Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
zanje na samu tsohuwa mai dattin kallabi ........." kafin yayi yunkurin bata amsa,ta bace kamar walkiya a fusace ya dauki tools dinshi ya bar wurin ko office,bai shiga ba ya wuce gidansu ......... 銆娿€娿€娿€娿€嬨€嬨€嬨€� Tana kwance landline din dakin tayi kara ta tabbata babu mai kiranta sae Abbanta,cikin sauri ta dauka tana share hawayen dake neman zubo mata a ido "Abbah ......"ta fada a hankali kamar me shirin kuka "Safeena ki sameni garden yanzu kinji ko " "to "ta fada tare da saukowa daga saman gadon takalmin ta zura sannan ta ja bakin gyalenta ta fita......gefe ta iskeshi ya shingida yana karanta dailytrust ,gefenshi ta zauna tare da lankwashe kafafuwa tana kallonshi ,aje newspaper yayi ya sake mata murmushi kamar ko yaushe "Safeena me ke faruwa � ...ya fada wit serious tlk "Abbah a ina � "Safeena bakya jin maganata ko me yasa bakya da kyakykyawar alaka da dangin maminki safeena ,ko kadan bakya darajasu me yasa ko don kina ganin mamin taki bata rayane � Idonta ya ciko da kwallah tayi saurin damke hannun abbanta tare da kallonshi "Abbah me nayi dan ALLAH ..."ta fada da shagwababbiyar muryarta kallonta yayi na seconds sannan yace "me ya hadaki da Uncle dinki � "Sorry Abbah... " ta fada a hankali tare da goge hawayen da suka zubo mata "To meye na kuka kuma yarinyar Abbanta ……"ya fada cikin sigar lallashi ,har ga Allah idan akwae abunda ya tsana bai euce kukan diyarshi ba duk duniya babu abunda yafi kauna sama da yarinyarshi "Sorry Abbah zagan,man abbana yayi ni kuma baran iya jurewa ba ka yafe man kaji ........." FEEDOHM 馃挒 [11:03PM, 10/21/2017] Feedohm 馃挒: 馃挧馃挧 *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU 馃尮馃尮馃尮 馃尮馃尮 馃尮 漏 *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Haske Writer's Association_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. ( _Haske Writer's Association_*Home of expert & perfect writers_Haske Writer's Association_* ) *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*NA_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*FEEDOHM 馃挒_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Devoted to Ummi A'isha 馃憣馃徎*ZAN RAYU DAKE.. 1 鈨�2 鈨� DAKE 馃尮*ZAN RAYU DAKE.. "Baki man komae ba Safeena amma ki kyautata alakarki da dangin maminki ji ko ,bara na kira Abdul maleek ya zo na aikeki abukur gidan inna kinji ko idan,kinje ki kwana acan bana son damuwa ......" "to ……"ta fada a hankali tare da gyara zama Wayarshi ya fito ya kira Maleek din da kanshi sannan ya mata fada sabida ya san halinta sarae idan taje Abukur dole sae sun kwabsa da inna suke rabuwa ……kafin Maleek din ya iso yace taje ta shirya Ko minti talatin bai dauka ba ya iso da ganinshi kasan ya wahala bai fito daga motar ba kamar yarda ya saba sae ma kifa kanshi da yayi a sitiyari ……� Zagayawa tayi ta side dinshi tana kallon yanayinshi haka kawae taji ya bata tausayi first time a zamansu ……"Maleek baka lafiya ne?ta fada a hankali tare da leka kanta ta glass din motar Duk da yana jinta amma sae yayi shiru yana sauraren ko zata sake magana a yanayin da tayi……kamar ta sani bata kuma cewa komae ba sae bude kofar da tayi kamar ta sani bata kuma cewa komae ba sae bude kofar da tayi tare da knocking din sitiyarin � Kalar tausayi ya sake komawa ya dago yana langwabe kai kamar yaro karami…… dariya ta sake da ta kara kashe mashi jiki ya bude baki yana kallonta "Madam" ya fada cike da shauki duk zaman da suke bata taba mashi dariya irin haka ba Dage gira tayi tana fadin "Yes common bani guri nayi driving din don baran yarda ka jani da irin wannan