ne baki yar a ƙasa ba, idan kuma kikace ni dake ta haka zamu buga wasan ƙasa zaki sha kuwa a hannuna). A fili kam maimakon bata amsa fruits da za'a gyara ta nuna mata da hannu fiskarta da murmushin har yanzu. Oum data ƙaraso inda Maanal ɗin take ta ce, “Yauwa gyara su kam Nuratu, sai a gama da wuri dan yau nasan Auta a jigace zai dawo gidan nan ba'a aika abincin rana ba hira da Hajiya Shuwa ta ɗauke min hankali”.........✍️
_Hhhhh gaskiya Maanal baki ƙyauta ba, ya zaki bama Nurry ɗinmu gyaran fruits 🤣🤣_
*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*
*09032345899*
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
*_BOOK 2_*
🅿️➖2️⃣2️⃣
______________
........Matuƙar tiƙe Nuratu takaici yayi, amma bata da damar cewa bazatai ba tunda itace ta kawo kanta. Sannan duk iskancin nan nata mugun shakkar Oum take ji, sosai matar na mata bala'in kwarjini, ga son da kowa yasan AA na mata tana son tai kamun ƙafa da ita. Kai bama ita ba, ko iyayen nata kan faɗi irin cika musu idon da Oum ɗin keyi, dan duk yanda suka shirya tunkararta da rashin mutunci suna yin arba da ita komai ke ƙwace musu. Cike da son ƙular da Nurry Maanal ta shiga yima Oum hira suna dariya. Aiki sosai Nuratu ta shaƙa, dan ji ta dingayi kamar ta juya ta caka ma Maanal wuƙar hannun nata.
Sunata aikinsu da hira, dan Maanal ma dai ke girkin Oum hira kawai take tayata, Nurry kuma anata aikin gyara fruits da take yi cikin takaici shiyyasa bata wani sauri, koda yake ba aikin ta iya ba dan bayi take ba sam. A gida komai masu aiki ne ke mata shi, idan iskancinta na ka ma hatta underwears ɗinta basu take su wanke sai tace matching baya wankewa da ƙyau. Su Inte dai sun gama sun gyara wajen sun fita suna gyaran falo da saka ƙamshi. Dai-dai nan AA ya shigo da sallama. Da sauri Nurry ta juya har tana neman yankewa da wuƙa, sai Oum da itama ta juya tana masa murmushi. Maanal kam tamkar batana san mike faruwa ba aikinta kawai take yi.
“Lallai yau Auta ne da tashi a office ko five baiyi ba ma?”. Oum ta faɗa tana miƙa masa ruwan data tsiyaya masa a cup. Amsar ruwan yayi, tare da jan kujerar work table ɗaya ya zauna. A kasalance ya janye idanunsa dake akan ƙullin da Maanal tai ta bayanta na rigar girki dake jikinta. Kamar wanda baya so ya ce, “Oum na gaji ne ALLAH shiyyasa na gudo”.
Murmushi kawai Oum ɗin tayi, dan tasan ba hakan bane ba, ta tabbata dan Maanal ta dawo ne. Cike da ɗan rawar murya Nuratu data tsaresa da kallo ta shiga gaisheshi. Ikon ALLAH, to shifa sai yanzu ma yasan akwai wani a kitchen ɗin bayan Oum ɗinsa da Maanal. Waiwayowa yay ya kalleta, sai kuma ya ɗauke idanun a taƙaice ya amsa, cikin kuma halin ko'in kular nan nasa kai kace baima gane Nuratun ba. Oum da bataji daɗin yanda yayma Nuratun ba tace, “Nuratu ce fa baka ganeta ba ne Auta?”.
“Na ganeta mana Oum! Nifa yunwa nake ji”.
