Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kece raini amma sam hankalin amaryar baya jikinta wajen 10pm aka gama partyn ……Safeena kin shiga tayi motar JB din duk nacin shi sae dae ya hakura Maryam ta tafi da ita …… "Feena wae lafiya kike ?ki zauna sossae man……" Maryam fada tana kallonta Girgiza kai tayi a hankali tana matse idonta ba tare da tace komae ba …… Kamo hannunta Maryam din tayi tare da damkewa cikin nata "Feenat me ne……? "Am totally comfortless Maryam ……"Ta fada tana kallon window "Fada man mene Feenat ……" Ta sausauta murya tare da kamo hannunta "Ki kaini gidan granny please ina son magana da ita yanzu ……"ta karashe maganar tare da mikewa daga kujeran motar da sauri har tana bigewa …… Shiru maryam tayi ganin idonta ya kawo ruwa kadan ya rage ta sakar mata kuka………dafe gefen cikinta da ke murda mata da karfi tayi ta kwantar da kanta saman cinyoyinta…… Kofar gidan granny din tayi parking ta fito tare da zagayowa ta bude gefen da Feena din take tana kallon yarda take ta uwar zufa duk da sanyin motar …… Dafa bayanta tayi tare da dukar da kanta tana fadin "Sorry besty mun iso ……" A wahale ta dago sannan ta mayar da kanta ta kife a saman cinyarta tana cije upper lip dinta da karfi , tafi kusan minti biyar sannan ta sauko da fararen kafafuwanta da ke sanye da hills red kasa ……a dafe ta fito daga motar tana dafa Maryam ,sae da ta gama saukowa gaba daya sannan ta juya tana kallon inda ta zauna lokaci guda ta kalli Maryam tana share hawaye da bayan hannunta na dama…… Dan murmushi maryam ta sake tana girgiza mata kai a hankali "I'll clean……" ta fada tare da kama hannunta ta rufe marfin motar suka shiga gidan Granny din …… Maryam nayin Sallama granny ta amsa tana fadin "A'a kaga yan albarka Haba shi yasa tun dazu nake jin kamshin amare Allah yasa kayan partyn nima aka kawo man ……" Karasa sukayi falon maryam na fadin "Wani kayan party zaa kawo maki granny? to ki ci su da wanne hakora ……" Yar dariya granny ta yi tare da rufe fridge din ta juyo tana kallonsu ,lokaci guda ta zubawa Feena ido tana fadin "Lafiya kike rike ciki Safeena ……" Bisa doguwar kujera maryam ta daurata ,tayi saurin zamewa tana kallon ta tare da sake kuka …… Idanuwan Maryam itama suka kawo kwallah tana fadin "kar ki kwanta a kasa Feena ……" "Maryam so kike na bata mata kujeru?ki barni a nan tun dazu nake saki aiki Maryam……"ta karashe maganar cikin kuka "Nace maki baran gyara bane Feena?ko nace maki na gaji ne? karki kwanta a tiles akwae sanyi besty……"ta fada murya na rawa Granny ta matso tana fadin "Me ke faruwane Maryam?bata lafiya ne?husaina menene……? Wani kuka ta sake mai ban tausayi maryam ta zame jikinta tare da rungumeta tana fadin " granny period take kuma cikinta na mata ciwo sossae shine tun dazu take kuka……please ki mata magana ta bar kukan……" Dan Karamin tsaki grannyn ta sake tana fadin "Ban san shashancin banza ,ta ci gaba da kukan mana dan kaniyarta ……dallah ku tashi ku bani guri ……kai wallahi ku zo ku fice man daga gida ma tun kafin na sab'a maku……" ta karashe maganar tana nuna masu kofa "Granny cikinta ke ciwo fa sossae ……"cewar maryam "Wallahi zan ci mutuncinku baki daya…… ciwon cikin ne bak'on abu gurinku ko ko me a ciki?Don iskanci sae ku sani gaba da kuka akan Abunda ya zama dole kuyi kuma ku ke yi duk month……Maryam ki jata ku barman falo ko naci mutuncinku ja'irai kawae ……" Kuka Safeena ta sake tana fadin "Granny ba normal jini bane da na saba yi ……" A dan fusace ta jiyo tana watsa masu harara "Die normal ne dan gidanku?wallahi maryam zanci mutuncinki ke da kika kawo man ita ……" Mikewa Maryam tayi tare da kama hannun Feena tana fadin "Besty sorry kin ji ko…… tashi muje daki na hada maki ruwan wanka ki canza kaya wadannan sunyi staining da yawa ……" Mikewa tayi a hankali tana cije lips dinta na kasa tare da dafa Maryam ……a Tare suka kalli inda ta zauna su duka ukkun sam ba kalan jini bane gurin yayi powly black kamar charcoal …… "Safeena ,Maryam me ye haka ku ka kwaso gurin da kallon mamaki man a falo ……?cewar granny tana bin Cikin rawar murya maryam tace "granny tun dazu menstruation din Safeena ya koma haka ,granny ban taba ganin haka ba a rayuwana…… please dama yana komawa black? Shiru tayi kamar tana tuna wani abu ,lokaci guda ta nufi Safeena tare da sa hannu ta juyota tana kallonta "Safeena da karfi da zafi kike jin menstrual din yana fita ko? ta tambaya duk ta rude Gyada kai tayi a hankali tana kallonta ba tare da ta amsa ba ……Rufe ido granny tayi gam tana nuna masu su shiga daki kawae ,haka maryam ta riketa har bakin gado ta zaunar da ita har lokacin idonta na rufe ta dafe gefen cikinta "Sorry Feenat you'll be ok kinji ko besty……"abinda ta fada kenan sannan ta shiga toilet ta hada mata ruwan zafi sannan ta dawo ta kamata ta shiga da ita ……Dan bakin gadon da ta zauna ma har yayi stain,yaye bedsheet din tayi tare da lekawa falo zata tambayi granny din ko tana da katuwar leda ta shimfidawa Safeenar sannan sae ta saka mata bedsheet gudun kar matress din tayi staining ,hango Granny tayi inda suka barta tsaye kamar an dasa ta ……Jikinta ya kara yim sanyi ta matsa a hankali tana fadin "Granny ko kina da babbar leda irin ta cikin buhun sugar haka ……? Juyowa tayi ta kalli Maryam din tare da girgiza mata kai tana fadin "Maryam tun yaushe Safeena ta fara wannan abun? "Granny bayan ta dawo daga gidansu Aunty Fatee meeting tace man ta fara ,kuma ta fada man duka two weeks kenan da ta gama normal period dinta ……shin dama ana irin haka granny she's too unwellfull am scared na rasata ,wallahi tun dazu take kuka ko zamu kaita asibiti ne?tunda da motan mu ka zo ……" Wayar Safeena ce ta fara ringing Maryam ta dauko ganin My Future husby ya sata gane JB ne ta daga cikin sanyin murya tare da sallama "Maryam ina Feenat din ……?ya fada jin ba muryar ta bace "She's too unwell JB ta samu bacci ne ……" "Me ke samunta Maryam?kuna ina yanzu ?i wanna see her please……"ya fada a rude Kallon granny tayi sannan tace "don't mind ta samu sauki har ma tayi bacci zuwa da safe kunyi magana ……" "Please kuna ina? "Dutsin safe gidan granny JB please ba sae kazo ba tayi bacci wallahi ……" Ba dan yaso ba ya hakura yace da safe zaizo ya ganta sannan ta aje wayar ta shiga kitchen ta hado mata coffee ta dawo ta wuce granny har lokacin tana tsaye ……Da kyar ta samu tasha coffee din sannan ta gyara mata inda zata kwanta ,sae da ta tabbatar ta kwanta sannan ta dawo falo gurin granny ta zauna tare da fito da wayarta ta kira Mamanta ta fada mata tana gidan grannyn besty acan zasu kwana 《》《》《》《》 A Hankali yake juyi ci kadae bisa madaidaicin gadonshi zufa ko ta ina ke yanko mashi mummunan mafarki yake akan wata kyakykyawar yarinyar dake ta gudu cikin daji tana kuka ,bayanta wasu irin mugayen halittu ke binta a guje ,dae dae wani katon rami kafarta ta daki wani dutsi ta fadi kasa ,gangarawa ta farayi zata fada cikin katon ramin yayi saurin damko hannunta ya rufeta da kirjinshi …… mugayen halittun dake binta suka zo suka wuce ba