yanayin ba ,koma wancan side din ka zauna……�"ta nuna mashi gurin mai zaman banza Kallonta kawae yake cike da mamakinta sannan ya tsallaka ya zauna ……bata bata kuma cewa komae ba har suka fita daga garin ganin ba kara kulashi zatayi ba ya sashi lumshe ido tare da langwabe kai yana tari Saurin kalloshi tayi tana fadin "Abdul Maleek baka lafiyane � Kamar yaro ya daga mata,kai tare da kokarin saka idanuwanshi cikin nata ,bata bari suka hada idon ba tayi saurin janye nata tana fadin "Sorry……�" 銆娿€娿€娿€娿€嬨€嬨€嬨€� Karfe hudu na marece Aunty faty ta shirya ta tafi gidansu dake layout a can ta tarad da aunty zuby yayarta da suke uwa daya suna falo suna fira da hajiyarsu mafi yawan firan ta safeena ce da Abbanta,wanda dama firar kenan idan sun hadu , kusa da zubyn ta zauna tare da jefar da jikkarta tana dafe kai "Wadannan mutanen su suke su saman ciwon kai wallahi , hajiya gaskia na gaji da wannan zaman ki san abinyi ……�" cewar Aunty faty Harara hajiyar ta sake mata tare da fadin "meye kuma ? "Meye ma bai faru ba hajiya , safeena fa aure zatayi da dan former minister abunda kuma bara ya yiyu ba……� Aunty zuby ta katseta "ke tsaya dallah wane former minister,please ki bar wannan batsar taya diyar AISHA zata auri wani dan mininster baya ga namu yayan nan zaune gida? Tabe baki Aunty fatyn tayi tace "ke ma kya gani dae……hajiya kice wani abu hajiya kice wani abu mana ga fadila nan ta girmewa safeena bare ma fauzy da rabi kuma su duka babu wanda yayi aure sae safeena?haba hajiya kar dae ace da gaske mutane suke munyi gadon bakin jinin gurinki ? Cikin fusata hajiyar tace "ke dallah rufe man baki ,gidan uwar wa kuka yo gadon bakin jinin?sae ku bari kuga idan tayi auren ya'yanku basuyi ba sannan kuzo ku man tsegumi ……� Kallon juna sukayi tare da kashewa suka dau ihu "Hajiyarmu……�" Aunty zuby ta bude jikkarta tana fadin "kinga yar uwa ga wani sabon hadi daga sabon shehi kya gwada sakawa ogan a kasan pillow kafin hajiya ta warware komae ……�" Bata bar gidan ba sae wajen isha'i ta koma , sam bama tasan safeenar bata nan ba tun da dama ba nemanta take ba sae da ta hadawa Abban safeena komae na bukata sannan tayi wanka ko sallah bata tsaya tayi ba ta shiga part dinshi tare da garin maganin da zuby tabata da zasu rabu ……hajiya kice wani abu cikin saa yana toilet yana wanka ta daga pillownshi ta bar bada kadan sannan ta mike ta bar dakin ta koma nata Jin wayarshi na ringing ya sashi fitowa daga toilet din ba tare da yayi alwala ba , bakin gadon ya zauna yana duba wayar ganin safeena ce ya sashi kiranta tare da shigidawa saman gadon yana sauraren yarda ta dage tana zuba shagwaba wae bara ta kwana gidan Inna ba saboda ta mata wulakanci ita gida zata dawo ……� Dariya sossae yake cike da so yana fadin "Haba SaFeenata ke da kakar taki , kinga dare yayi kiyi hakuri gobe da kaina zanzo na dauko ki kinji ko ……�" Cikin shagwaba tace "Abba cewa fa tayi baran kwantar mata a wannan tsohon gadon nata ba ……�" Yar dariya ya sake a hankali ……dif wayar ta dauke girgiza kai yayi ganin chajin shi ya dauke shi bai ma san baya da chaji ba sae yanzu "Safeena � FEEDOHM 馃挒 [11:03PM, 10/21/2017] Feedohm 馃挒: [3:47AM, 10/18/2017] Feedohm 馃挒: 馃挧馃挧 *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU DAKE 馃尮*ZAN RAYU DAKE.. 