Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sosai ma nice kadai nasan sirrin Nanfa Binta ta tafi tuna ni Ke tina ninme kikeyi Abu gaskiya nima zan fara fashin Wanka konima turaren jikina zefito kwana nawa zanyi banyi wankaba Abu tace yauwa yar gari kinga bake ba Wanka indai kinaso tiraren yazauna tareda ke duk inda kika higa ansan kin higo Binta tace To hi kenan nagode kawata Tadauko farantin gurjiya tace debi kici iya San ranki aikin bani sirri babba Abu tace Bakomai yiwa Kaine Binta amma ya zakiyi da umman ki idan tagane kin dena kwanka Kibari kawai nikaina bansan abinyi ba mutafiko kinga yamma tayi kar a fara bugawasa bama nan Abu tace ga aiki zan saki indan mun higa dan dali ki ki zuba ido kiga abin mama ki gurin sama rida yan mata To hikenan muje Abu Suka je dandali hakan kuwa akayi Abu nazuwa masu toshe hanci nayi masu dariya nayi Abu harda sake tafiya Kawata Abu gaskiya nima na rike sirrin nan hannu 2 Sukayi dariya suka tafa Suka sha kallo sukayi tsokana iya son ransu suka koma gida Daga ina kike Waye Wannan Abu tace tana daga kai taga Nura Daga dandali nake Yariko hannunta yawuce da ita ciki ya watsar da ita kamar kayan wanki Nura ya fara shin shine shin shine Yace Inna bana tunaninda Abu ta shigawanka tayi Inna tace Ko hmm zata aikata nasani Wannan nan gaba kadan nizan fara yimata Wanka da kaina Abu tace Waaa niii tab bawanda ya isa dan bakin ciki turaren nawama rabani dahi za a yi Nura ya Wanka mata mari tafashe da kuka Inna abinda ya dace kenan kifara yi mata da kanki tinda ita bata yi Nifa bawanda zemin wanka Nifa yaya anyi walkiya na ganka bakin ciki kawai ka keyi dani dakaji kanhin tirarena saika dinga yamutse fuska saboda bakin ciki Tirare ko wari kinga kidena shiga cikin mutane kina kiran waikin fesa tirare dariya zasu miki Wannan warine warinma mara dadi qazama cewar Nura hi kenan Inna kina jinhi ko ni ya kira qazama tafara timami akasa Nura yace Inna kice mata ta tashi kokuma yanzu jikinta ya fada mata Bashiri ta mike tana gunguni harya fito fili tace nagaba yayi gaba kanshi kuma nayi bawanda ya isa yakwace Ehhhe Waye ze kwace inbanda Wanka Inna duk sanda kika tashi wankar *'YAR KWALLIYA* kitanaji kwalin sabulu saboda tsoro Inna saida safe Yana fada yayi fice warsa Allah yakaimu Inna kinji shi ko Yasin yaya kajawa budur warka Allah ya hadani da ita Kinga Abu bana son neman tsokana karki sake kitaba musu 'ya kisamu wanda yamiki badai itaba ki kwanta saida safe To Inna Allah ya kaimu WASHE GARI DA SAFE Abu ta fito tana hamma Inna Allah dai yasa kin gama abinci dan yau yunwa nakwaso abaccin Bagai suwa ba komai sai Neman abinci baza kiciba saikin goge baki kinyi sallah tukunna cewar Nura Tamatso kusa dashi tace yaya a gidan nan kaine kwai matsalata yanda sauran suka tafi suka barini kaima zaka tafi ko ince kagaji kabarni Yatoshe hanci tinda tafara magana harta gama Nura yace Wai Wannan bakin naki Abu ai sai ya kashe me rai yaushe rabonki da goge baki AF anzo wajan nikaina na manta gawayin da gihirin na ban wuya Yasin hiyasa na dena wankewa yawan goge baki na kahe hakori Nura Yana nesa da ita yanda bazeji warin bakin ba Injiwa Yau saikin goge baki yaushe rabonki da sallah dan Inna tace rabonda taga kin kalli gabas harta manta cewar Nura Eh hakane yaya hadasu nakeyi hiyasa