tare da sun lura da su ba …… yana ganin sun wuce ya dago fuskarta tare da yaye gashin da ya lullubeta mata fuska yana kallonta …… A firgice ya farka yana kiran "Nana ……" tare da karewa duka dakin kallo ganin rana ta fara shigowa ta windown dakin ya sashi mikewa da sauri tare da leka window, calender dake manne jikin bango ya kalla tare da dafe kanshi ya juya baya "I failed……"hawaye suka gangaro mashi a hankali saman chicks dinshi *ZAN RAYU DAKE..FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. [4:58AM, 10/29/2017] Feedohm💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU 🌹*🌹*🌹* 🌹*🌹* 🌹* © *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Haske Writer's Association_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. ( _Haske Writer's Association_*Home of expert & perfect writers_Haske Writer's Association_* ) *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*NA_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Devoted to Ummi A'isha👌🏻**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Bestowed to Aunty Sis💕**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Feedohm novella kuna ina wannan page din nakune na baku shi kyauta ……I heart you wollah Allah ya barman ku……🌹*_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. 2⃣7⃣ Wayarshi dake saman gado ta fara ringing kamar bara ya dauka ba ya matsa cikin sanyin jiki ya dauka ,shiru yayi ba tare da yace komae ba jin wanda ya kira bai magana ba ,kusan seconds 15 sannan ya cire wayar daga kunnenshi yana kallonta har lokacin wanda ya kira yana online ……katse kiran yayi ya koma jikin window ya tsaya yana kallon waje ……yana jin wayar ya sake ringing amma har ya katse bai kalli gurin ba ,toilet ya fada ya watso ruwa sannan ya saka shirt fara da blue din jeans ya fesa turare ya dauki wayar ya fito ……Food palace ya shiga yace a kawo mashi paula deen's coconut potage……yayi kusan 20mints yana juya spoon din ba tare da ya kai abincin a baki ba Karar shigowar message ya sakashi dube wayar yana budawa new number ce …… _Haske Writer's Association_*" The more u go away from me,I'll closer forward my self to you.……I May not say any word only my heart will tell you're special Abdul Maleek ……"_Haske Writer's Association_* Tabe baki yayi ya mayar da wayar ya aje tare da aje spoon din ya kife kanshi…… hawaye yaji suna neman zubo mashi a fuska "I failed ……I Love you Safeena you're my life i can't asse without you Madam please don't neglect me Safeena Wallahi na fi kowa kaunarki *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU DAKE*ZAN RAYU DAKE.. Safeenah……" Bayanshi yaji an dafa ya dago da sauri yana share hawayenshi wata yar budurwar yaren igala ya gani ta kura mashi ido …… Bata fuska yayi tare da sake mata harara yana fadin "What……? Ganin ba wasa a fuskarshi ya sata juyar da kai sau biyu tana smiling ……"Cutie……"ta fada a hankali …… Karamin tsaki ya sake ya mike ba tare da ya kara bin ta kanta ba ……ji yayi zaria gaba daya ta isheshi bare ma mafalkin da yayi masifar daga mashi hankali …… Girgiza kai yayi baya jin zaya iya komawa garin a daurawa Safeena aure yana garin …better ya bari zuwa monday ya koma lokacin ya tabbatar da ya rigaya ya rasa Madam ……Tafiya yake amma sam hankalinshi baa jikinshi yake ba ……mai motar da ke ta mashi horn ya tsaya tare da fitowa yana bala'i ……wanda yake yin bala'in donshi sam bai ma san anayi ba …… 《》《》《》《》 Ranar Saturday da safe granny ta saka aka kira mata Abban Safeena cikin mintina kadan