馃尮馃尮馃尮 馃尮馃尮 馃尮 漏 *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Haske Writer's Association_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. ( _Haske Writer's Association_*Home of expert & perfect writers_Haske Writer's Association_* ) *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*NA_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*FEEDOHM 馃挒_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Devoted to Ummi A'isha 馃憣馃徎*ZAN RAYU DAKE.. _Haske Writer's Association_*Assalamu Alaikum dan Allah masu bibiyar littafin *ZAN RAYU DAKE..BAKONMU HASKENMU*ZAN RAYU DAKE.. su gafarceni na daina posting dinshi for some reasons Amma insha Allahu nan gaba zai fito amma bata social media ba sannan kuma bata siffar novel ba ,ko ma tayayane insha Allahu zaku ganshi kuma nasan sae yafi maku dadi fiye da ta novel...._Haske Writer's Association_* 1 鈨�3 鈨� Ita kam safeena tana jin wayar ta yanke ta fara bubbuga kafafuwa kasa tare da turo baki , muryar inna ta jiyo ta shigo dakin tana fadin "Ayi dae mu gani dan uban mutun dama na fada har gida mara kunya zai iskeni anan nima zanci kaniyar mutun" Dan turo baki tayi tana hararanta ta kasan ido tare da barin dakin gaba daya Dariya inna ta sake sannan ta shinfida abun sallah tana fadin "Naga yarda mara kunya zai shigon daki ya kwana tunda nima bada kudin uban mutun na cika na sayi gidan ba" Daga waje Safeena ta bata amsa "ai da yake aikin gwamnati kike ko business da zaki iya sayan wannan gidan " Kamar jira inna take tayi wuf ta fito tana fadin "to mara kunya fada man ubanki ne ya saya man da zaki fadan magana ……� " Ganin idan ta biyewa inna rigimar ba karewa zatayi ba tunda dama tana da cikinta ya sakata langwabe kai tana lumshe idanuwa tace "Haba kakus ni fa ba haka nake nufi ba , kece tunda nazo kinki ki saurareni sae tsiya kike , ni kuma Allah ma ya sani ko lafiya banda ita hakanan nazo gaidake saboda kwana biyu ban ganki ba , amma idan zuwan nawane bakya so to kiyi hakuri gobe da safe sae in tafi ……" Dayake Inna irin mutanan nanne masu masifar son jikokinsu ya saka jikinta yayi sanyi don ta yarda da cewa safeena batta lafiyar , kusa da ita ta matsa tana fadin "Kece Safeena sam baki da mutunci muddin idan mutun ya iskeki gidanku sae ki rufe ido kiyita rashin kunya bayan a zahiri ba haka kike ba ,amma komae ya wuce kinji ko zo mu shiga ki fadan meke samunki sae a aika a siyo maki magani,sannu kinji ko ,haba shi yasa naga duk idanuwanki sun canza Allah sarki……" ta karashe maganar tare da jan hannunta suka koma dakin Sabon tara Inna ta sake mata tana lallabata kamar wani kwae ,a bisa kafarta ma tayi bacci 銆娿€娿€娿€娿€娿€嬨€嬨€嬨€嬨€� Tunda safe mahaifan JB suka samu Abba a gida , da yake yasan da zuwansu sossae yasa Aunty fatee ta shirya masu duk wani abun bukata ,sunyi farin ciki sossae da karramawar da aka masu ,nan take suka bayar da kudin neman aurensu naira dubu dari biyar ,Yayan Abba ne ya yanka masu sadaki naira dubu dari biyar , nan take suka fito suka bayar sannan aka saka masu ranar aure nan da wata biyar ……� Iya rudewa Aunty faty ta rude lokacin da Abba ke fada mata yarda sukayi da mutanen , kasa boye bakincikinta tayi tace"Million daya fa kace Alhaji ,kuma shine zaku bayar da ita kamar kun sayar……�" Dan murmushi yayi yace "Million daya shine kamar na siyar da diyata fati ? "Kwarae kam Alhaji , kaga dae diyar nan amanace kar mu bayar da ita ga mutanen da basu son darajar kowa ba ,don wallahi duk yawancin musu mugun kudinnan basu san darajar kowa ba" "Atunanina fati mutumin nan bai fini komae ba don haka bana tunanin zai wulakanta man diya tunda ya san itama ba daga gidan tsiya ta fito ba ……�" Shiru ta masa tana karkada kai a hankali……hajiya kice wani abu mintina kadan ta dauka sannan ta mike ta koma dakinta ,wayarta ta fito ta kira hajiyarsu ta fada mata komae Hajiyar ce mata tayi ta jira zata nemeta ……� 銆娿€娿€娿€娿€娿€嬨€嬨€嬨€嬨€� A Sanyaye ta kira sunanshi