Sarai Oum ta fahimci zancen Nuratun yake so a kawar, dan haka ta girgiza kai kawai da juyawa ta kalla Maanal dake ta aikinta. Juyowa tai ta kalla AA kuma, sai taga ya zubama Maanal ɗin ido ne a kaikaice. A take Oum ta fahimci akwai abinda ke faruwa a tsakaninsu, dan da wuri take gane idan sunyi faɗan nasu. Nan ma kanta ta ɗan girgiza, batare da tace komai ba ta buɗe ƙaton freight ɗin kitchen ɗin ta fiddo kwalin fresh milk, a gabansa ta ajiye tana faɗin, “Fara da wannan ga Baby nan na mana girki an kusa kamallawa”.
Idanu ya waro waje, “Kai Oum ana dai mana jagwalgwalo, miyasa baki mana da kanki ba?”.
Dariya Oum tayi, ta nufi hanyar fita tana ƙoƙarin ɗaga wayarta dake ring, ta ce, “Oh jagwalgwalo ko? Babyn ce ke jagwalgwalo! ALLAH yasa ta hanaka abincin nan mu gani”. Ta fice batare data jira mizai ce ba. Shima bai ce komai ba, sai ma ajiye kofin fresh milk ɗin daya ɗauka zai fara sha yay ya miƙe. Nuratu da gaba ɗaya jikinta ke wani irin tsuma, tana jin kamar ta daka tsalle ta rungumesa take ji ta bisa da kallo, duk da tun kwalliyar safe ce a jikinsa yama cire jacket ɗin samna suit ɗin sai fara tas ɗin long sleeve shirt dinsa dake clean harda karin gugarta kamar yanzu ya sakata wani irin ƙyau yay mata, ga ƙamshinsa mai saka kasala na tashi kamar a yanzu ne ya saka turaren.
AA kam ko kallon inda take baiyi ba, hankalinsa kwance, kansa kuma tsaye ya ƙarasa inda Maanal take ya tsaya dab da ita. Ita ko da yake ta juya masa baya bama tasan da zuwansa wajen ba, tadai ji yawaitar ƙamshin turarensa sosai. Hannayensa duka biyu ya zagaya a saman cikinta ya rungumota, tare da ɗora kansa a wuyanta duk a lokaci guda. Harga ALLAH tsorata tayi, dan haka tai wata ƴar zabura tana ƙoƙarin juyowa. Amma sai ya sake riƙeta da ƙyau ta yanda hakan ya gaggareta.
“Ni kika wulaƙanta kika tawo a taxi ko? Ki saurari hukuncina dan sai na saɓa miki”. Ya faɗa a cikin kunnenta cike da isa babu alamar wasa a furucinsa. Amma irinsu Nuratu dake a gefe sai su ɗauka wata maganar soyayya yay mata a kunnen, dan daya gama faɗa harda su manna mata ƙaramar sumba a kan wuya ya ƙara faɗin, “Ai dama kinfi kama da Kukun”.
Haushi ya saka Maanal ɗaga ludayin hannunta kamar zata ƙwala masa saboda yace tafi kama da kuku. Sakinta yay yaja baya yana murmushin ƙeta na cin nasarar ƙular da ita, dai-dai ta juyo gaba ɗaya yay mata gwalo kuwa, zaburowa tai kansa da ludayin. Aiko da ɗan gudu ya ɗauka fresh milk ɗinsa ya fice a kitchen ɗin yana dariyar data saka Nurry yin sumar tsaye dan mamakinsa da al'ajabi da yanda dariyar tasa tai bala'i bala'in tafiya da imaninta. Dan zata iya rantsewa bata taɓa ganin yana dariya kamar haka ba a rayuwar sanin datai masa kaf. Bawai yana ƙyaƙyalƙyalawa bane sosai a yanzun ma, amma illahirin haƙwaransa sun bayyana a waje. Oum dake shigowa itama tana dariyar yanda AA ɗin ya fito a kitchen ɗin da ɗan gudu ce ta riƙe ludayin Maanal, tana dariya ta ce, “Amasa haƙuri babyna bazai ƙara ba”.