ya iso a falo suka zauna bayan sun gaisa tace "Safeena bata jin dadi ko za'awa iyayen mijin magana a daga bikin zuwa ta samu sauki ……" A rude yace "Me ke damunta Umma? Iyakar abunda take iya fada mashi ta mashi bayani ,shi kanshi sae da jikinshi yayi sanyi ya kalleta a sanyaye yace "Umma ina Safeena ……? "Tana daki tare da Maryam ,na karbo mata wani magani dazu gurin malan habibu nan makwabtanmu kafin mu gama magana naje daura ……" Numfashi yaja a hankali sannan yace "Idan d'aga bikin ne mafita Umma a kira angon sae a gaya mashi su hakura zuwa lokacin da zata samu sauki ……" "Gaskia kam dan duk yarda kake tunanin abun ta wuce nan don wallahi yau yadda kasan icce haka take komae Maryam ke mata nan da can ta kasa matsawa saboda azabar ciwon ciki ……garama yanzu naga maryam din ta kamata sun shiga toilet tayo wanka ……" Maryam ta fito rike da plate zata kai kitchen har kasa ta duka tana fadin "Abba ina kwana ……" "Lafiya lau Maryama ya jikin Safeena? Rau rau tayi da ido tana fadin "Ba sauki Wallahi Abba……" Mikewa yayi jikinshi na rawa ya shiga dakin ,akwance ya isketa tana kallon sama ,juyowa tayi tana kallonshi hawayen dake makale a idonta suka gangaro lokaci guda ta sake murmushi tana fadin "Abba……me yasa?Abbana mutuwa zanyi,wallahi cikina kamar zaya kone Abbah dan Allah ka man addu'a na samu sauki ……" Da sauri ya matsa tare da riko mata duka hannuwanta yana girgiza mata kai "ki dauki kaddara kinji Safeena ,bara ki mutu ba insha Allahu zaki samu sauki kinji ko ……ba ciwon ciki kawae bane ……" Kuka ta sake tana fadin "Abba kawae ne?jibi Abbah ……"ta fada tana kokarin mirginawa ta sauka daga shinfidar da Maryam ta mata …… Dafe kai yayi ganin gurin kamar wacce ta haihu yanzu, sannan yayi powly black sossae "Karki damu kinji ko ……Allah yana ganinki insha Allahu zuwa ranar monday zan nema maki visa a kaiki india indae bai tsaya ba ……" Gyada kai tayi a hankali tana share hawayen "Abba bana son auren kacewa JB ya hakura Abbana sae na warke ……" "Daina kuka mana ,ko so kike ki karyawa Abbanki zuciya Safeena?bara na kirashi sae a bashi hakuri ……"ya karashe maganar tare da lalubo wayarshi ya kira JB din yace ya sameshi nan dutsin safe yana son magana dashi yanzu …… Cikin mintina kadan ya iso ,a harabar gidan yaga maryam a rude yake tambayarta ya jikin Feena…… "Da sauki "ta fada tana rufe window din dakin granny sannan ta mashi jagora zuwa cikin falon granny …… Cikin Fahimta Abba ya mashi bayanin halin da ake ciki tare da bashi hakuri a dage bikin zuwa ta samu sauki …… A rude ya fara fadin "A'a Abba dan Allah kar a daga mana biki ,ka taimaka man ka bari a daura auren yau wallahi ,ko ya Feena take zan iya rayuwa da ita na rokeka Abbah dan girman Allah ……" "Ka kwantar da hankalinka Jabir bawae baran aura maka Safeena bane a'a wallahi kawae ina sone na sama mata magani zuwa wani lokaci sae ayi auren kaga ko a musulunci bai kamata a baka auren yarinya ba tana dauke da lalura ……" Hawaye ya fara bi mashi fuska yana fadin"Wallahi Abba na yarda zan zauna da ita a haka dan Allah ka barni da ita ……" Duk yarda Abba yaso ya fahimceshi a fasa auren kin yarda yayi ,Granny tace a barshi kawae a daura auren tunda yace ya yarda "Allah ya alkhairi……" addu'a kam ya shata gurin Abba don ba karamin dadi yaji ba shi kanshi yasan idan aka fasa wannan auren ba karamin bakin ciki zai shiga ba ……ya kuma kara tabbatarwa da JB zai rike mashi Safeena da kyau …… Dakin da Safeena ke kwance ya shiga ,tana ganinshi ta mike da kyar zaune tana