tace ya bari suci abinci tukkunna tunda Saheeba sai daren nan ma ta dawo gidan shi kuma yace ya gaji kwanciya zaije yayi yau bazai dawo hira ba AA bai tashi ba har sai da su dukansu suka isa dining ɗin. Maanal ma dai tana haɗa takardunta ne. Ita bama tasan AA ɗin bai tashi ba, sai da ta yunƙura zata miƙe suka haɗa idanu. Harrarta yay ita kuma ta taɓe baki. Dan tasan bawai ya daina jin haushin nata bane daman, ko ɗazun saboda ganin Oum ne.
Bata sake kallon inda yake ba ta nufi dining ɗin, sai lokacin shima ya miƙe. Kujerar kusa da Maanal ɗin yaja ya zauna, Fawzan dake kallonsa cike da neman tsokana ya wani ɗage masa gira ɗaya. Harararsa AA ɗin yayi ya ɗauke kai. Shima Fawzan ɗin sai yay gyaran murya, kallonsa duk sukai, sai kawai ya basar. Babban Yaya daya san halin tom and jarry ɗin ƙannen nasa kansa kawai ya girgiza, dan ya tabbatar da AA Fawzan ɗin yake. Kowa zai fara ƙoƙarin zuba abinci karaf Nuratu ta miƙe acewarta bari ta saka musu. Babu wanda ya hanata, dan haka ta fara zubama Oum, sai babban yaya da Fawzan, gaban AA ta dawo har tana ɗan duƙo masa wai zata ɗauki plate. Wani irin zafi ne ya turniƙe zuciyar Maanal, shiko AA ɗin ma hankalinsa ba'a nan take ba, waya yake latsawa, tabbas yana jin ƙamshin turare mai ƙarfi a kusa da shi, amma baima san na wanene ba duk da ya fahimci baƙon ƙamshi ne bai taɓa jinsa a wajen kowa ba a gidan. Nibras ce ta shigo da sallama a cikin tata kwalliyar.........✍️
_Maanal tamu kenan, gaki kuma a tsakiyar kuraye😂, bari muga yaya wasan zai kaya🏃🏃🤣_
*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*
*09032345899*
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
*_BOOK 2_*
🅿️➖2️⃣4️⃣
______________
........Cikin ladabin son birge AA ta shiga gaida Oum, da kulawa Oum ɗin kuwa ta amsa mata tana tambayarta yaya aikin?
“Alhamdullah Oum, tumma ɗazun na tashi na biya ta gida ne ganin Mom da tace ƙafanta na ciwo”.
“Wayyo ashsha ALLAH ya bata lafiya, yaya jikin nata?”.
“A Alhamdullah da sauƙi sosai, bama a kwance take ba”. Ta faɗa tana harrar Nuratu dake zubama AA abinci, tunda ta shigo akanta idannunta suka fara sauka, ji tai kamar ta shaƙo shegiya, dan tayi ma mamaki ubanmi ya kawota gidan. Maanal da itama dai ta shaƙa ɗin da iskancin Nuratu amma ta fiske babu wani alamar komai a fuskarta atare ita da babban yaya suka jajantama Nibras ɗin batun jikin mamanta. Sai Nuratun itama tayi mata jajen. AA dai kamar ma bai jisu ba sai da Oum ta kallesa, a taƙaice batare daya ɗago ba ya ce, “Sorry ALLAH ya bata lafiya”. Cike da sanyaya lafazi Nibras ta amsa, kallonta Maanal tayi ta gefen ido, dan bata sani ba ko ita kaɗaice ta fahimci Nibras ɗin ta canja murya wajen amsa AA ɗin. Sai ko amamakinta taga hankalin Nibras gaba ɗaya akan AA yake. (ikon ALLAH) Ta faɗa a ranta, a zahiri kam kamar ma bata san mike faruwa ba a wajen. Sai ma Nuratu data kawo hannu zata zuba mata itama, fuskarta da murmushi ta girgizama Nuratun kai murya ƙasa-ƙasa ta ce, “No barshi ma na Besty zai ishemu”. Tai maganar tana ɗaukar spoon ɗin da Nurry ta sakama AA, ita kuma ta ɗauka wani ta saka masa.