Cike da shagwaɓa Maanal ta ce, “Oum gwalo fa ya min, yace nafi dacewa da kuku, kinga yana sake yimin gwalon ko”. Tai maganar tana nuna bayan Oum da AA yake tsaye daga can waje. Juyowa Oum tai ta kallesa itama, sai ya haɗe fuskar kamar bashi ke yin tsokanar ba. Oum data tabbatar yayi ɗin ta ce, “Okay na bari ta kwale ka ko”.
“Tadai fasan kai Oum, kuma dan ALLAH kinga na kulata tunda na shigo?”.
“To ya zan sani tunda fita nayi, sai dai a tambayi Nuratu.” Oum ta faɗa. Maanal ce ta amshe da faɗin, “ALLAH Oum yayi, kuma a tambayi Nuratun ma ai tana ganinsa”.
Ai kafin ma Nuratu da takaici ya kume tsigar jikinta har wani tashi take yi tayi magana ya sake ma Maanal gwalo yabar wajen. Karaf kuwa a idon Oum. Salati Oum ta ɗauka da faɗin, “ALLAH ya shiryaka Auta ka daina tsokalar min yarinya kaikuwa. Sai kuma ta kama hannun Maanal, kinga manta da shi zaki rama ne, badai zai dawo cin abinci ba taron dangi zamu masa harda Fawzan in ya dawo”. Daga haka suka koma Oum ta tayata suka ƙarasa girkin aka bar Nuratu da takaici. Gashi babu damar barin kitchen ɗin kuma. Dole ta haƙura suka kammala ikin duka suka shirya a dining sannan suka tafi salla. Sanin AA nan zai dawo yasa ta maƙale abinta, acewarta sai ta sake ɗaura ɗammara na maganin Maanal ɗin, hakan kuma bazai faru ba sai ta nutsu ta fahimceta....
________★
Shagali sosai aka sha a gidan Sen.. Bukar, sai dai shi gaba ɗaya hankalinsa nakan Rabilu ne dan ya fahimci akwai magana a bakinsa. Duk kuma yanda yaso su kebe da Rabilun hakan ya gagara, dan uwargida yau tayi masa kane-kane. Kuma tsaf ta fahimci inda hankalin nasa yake dan haka taita dariya a ranta. Zuwa yanzu babu abinda bata sani ba game da Maanal. Tun sanda mijin nata ya kawo mata batun ƙara auren nasa ta shiga bincike da bibiyarsa har sai da ta gano akan wadda yake rawar ƙafar. Da farko ta shirya tsaf domin nakasa rayuwar Maanal ɗin, dan ta ɗaukama kanta alwashi wata bazata sake shigo mata gidan miji ba, wanda suke a cikin ma tana shirin ficewarsu ne. Sai kuma UBANGIJI mai hikima ya nuna mata ikonsa rana tsaka ta samu labarin auren Maanal ɗin da AA Darma, yaron data taɓa ji a bakin mijin nata yana aibantawa da ɗaukar alwashin wulakanta rayuwarsa saboda yafi su kusanci da shugaba ƙasan. Dariya sosai sukaci ita da ƙawayenta masu ɗaurata a hanya, dan ita babu abinda ya dame ta da wata matsalar mijinta da AA Darma, ita AA Darma ma ya biyata a yanzu tunda ya ɗauke Maanal. Farin cikin wannan aure yasa ta shirya wannan liyafar ta Anaversary ɗinsu, abinda bata taɓa yi ba kuwa. Shi kansa Sen yayi mamaki, amma sai shanye a ransa yana faɗin (Hakan dai bazai hana ƴar shilata Maanal shigowa ba).
Bayan an gama shagali yanda ta kanainaye shi dole ya haƙura, dan ya ma nema Rabilu ya rasa. Bai san ita ta kora Rabilun ba dan dama ta mugun tsanarsa saboda tasan shine mai nema masa matan auren kuma kawalinsa na matan banza. Ta jima da son rabasu sai dai hakan ya gagara....