ganin zaya tashi motar "Maleek" Zalla soyayya ya juyo yana kallonta ba tare da ya amsa mata ba , so take ta tambayeshi amma sam ta kasa , ta rasa wanda zata fadawa damuwarta cikin yan kwanakin nan , sam Abba yaki saurarenta kullun ta tunkareshi sae dae yace ta jira shi yana aiki idan ya gama zai kirata haka zatayi ta zama amma sam bara ya nemeta ba ……idonta ya ciko da kwalla ba tare da ta sani ba…… Lumshe ido yayi lokacin da kwallar ke fitowa daga kwayar idonta wani irin sonta ke fizgarshi duk da ya san cewa ta kusa mashi nisa ……� Cikin sanyin murya yace "Madam dan Allah ki koma cikin motar muyi magana ,ba dan na isa ba ……�" juyawa tayi da sauri ganin kukan na niyar subuce mata ga mutanen dake kai da komowa a harabar makarantar bayan motar ta fada tare da kife kanta a cinya tana kuka bata san lokacin da take surututai ba tare da kiran sunan Abbanta"Abbana me na maka dan Allah?me ya saka zaka juyan baya bayan kasan kai kadai ka rageman Allah ka jibanci lamurrana ni marainiyace kafi kowa sanin halin da nake ciki …… �" *ZAN RAYU DAKE..FEEDOHM 馃挒*ZAN RAYU DAKE.. [11:03PM, 10/21/2017] Feedohm 馃挒: 馃挧馃挧 *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU 馃尮馃尮馃尮 馃尮馃尮 馃尮 漏 *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Haske Writer's Association_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. ( _Haske Writer's Association_*Home of expert & perfect writers_Haske Writer's Association_* ) *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*NA_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*FEEDOHM 馃挒_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. DAKE 馃尮*ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Devoted to Ummi A'isha 馃憣馃徎*ZAN RAYU DAKE.. 1�4� Cikin sanyin jiki shima ya shiga motar , kifa kanshi yayi a sitiyarin yana kallon yarda ta matse kanta da cinyoyinta ,wani irin sonta ke fizgarshi a sanyaye yace "Madam dan girman Allah ki bar kukan ki fada man me ke faruwa�" Girgiza kai take a hankali ta kasa magana ,ina ma zata iya da ta fadawa maleek cewa Abbanta ne ke neman juya mata baya ,amma sam barata iya jin zata yarda da wani mutun ba a rayuwarta har ta iya fada mashi matsalarta � "Please Madam dan Allah kiyu shiru wallahi bana jurar kukan mace bare ma naki madam ko bakya lafiyane� Tambayar duniyar nan ya mata taki kulashi sae ma wani sabon kuka da take …… hankali ya tashi motar ya fita daga makarantar direct dutsin safe ya nufa da ita ,bakin gidan Granny yayi parking a iya zaman da yayi da ita yasan nan kawae take zuwa ta samu farinciki ……� Cikin sanyin jiki ya fito ya bude mata motar sae a lokacin ta dago da kanta ta ga inda suke da sauri ta fito ta shige gidan ba tare da tace dashi komae ba bayanta ya bi da kallo tare da lumshe ido Tana shiga gidan ta durkushe a tsakiyar falon tana kuka , Granny dake zaune bisa doguwar kujera ta mike tare da karasowa gurinta ……� "Menene kuma Hussaina ,fada man me ke faruwa �" Cikin kuka tace "kaka shin Abbana bai san shi kadae gareni ba � ko ya manta cewa mamina batta raye ?aka me yasa yake neman juya man baya �" "Me ya maki Hussaina�" "Granny Abbana ya daina sona�"ta fada tana shashshekar kuka "Karyane Hussaina ko ma mene Allah ya fisu , kin fi kowa sanin kece rayuwar Abbanki me ya saka zaki damu ,bana son wannan kukan kinji ko ,tare da Abdul maleek kika zo �" Daga mata kai tayi a hankali tana sharan kwallah "Jeki kira manshi " Ahankali ta mike ta fita ganin ba motar ya sakata dawowa ta fadawa kakan ya tafi …… 銆娿€娿€娿€娿€娿€嬨€嬨€嬨€嬨€� Alhaji khaleed kam tun da ya zauna office ya,kasa tabuka komai ……cikin kwana kinnan