Idan Nuratu tace bataji kamar ta shaƙo wuyan Maanal ba tayi ƙarya, dan tuni annurin daya cika fuskarta sanda take zubama AA ɗin abinci a yanzu ya ɓace ɓat. Ɗauke kai Maanal tayi kamar bata ganta ba, sai ma kai hannu da tayi ta zare wayar AA ɗin ta ajiye a gefenta. Ɗagowa yay ya kalleta, itama kallon nasa take, dan haka suka ɗan zubama juna idanu har sai da Fawzan yay gyaran murya. Maanal ce ta fara janye nata cike da basarwa ta ɗauka spoon ɗin ta fara cin abincin, shiko yaƙi daina kallon nata. Fiiiyyy Nuratu tabar wajen ta koma wajen zamanta, Nibras ma sai da taji ƙwalla sun cika mata idanu. Zuciyarta raya mata take anya bazata kashe Maanal ba a gidan nan wataran. Dan sam idanun AA basa iya ɓoye abinda ke cikin zuciyarsa game da ita. Jitai gaba ɗaya abincin ya fitar mata a rai, amma tasan tana ƙin ci Oum zata dameta da tambaya ita da Fawzan.
Duk abinda kowa keyi Oum na karance da shi. Oum ta jima tana auna abubuwan da Nibras kema AA, musamman idan ta shagaltu da kallonsa ko idan tana masa magana. Sai dai duk da abinda zuciyarta ke fassara mata takan ture hakan a ranta. Amma a kwanakin nan sai irin kallon da take jifan Maanal da shi ke tsaya mata a rai, dan kallon yana kama da irin kallon kishi da jin zafi. A ganinta ko kishi ne irin na facalanci bai kamata a yakasance haka ba, dan kishin facalanci ga wanda ya saka kansa kusan na hassadar mijinki yafi mijina ne, ko mijinki yafi miki hidima fiye da nawa. Abu na ƙarshe yanda sam Nibras bata acting irin na matar gida ga mijinta a wajen Fawzan. Fawzan kullum a nan sashenta yake cin abinci safe da yamma, weekend harda na rana, itama kuma nan ɗin take zuwa taci. Sannan ko zaman cin abincin akai bazata tashi ta zuma Fawzan ba, sai dai ya zuba da kansa. Kai zasu iya zaman awa biyu a sashen ma bakaga sunyi magana da juna ba, amma idan AA na nan da yayi magana ko bada ita yake ba zata saka baki. Idan kuma har AA baya sashen ko yay tafiya to bazaka ƙara ganin Nibras a sashen ba. (Ya ilahil alamin, ALLAH kada kasa abinda nake hasashe akan yarinyar nan hakane. Lallai data cika mara hankali kuwa, da auren Fawzan a kanta ta ringa jin son wani namiji, namijin ma ɗan uwansa. Kai kai wannan kwamacala basa fatanta kuwa koda a mafarki).. shigowar Saheeba da yara ya katse Oum daga tunani, fuska cike da murmushi ta kamo su Naufal jikinta, Saheeba kuma ta zauna tana gaisheta. Itama dai abincin ta zuba, Oum ta girgiza kai kawai. Wannan lalace na surukansu na bata mamaki, matsayinsu na tsoffi su basu dafa sun kawo musu ba, sai dai kullum suzo sashensu su ci. Koda yake nan ɗin ma dai ne suke zuwa, dan ita Mamy bata ɗauka ma kanta hakan ba. Hasalima faɗa take akan ya kamata Oum ɗin ta taka musu birki. Itako sai dai tayi dariya kawai dan bazata iya ba, koba komai da yaranta su wahala da rashin abinci daga matansu gara suzo nan su ci ɗin hankalinta zai fi kwanciya.