bata ganina Hadasu kamarya Abu Nasati1 nakeyi a rana1 sauran ranakun kuma ina hutu tafada tana dariya Nura yace Abin ma dariya yabaki ko Abu amma kin dena zuwa isilamiya ko Tab tsohon zance tin yauhe nadena zuwa bari kaji laifi nayi yace ze dakeni nikuma nace be isaba shine yasa yara suyimin waka waini *HODA BA WANKA* hine na sace mai tayar keke hine fa yake ne mana ruwa a jallo Tana fada tana Sosa kai da jikin ta Inna haka lamarin Abu ya kara lala cewa cewar Nura Inna tace kaji da kunnan ka kakuma gani da idonka yazu kuma abin zekara finnada tinda ta hadu da Binta Ido yazare yace Binta gagare Ita dai yanzu kawartace sosai duk inda Abu take zakaga binta Cewar inna Dole nakara samiki ido Abu jeki kwanke baki kiyi Alwala kizo kiyi sallah a gabana kuma ma inbanda rashin hankali irin na Abu a i na akace miki hada sallah a keyi kowacce ana yinta akan lokacin ta kina jiko cewar nura Abu tace Yashiga tanan ya fita tanan bayan kai ba malami bane me zaka fada min nayarda bayan sanin ma nafika Na yarda jekiyi alwalar kizo Taje tayi ta zo gabanshi tace yaya na hutar dakai dama yau nake hadesu guri guda barima nayi ka gani Nura yace Ke bana son hauka fa sallar Asuba raka'a nawane Lallaima yayan nan nawane inbanda 2 Sallama Alaikum Nura yajiyo sallama daga kofar gida girgiza kai kwai yayi yatashi yatafi Nura ya Inna taku Lpy kalau cewar nura To Alhamdulillah megarine yace kuzo dakai da inna dakuma Abu Allah daiyasa lpy cewar nura Ehhhhhto lpy ba lpy ba saidai koma meye idan kazo fada kaji To gamu nan zuwa yace yakoma ciki Inna yarinyadai tasake ballo ruwa megarine yake Neman mu To Bakomai bari ta idar da sallah saimu tafi cewar Inna Abu tace Inna Nifa ba inda zani idan banci abinci ba Ehhhhe Waiba sallah kike yiba Abu cewar Inna Abu tace Inna kwantarda hankalinki na idar bani na bawa cikina tukunna Inna ta bata ta ansa tana hannu baka hannu kwarya harta gama Tasha ruwa Tace Inna saura kwalliya idan banyiba bazan iya sa kafata wajeba Nura yace kin isa waye ze zauna jiranki Inna tace kai kanka kasan hakan baze yiyuba kabarta tayi mutafi Abuta baje kayan KWALLIYA tayi kamar yanda ta saba fukarnan kamar Aljana Inna mutafi naga ma Warin bakinta yadoki hancin Nura Kaiiiiiii Abu baki wanke bakiba ko Eh ban wankeba bakina ko naka Tayi gaba abinta sukuma suna binta a baya harsuka karasa fada kowa na gaida megari amma banda Abu Megari yace Ke Abu me yarin yata tai miki kika daketa jiya tareda bakuwar gidana Tawatsawa yarin yar harara tace kuma na dake ta nadaki banza ba uwar dayasa tace min HODA ba Wanka Ke Abu baban nawa kike fadawa haka cewar yar megari Anfada mihi ubanki ubanane cewar Abu Kaji yarinya mara kunya me garin kike fadawa haka Ayi hakuri yarin yace cewar Inna Abu tace Inna saboda ni karki fara karya niba yarinya bace hekarata goma shabiyar Inna nayimata alama tarufe baki amma ina zance kwai Abu take saki New writer's Taku *husba'ahfama*馃尮馃尮馃拫 馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼 馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹 馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼 馃憹馃憹馃憹 馃憼馃憼 馃憹 馃拕馃拝 *'YAR KWALLIYA* 馃拝馃拕 馃憹 馃憼馃憼 馃憹馃憹馃憹 馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼 馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹 馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼 Written