ya rasa meke damunshi sam baya kaunar Safeena ta rabeshi amma idan bata kusa dashi sae yaji ita kadae yake bukatar gani ……har ga Allah ya san duk duniyar nan babu abunda yake kauna sama da diyarshi amma ya rasa meke damuwa …… Wasu yan siraran hawaye ke bin kumatunshi yayin da zuciyarshi ke bugawa da karfi,tsoro da fargabar rasa diyarshi yake ,yana sane da yanayin da take shiga yan kwanakinnan……cikin sauri ya janyo wayarshi tare da kiran Abdul maleek don ya tabbata ko wane yanayi take Abdul maleek zai fi kowa sani Ringing daya a na biyu ya dauka tare da barin office dinsu ya fita harabar court din , kamar yana ganinshi ya russuna yana gaidashi Cikin rawar murya yace "Maleek ina safeena tana lafiya dae ko?" Karo na farko daya farawa uban gidanshi karya yace"Alhaji tana lafiya lau yanzu na kaita makaranta na dawo " "Bata cikin damuwa ka tabbata Abdul maleek ……? "Alhaji tana cikin kawayenta ma suna karatu kuma banga alamun damuwa a tattare da ita ba ,Alhaji lafiya ? "Ba komae Abdul maleek dama kawae ina so naji yarda take ne ,Abdul Maleek ba kai safeena unguwa kadae na saka ba harda amanarta na baka don Allah ka kular man da safeena ……�" 《》�《》 Aunty faty kam daga gidan hajiyarsu gidan Aunty zuby ta nufa ,a falo ta iske ta zaune ita da mijinta ,janta tayi daki sannan ta fito da wasu magunguna ta mika mata a hannu � "Kina jina ko ki tabbatar kin saka mashi a ruwan wankanshi na safe sannan ki zuba mashi a abincin da zai fara ci a safiyar gobe……hajiya kice wani abu shi da wannan shegiyar diyar sae daga hannu ……�" Dariya ta sake tana fadin "Sae Aunty to ina na safeenar kin san dae sauran wata biyu bikinta ,kuma ni wallahi bana son wannan shegen auren don bara ta yiyu diyar Aisha tayi aure ba ta bar yayanmu zaune ……�" "Ke kau me kika ci na baka na zubahajiya kice wani abu na mashi maganar yace sae bikin zaa sakar mata jini kinga kau dole ango ya kora masu yar bazawara ba budurwa ba ……hajiya kice wani abu idan akace a hana auren tana budurwa samun wanda ya fi wancan tunda dan ubansu kamar a jininsu yake *ZAN RAYU DAKE..FEEDOHM 馃挒*ZAN RAYU DAKE.. [5:06PM, 10/20/2017] Feedohm💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU 🌹*🌹*🌹* 🌹*🌹* 🌹* © *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Haske Writer's Association_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. ( _Haske Writer's Association_*Home of expert & perfect writers_Haske Writer's Association_* ) DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. ana saura sati su a matsayin to kinga zata iya ……�" *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*NA_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Devoted to Ummi A'isha👌🏻**ZAN RAYU DAKE.. 1⃣5⃣ "Amma Aunty zuby kina tunanin JB din zai rabu da ita ……yana fa sonta kada ya nema mata magani yaki sakinta ……"ta fada a sanyaye Harara ta sake mata"Baki yarda da abunda na fada maki ba kenan ……shi banzane da zai zauna da mace tana bleeding ,kiyi amfani da kai mana ,tunda uwarta ta yi ta barmu itama babu abunda zata iya , ke dae kawae ki zuba man ido ……" Mikewa Aunry fatin tayi ta sabi jikkarta tana fadin "Bara na wuce aunty zuby komae kenan na kiraki ,yauwa hajiya tace ki aika Fadila ta karbo maki sakonki ……" Kusan tare motarta data Safeena ta shiga harabar gidan Abdulmaleek dinne ya fara parking sannan Aunty fatin tayi a tare suka fito da safeenar ,da Sauri aunty fati din ta matso tana fadin "Feena ina kika tsaya tun dazu nake kiran wayarki naji ko kin dawo gida ……" Harara ta sake mata kasa kasa tace "ki godewa Allah kin samu da baki samu damar fita ba……" da baki