cije lips ……sam bata bakin ciki idan an fasa auren ko kadan saboda ta san babu namijin da zai zauna da ita da wannan kazantar ,daga jiya zuwa yau tayi amfani da pad yafi 50 amma a banza duk inda ta zauna sai gurin yayi staining …… Rungumeta yayi sossae yana fadin "Feena kina jin Abba na fadin wae a fasa aurenmu? Da murmushin yake a fuskarta ta janye jikinta tana fadin "To meye JB hakan shine dai dai saboda ina dauke da lalular da babu wani namijin da zai zauna dani ko da minti biyar ne ……" "Sae ni Safeena wallahi *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU DAKE*ZAN RAYU DAKE.. A duk halin da kike ……na bawa Abba hakuri ya bar man ke kar a daga bikin kuma ya yarda ……Safeena indae har aka fasa bikinnan son da nake maki karyane wallahi ……ki sa a ranki ni JB *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU DAKE*ZAN RAYU DAKE.. Ko da lalurar dake jikinki ta linka wannan sau dubu ……Ina sonki Feena soyayya ta gaskia wacce babu algusur a cikinta ki yarda dani……" Wani kuka ta sake tare da kifa kanta a cinyarshi ……ta rigaya ta yarda cewa Jabir na mata wani irin so wae wuyar fahimta …… Karfe 12:30pm aka daura auren Safeena Khaleed da Jabir ……daurin auren da ya samu halatta dumbin mutane daga sassa na duniya…… *ZAN RAYU DAKE..FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. [4:39AM, 10/30/2017] Feedohm💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. 🌹*🌹*🌹* 🌹*🌹* 🌹* © *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Haske Writer's Association_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. ( _Haske Writer's Association_*Home of expert & perfect writers_Haske Writer's Association_* ) *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*NA_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Devoted to Ummi A'isha👌🏻**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Bestowed to Aunty Sis💕**ZAN RAYU DAKE.. 2⃣8⃣ _Haske Writer's Association_*I'll write this in bolc *ZAN RAYU DAKE..DUK SHEGEN DA YA KARA KARBAR KUDI AKAN YA TURA LITTAFINA ALLAH YA ISA BAN YAFE MASHI*ZAN RAYU DAKE.. to you reader duk wacce ta sake bayar da kudi aka tura mata littafina ta karanta Allah ya isa wutar jahannama bal bal🔥🔥 banyi littafina don kudi ba don haka kar wani shege ya kara mayar man da littafi na kudi shegu munafukai suna amfani da basirar wasu suna kasuwanci😡__Haske Writer's Association_* "Haba Jabir duka nawa kake da zaka yarda da auren mace da lalura a jikinta……" Mum ta fada a harzuke Bata fuska yayi sossae yana fadin "Mum nace ki taimaka man ne ……ni ne fa nace na yarda kuma ni zanyi mata komae then meye damuwarku akai ……? Kwantar da Murya tayi sanin halin dan nata tace " Amma son yarda dad dinka ya man bayani bara ka iya ba……" "Look mum baki son soyayya bane?ko ba auren so kukayi da dad ba……i can do anything akan Feenatah karku saman ciwon kai please ……" "Ni dae……" "Ki saketa idan ke kika aura man ita ……" ya fada tare da mikewa ya shige daki ya barta zaune , binshi tayi tana fadin"yi hakuri son wallahi na yarda kazo ka zauna kaci abinci……" "Baran ci ba……" ya fada kai tsaye 《》《》《》《》 Su Aunty fatee kam hadadden biki suka shirya na gani da fada duk family da abokan arziki an hadu sae raha ake Inna ce ta kalli Aunty Fatee tane fadin "Fateema ni kam ina diyar taki ? tunda nazo ban ganta ba ……" Murmushi tayi tana fadin "Safeena amarya…… kinga nima inna tun jiya nake kiran wayarta a kashe amma bara na kira maryam nasan suna tare……" Cikin jin dadi inna tace "Kira man yar kusuwa