by *husba'ahfama* 7-8 Can saiga Binta ga gare sarkin kwadayi da umman ta suna ta howa Yauwa Allah na gode maka ga binta cewar Abu Dan rainin wayo da sassafen nan a aiko gidan mutane ace suzo ko uwar me za a mana cewar Binta Abu tace Kema dai kya fada gamunan ana surfo mana zancan banza Eh waye yake zancan banza ke kuma Binta ba a koya miki gaisu waba bakya ganin manyane a gurin nan cewar liman dake zaune a gefen me gari Binta da umma suka samu guri suka zauna Abu tace Wanda yatsargu dahi nake Babba bangan shiba saidai naga me gari tinda ba a barni naci abinci ba nazo nan to kowa yayi hakuri da abinda zeji koya gani cewar binta Liman yace kaji yara da rashin kunya Barsu dani liman cewar megari Umma ta gaida me gari binta kuwa aikin gun guni kawai takeyi Sauran mutanen gurin hanci a to she sun kasa cewa komai daga liman sai megarine kawai suke magana Binta kinji wai dan mun daki wa yancan 'yaran hine aka kawo mu nan gasu 'ya'yan kuli da mai cewar Abu Binta tace Kan uba Yasin bazan zauna ba akan su aka hanani cin abinci tafiya zanyi Yasin karki yarda binta kanki tafi kizo ki daki rabon ki zan taya ki cewar Abu Sukayi kansu zasu daka liman da megari mutuwar zaune sukayi wato kanhin jikin Abu dana binta da itama tafara hawa layi sukaji sukayi lup kamar basa gurin Megari yace Karku sake Ku tabasu kuna jiko wai warin me nake ji haka ina kuke kusa baki mana meye aikin ku liman Caraf Abu tayi da cewa nice nan kanhin tirarena babu inda baya zuwa megari ka gode Allah tinda kaji kanhin tirarena Megari yace Tirare kuma tab Wannan uban warin shine tirare liman ba lbr yakasa cewa komai sai kallo da ido sauran ma sunyi shiru Megari cikin bacin rai yace waime nake gani haka kun dena magana ne kuma banson sha shanci kunwani zuba min ido me kuke nufi Me gari sai hakuri binta Abu kuzauna cewar inna da umma Binta hannu a dun kule tana shirin kai naushi take cewa Inna kubar mu dasu yanzu mu koya musu hankali Nura cikin muryar tsawa yake cewa kuzauna karku bari na kara magana Ganin fuskarshi ba alamar wasa yasa suka zauna Megari yace gaskiya yaran nan abin naku azimun ne kuma da laifinku wajan bata yaran nan kuduba fa Ku gani baruwansu da babba koyaro duk wanda ya musu yi mishi zasuyi Me gari ayi hakuri zamu gyara insha Allah cewar umma Me gari yace To shi kenan gaskiya kudau mataki inba haka ba ni da kaina zandau mataki Wani yaro ya fito daga gidan me gari hannun shi rikeda samira Tinkafin ya karaso Binta sarkin kwadayi tafara hadiyar yawu wayanda suke kusa da ita saida sukaji karar Yaron ya gaidasu ya ajiye kwanon a gaban liman Binta idonta na kan kwanon ko kiftawa bata yi ta janyo kwanon kusada ita Kanshin abinci yadawo da liman daga dogon suman da yayi Liman yace Ke me kike nufi yajanyo kwanon gaban shi Binta ko magana ta kasa hankalinta nakan kwanon Liman Allah ya yanka maka binta taga abinci ranta ya biya dan haka ka bata taci cewar Abu Liman yace In naki fa dawani bakinki dayake zuba wari anya kina wanke shi kuwa Abu tace Yasin wanke baki kahe hakori yake hiyasa bana yi liman kaida kanka kace hi bakin me azumi kanhin Almuski yakeyi hiyasa nima na dena wanke baki saboda Almiskin yazauna a bakina nafita daban daku nawa basai ina azumiba ta fada tana Dariya Liman baki yasaki yana kallon