Kowa nata cin abincinsa hankali kwance, sai dai hankalin Saheeba, Nibras, Nuratu, duk akan AA da Maanal ne, yayinda su kuma hankalin baya kan kowa, abincin su suke ci kawai a plate ɗaya, ƙasa-ƙasa AA na takalarta wai abincin babu wani daɗi. Itako tana harararsa ƙasa-ƙasa batare data tanka masa ba. Sai da ya isheta ne takai hannu ta ƙasan table ɗin ta mintsinesa. Idanu ya ɗan rumtse tare da cije lips dan yaji zafi, kafin yasa shima nashi hannun ta ƙasan table ɗin ya riƙe natan dake mintsininsa, tayi-tayi ta kwace yaƙi saki, dole ta haƙura. Shi ko ya cigaba da murza hannun dan wani irin laushi da santsi yake masa. Yanda yake mirza hannun sosai tsigar jikin Maanal ke tashi, amma ta dake abinta..
Abinda Maanal bata sani ba tuni ƴan sa'idonsu sun fassara abinda hannayensu keyi a ƙasan table, musamman daya kasance lokacin da Maanal ta mintsini AA ya lumshe ido da cije baki. Itama kuma yanayinta ya canja da ya kama hannunta yana murzawa. Su duka ukun zukatansu yi suke kamar zasu babbake. Yayinda sam babban Yaya da Fawzan da Oum su basu san ma mike faruwa ba. Hasalima hirarsu sukeyi. Rashin saka bakin AA a hirar kuma sun san wannan normal ne daga halinsa. Ba kowace hira bace zakaji bakinsa sai idan yaso tankawa, balle ma su Saheeba na wajen, kowa yasan baya hira da su, daga gaisuwa babu abinda ke sake shiga tsakaninsa da su..
AA neman harmutsama Maanal jiki yake, dan haka babu shiri ta miƙe tana fisge hannunta wai ta ƙoshi. Kallonta Oum, Babban Yaya da Fawzan sukai, yayinda AA yay wani shegen murmushi yana cigaba da cin abincin sa. Murmushin nasa ya ƙara tabbatar ma da ƴan saka ido abinda suke hasashe, ta wani gefen kuma ya motsa zukatan Nuratu da Nibras dan abune da basu saba gani ba. Lallashin Maanal Oum keyi akan ta ƙara ko kaɗan. Cike da shagwaɓa tace, “ALLAH Oum da gaske na ƙoshi zan yi amai idan na ƙara”.
A mamakin kowa sai ji sukai AA yayi ƴar dariya. Shagala matan sukai a kallonsa, dan har Saheeba ma dai mamaki ne ya dabaibayeta wai AA da dariya. Babban Yaya kam murmushi yayi, zuciyarsa fes da ganin farin cikin Autansu nata dawowa. Fawzan kuwa tsokanar tasa daya saba yayi. Yayinda Maanal ke kallon Oum kamar zatai kuka.
“Oum kin ganshi yana mun dariya ko”.
Kallonta AA ɗin yayi, “Kefa matsalata dake sharri Besty, shike nan bazanyi dariya ba, to inba tsargar kai ba mi kikayi da zan miki dariya?”.
Harararsa tayi, fuuu tabar wajen. Dariyar ya ƙara sanyawa, cikin ɗan ɗaga murya yace, “ALLAH ya raka taki gona”.
“Amma fasa tafiyar to”.
Manaal ɗin ta faɗa tana dawowa. Sai dai kujerar gefen Oum ta jawo ta zauna yanzu. Hatta Oum dariya takeyi, hakama Babban Yaya da Fawzan. Su dai matan da alama abin haushi ma ya basu, dan kowacce ta ɗauke kai. Cike da lallashi Oum tace, “Kinga ƙyaleshi Babyna, ya kamata zuwa yanzu ki saba da halin Auta, dan yaga ma kina fushi shiyyasa yake tsokalarki. Kin bari yaga lagonki ne, amma ki bari muma zamu gane nasa ai”.