sameni ba, don da Kwantar da murya tayi tana fadin "haba feena me yasa kike man haka yanzu neman naki ma a waya laifine ……" "kya ji dashi Aunty fatee ,Maleek gobe da safe kaje dutsin safe granny na nemanka ……"ta karashe maganar tare da yin gaba abunta Aunty Fatee ta juyo tana kallon Maleek daya zuba masu ido yana kallon duk abunda suka ,lallae sae yau ya tabbatar da safeena bawae shi kadae bane batta so aa duk wanda ke rabe da ita ne takewa haka ,amma tana da kyakykyawar dangantaka da mutanen da bata da wata alaka dasu …… "Abdul maleek kaga safeena ko, yanzu dan Allah abunda take man ya dace ……? Dan girgiza kai yayi a hankali yana kallonta ,cigaba tayi da fadin "Wallahi Maleek sam safeena bata da halin kirki ,yarinyar muguwace bata da tausayi ,kai kanka jiba yarda duk ka lalace ai lokacin da kazo ba haka kake ba ,ni……" Katseta yayi ta hanyar cewa "hajiya sae Allah ya kaimu ……"bai jira abunda zata fada ba ya bar gurin , ko motar bai tsaya dauka ba …… Daga nan gidan granny ya nufa da yake sun riga sun saba shiga kawae yayi ya isketa a falo tana gyangyadi …… "Yar tsohuwa kuma bacci ake yi " ya fada cike da xolaya "Abdul maleeku ne ,yaushe ka shigo ……" "Yanzu wallahi madam tace kina nemana ……" "Eh aikenka nake son nayi a daura gobe idan Allah ya kaimu ……" "Allah ya kaimu goben ……"so yake ya mata zancen safeena amma yana kunya daurewa yayi ya dukar da kai yana fadin "Hajiya ni ko dan Allah ko kin san meke damun Madam ne naga tana cikin damuwa……" A jiyar zuciya ta sake sannan tace "Abdulmaleeku laifina ne ki bibiyar jikata ……" "Ya laifinki kuma hajiya ……? "Karka damu kaji ko ,na yarda da kai sissae Abdul maleeku idan Allah ya kaimu gobe zan fada maka wacece safeena ,tana rayuwane kewaye da makiyanta ……" Wata yar takarda ta fito dauke da address da number waya a kasan number an rubuta Malam ibrahim daurama ta mika mashi tana fadin "Ga address da number wayar mutumin da zaka nema , zaka karbo man sakone daga gareshi idan kaje ka kira numberta zamuyi magana dashi ……" Karba yayi ya mike yana mata bankwana Ko da yaje gidan bai iske nana a tsakar gida ba ,da yake yanzu tana samun saukin Inna tunda yana kawo kudi da kayan abinci ……Dakin inna ya leka ya gaida ita lokacin har nanar tayi bacci ……kudin cefanen gobe ya bata sannan ya tafi inda yake kwana don so yace tunda safe ya wuce aiken granny …… 《《《《《》》》》》 Baisha wahala gurin gane malamin ba ,da yake sanannene ,bayan sun gaisa ya masa bayanin daga inda yake cikin faraa ya amsheshi sannan ya saka aka kawo mashi fura mai sanyi …… ,shi ganshi ya gamsu da malamin domin yana cike da kamala da natsuwa sannan a falon da aka saukeshi babu komae face litattafan addini da,kamshin miskin dake tashi ……Ga tsantsae kama da yake da granny kamar an tsaga kara ,ko baa fada mashi ba ya san cewa dan uwanta ne,…… Waya ya fito ya kira granny suka gaisa cike da barkwanci yana tambayarta ya safeena,…… Baiji me take cewa ba sae dae yaji yace "In Allah ya yarda babu abunda zai cutar da safeena don Allah ba Azzalumin bawansa bane ,wancan ma da sukayi Allah ya ara masu rana ne kafin ya karbi abunsa ……" Sun dan,jima suna maganganunsu kafin ya kashe wayar yana kallon fuskar Abdul Maleek din yace "Kanaji muna ta surutu ko ……" "aa bakomae wallahi "ya fada fuskarshi dauke da murmushi …… Dan murmushi malamin yayi sannan ya mike ya shiga wani daki ya,fito rike da wani dan karamin littafi na larabci sae wata karamar kwalba kamar almiski ya mika mashi yace ya kai mata …… *ZAN RAYU DAKE..FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. [9:37PM, 10/20/2017] Feedohm💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE..ZAN RAYU DAKE🌹**ZAN RAYU DAKE.. 