Abu Megari yace ke Abu anya kina da kai kuwa Abu tamika mishi kanta tace shafa kaji Inna ta rufe bakinta tana kallon Abu Megari ina fada maka saika dauki babban mataki akan Abu da binta cewar liman Bakomai kubani lokaci zansan abinyi kuna iya tafiya amma kubar binta da Abu liman ze musu fada cewar megari Waaaanii gaskiya babu abinda zan iya fadawa wayan nan yaran banshirya takun saka da suba sunyi nisa basa jinkira cewar liman Yi shiru liman nagama magana cewar megari Inna,umma da Nura suka tafi Binta batama San tafiyar suba itadai burinta taji abinda ke cikin kwanon a cikinta Liman kabata abincin nan taci yasin tanada cutar duka idan aka hanata abinda takeso hine suke tahi cewar Abu Liman Ya kalli binta dake zaune hannu a dunkule ido akan kwano tana sude baki Liman yace Me gari Abuya tabbata duka zatayi kalli kaga Liman karka zama soko mana kayi musu fada sutashi su tafi ita kuma binta ka bata taci cewar megari Kwanon ya miki mata ta ansa tabude tana ci kamar kura yaga nama Binta ta gama ci tasa kafa ta ture kwanon ta kalli 'yar me gari tace jeki kawo min ruwa Niii kalle ni sama da kasa nayi kama da 'yar aikin gidan Ku cewar yar me gari Zancen banza meye dan kin debo min ruwa yan matan garin nan kaf yan aikina ne saboda na fisu haduwa cewar Abu Ya isa kunutsu kuyiwa kanku fada kungirma aure zakuyi gidan wani zaku kuyiwa Allah kudena abinda kukeyi Dariya suka yi suka tafa kinji wai aure cewar Abu Binta tace kaika sanshi nidai tinda ba a bani ruwaba bangode ba taso mu tafi To tace suka tashi zasu tafi Binta tarike ciki tace washiii cikina ya motsa Binta tayi nishi saiga tusa ya biyo baya Megari yatoshe hanci yace liman Sa a kamo min yarin yarnan Binta da Abu najin haka suka sa gudu **** *WACECE BINTA DA ABU* ABU 'yace ga munzali malam munzali fatauci ne sana arsa shikadai yake tafiya inya tafi saiya jima kafin ya dawo sai matarsa Suwaiba yaranta na kiranta da Inna yaransu 4 Ramatu itace ta farko tana aure a garin da suke me suna *DARAUDAU* sai zulai itama tayi aure sai Nura da Zainabu Abu itace auta ABU yarin yace mara tsoro duk girman mutum inya mata saita mai farace tas amma qazanta ya maida ta baka dan qazanta kokitso intayi saiya dankare layin ya bace kafin inna tai mata ta karfi ta tsefe Binta 'yace ga murtala Malam murtala mahaucine Allah ya masa rasuwa tin Binta tana karama a hannun ma hai fiyarta ta tashi sunan ta Baraka binta kadai ta haifa BINTA yarin yace mara nutsuwa ga kwadayin tsiya idan taga abinci jikinta har rawa yakeyi itama bata barin ta kwana dan haka tasu tazo 1da Abu gasuda taurinkai ***** Binta da Abu na cikin gudu wata yarinya kanta dauke da buhu ta tsaya a gaban su ta shaki wuyan Abu Ke meye haka a ina nasanki cewar Abu Tace idan maye ya manta uwar diya bazata mantaba nice wadda kika daka kika cimin gyada kika kuma zubarda sauran Abu tace Kinsan abin da yawa yanzu me kike nufi da kika shaki wuyana Dukanki zanyi na kwashi saura nakai gidanku cewar yarin yar Banga Alamaba ance da kuturu a gama lpy ni Abu banga wanda ya isa yamin abinda kika fada ba ba a hai fehiba Binta tace ke ware inba haka ba hmm jiki zeyi tsami Ke waya sa dake ni din nan da kike jida gani ban tinkare kuba saida na samo makarin ki ke binta dan nakula kema matsalace ta daban cewar yarin yar Makarina kuma