Gwalo Manaal ta masa tare da kashe ido ɗaya. Sai ya haɗe fuska yana harrarta. Akan lips ya furta, “Zan kama ki ne ALLAH ya kaimu Chaina”.
Tsaf taga abinda ya faɗa, dan wannan sigace da sukema juna magana a baya idan basa son wanda ke kusa da su ya fahimta. Sosai taji gabanta na faɗuwa. Ita dai wannan Chaina da tana da yanda zatai sai ta cire kanta a ciki ALLAH. Gashi taga Abah baida niyyar hanawa..
Babban Yaya ne ya fara barin sashen, dan yace ya gaji barci yake son yi. Sai Oum ta kora Saheeba ta bisa. Maanal ma bata zauna ba ta tattare kayanta ta wuce ɗaki, acewarta aiki zatayi. AA ne ya zama na huɗu, acewarsa shima zaije yay aiki ne. To dama dai Nibras da Nurry dan shi suke zaune, sai dai da kunya ai su ce suma zasu wucen. Dan haka suka ɗan daure suna taya Oum hira. Dan AA yaja hannun Fawzan sun fice tare kamar zasuyi magana ne ya dawo shima dai shiru. Dole suma cikin dabara sukama Oum sallama suka gudu. Da kallo kawai Oum ɗin ta bisu, sai ma duk taji sun fara bata tausayi musamman ma Nibras, zata cigaba da mata addu'a ALLAH ya cire mata shaiɗancin nan a zuciyarta, za kuma ta dinga bata shawara a cikin hikima ko ALLAH zai sa ta gane ta tsaida hankalinta waje guda ga mijinta.....
_________★
Matuƙar zafi rayuwa tama Hajiya Basariyya. Dan tana dira gidan Kawu Manu dake wani ƙauye a ingawa local government ya ƙwace wayoyinta duka. Ya kuma shimfiɗa mata sharuɗan zaman gidansa. Zata hau yimasa magiya daban haƙuri yace baya buƙata. Lokacin da suka iso dambun tsakin masara sukai mai daɗi, yaji zogale da gyaɗa abinsa kuwa ga man ƙuli mai ƙamshi ɗan asali. Amma ita ƴar rainin wayo sai cewa tai bazata ci ba. Babu wanda ya kulata kuwa. Da dare akai tuwo na dawa mai daɗi nan ma. Harda naman zabuwa a miyar, dan duk da Kawu Manu na ƙauye miyar gidansa kullum da nama. Kiwo yake sosai na dabbobi kala-kala. Nan ma ƙin ci tayi, taci biscuits ɗin data ɓoyo a kaya da drinks. Duk bawai ya isheta bane ta dai daure. Washe gari da safe ana idar da sallar asuba da kansa ya kwankwasa mata ɗaki, yanda ta fito ya fahimci bama tayi salla ba. Aiko ya balbaleta da masifa, ya kuma tabbar mata shi ba'a masa lallaci a gida musamman na ibada. Dan haka ta tattara ta koma ɗakin Iya matarsa. Sosai hankalinta ya tashi da jin hakan, amma babu yanda ta iya. Haka taje tai salla, tana idarwa yace ta fito, tsintsiyar kwakwa ya jefa mata ya nuna mata tsakar gidan alamar shara, ya koma kan ɗan dutsen da yake zama a tsakar gidan daga can gefe ya zauna. Ba ƙaramar raunana zuciyarta tayi ba, dan tasan babu abinda ya damu Kawu Manu da shekarunta horata zai yi yanda ya kamata. Shiyaysa taso ta gudu gidan mijinta. Babban tashin hankalinta kayayyakin da suka amso da Maman Yaseerah suna can ta baro a Kaduna gidan yayanta, ga Huznah bata san a halin da take ciki ba a yanzu. Haka dai tai sharar s jigace saboda abune da ita kanta basan adadin shekarun data ɗauka batayi ba, ga tsakar gidan ƙaton gaske kun san dai gidan ƙauye akwai yalwar albarka. A gidanta komai yan aiki ke mata. Wataran ma suyi tace baiyi ba sai sun maimaita. Tana gama share ƙaton tsakar gidan yace ta shiga turken dabbobinsa dake zagaye da danni na itace. Wani irin amai ta dinga ji na masifa na taso mata, dan sunyi ɗanyen kashi ya haɗe da fitsari abin ba'a magana. Sai kawai taji hawaye sun ciko mata ido. Haka ta duƙa tayi sharar, da ƙyar ta gama, sai da ta koma tayi amai sosai. Yi kawu Manu yay tamkar bai jiyota ba, balle kuma Iya daketa hada-hadar ɗora wainarta ta sayarwa ta safe da take yi. Gefe kuma ta dama koko ta ɗaura ɗumamen tuwo na gida.