“Sen... Namu”. (ALLAH sarki Uncle ɗina KA BARI YA HUCE MAI RABON YA ƊAUKE🤣)
__________★
Daga sashen Oum AA sashen Mamy ya nufa domin gaisheta, dan ƙa'idarsa ce yin haka daga shi har ƴan uwansa. Da safe zasu shiga su gaisheta, hakama idan sun dawo aiki, sai dai da wahala kaga sunyi zaman mintina ashirin a wajen nata. Saboda tun farko bata jasu a jikinta ba, ita a dole tanama Oum kawaici. Wanda sai daga baya AA ɗin ya fahimci ba hakan bane ba...
Zaune ya sameta a falo Haule na gyara mata ƙumba suna kallo, glass bowl ne a gabanta tana shan fruits da aka yanka ƙanana a ciki. Cike take taf da haushin zaman Nuratu a sashen Oum. Da sauri Haule ta shiga gaisheshi. Batare daya kalleta ba ya amsa ciki-ciki yana kaiwa zaune a kujerar kusa da Mamyn, ganin yanda taketa faman ɓata fuska ya sashi yin murmushi a zuciyarsa. Shi wlhy wani lokacin yanda ta saka kanta a ƙunci babu gaira babu sabar tausayi take bashi. Da ace zata ajiye makanamta dai zata kasance cikin farin ciki ne da nishaɗi ta kuma samesu fiye da yanda take so su da take faɗan a kansu. A hankali ya matsar da jikinsa kusa da ita gab, batare da yayi magana ba ta zare spoon ɗin dake hannun nata ya ɗauka yanka ɗaya na apple ya kai mata baki. Ƙuri tai tana kallonsa kamar wadda ta suma. Domin abune da bai taɓa kwatanta yimata ba sai dai taga yanama Oum. Shi kuma ya ɗauka aniyane a ransa na canja salon mu'amularsu ko hakan zai sassauta zuciyarta ta ajiye makaman yaƙinta akan Oum, dan baya fatan wani a gidan ya fahimci halayyar nan ta Mamy. Ganin yanda take kallon nasa tamkar hawaye na son taruwa mata a ido ya sashi jinjina mata nasa kan tare da sakar mata murmushi mai sanyi, sai kuma ya ɗan buɗe bakinsa alamar (haa). Kamar sakarai a hankali ta buɗe lips ɗinta kuwa ya saka mata yankam apple ɗin, ta shiga taunawa tana kallon nashi. Sai ta samu kanta itama da amsar spoon ɗin ta ɗauka kankana ta bashi. Babu musu ya amsa yana mata murmushi, kafin ƙasa-ƙasa ya furta,.....✍️
*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*
*09032345899*
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
*_BOOK 2_*
🅿️➖2️⃣3️⃣
______________
.........“Jazakhallahu khairan Amaryar Abah, aminiyar Oum, Maman Fadeel da Fawzan da Auta Ajwaad”.
Yanda ya jero kalaman nasa masu kama da kirari ya sata sakin murmushi a bazata, sai kuma a hankali takai hannunta ta shafa kwantaccen gashin fuska tana sakin murmushi mai haɗe da ƴar dariya. Samun kansa yay shima da yin dariya, ya kama hannun nata ya sumbata. Ji Mamy tai tamkar zuciyarta na ɓaɓɓarewa gida biyu, cike da shauƙi mai girma ta sake kai hannun nata saman sumar kansa ta barbaza. Nan ma dariyar yay mata. Tare da faɗin, “Thanks you Mamy. Dan ALLAH ki daina damuwa akan komai, nafi son kullum nazo naga fuskarki cikin farin ciki. Na tabbata kuma idan kika ajiye komai zaki samu fiye da haka. Bakiga Oum ba, koda yaushe tana cikin farin ciki, saboda tana da ƙoƙarin ɗaukar jarabawa da sauƙi. Mamy muna sanki kamar yanda muke son Oum, yanda kuke treating ɗin rayuwarmu ne ya banbanta. Dan ALLAH ki ajiye komai kinji Mamyna”.