ni binta banganshiba anan gurin yau banga abinda zesa na bar kiba batareda na sosakida bulala ba Ko to shikenan nida ke za a ga me gaskiya yarin yar ta Bude buhun taciro goriba,kurna,magarya da gyada Tinda ta Ciro Binta ta hadiyi yawu kamar yanda ta saba tabi hannun yarin yar da kallo Abu tace Ke karki sake ta rudeki da abin hannunta Binta nizan siya miki fiye dahi Ko jinta binta bata yiba Tamika hannu alamar ta bata harya rinyar ta miko mata saita janye Binta tace meye haka kuma bana son irin Wannan Kina zaton kai tsaye zan baki batareda na kafa miki doka ba Meye dokar cewar Binta Yarin yar tace zakiyi Alkawarin cewa bazaki sa hannu a fadana da Abu ba inkikasa hannu zan kwace abina Binta ta kalli Abu ta kuma kalli ledar hannu yarinyar da irin abinda ke ciki Nan tashiga raba idanu New writer's Taku *husba'ahfama* 馃尮馃尮馃拫 👠👠👠👠👠👠 👝👝👝👝👝 👠👠👠👠👠 👝👝👝 👠👠 👝 💄💅 *'YAR KWALLIYA* 💅💄 👝 👠👠 👝👝👝 👠👠👠👠👠 👝👝👝👝👝 👠👠👠👠👠👠 Written by *husba'ahfama* 9-10 Jikin Binta sai rawa yake Na amince bani Yarin yar tace in na baki ki tafi ko juyowa karkiyi Binta tace to bani dai Tana ba binta tawuce ta tafi Yarinyar tace yanzu daga ni seke Abu tace hakane kuma zam miki dukan tsiya kamar mu2 muka miki Yarin yar ta kama Abu da duka Abu na ramawa Abu ta Bude baki ta sakar mata cizo a hannu Waiyoo kika cizeni Yasin bazan yarda ba koni koke a gurin nan cewar yarin yar Saukar duka yarin yar taji bazata koda ta juyo Binta ta gani zatai magana binta ta dauketa da mari binta da Abu sukayi mata taron dangi saiga yarin yar a kasa wanwar tana kuka Abu ta bude buhu ta leka taga garin tuwo tayi dariya Binta ta daga ta juyewa yarin yar a jiki Inkinje gida saikiyiwa tsohuwa bayani yanda Akai da garin tuwo cewar Abu Suka tsalla keta suka wuce Binta tace Abu kina jin abinda liman yayi mana dan yaga me gari waimun girma aure zamuyi Rabu dashi nasan abinda za muyi mihi damu yake magana ba a taba mubama munyi fada bare ka ta bamu zomuje cewar Abu Ina zamu cewar binta Zaki gani cewar Abu Koda suka tafi basu tsaya ko ina ba sai gidan liman Abu tace Sallama Alaikum goggo me tuwo Goggo me tuwo ta amsa da Wa'alaikumus salam Abu Binta yaukune agin namu Eh wlh cewar Binta Goggo me tuwo tace Gashi kuma ban gama tuwonba yanzuma na dora Bakomai mu abindaya kawo muma daban ne bansan ta yanda zanfara fada mikiba goggo cewar Abu Kar kuji komai kufada min idan baku fada minba wazaku fadawa bayan nasan Ku tin kuna yara nan kuke zuwa cintuwo cewar goggo Binta tace Hakane munsan da wannan goggo hine dalilin da yasa mukejin nauyin abinda zamu fada miki Binta Abu kufada min bakomai komai girmanshi zansan abinyi Abu tafashe da kukan karya taceTo hikenan goggo kiyi hakuri da abinda zakiji sai Abu takara sautin kun da takeyi Binta ma kukan karya takeyi tace yi hakuri Abu bakomai sakai yar daze mata kenan Nanfa hankalin goggo ya tashi tace kunga kufada min duk kunbi kun daga min hankali Abu tace goggo dagir manki da komai liman ze miki kishiya Gogo ta mike tsaye tarike kirji tana huci Ni liman zewa haka zezo ya sameni bemin kishayaba tin ina yarinyata saiyanzu dana tsufa Goggo abinda ze kara daga miki hankali hine irin kalaman da yake mata idan yaje zance cewar binta tafada tana kuka Dan rahin mutunci hine ta aiko mu da kala man soyayya muzo mu fada mihi Takuma ce karya manta