Hajiya Basariyya na kammala sharan Kawu ya shigo turken, ɗakin dake a gefen wajen ya nuna mata, yace ta fiddo abinci ta raba musu, ta kuma wanke manyan kwatanniyar dake wajen guda biyar ta haɗa musu ruwan dusa a ciki. Daga haka yay ficewarsa ya barta..........✍️
*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_*
*09032345899*
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
*_BOOK 2_*
🅿️➖2️⃣5️⃣
______________
25
.......Sosai Rabilu ya gigice da tsawar da Sen.. Bukar ya buga masa. Shi ko cikin matuƙar rufewar idanu da shiga tashin hankali mara misaltawa ya cigaba da faɗin, “Kai wawan inane da bazaka kirani ka sanar min ba tun a lokacin Rabilu, sai yanzu zakazo kana gaya min wannan shashashar maganar. Aiko wlhy ko ɗan uban wanene wanda ya auretan sai ya saketa, dan ban taɓa san wata mace kwatankwacin yanda nake son yarinyar nan ba”.
Cikin girgiza kai Rabilu ya ce, “Ranka ya daɗe kayi haƙuri, nima na rasa ta yanda zan isar maka da saƙon nan ne wlhy, tunda kaga tunda ka tafi bamuyi waya ba balle na samu lambar. Amma ka gafarceni. Auren yarinyar kuma yazo da ƙura, dan in har akace za'a ƙwatota akwai rikici. Saboda AA Darma ta aura”.
“AA what?!!”.
Sen.. ya faɗa cikin matuƙar zabura jijiyiyin jikinsa na mimmiƙewa. Dan baya jin a kusan nan an taɓa faɗa masa abinda ya girgiza masa zuciya kamar wannan da yaji a yanzu. AA Darma ne ya aura ƴar shularsa fa. Eh lallai akwai yaƙi kenan a Abuja. Tsabar yanda Rabilu ya sake firgicewa da yanayin ogan nasa shi kansa jikinsa rawa yake yi. Sai da yaji dana sanin ma sanar masa zancen. To amma yasan dole ne ya sanar masan, kodan yanda tun jiya ya fahimci yanda ya matsu da jin wani abu a bakinsa game da Maanal ɗin. Yau kuma yana fitowa a gida shi ya fara nema yace yazo office ya samesa. A ɗarare kuwa yazo amma bashi da damar zillewa dole ya faɗa.
“Munafuki tashi ka fitar min a office. Kuma karna sake ganin fuskarsa sai na nemeka”.
A rikice Rabilu ya fara bama Sen.. haƙuri, amma bai sauraresa ba, sai ma cewa yay idan bazai fitan ba zai sa security suzo su fidda shi. Yasan zai iya, dan Sen.. bashi da kirki, shi kansa alaƙarsu tayi tsaho ne saboda yana samo masa irin matan da yake so ne a kuma duk lokacin da yake buƙata. Haka ya tashi ya fito jikinsa a sanyaye. Dan wannan hanya dai shi kam itace hanyar cin abincinsa. Gashi tafiyar Sen... Ɗin wata da watanni ta sashi a halin rashin kuɗi, ya dawo da tunanin yanzu zai jiƙe ga kuma wannan akasi ya shigo. Amma ba komai zaije yay tunanin hanya mai bullewa, yasan wutar da zai kunno ta yanda dole Sen... zai nemosa da wuri-wiri......
