Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
arms tayi tana fadin"Yeah ki daina Insulting nashi because I love him……" "Lallae Fadila ……"cewar hajiyar tare da mikewa ta bar falon ……Fitowa ta kuma yi rataye da gyalenta da gani kasan tsofa yayi gardama gurin "hajiya sae kuma ina?cewar fadila da ta bita da kallon mamaki Harara ta sakar mata tana fadin "Gurin tsalli zani na kai mashi wannan number tun kafin ki fara duka idan an zageshi ……" "Ban gane ba Hajiyarmu……" Gaba tayi tana fadin "idan na dawo kin gane……" 《》《》《》《》 Karfe 10:15 ya iso katsina kasancewar tun da safe ya iso ……Gabanshi ke masifar faduwa banda addu'a babu abunda ke fita daga bakinshi , da kyar yaje gida a bakin zaure ya iske inna sahu tana neman aike saboda duk su nana sun tafi makaranta ……karbar Aiken yayi ya sawo mata sannan ya dawo suka gaisa sama sam yana tambayarta "duk yaran na lafiya……" ta amsa da "Lafiya lau ……" kadan kadan suka taba hira duk hankalinshi baya jikinshi so yake ya kira ko Maryam ce yaji yarda suke amma ya kasa ya dauki wayar da niyyar ya kira ya fi sau biyar amma ya kasa …… Sassayar ajiyar zuciya ya sake lokacin da yake mikewa ,kawae ya yanke yaje ya gaido Alhaji kila ya samu saukin radadin da zuciyarshi ke mashi …… A Falo ya sami Aunty fateen zaune tana breakfast har kasa ya duka ya gaidata sannan ya tambayeta ko Alhajin nanan …… Hankalinta ta maido kanshi sannan tace "Yana wanka Abdul Maleek ka jirashi dama ina son muyi magana da kai……" Kanshi na kasa yace "Ina saurarenki Aunty Fatee……" "Yauwa Abdul Maleek dama diyata Fadila ce ta dameni tana sonka kuma kaki kulata ko ta kiraka baka dauka shine nace ta bari na maka magana naji ……" "Ita tace maki da bakinta tana sona?ya fada tare da dagowa yana kallonta "Ita da kanta Mana Abdul Maleek ,kuma wallahi diyata ba mummuna bace idan kana so ma bari na kirata yanzu sae tazo ka ganta ,don tace man baka santa ba……" Murmushi yayi mai fitar da sauti yana fadin "Am sorry to say baran iya soyayya da macen da ta zubar da kunyarta ta ya'ya mata da Allah ya mata tace tana son namiji……" Shigowar Alhaji ce ta katse maganar ya mike da sauri yana mashi barka da fitowa ,ko zama baiyi ba ya nufi hanyar Fita yana fadin "Yauwa Abdul Maleek zo ka kaini tunda gaka kazo wallahi tun dazu Jabir ke man waya don shaf na manta jirgin marece zasu bi na dauka sae na dare ……" Bin bayansa yayi yana fadin "to Alhaji……" a zahiri jin sunan jabir da yayi a bakin alhaji ya saka gabanshi yayi mummunar faduwa ……jiki a mace ya fitar da motar suka dau hanyar fita unguwar murya Alhaji yaji yana fadin "Dutsin safe zamuje mu dauko Safeenar Abdul Maleek sae mu samesu bakin round din dandagoro Kano zamuje ……" Safeena……ya fada a ranshi kasa hakuri yayi ya juya yana kallon Alhajin a raunane yace "Wace Safeenar Alhaji ba tayi aure ba me ya kaita dutsin safe ko acan aka ajeta……" "Tayi aure mana Abdul Maleeku ,Bata lafiyane shine zamu kaisu kano ita da mijin nata zasu fita india a dubata……" Lumshe ido yayi hawaye na bin kumatunshi ya rigaya yayi failing ……da yake Alhajin a baya yake sam bai kula da halin da Maleek din yake ba……kofar gidan yayi parking kafin ya zagayo ya budewa Alhajin har ya rigaya ya fito ya shige yana fadin "Shigo Abdul Maleeku……" Girgiza kai yayi a hankali kamar Alhajin na kallonshi sannan ya kwantar da kanshi jikin gaban motar yana numfashi a hankali……Murya Granny da yaji ta sashi naimo natsuwarshi ya dago da kanshi yana yake…… Maryam da ya hango ya sashi juya masu baya da sauri don