Kanta kawai ta jinjina masa, duk da kalamansa sun mata daɗi matuƙa a zuciya wani yanki na cikinsu sun mata zafi da ɗaci, ba komai ya kawo hakan ba kuwa sai jingina Oum da yayi a ciki har yana nuna mata yin koyi da ita. Cikin basar da komai ta ce, “ALLAH ya shige mana gaba Ajwaad! Kaga Nuratu?”.
“Amin ya rabbi, na ganta tana sashenmu”. Ya bata amsa a tausashe cikin danne komai, dan harga ALLAH ko sunan yarinyar nan baya son yaji ta ambata masa. Cikin tausasawa Mamyn ta katse masa tunani da faɗin, “Ajwaad kaga dai komai kace zan yisa domin samun farin cikinka, kaima ina son ka kula da Nuratu domin samun farin ciki na a ɗan zaman nan da zatayi da mu na azumi, Hajiya Turai ce zata umrah shiyyasa ta dawo nan ta zauna. Idan ka kwantar da hankalinka zaku fahimci juna a ɗan zaman nan da zatayi kafin bikinku. Ajwaad Nuratu na sonka sosai, irin son da duk yanda ka taƙwanrata zata maka biyayya, bar ganinta haka a tsaitsaye tana da hankali, gata ne kawai da Hajiya Turai ke mata na tsiya ya mata yawa. Amma nasan kai ɗin jarumi ne, zaka gyarata a yanda kake so yarona”.
Kansa kawai ya jinjina mata, dan baya son raunana mata zuciya, sannan yana son binta da wannan salon ko ALLAH zai taimakesa ta canja. Itama dai kusan tunani iri ɗaya sukeyi, dan tana ganin AA ɗin ya amshi batun nata da muhimmanci a yau, dan haka zuciyarta gaya mata take lallai tana da buƙatar canjawa, canjawa irin wadda Ajwaad ɗin keso kodan samun nasara a kansa, dan ta ƙarfin tsiya tabbas bazata taɓa samunsa ba, tunda ta gwada hakan tsahon shekaru kenan babu wani canji saima caɓulewar abubuwa. Ita dama bata jin su Fadeel, a ganinta duk a tafin hannunta suke. Ajwaad shine uban taurin kai da kafiya, sannan shine baisha nn ɗinta ba, zaifi mata wahalar janyewa fiye da su Fawzan da suka sha daga jikinta bayan dakon ɗaukar ciki dana haihuwa. Dan bazatace raino ba wannan kam Fateema tayi tare da cin kashinsu da fitsari. Dan in har batai ƙarya ba zata iya irga adadin wanke musu koda kashi da fitsari ne, shima sai in Oum ta fita wani uzirin ne ma.
AA nason tashi ya tafi sashensa ya watsa ruwa amma hirar da Mamy ke jansa da ita cike da farin ciki yasa ya haƙura ya zauna har akai kiran magrib, ƙarshe alwala ma catai yaje ɗakinta yayi. Haka kuwa ya haura saman yayo duk dan sanyata a farin ciki. Daya fito taita sanya masa albarka jitake kamar kada ta barshi ya tafi, sai dai hakan ya zama tilas babu yanda ta iya. Bayan fitarsa da wannan farin cikin ta kasance, tana idar da salla kuwa ta kira Maman Saheeba ta sanar mata komai. Suna yanke wayar daga can Maman Saheeba tace “Ina yaya Kamila bazai yiwuba, lokacin samun irin wannan farin cikin naki baiyi ba, ai idan har na bari kikai nasarar jawo Ajwaad jikinki to tabbas aurenshi da Nuratu bamai yiwu bane ba, nasan halin MAKIRIN yaron nan, tsaf zai juya miki tunani da hatsabibancin sa, dan yafi sauran ƴaƴanki taƙadaranci kema kina faɗar hakan da kanki. Kansa a buɗe yake matuƙa da sanin duniya, in har ba a yanayin da kuke ciki a baya ba lallai zai botsare ne”. Nanfa ta shiga kai-kawo na neman mafitar hanyar ɓata komai....