_______★
Washe gari kasancewar Maanal tasan ba fita aiki zatai ba tana idar da sallar asuba ta sake komawa barci bayan taba Oum saƙon wani document taba AA. Oum bata hanata kwanciyar ba, dan taga raba dare tai jiya tana aiki, sai da ma tace ta kwanta sannan tace to. Amma badan haka ba ai bazata barta kwanciyar nan ba. Dan ta ɗauki ɗamarar hana Maanal zama irin su Nibras a gidan, tana son babynta ta horu da kula da mijinta, duk da tasan Ammie ma ba wasa bace wajen tarbiyyar yara, hakan ma a bayyane yake ga Maanal ɗin.
Yau Oum ita kaɗai ta haɗa breakfast ɗin da taimakon su Inte. Bayan ta kammala ta bar musu su shirya a dining ita kuma ta nufi yin wanka, dan tasan itama Abah na hanyar dawowa tunda yace shigar safe zaiyi. Har yanzu Maanal na ƙudundune a duvet tana barcinta hankali kwance...
Bayan kammala wankan Oum ta shiryawa ta samu Fawzan kawai a falon yay zaman karyawa, dan yana son fita da wuri-wiri ne acewarsa. Gaishe da Oum yayi, ta amsa masa da kulawa tana tambayarsa iyali. Shima ya tambayeta Maanal tace tana barci.
“Oh na manta Oum tace yau bazata aiki ba tana hutu”.
“Eh, ai kasan saboda tafiyarsu gobe ne”.
“Wai Chaina ɗin dai?”.
“Eh, duk da bamu da matsaya dan Abanku baice komai ba har yanzu”.
“A Oum karki damu zaima barta, ai aiki ne”.
“To ALLAH yasa Fawzan Abanku ne rikicinsa yawa garesa”.
Ƴar dariya Ya Fawzan yayi, dai-dai lokacin kuma AA ya shigo da sallama. Yau dai normal shiga akai ta yadi ruwan toka mai duhu sosai. Kai daka kallesa kasan an sayesa da kuɗaɗe masu tsada, dan ya kwanta luff-luff kamar ajiyayyar ƙanƙara. Rigar ba wata mai tsaho bace, hakama hannunta gajere ne ko gwiwa bai kai ba. Babu dai hula amma yayi ƙyau sosai. Briefcase ɗinsa ya ajiye a saman kujera kusa da wadda ya ja zai zauna cikin muryar nan tasa mara hayaniyar sauti ya ce, “Good morning Oum, Ya Fawzan morning”.
A tare suka amsa masa, Ya Fawzan ya ce, “Ya dai Autan Oum naga kanata kunbura?”.
Ƙin kulashi AA yayi, sai ma jan flaks ɗin gabansa da yay ya buɗe dan yasan maybe kunu ne. Sai Oum ce ta bama Fawzan ɗin amsa da, “Fawzan kadai sakama autana ido a gidan nan”.
Da ƴar dariya Fawzan yace, “Oum babu wani sa ido, shi ɗin ne sai a hankali, yanzu haka fushin nan dan Lilly bazata aiki bane yau.”
“Oum ALLAH zan bar masa wajen”.
AA ya faɗa cike da shagwaɓa. Dariya Oum ta danne ta ce, “Kaga manta da shi my baby, ci abincin ka. Ni zan maka maganinsa. Dan kawai mutun ya tashi da ɗan rashin son maganarsa sai kuma a fassara shi”.