ya tabbata tana tare da Safeena Kuma bayajin zai cigaba da rayuwa indae yana kallonta …… "Dole ka juya man tunda baka da gaskia……"cewar granny dake kokarin shinfida katuwar leda a bayan motar …… A hankali ya juyo yana yake tare da maida kanshi kasa don har ga Allah baya jin zai iya kallon Safeena a yanzu da ya tabbata ta mashi nisa……"Ba haka bane granny tafiya ta kamani ……"ya fada da murmushin yake a fuskarshi Zuciyarshi ke neman rusa mashi duk wani plan na kar ya kalleta sam ya kasa jurewa……a hankali ya fara bin kafafuwan mutanen dake tsaye gurin har ya sauke bisa kafar daya tabbata ta Safeena ce …… Sae da ya lumshe idon sannan ya fara kallonta tun daga kasa har ya kai kan kugunta da razanannan kallo ya karasa kallon fuskarta ……Lumshe idonshi yayi yar kwallar dake makale ta fado maida idonshi yayi ksn kugunta domin ya tabbatar da abunda ya gani ……Tabbas idan idanuwanshi ba gizo suke mashi ba uwar tulluwa ya hango a bayan kugunta sannan ga uban kalar da zanin ya sake daga sama …… *ZAN RAYU DAKE..FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. [9:27PM, 11/2/2017] Feedohm💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU 🌹*🌹*🌹* 🌹*🌹* 🌹* © *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Haske Writer's Association_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. ( _Haske Writer's Association_*Home of expert & perfect writers_Haske Writer's Association_* ) *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*NA_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Devoted to Ummi A'isha👌🏻**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Bestowed to Aunty Sis💕**ZAN RAYU DAKE.. 3⃣0⃣ A razane ya karasa yana kallonta "Wat happen Madam?ya fada yana kallon fuskarta Shiru ta masa tare da janye hannunta daga jikin Maryam ta shiga bayan motar…… da ita da Abba ne a baya sae maryam da ta zauna gaba ……bakin fita gari suka hadu da family din JB da Suka yo mashi rakiya wanda har mom dinshi ciki ……Bayan sun gama gaisawa maryam ta koma baya JB din ya zauna gaba tare da juyowa yana kallon Safeena ba wata kunya ya kashe mata ido yana fadin "Babynah ya dae?……You'll be ok kinji ko da munje zakiyi enjoying life dinki better than nan garin,I'll be so caring ……" Lumshe ido tayi tare da kwantar da kanta a kafadar Abba ba tare da tace komae ba ……kallon maryam yayi yace "Sister ya jikin baby? Ita kam kunya ma ya bata gaban Abban zai dinga kira masu wani baby dan murmushi ta saki tana kallon safeena sannan tace "She's ok……" "Good " ya fada tare da juya ya fito da wayarshi yana latsawa……Maleek kam da kyar ya iya controlling kanshi babyn da JB ya fada ya hargitsa mashi kwalwarshi …… Masallacin kankia zuhur ta masu Abba yace su tsaya suyi sallah tukun ……Duk suka fita sae Safeena dake zaune ita kadae ta kwantar da kanta baya ……har Maleek ya gama alwala amma baiga ta fito ba…… Ruwa ya diba a buta ya matsa tare da bude bayan motar "Madam ki fito kiyi sallah……" Wani irin kallo ta watsa mashi tare da maida idonta ta rufe ……Ajiyar zuciya ya sake a bayyane don ko hararan madam abun so ce sannan yace "Sorry Madam na fahimci matsalarki amma kiyi tunani abunda ke jikinki ba normal Pes bane na ciwone kuma Allah bai yafe sallah baga mai irin wannan ciwon indae ta tabbata a normal pes dinta bane kiyi kokari kiyi sallah tunda tana kanshi ko bakiyi ta yanzu ba sae kin ramata……" Dan bude ido tayi tana kallonshi idan bata manta ba malamai suna fadin an dauke sallah ne ga macen dake jinin al'ada ba wae jinin cuta