🌹*🌹*🌹* 🌹*🌹* 🌹* © *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*Haske Writer's Association_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. ( _Haske Writer's Association_*Home of expert & perfect writers_Haske Writer's Association_* ) *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*NA_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*FEEDOHM💞: 💧💧 *ZAN RAYU DAKE🌹*_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE..Devoted to Ummi A'isha👌🏻**ZAN RAYU DAKE.. *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*YA ILAHI 🏻*♀ jama'a ku duba da kyau ba novel bane kawae happy birthday nawa billy ladan amma ba wae yana nufin zan cigaba da typing dinshi ba ……wasu ma wae na badu complete document aa ba document ba decomo😂😂_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. 1⃣6⃣ Wajen Karfe 11 ya dawo katsina sae da yaje office yayi signing sannan ya wuce gidansu safeena don yana bukatar kara ganinta kafin ya wuce gidan granny …… Garden ya hangota zaune ita da wani mutumi duk da sun juya baya hakan bai hanashi gane JB bane ……wani abu ya tokare mashi kirji bai karasa ba ya juya da sauri zai fita karo yayi da mutun ya dago yana fadin "Sorry……" "Sorry ……"itama ta fada cikin saurin maganarta tare da dukawa ta dauko mashi,key dinshi da ya fadi …… "Very Sorry ban lura da kai bane kaji ……" ta fada tana kallon fuskarshi Gaba yayi abunshi yana kallon kasa ba tare da ya amsa ba ……ita kam binshi tayi da kallo har ya bar harabar gidan sannan ta sake ajiyar zuciya, ta shige gidan da sauri tana kwala kira "Aunty Fatee……! Aunty fateen ta fito daga part din Abbah tana fadin "wannan kira haka fadila kamar mai shirin cika gidan ……" "Aunty nayi gamo wallahi duk na rude ……" "To Allah ya kyauta ,tukun ma me ya rudaki haka ……" "Wani gentle na gani ya fita daga gidan nan Wayeshi Aunty ……" "Mtsww ke mahaukaciya ce wallahi shine zaki shigo kina kwala man kira haka , to ba wanda ya fita anan sae dae idan da aljan kikayi gamon……" Itama karamin tsakin taja sannan ta zube saman kujera tana kallon labulen dake yayewa a hankali ……ganin safeena ce ya sakata sake jan wani karamin tsakin tana daukar remote…… Kujeran dake facing din fadilan ta zauna ba tare da ta kulata ba ,gyarawa tayi ta kwanta sossae tana danna wayarta …… "Ke bakya iyawa mutane magana dan ubanki ……"fadilan ta fada tana kallonta, "Mtsww ni wallahi na rasa me ke damun hajiyarku ,tana ganin mutane na hauka bara ta iya kaisu asibiti ba ,salon su fara dukan mutane kuma a rasa yarda zaayi dasu ……" ta fada hankalinta na ga wayarta Aharzuke fadilan tace "ke da ubanwa kike ……" Kallonta tayi na yan mintina sannan ta mike ta bar gurin …… 《《《《》》》》 Abdul maleek kam jiki a sanyaye ya karasa gidan granny sakonta ya bata sannan ya zauna ……ba tare da bata lokaci ba ta fara bashi labarin …… *ZAN RAYU DAKE.._Haske Writer's Association_*TUSHIYAR LABARIN……_Haske Writer's Association_**ZAN RAYU DAKE.. Abdul maleeku kamar yarda ka sani sunana Hajiya rabi mijina kuma Alhaji shehu tun lokacin da bai da komae na aureshi har Allah ya bude mashi kasuwa arzikinshi ya fara bunkasa ……ina da kawata aminiya hajiya shafa'u mahaifiyar su Fatee auntynsu safeena kenan ……shafa'u aminiyatace sossae duk wani sirri nawa dana mijina ta sanshi babban kuskuren dayi kenan na sanin sirrin mijina da tayi ,a lokacin bata da gurin zuwa sae gidana ,na mayar da ita kamar yar'uwata na saki jiki da ita yarda baka tunani ……mijina ya san amintar dake tsakaninmu da ita don Haka shima ya sake da

Chapter 3 of 16