★Ana idar da salla AA dole gida ya dawo domin yin wanka kafin isha'i, tunda Mamy ta cinye masa wancan lokacin. A tare suka shigo da Ya Fawzan, babban yaya bai dawo gidan ba har yanzu. Sashen Mamy Fawzan ya nufa domin gisheta, shi kuma AA ya nufi nasa sashen dan yin wanka.
Bayan Fawzan ya gaida Mamy zai tashi sai ta ɗakko masa hira, mamaki ne ya kama shi, dan sam babu hakan a tsakaninsu tun suna yara. Tsakaninsu da Mamy umarnine nayi ko bari kawai sai gaisuwa. Amma batun shaƙuwa ko hira ko wasa da dariya Oum ce kawai ke musu da Abah. Daurewa yay yana amsa mata sama-sama, tsulum sai ga Saheeba da yara, da yake fita tayi Mamy bata kawo komai a ranta ba. Dan sai yanzun ne suke dawowa, zama Anum tai a jikin Fawzan tana masa labarin inda zukaje, yayinda Naufal ya nufi Mamy, a mamakin Mamyn sai Saheeba ta nema wajen zama tana faɗin, “Washa Mamy na gaji”.
Murmushin yaƙe Mamyn tai mata kawai da sannu a taƙaice dan harga ALLAH batayi murna da zaman Saheeba ɗin ba, dan zuwanta ya katse mata kasancewa da Fawzan. Kiran sallar isha'i ya saka Fawzan miƙewa ya ajiye Anum data fara barci saman gadon Mamy, cike da kulawa yace ma Naufal, “Tashi muje massallaci my boy”.
Da kallo Mamy da Saheeba suka bisu, suna gama fita Saheeba ta saci kallon Mamy ta gefen ido. Baki ta taɓe kaɗan, sai kuma ta ƙawata fiskarta da murmushi dan kaf MAKIRCIN Mamyn ta iya itama. “Lah Mamy wai ina ƴar hutun taki? Banji motsimta ba”. Ta faɗa baki a washe.
Miƙewa Mamyn tayi, sai kuma a ɗan yanayin jin haushi ta furta, “Tana sashen ƙanwar uwarta Fateema”.
Cike da mamaki Saheeba tace, “Tomi ya kaita can Oum?”.
“Oho mata”.
Mamyn ta faɗa cike da takaici tana kabbara sallarta. Harara Saheeba ta dalla mata cike da jin haushi ta fice a ɗakin zuwa nata sashen....
★Nuratu dai tunda aka idar da sallar magrib ake dakon dawowar AA sashen, sai dai kuma taji tsitt. Sai faman hararar Maanal dake karatun Alkur'ani takeyi, itako bama tasan tanai ba. Lokacin isha'i yayi suka gabatar, suna idarwa Maanal ta shiga bayi da nufin yin wanka. Hakan da Nurry ta gani itama sai ta fito ta nufi sashen Mamy. Oum ca take ta tafi kenan, sai take cemata ya zata tafi bataci abinci ba. Batare data tsaya ba tace, “Oum ina zuwa yanzu zan dawo”. Daga haka ta ƙarasa ficewa da sauri. Sanda Nuratu ta koma sashen Mamy bata sani ba, sai da ta fito cikin kwalliya da uban ƙamshi daga ɗakin data sauka sannan Mamy ta ganta. Harara ta zuba mata, zata fara mata faɗa tai saurin rungumeta tana faɗin, “Mamy ki fahimceni, na zauna ne dan nayi maganin shegiyar can, kin san kuma Ya AA ma acan yake, dole na nema mana kusanci ai. Yanzu ma komawa zanyi. Sai na dawo”. Daga haka bata jira cewar Mamy ba ta fice a sashen. Sai Mamy ta samu kanta da sauke ajiyar zuciya kawai, ita kanta rawar kan da Nuratu keyi akan Ajwaad na damunta, dan tasan halinsa baya son mace a haka...