kunya ta hanata shigowa ……" Dariya Aunty fatee tayi tana kiran number maryam ,ringing daya ta dauka tare da sallama ,handsfree ta saka tana fadin "Maryam ina kika kai man diyata duk yau ban ganta ba……" A Raunane tace "Muna gidan granny aunty fatee ……bata jin dadi Abba bai maki bayani ba……" Dafe kirji tayi tana fadin "Subhanallah me ya sameta? Zatayi magana Aunty fatee tace "Ina zuwa maryam ga Abbanta nan naji ya shigo bara naje na sameshi ……" ta katse kiran ta nufi gurin Abban A rude a tare suka shiga part dinshi ko zama baiyi ba tasha gabanshi idonta cike da hawaye tana fadin"Alhaji meke samun diyata? dan Allah ka fada man me ke faruwa da Safeena tun jiya banganta ba yanzu kuma na kira maryam tace bata lafiya……meke faruwane? Rufe ido yayi yana kallonta duk ta birkice jin cewa Safeena batta lafiya tausayinta ya kamashi sossae a hankali ya zaunar da ita gefen gadonshi sannan ya zauna yana fadin "Ki kwantar da hankalinki Fateema Insha Allahu zata samu sauki ……matsalarku ta mata ce to sae ta zo mata da wani irin yanayi ni kaina hankali ya tashi saboda hakan ma yasa ko asibitin nan bai kaita ba zuwa monday idan abun bai tsaya ba sae na fitar da ita india zata samu kulawa sossae……" Cikin kuka tace "Meye abun mata alhaji dan Allah ka man bayani sossae ……" Cikin natsuwa ya mata bayanin jinin dake fita daga Safeena da irin yanayin da yazo mata har sae da ya kai aya sannan ya ja numfashi lokaci guda idanuwanshi suka canza yace "Fateema irin yanayin da Aisha ta shiga shine Safeena ta shiga……" "Na shiga uku Yanzu abunda ya samu Aisha shi ke shirin samun Safeenata ……Wayyo Allah wannan wace irin rayuwace muke ciki Ya Allah ka tausaya man ka bawa diyata lafiya wallahi itace haskena ……"ta karashe maganar cikin kuka sossae Ganin ta fishi shiga tashin hankali ya sashi lallashin tashi zuciyar ya fara lallashinta tare da bata hakuri ta dauki kaddara ,da kyar ya samu ta yi shiru sannan ta mike tana fadin "……Ya Allah ka daukewa diyata wannan ciwon ka dawo dashi kaina……" "Kul Fateema ki daina wannan addu'ar mana kiyi addu'ar Allah ya yaye mata itama ……" "Ya zanyi Alhaji wallahi da Safeena ta zauna da wannan ciwon kara ni,na zauna dashi ……Dan Allah kama izni naje na gano diyata yanzu wallahi baran iya kara minti goma ba ba tare da na ganta ba ……" Lumshe ido yayi tare da gyada mata kai a hankali yana sakar mata wani irin kallo ……kalamanta sun tabbatar mashi da Fatee na son Diyarshi har ga Allah wani girma na musamman ya kara mata a zuciyarshi…… Dakinta ta shiga ta iske Aunty Zuby na tattara kayan da yan bikin suka zubar ,Aunty zubyn ta kalleta tana fadin "Ke kuma daga ina idonki yayi ja kamar an maki duka……" Tabe baki tayi tana fadin" Wannan shegiyar yarinyarce Abbanta yake fada man bata lafiya shine na sake mashi kuka farin ciki dan banyi asarar kudina ba ……shi kuma sae ya shige sossae yana wani jin dadi ina son diyarshi ……" Dariya ta sake tana fadin "Amma baki da dama wato kukan farin cikin bakiyi asarar kudinki kike ba ko ……? "To Zuby na bakinciki zanyi ……? Harara ta sake mata tana fadin "Da banci ubanki ba ……yanzu angon ya sani koko? Tabe baki tayi tace " Yace man an fada mashi JB dinma ya dage sae an daura auren ya yarda ……kinga bara naje na gano shegiyar don nace mashi yanzu zanje ……" Dariya ta sake tana fadin "Allah ya kara zafin ciwo……" Da "Ameen " ta amsa ta fita tana dariyar mugunta A falo ta iske granny zaune tana shan kunun tsamiya da alama daga makwabta aka kawo mata shi har kasa ta duka ta gaida