yau yazo zance ita kadai tasan abinda ta tana dar mihi cewar Abu Kafar goggo ya haurawa taji juwa na ibanta tajin gina da bango ta ciji lebe a nan gidan ze kwana daiko badamuwa ina jiranka cewar goggo Binta takara sautin kuka tace babban abin hine mahaifin yarin yar yace liman yaturo anbahi ita Suna fada goggo ta zube kasa ba nunfashi Munhiga 3 Abu munyi kisa cewar binta Abu tace ke bata mutuba tsabar kihine kawo ruwa kigani Binta takawo ruwa Abuta watsa mata taja dogon nunfashi tabude ido tana Cewa ina yake kumiko min shi Abu tace goggo aibaya nan bari zahigo saiku yita takare Goggo tace bakomai zaka dawo kasa meni liman nida kaine yau agidan Goggo mu zamu tafi Nagode muku binta da Abu Allah ya muku Albarka Goggo me tuwo macace me kishi akan kishi zata iya yin komai sanin hakane yasa Abu da binta sukazo gurinta sunsan ita zata hukun ta musu liman yanda suke so Ameeen goggo aiyiwa kaine suka ce suka nufi hanyar fita harsun sa kafa zasu fita Abu ta gano liman yana ta howa da alama gidan zezo da sauri ta riko binta suka boye cikin wani duhuwa dake zauren gidan liman Liman yayi sallama ya fada gida kai tsaye ya nufi bandaki Goggo na jinshi binta da Abu Suka dauke sawun takalmi suka matso tayanda zasuji kuma suga Abinda ke faruwa Liman yafito yashiga daki yasa sababbin kaya yafesa tirare Nanfa kishi ya turnike goggo me tuwo tashiga waigen Abinda zata samu tarike ta hukun tashi dashi Me gari ya fito yana gyara hula yace in na kike na fito zan tafi Goggo tafito tana huci tace nasani kagai sheta wato danka raina min hankali nika ajiyeni a gida kaikuma ka fita kana neman aureko har ance katuro Yace ni liman a ina kikaji zan cen nan wlh bana ne man aure a ko ina ni liman ke kadai kin ishe ni Tace karyar banza ba abinda zaka fada min na yarda bayan nasan komai yanzu kayan nan dakasa kafesa tirare ina zaka Abuda binta na labe suna ji kuma suna ganinsu suna dariya Yace daliban malam rabi'u ne zasuyi sauka yau shine aka gai yace ni na shirya yanzu zan tafi Bata gamsu da abinda yace ba yasa tafara buga kafa tana tsaki Tace malam malam ni goggo ni zakai wa kishiya Tana juyawa taga murhuna cida wuta ta Ciro icen dayafi ci tasa mai ababban Riga wuta yafara ci liman na ihon temako yana kokarin cire baban riga dakyai ya samu ya cire abin beyiwa gogoba ta dauko tukunyarda ta gama hada kayan hadin miya ta kwaramai a fara ren kayan shi Binta da Abu dariya harda faduwa Ta rarimo bokiti tana jifan shi dashi ganin abin nata bana Kare bane yasa liman ya mike ya zuba da gudu Binta da Abu suka Tsaya a gaban shi Abu tace liman mun girma aure zamuyi ko toga auren mun gwada maka tafada tana dariya Binta tace waiyoo cikina liman mezan gani haka yazaka gudu kaida yadace kai mata fada kamar yanda kayi mana dazu Amma dai yaran nan kwai shedanu kune kuka hadani da matata bakomai dani kuke magana Abu tace gogo me tuwo gashinan Liman yasa gudu binta da Abu na dariya Raina fesa cewar binta Duk wanda yace ze higa harkarmu to yadebowa kanhi kwarkwasa cewar Abu Sukayi dariya suka tafa Suka nufi gidan su Abu Liman be tsaya ko inaba sai fada gurin me gari wayanda suke tareda megari ganin liman yashigo da gudu suma suka mike zasu gudu Megari yace kudawo Ku zauna liman mezan gani haka da girmanka da komai Allah yabaka yawan

Chapter 2 of 12