Dariya sosai Fawzan yake yi, sai ma ya miƙe abinsa dan ya kammala karyawa, duƙowa yay saitin kunnen AA ɗin cike da raɗa ya ce, “Saboda kai kwar-kwar ne shine ka tsara su Oum da sunan aiki kai da Lilly a Chaina ko, to ka turan hundred k kona tonaka cewar honeymoon zakaje ehe”. Yana gama faɗa yay gaba, sai da ya je ƙofa sannan ya juyo, kamar yanda yay zato kam harararsa AA ɗin keyi.
“Harareni da ƙyau nidai inji alert, idan ba haka ba zakaga tone-tone yau”. Yay ficewarsa. Karan farko AA ya saki murmushi tare da girgiza kansa. Har cikin ransa yana ƙaunar ya Fawzan ɗinsa. Dan soyayyar ƴan uwansa ta musamman ce a garesa. Abincinsa ya cigaba da ci suna ƴar hira da Oum, shigowar Nuratu ya sashi yin shiru. Sosai ƙamshin turaren data bulbula ya fara hawa masa kai, dan ko kaɗan bai kalla ma inda yasan take ba. Gaisheshi ma da tayi hannu kawai ta ɗaga mata. Tabbas yana son ƙamshi, amma ba irin wannan mai hawa kan ba na mahaukata, balle ma ga mace, shiyaysa kaf turaren da Maanal ke amfani dasu suna masa daɗi da saukar masa nutsuwa, musamman ma traditional. Sallamar Nibras itama da nata salon gayun yasa shi miƙewa badan ya kammala cin abincin ba, matsawa yay inda Oum take ya kama hannunta ta sumbata. “Oum yimin addu'a”.
Addu'ar ta masa harma da sauran ƴan uwansa sannan ya mata sallamar tafiya. Har ya nufi ƙofa ta ce, “Af Auta na manta. Akwai takardu da Baby ta ajiye na baka, suna nan a side drawer na manta na fito da su. Kansa kawai ya jinjina mata, a ransa kuwa faɗi yake, (Lallai ƴar Oum ta gama rainani, ina boss ɗinta a wajen aiki amma ni zata aika na kai mata aikinta. Ba komai zamu haɗe ne). Da wannan tunanin ya shiga bedroom ɗin Oum. Saukar idanunsa a kanta ya sashi sauke ajiyar zuciya duk da bawai yana ganin fuskarta bane. Sai kuma ya shiga takawa a hankali har zuwa gaban gadon. Dai-dai fuskata ta ya tsaya cak, samun kansa yay da zubama ƙyaƙyƙyawar fuskarta datai wani fresh fararen idanunsa. Yanda ta ɗan tura baki gaba baima san ya saki murmushi ba. Sai kuma ya kai duƙe gaban gadon a saitin fuskar tata. Yatsarsa manuniya ya ɗaura a saman lips ɗin da suka ɗan bushe suka sake takurewa waje guda ya shiga shafawa, kafin ya janye ya maida saman goshinta ya gyara mata gashinta da suka ɗan barbaje har saman idonta. Duk yanda yaso daurewa ya kasa, sai da ya kai nasa lips ɗin a slowly ya sumbaci natan. Sai ko kamar tasan mike faruwa ta motsa, idanunsa ya ɗan rumtse dan sam baya son ta farka ta ganshi. Sai kuma ALLAH ya taƙaita abun kwanciya aka gyara. Shima miƙewa yay ganin ta cigaba da barcin, inda Oum tace file ɗin yake ya ƙarasa ya ɗauka. Daga haka ya fito. Oum kawai ya cema “bye”. yay ficewarsa ko kallo Nurry da Nibras basu ishesa ba. Da baya ya dawo, hakan yasa su duka sake kallonsa. Ya ce, “Oum idan Besty ta tashi Please ta min shara. Sashen yayi daty”.
“A'a bola fa? Yanzu ya daina gyarawa?”.
“No Oum na dakatar da shi, saboda akwai banbancin da da yanzu ai ko”.
“Eh gaskiya hakane kuma
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 13 Chapter of 15