ba ……idan har jinin ya zama na cuta to duk lokacin sallah zatayi tsarkine sannan tayi sallarta…… "Thank you……idan mun isa inda zamu zanyi maleek"ta fada a hankali Murmushi yayi sannan ya mike ya koma yayi sallar lokacin duk sun gama suna addu'a ne sae da ya gama tashi sannan ya dawo suka cigaba da tafiya …… Kusan karfe 3 Suka isa airport din dan restaurant din dake gefe suka zauna amma banda Safeena dake zaune taki fitowa ……JB ya kirashi "Kai zo nan ……" Ko nuna yaji alamun kiran baiyi ba har dae Abbah yace "Abdul Maleeku zo mana……"sannan ya matso tare da dukar da kai gaban Abba "Kazo kaci abinci mana ka ja ka tsaya gefe……"ya fada tare da nuna mashi kujeran dake gefenshi Dukar da kai yayi yana fadin "No Abba koshi sae dae wanda zaa mikawa madam naga bata fito ba ……" Kallon motar Abba yayi tare da juyo da kai yana kallon Maleek din sannan yace "Bara ta ci ba Abdul Maleek tunda zamu fito na tambayeta me take so tace man ta koshi……" "Abba to ko cake na kai mata ……"ya fada a hankali ……Dan murmushi Abba yayi sannan yace "To Abdul Maleeku ka shiga ciki ka dauko mata ka kai mata idan zata ci……" JB yayi saurin fadin "Abba kyaleshi ba wani cake din da zata ci yanzu……" "May be taci Jabir kasan tana da kusanci da shi sossae ya fi kowa sanin abunda zake bukata ……Jeka Abdul Maleek ka zabar mata sae ka kai mata kaga idan zata ci kaji ko……"cewar Abba da murmushi shinfide a fuskarshi Eclair cake ya daukar mata da freshmilk sannan ya nufi motar da addu'ar karta yarfa shi don yafi kowa sanin yarfin madam…… Bude motar yayi ya shiga sossae sannan ya mika mata cake din yana fadin "Madam ga cake……" Dan Murmushi ta saki sannan ta bude idonta tana kallon cake din ……karba tayi tana fadin "Thanks ……"sannan ta aje bayan motar ta lumshe ido "Please madam ki ci yanzu dan Allah ……"ya fada kasan makoshi "Na koshi maleek"ta fada atakaice…… "Dan girman Allah madam ba dan na isa ba……" bai rufe baki ba ta dauko cake din tare da budewa ta kai bakinta tana kallonshi ta kasa kasa ……Tunda ta fara ci ya kafe ta da ido yana jefa mata wani irin sassanyan kallo ……har sae da taci rabi sannan ta dago tana kallonshi ,First time kenan da ta ji kunyarshi a rayuwarta ,saurin maida kanta tayi kasa tare da juyawa ta kalli window …… A wahale yace "Sorry…… Ba tare da ta juyo ba tace "How did you bear when i insulted you so badly without understanding you? Da sauri ya bude mata marfin fresh milk din tare da mika mata ……Idanuwanta cike da hawaye ta juyo tana kallonshi,bai dauke nashi idon ba sae ma salon kallon da ya sake mata …… Muryar JB yaji yana fadin"Kai meye haka why are staring her?common dallah fito malan baka san matar aure bace zata tasa ta gaba da wannan shegen kallo ,Baby what happen? Saurin juyar da kanta tayi ba tare da ta amsa Maleek din ya bar motar sae da kamshinshi da ya tana fitar da kwallah ……tabbas tana son JB amma ranta to idan hakane tana Kaunar Maleek ne tana masu ba tana jin lokacin da bar mata rintse ido tayi gam ta tabbata tana jin Maleek A son Jabir…… Ganin Maryam da Abba sun taso ya tabbatar mata da tafiya zasuyi……shigowa maryam tayi tare da sake bglass na motar ta mika mata zani ta canza sannan ta kamo hannunta suka fito tare ……Da sauri JB ya karbi hannunta tare da rungumota jikinshi …… Juyawa tayi tana neman Maleek amma duk arean babu shi sae kamshin turarenshi da ya cika masu gurin ……Hawaye suka taran mata a ido ta daga kai a sanyaye tana kallon JB shima ita din yake kallo ……cikin salo ya kashe mata ido tare da kanne