya da karamci ke din ta da banne,Allah ya albarkaci zuri,a🙏🙏
GIDAN GADO FANS group ina yinku Allah kara habaka group din ya bani ikon fadakar daku da nisha dantarwa ya kara hada kan mu🙏🙏ga masu bukatan shiga group sai suyi min mgna ta wannan number 09025305818 thanks.
Wai uncle ina zaka kaini iyeeeh? ta karishe maganar tana shirin yin kuka, ko kulata baiyi ba yana ci gaba da tukin shi yana kuma jin kukan ta har cikin zuciyan shi, kuma bazai iya lallashinta baa, cigaba tayi da kukanta kawai gani tayi sun wuce gidan su guggo sun dau hanyar zaria, ita gaba daya ma abun nashi ya dena bata mamaki tsoro ya koma bata ita dai tasan bata taba gaya mai ga garinsu ba, kuma taga ya kama hanyar zaria kuma tasan ance shi dan yola ne,
tafiyane mare dadi ga ummi, shiko uncle baiki su kasance a haka ba jin shi yake a cikin farin ciki, ya rasa meyasa zuciyanshi take mai haka ta rasa wanda zata fara so sai wannan yarinyar, kanwar kanwar shi, a haka har suka iso zaria, kawai kallonshi take taga ikon Allah sai gashi sun iso har cikin kusfa kasancewar mota baza takai kofar gidansu,yasa yayi parking a bakin titin da zai kai ka zuwa kofar gidansu fita yayi yana waya hakan yasa ita ma ta fito,can sai gasu yaya umar da jafar dasu bilki sun iso suna oyo yo yar bording ta dawo, tunda jafar ya doso idon shi a kanta, duk da tana cikin mamakin uncle bai hana ta murguda ma jafar baki ba tana cemai lpy? shima uncle ya lura da kallon da jafar yake mata wani abu ne ya taso mai ya tsaya mai a makogoronshi da sauri ya kareta daga kallon da jafar yake mata gurin taran su ya mika musu hannu don su gaisa,niko nace hooo uncle namu kishi ya motsa😜😜,
mallam umar da jafar koh sannunku fa ya gida ya aiki? Alhmdulillah ya kaji da dawainiyar kanwar mun gde juyawa ummimi ta karayi tana kallon uncle mubarak da mamaki a fuskanta hada ido sukayi ya sakin mata murmushi tare da🤫 irin ki shiru din nan, ya umar ina wuninku lpy ummimin hajiya barka da zuwa yauwa daukar jakanta tayi tayi gaba abunta, tana shiga gida hayaniya ya fara mata well come, runtse ido tayi tana jin tsanar halin yan gidan nasu tasan dai bai wuce fadan dasuka saba hakan kuma ya nuna mata Alhji mallam baya gida,oyo yoyo auntyn mu mami ne ta rugo da gudu tazo ta rungumeta ni na riga ganinki,gaba daya sai kallo ya dawo kan ummimi a,a yan makarantan kwana an dawo maman su jafar ne take fadin haka yayi da maman su bilki take cewa ikon Allah wannan makaranta ta karbeki ummimin hajiya kinga inda kikayi bul bul abinki sai dan rama da kikayi, kowa dai sai da ya tofa albrkacin bakinshi,ita dai ummimi ta gaidasu tayi gaba abunta sai ga hajiya yaya ta fito oyoyo oyo ummimina na kasa hkr ki karaso sbda nayi kewarki sosai da gudu ummimi ta karasa ta makalkale hajiya yaya, i miss u too hajiyana to kaji turawa meye kuma muss u kamar kiran mage kwashewa ummimi tayi da dariya🤪🤪kai hajiya ni ba haka nace baa,to mukarasa ciki mana, uhmmm iyayi yar son su ta dawo ni wlh inda na tsani mutuwata haka na tsani yarinyar nan ke kenan maman jafar ai in ana sallah ba,a mgna mtsssww yarinya kaman aljana ni naga kyau ma take karawa wlh, ba dole ba wayasani gantalin ta takeyi a makarantar ita fa da wannan yaron ne dayake zuwa gurin Alhji mallam dan abokin nan nashi da yake yola😱 ki bari don Allah wlh kuwa kardai yace yana sonta, ki bari kawai ai wlh da kyar in baice ba, tab ai wlh zuwa gurin mallam mai gobe da nisa zan je goben nan kuwa don da Aminatu ya dace bada ita ba,ai maje tare don nidai na tsani yarinyar nan taci gaba,bayan sun gama gulmansu kowa ya watse ya kama gabanshi, niko nace ta Allah ba taku ba mahassada,
sallama akayi duka suka waiga yaya umar ne da yaya jafar suka shigo sai yanzu ta tuna sunzo da uncle yaya umar ne ya kawo mata rankwashi jafar yayi sauri ya rike hannun shi meye haka kai kuma zaka rankwasheta, wayyo hajiyata kinga ya umar ko!! daga dawowata zai fara cin zalina,umaru ka fita idona in rufe wlh,haba hajiya yaya wai yaushe yarinyar nan zatai hankaline iyeh? tare fa sukazo da wanan malamin nasu dan gidan abokin mallam dake yola shifa ya kawota amma yarinyar nan ko ruwa bata iya ta kai mishi baa,tazo amma ita kin tasa mata abinci kala kala tana ci tana surutu,uhmmm toni bana mance bane😏, kai ummimi baki kyauta ba tashi ki dauko flask din can kije ki kaimai ga ruwanan a fridge kije kitchen ki dau plate to ta tashi tana zunbura baki yaya jafar ne ya tari gabanta kawo kinji ummimin hajiya in kaimai jeki ci abincin ki ki huta, yauwa yaya jafar ngd juyawa yayi yama umar 😛 ya fice, itama ta cigaba da cin abincinta tana hararan yaya umar, ke ni sakon kine, hhhhh to da kai meye in ba sakonta ba umaru inji hajiya.