ita tare da zama kasan carpet tana kallon kasa …… Wulakantaccen kallo Granny ta watsa mata tana fadin "Su Fateema ne? Hala kunji labarin Safeena batta lafiya? ta fadi maganar da zance biyu A hankali ta ja majina tana share hawayen da suka zubo mata tace "Eh wallahi Hajiya yanzu ma Abbanta ke fada man shine nazo na ganta ……" Ita kam kukan ma dariya ya bata ……ta saki dariya irin ta manya tare da rike haba tana fadin"Ikon Allah har da kuka Fateema……" Salon kukan ta canja tana fadin "Ba dole ba inyi kuka hajiya ……ki duba fa yarinya sae da aurenta yazo ace jini ya balle mata kuma na cuta haba dan Allah ai abun da tausayi ……" Yar siririyar dariya ta kara saki tana fadin "To fa ……ki shiga suna daga ciki ……" Mikewa tayi da sauri ta fada dakin tana goge hawaye *ZAN RAYU DAKE..FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. [5:39AM, 11/1/2017] Feedohm💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. 🌹*🌹*🌹* 🌹*🌹* 🌹* © *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Haske Writer's Association_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. ( _Haske Writer's Association_*Home of expert & perfect writers_Haske Writer's Association_* ) *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*NA_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Devoted to Ummi A'isha👌🏻**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Bestowed to Aunty Sis💕**ZAN RAYU DAKE.. 2⃣9⃣ Safeena na jingine jikin gado maryam na mata fira kadan kadan suna dariya …… Shigowar Aunty Fatee ta batar da duk wani annurin dake fuskar Safeena kallo daya ta mata ta mayar da ldonta ta lumshe tare da zame hannunta daga na maryam "Subhanallah Safeena garin ya haka ta faru kuma fisabillahi baki kirani kika fada man tsawon kwanakinnan……" cewar Aunty fatee tare da zama gefen gadon Ko kala bata ce mata ba sae ma kwantar da kanta da tayi jikin gadon tana kokarin janye kafarta dake kusa da Aunty fatee …… "Safeena ……" ta kara kiranta tare da kai hannu Ta riko hannunta Da Sauri ta bude idonta tana watsa mata harara" Kar kuskura kiyi wasan ta bani wallahi……" Kwantar da murya tayi "Safeena meye zafi duba ki fa nazo yi ,wallahi tunda naji bakya lafiya hankalina ya tashi ……" Rufe ido tayi tana fadin "Aunty Fatee kenan ki bar duk wadannan jokes din ai'nt a kid wallahi ……Irin abunda ya samu mamina shi ya sameni ,Idan har ciwon da Mamina tayi kune sila to nawa waye sila?stop decieving your self please kawae ki tashi ki bar mana gida tun kafin na maki abunda bakiyi tunani ba……" "Ki saurareni mana……" "I said get out ko bakya da kaine?ta fada a tsawance, Jiki babu kwari ta tashi,ta fita tana waigenta Maryam dake zaune gefe ta kalli Safeena tana fadin "Amma bakya kyauta……"Shiru ta mata ba tare da tace komae ba 《》《》《》 "Wae Fadila waye kike kira haka tun dazu sae uban tsoki kike mana……"cewar hajiyarsu dake zaune tana yankan kumba Tabe baki ta kuma yi tare da sake karamin tsaki tana yatsina fuska"Abdul Maleek ne wallahi tun da nake bai taba daga kirana ba sae dae na mashi text shima baya replying……" "Amma ke sakara ce……Gafara can dallah ni bani numbershi shi din banza ya wahalar man da yar jika……"ta fada tare da mika hannu "Hajiya me zakiyi da Number?ta fada da alamun mamaki "Ke dae ki bani mana ,bani nace ba sannan ki kwantar da hankalinki Abdul Maleek kamar kin samu ne shi din banza……" "ah Hajiya ki daina insulting dinshi mana……" ta fada tana turo baki ……rike baki hajiyar tayi tana mata wani irin kallo ……Spreading

Chapter 6 of 16