guda daya ……murmushi ta danyi sannan ta juya tana kallon Abba dake gefenta shima ita yake kallo idonshi cike da kwallah Sae maryam dake kallon kasa ko baa fada mata ba tasan kuka take ,idanuwanta suka ciko da kwallah ……"Abba……"ta fada hade da bata baki zatayi kuka Lumshe ido yayi yana juyar da kai "May God be wit you love……" ya fada a hankali tare da juyawa ya rike hannu Maryam suka tafi ,Wani kuka ta sake tana fadin "Please Abba maryam dan Allah wallahi na fasa zuwa *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU DAKU*ZAN RAYU DAKE.. Abbana karku barni ……" Ta fada tana kokarin fizgewa daga rikon da JB ya mata……sossae ya kara rungumeta yana shafa kanta har suka shiga waiting room …… *ZAN RAYU DAKE..FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. [3:00PM, 11/3/2017] Feedohm💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU 🌹*🌹*🌹* 🌹*🌹* 🌹* © *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Haske Writer's Association_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. ( _Haske Writer's Association_*Home of expert & perfect writers_Haske Writer's Association_* ) *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*NA_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Devoted to Ummi A'isha👌🏻**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Bestowed to Aunty Sis💕**ZAN RAYU DAKE.. 3⃣1⃣ *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*This page is for you swthrt Aysha hameed🌹* Maryam Auntyn Maleek🌹* Maman hanif🌹* besty firdaws Ahmed🌹* Meenarh parrot🌹* Meela Adeel🌹* Aunty Maijiddah musa🌹* Ummi Muhsan 🌹*Abdul Maleeku Heart you 💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. A cikin motar suka iske Maleek zaune ya kifa kai a sitiyari har suka shiga ba wanda yace kala jin sun rufe kofar motar ne ya sashi kunna motar suka tafi …… tafiya suke kamar kurame Abba na kallon window gefenshi Maryam na kallon ta gefenta tana fitar da kuka a hankali ……Maleek kam gabanshi kawae yake kallo ba tare da dauke ido ba …… 《》《》《》《》 Da daddare suka isa hotel din dake kusa da asibitin suka sauka tana rungume jikinshi,har suka shiga dakin sannan ya zaunar da ita gefen gadon ya koma yana kokarin shigo da kayansu …… Lokacin da ya dawo tana kokarin shiga toilet da sauri ya matsa tare da rungumota jikinshi ganin zata fadin "Baby bara ki jira nazo na kaiki ba……" Dan murmushi tayi ba tare da tace komae ba ,hancinta ya dan ja yana fadin "Inda kin fadi ba?Karki sake kinji ko zan maki komae kike bukata beside ma me zakiyi toilet din? A hankali tace "Zanyi wankane nayi sallah……" Dan waro ido yayi cike da mamaki "Wane irin sallah kuma baby bayan kina Pes…… Common muje na taimaka maki kiyi wanka ……" Shiru ta masa suka shiga toilet din a tare sannan ta kalleshi da raunannun idanuwanta tace "Please ka fita zan iya wankan da kaina……" Spreading arms yayi sannan ya fita tare da janyo mata kofar ……Mintina kadan ta fito daure da towel sannan ta dauki kayanta da pad ta koma toilet din ta saka …… "Bara nima nayo wankan ko baby ……"ya fada yana dan rungumota tare da kissing wuyanta …… Tsigar jikinta ne ta tashi cikin dubara ta janye jikinta tana murmushi …… Shinfida abun sallah tayi shi kuma ya fada toilet din ,Da sauri ya fito yana yatsina fuska "Baby wadancan kayan da kika cire ya za'a maki da su……" A tunaninta ya san dae wankewa za'ayi sannan yana sane da barata iya wankewa da kanta ba ……Shirun da yaga tayi ne yasa yace "Baby zaa zubar dasu ne ko? "Zubarwa JB?Ta tambaya tare da kura mashi ido …… "Yeah baby kinsan dae baran iya wanke wadancan kazantar ba ko?infact ma nayi hating jini ko wane irina kinga kenan sae dae a zubar dasu……"ya karashe maganar tare da fadawa saman gado Gabanta ne ya fadi ta bishi da kallo sannan tace "Amma kasan baka son jini ka yarda da aurena sannan kuma ka biyoni ai da kayi zamanka nigeria mun taho da Maryam am sure zata man duk abunda nake bukata……" "No baby jinyarki ai dole sae muharraminki zan maki komae jinin ne kawae baran iya tabawa ba ……please ki dan shiga ki sakasu cikin leda sae na yardo ina son zanyi amfani da toilet din……" Uwar harara ta sake mashi tare da kabbara sallah abunta ……har ta gama sallolinta yana kwance ya kasa shiga toilet din sae da ta gama addu'a sannan ta dafa bango zata shiga toilet din ……da sauri ya taso yana fadin "Baby nace maki ki bar tafiya ke kadae kada kije ki fadi ……" Banza tayi masa har ya kaita toilet din ya fito yana rufe hanci ,ko da ta zuba a ledar kin bashi tayi ta kama hanya zata je ta zubar kamar yarda yace ……tana masifar don doguwar riga saboda lokacin da Abbanta yaje US ya sawo mata ita amma tana gani ta jefar da ita a cikin GG din harabar hotel din ……ko da ta dawo yana toilet yana wanka Cikin jikarsu ta bude ta fito da katuwar leda ta shifida saman bed din sannan ta kwanta tare da rufe dukkan jikinta ……ya fito yana goge kanshi da towel ganin ta lullube ya sashi karasa bakin gadon ya zauna yana fadin "Baby ba dae har kin kwanta ba bakici abinci ba……"ya karashe maganar tare da yaye blanket din yana kallon bayanta Dan karamin tsoki yaja yana fadin "Gaskia wannan abun bai kyauta mana ba baby da yanzu muna can muna enjoying life dinmu wallahi ……ko da yake sati biyu ne zamuyi kuma assure kafin lokacin kin warke kinga daga nan istabul zamu je muyi honeymoon dinmu ko……? Ba tare da ta juyo ba tace "Waye yace maka sati biyu zan warke ……idan sati biyun yayi ban warke ba fa? "Daina fadar haka man baby ……yanzu dae tashi kici abinci ……" Bata kuma cewa komae ba ta gyara kwanciyarta "Au bara ki ci abincin ba baby ……shikenan ai cikinki ne ni dae baran iya kwana da yunwa ba ……" 《》《》《》《》《》 Bayan sun isa garin Abba yace a fara kai Maryam gida sannan suka karasa cikin unguwarsu kusa da wani mai dama fura Abba yace a tsaya yana so Abdul Maleek dinne ya fita ya sawo mashi sannan ya dawo suka karasa shiga gidan …… Cike suka iske gidan kamar ana wani biki Maleek na rike da ledar Furar suka shiga falon Su Uncle Abbah ne da Fadila anyi rashe rashe kadsn carpet ana cin abinci ……Suna ganin Abban suka mike tare da gaidashi ,daga masu hannu yayi cikin fara'a sannan ya karbi ledar hannu Maleek din yana fadin "Karka tafi Abdul Maleeku yanzu zan fito na baka sako ka kaiwa Hajiyar Safeena" A falon ya zauna tare da fito wayarshi yana latsawa Number Safeena ya kurawa ido yana yawo da hannunshi saman screen din wayar …… Fadila ta kalli Uncle Abba tare da kanne mashi ido sannan ta dauki bottle na swan da cup ta rarrafa kusa da Maleek din tana fadin "Ya Maleek ga ruwa ……" Murmushin yake yayi sannan ya girgiza mata kai yana fadin "Alhamdulillah……" Dan shagwabe fuska tayi tana fadin "Ruwan ma bara kasha ba?Dan Allah kasha kaji……" Kallonta yayi na secs ko baa fada mashi ba ya san sarae ita ce Aunty Fatee ke mashi magana sannan itace ke yawan kiranshi da turo mashi message…… "Ka karba mana ……ta sake fada cikin muryar jan hankali "oh na manta ashe ban zuba maka ba sorry……"ta karashe maganar tana kokarin zuba mashi a cup Samun kanshi yayi da kiran Number