A falo Nuratu ta sami su Oum, Maanal na zaune a ƙasa ta baje takardu da laptop tana aiki, sanye take da simple riga mara nauyi tashan iska milk color, sai veil ɗin rigar siriri data naɗa a kanta, ɗan zamawar da yay baya ya bama kwantaccen gashin goshinta damar fitowa. Sam babu ɗigon kwalliya a fuskarta, babu alamar ma ta shafa mai dan fuskar tai irin fayau ɗin nan. Hatta lips ɗinta a ɗan bushe suke kaɗan. Sai ƙamshi mai sanyi dake fita ƙasa-ƙasa. Gaba ɗaya sai Nurry tai sororo tana kallon ta, dan tayi tsammanin zata dawo taga Maanal ɗin ta caɓa kwalliya ne kamar mai shirin fita waje. Amma sai ga akasin hakan.
Itako Maanal ɗin ma kallo ɗaya datai ma Nurry ɗin sai ta bata dariya. Kwalliya fa ta ciwo sosai abinta. Anci uban shadda da yaji aikin stones sai ƙyalli suke. Kwalliya sosai a fiskarta harda lipstick ja da brawn sama gira tasha jagira, gashi ido a tsaitsaye an baza masa maskara a hakan ma na ƙari ne dan sunyi dogaye sosai. Anci ɗaurin ture kaga tsiya harda ɗan karkatashi gefe akai. Ƙamshi kam ba'a magana duk ta bulbule falon. Ita Maanal ma sai ta bata dariya, a zuciyarta tace (Aiki ja) a fili kam murmushi ta saki mai sanyi hankalinta a aikinta bazaka taɓa cewa da Nuratun take ba.
A haka babban Yaya da sai yanzu ya shigo gidan ya samesu. Shi kansu sai da ya kalla Nuratun da ƙyau, ganin kallon da yake mata ta shiga gaisheshi. Amsa mata yay da kulawa tare da tambayarta mutanen gida. Dan shi a zatonsa ma yanzu ne tazo shiyyasa. Sannu da zuwa Maanal tai masa, tare da gaisheshi. Itama ya amsa mata da kulawa yana tsokanarta da cewar “Lilly yau kuma aikin office ɗin ne har a gida haka?”.
Fuskar Maanal da murmushi ta ce, “Yaya ina ragewa ne, saboda yau na taso aiki da wuri”.
“Masha ALLAH haka ake so, ai gara kada ki koya over time ɗin tsiya ɗin nan na Auta”.
Sosai Maanal tai ƴar dariya tana nufar freight ɗin dining da faɗin, “Ai bazan koyaba Babban Yaya”. Dai-dai nan Oum ta fito daga hanyar upstairs. Itama dai kallon Nuratun tayi da ƙyau sai kuma ta janye ta maida kan babban yaya tana murmushi irin na manya. Ruwa Maanal ta miƙama Babban Yaya ya amsa yana sanya mata albarka, cike da farin ciki ta gyaɗa masa kai ta koma wajen zamanta ta cigaba da aikinta. Shi kuma suka fara gaisawa da Oum. A haka AA da Fawzan suka shigo sashen. Zama duk sukayi, cike da iyayi Nuratu tai musu sannu, sai kuma ta miƙe ta nufi freight kamar yanda taga Maanal tama babban Yaya suma ta ɗakko musu ruwan. Fawzan ne kawai yace mata “thanks”, shima kuma rabin hankalinsa naga duba takardun Maanal datai zane daya ɗiba yana kallo. AA kam ko kallon ma inda take baiyi ba, magana suke da babban Yaya ƙasa-ƙasa. Koda Babban Yaya ya miƙe Oum
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 15