oyoyo my amarya ashe kin dawo dan albrka ashe ya kawoki ai mubarak akwai kirki shiyasa na bashi amanarki,duk sati sai yazo nan ai,zaunawa yayi suka gaisa ta kawo mai ruwa, sai ta tashi ta tafi shashinsu,can ta tarar da Abbu ya dawo sun shinfida tabarma a waje kasan cewan lkcn zafine, yana jin labarai a rediyo karasawa tayi ta zauna kusa dashi ya shafa kanta uwata an dawo lpy ya karatu? Alhmdulillah Abbu mun sameku lpy? lpya lau,aunty momi brka da dare, yauwa kin dawo lpy lfiya lau,mama tashi tayi ta koma kusa da mamanta, nayi kewarku mamana bayan sai yanzu aka zo ganina, sorry mamana.
kwanci tashi ba wuya gashi yau har hutun su ummiimi ya kusa karewa suna shirin komawa makaranta,inda jafar ya cigaba da shige ummimi abunda da bayayi tsakaninsu fadane da yar harara.✍✍✍✍
kuci gaba da bin yar mutan zazzau zata cigaba da san bado muku gami da suburbodo muku typin comment and share,
Arewa writter Association ina yinku irin sosai dinnan Allah ya kara daukaka kungiya🙏🙏🙏
[6/8, 14:26] 💞FAST CLASS💕: 💗💗💗💗💗💗
*GIDAN GADO*
💗💗💗💗💗💗
*(RESURMING HOLIDAY)*
*WRITTING BY ZEEEYTERH YAR MAMA YAR MUTAN ZAZZAU.*
بسم الله الرحمن الرحیم
حسبی الله للا اله الی هو علیه توکلت و هو رب العرش العظیم🙏
*🌹🌹EPISODE TWENTY&TWENTY ONE🌹🌹*
________________________________
*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com
*page din nakane NURRADDEEN LIGHT ina godiya sosai Allah ya bar zumunci ina yinka irin over dinnan💕💕*
*ina tayaki murnar fara sabon novel din ki sister LAURAT Allah yasa a gama a sa,a Ameen.*
*Aunty bazan yi tuya in mance da albasa ba aunty mu Allah ya kara miki lpy da nisan kwana ina yinki AUNTY HAUWA 💖💖*
Ummimi wai bazaki fito ki tafi kasuwan bane kinsan in yamma tayi ba wanda zai barki ki fita koh,
uhmm ni hajiyata nifa kawai ki aiki su ya umar kinga bili tace bazata rakani ba zata gidan innanta a kaura, oh ni nusaibatu shiyasa dama tun dazu kike ta shiririta koh?*
*Sallaman da akayine duka suka juya suna kallon me shigowa,
uhmmm ai wlh hajiyata karki bani hkr ni ba ruwana da yaya Ameeen tun fa randa na dawo nake fadimai na dawo ko yazo ya ganni, ayyah my kanwancy don Allah a mun afuwa wlh karatu yasa yayanki a gaba, uhmm!! ni sai ka kama kunni zan hkr, ok ai sai inyi dukawa yayi,tayi sauri ta rukoshi lahhhh,!! my yayancy da wasa fa nakeyi tashi, tashi yayi yana dariya ae nasan kanwancy na sona,bari in kawo abinci kasan me hajiyata yau tayi? a,a sai kin fada uhmmm best food dinka fa tayi, da gaske ? Allah kuwa kaman tasan zaka dawo bari in dauko maka kitchen din fallon ta shiga ta kwaso mai
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 12