Safeena bai damu da iyayin da Fadilan,ke mashi ba ……Cikin saa ringing biyu ta dauka cikin sanyin murya tayi sallama "Madam……"ya fada tare da lumshe idonshi Zaune ta mike jin muryan Maleek din sannan ta kalli gefenta inda taji JB ya kwanta amma wayam babu shi tabe baki tayi ganin baya dakin sannan ta maida hankalinta gurin wayar da taji Maleek na fadin "Madam kina jina……? "Eh ……" ta amsa a takaice "Ya jikin naki? "Am okey……" "Alhamdulillah ……" ya fada tare da yin shiru na yan mintina sannan yaja numfashi tare da fadin "Sleep well madam……ki rike addu'a Nothing will happen to you Madam kinyi duka sallolinki……" Gyada kai tayi kamar yana kallonta tare da goge yan kwallan da suka zubo mata he's such a caring person ta fada a ranta ,jin ya sake yin shirun ne ya sata komawa ta kwanta wayar na makale a kunnenta A hankali tace "You done much to me Maleek……" Katse wayar tayi ba tare da ta jira abunda zaice ba …… Sam ya manta da Akwae mutane a falon sae da ya ga Fadilan ta mike tare da fadawa dakin Aunty Fatee da gudu "Ikon Allah……"ya fada a fili tare da kallon Uncle Abba dake ta faman zuban mashi harara Yar dariya ya sake mai sauti to meye hadinshi dasu Spreading arms yayi ya mike ganin Abban yana saukowa,Kudi Abban ya mika mashi yana fadin "Hajiyar Safeena zaka kai mawa kace ta fara amfani da wannan gurin maganin kafin na shigo ……" Hannunsa ya janye daga karbar kudin yana fadin "Zan bata Alhaji akwae kudi hannuna……" "Ka karba mana ka kai mata ……"Abban yace tare da sake mika mashi Girgiza kai yayi kanshi na kasa alamun bara ya karba ba "Meye haka Abdul Maleeku gardama zan tsaya da kai?ka karbi kudi ta kaiwa hajiya final……" "Afuwan Alhaji in dai ni zan karbi kudinka na kai awa Madam dita magani banga amfanina ba a rayuwarka ……dan Allah kayi hakuri na nemawa Madam dita magani da zufar Aljihuna……" ya karashe maganar muryarshi na rawa Shiru yayi yana kallonshi tabbas Maleek mutunne mai tsananin tausayi da alkhairi shi Kanshi ya yarda da cewa Abdul maleek ya aje diyarshi wani guri na daban a rayuwarshi ……hannunshi ya kama yana gyada mashi kai "Nagode Sossae Abdul Maleeku Allah ya albarkaci rayuwarka……" *ZAN RAYU DAKE..FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. [10:24PM, 11/3/2017] Feedohm💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU 🌹*🌹*🌹* 🌹*🌹* 🌹* © *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Haske Writer's Association_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. ( _Haske Writer's Association_*Home of expert & perfect writers_Haske Writer's Association_* ) *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*NA_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Devoted to Ummi A'isha👌🏻**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Bestowed to Aunty Sis💕**ZAN RAYU DAKE.. 3⃣2⃣ *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Wannan page din nakine khadija bee bee ta Allah ubangiji ya raya mana ilham sda sulteen Aunty Sis💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. Shiru yayi yana kallonshi tabbas Maleek mutunne mai tsananin tausayi da alkhairi shi Kanshi ya yarda da cewa Abdul maleek ya aje diyarshi wani guri na daban a rayuwarshi ……hannunshi ya kama yana gyada mashi kai "Nagode Sossae Abdul Maleeku Allah ya albarkaci rayuwarka……" Fadila kam dan yalolan gyalenta ta dauko dake aje saman gadon Aunty fatee ta fito tana kuka ……Aunty fateen ce ta biyota tana fadin "Ke fadila lafiyanki kuwa me aka maki kike kuka……? Shiru ta mata ta fita daga gidan ,har ta isa gidansu tana kuka ta fada dakin mamanta ,"Me ke faruwa fadila?Aunty zuby ta fada cikin sauri tare da rungumota jikinta Cikin kuka tace "Mum wallahi sonta yake……" ,"Wacece ya ke so kuma?waye ma fada man kinji fadila……"ta fada cikin lallashi "Mum Maleek mana wallahi Safeena yake so kuma na rantse da girman Allah sae dae ya mutu mu duka mu rasa shi……"ta karashe maganar tare da sake kuka da karfi "To Uban wa yace maki sonta yake?kuma an fada maki ana aure cikin aure ne…… Sakara ki kwantar da hankalinki ko jiya Hajiyarmu ta kai numbershi gurin boka kuma ya tabbatar mata da naki ne……" Share hawayen tayi tana kallon Mum din tata tana so ta gasgata abunda take fada ……Tabbas indae Maleek ya zama nata She's the luckiest person a duniyar nan ……Cikin farinciki ta rungumo Aunty Zuby tare da manna mata dan kiss tana fadin "I Love you Mum……" Cikin Wasa Aunty zubyn ta harareta tana fadin "Da kinzo zaki daga man hankali akan abunda kinsan dole ki sameshi ……" "Sorry Mum……" ta fada hadi da turo baki 《》《》《》《》《》 Karar shigowar Message da tajine ya sata bude ido a wahale tare da kallon JB dake kwance bisa doguwar kujera kafafu a hanbare kamar wani sabon arne ……Dan karamin tsoki ta sake tana duba agogon dake makale jikin bangon dakin…… 5:15am ta gani wayar dake haske ta saka hannu ta dauka sunan Maleek ke yawo baro baro a jikin message din da aka turo ……Dan guntun message ne ya turo "Madam ki tashi kiyi sallah……"Lumshe ido tayi sannan ta mike da kyar tana kallon inda ta kwanta sam babu sauki, ta fasa a ranta……duk da kwannansu uku ana treating din ta tare magunguna masu dan karan tsada…… Bango ta dafa da kyar tana hararan JB dake ta uban baccinshi sam bai da kula da addininshi wani abu ya tokare mata kirji ,bata samu sauki ba sae da ta dauki robar lemun dake aje gefen gadon ta wurga mashi a fuska ……duk da ta dakeshi sosae amma ko motsi baiyi ba ……tayi tsoki yafi sau 10 sannan ta shige toilet din da kyar tayi wanka tare da tsarki ta fito tayi sallah ,har lokacin baccinshi yake Kamar ta kyaleshi ta dai daure ta kai hannunta tana dukan pillow da ya daura kanshi a hankali tare da kiran sunanshi"Jabir ka tashi kayi sallah ……" Hannun da take dukan pillow dashi ya rike gam tare da bude idonshi a hankali "Baby kin cika takura……" ya fada cikin muryar bacci Tabe baki tayi tana harararshi ta kasan ido sannan tace " Sallan ne takura? "Baby ai ko karfe 11:59am zan iya sallan asuba tunda baa shiga pm ba ……"ya fada yana kokarin gyara kwanciya Bata san lokacin da tace "In ji wane jakin malamin? "Please Ki barni nayi bacci baby promise da na farka zanyi kin ji ko ……" Banza ta masa ta cigaba da addu'o'in da Maleek ya turo mata …… 《》《》《》《》《》 Duk wani abu da granny zatayi Maleek ne ya fansheta, har ga Allah nema mata maganin musulunci yake iya karfinshi Tun lokacin da granny ta fada mashi cewa ciwon Safeena bana asibiti bane hankalinshi yaki kwanciya…… harta office idan yaje karfe sha biyu yake baroshi ,Duk inda yaji wani babban malami yana gurin…… Baya k'ashin kashe ko nawa ake bukata sannan ko Abba bai san me yake ba Iyakarshi da Abban kullun dare zai kai mashi fura sannan su danyi fira kadan ya tafi…… ko yarda baya yi su gaisa da Aunty fatee saboda wani mugun haushinta da yake ji Hajiyarsu Aunty Fatee kam ta dage iya karfinta dole Maleek din ya so Fadilanta ko ta halin kaka…… Yau ma tun da safe ta kira Aunty Zuby tace ta turo mata Fadila su tafi gurin bokan tare ……Mintina kadan Fadilan ta zo ,basu bata

Chapter 7 of 16