Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yau, wato keda Sarkin fada kundade kuna aikata alfasha, saboda kinga Sarki beda lafiya, kai, wama yasan tun lokacin da kuke tare? Hmmmm dama nafada, shiyasa duk abinda yafaru daku wlh bazanji tausayinku ba, kema kijira sammaci anjima ko gobe, dan tunda Waziri yakamaku da kanshi, kema kinsan hukuncin kisane akanki. Tir da ke, kina matar Sarki kinabin maza, mazan ma wai Sarkin Fadan Mijinki. Kodayake ba laifinki bane, dama shi talaka kome akayi dashi, seya baka kunya, yanzu tayaya wanda yafito daga jinin sarauta ze aikata irin abinda kikayi? To wlh bari infada maku dake dasu gaba daya, daga yau babu ni babu ku, kuma koda kunbude baki kunfadi abinda nasa akayima Rayhana, babu wanda zeyarda daku, dan bakuda sheda, kuma ni daga gidan sarauta nake, zan iya amfani da karfin mulkina inkwaci kaina, dan kunsan atsari na sarauta ba,a yanke hukunci dole seda sheda bayyanan na, ku kam bakuda wata shedar dazata nuna akwai sa hannuna aciki. Kitashi kibani guri tunkafin azo aganki agurina. Cikin kuka Medaki tace dan Allah kada kinmani haka, nabaki duka yarda, banda kowa aduniyar nan kece silar jefani cikin wannan harka dan Allah kada kice zaki juya mun baya, kinsani duk wani abu da muka aikata shawararki mukebi, saboda kece babba. Hannu tadaga mata tamike tsaye tace nace kitashi kibani guri kada inkara ganin kafarki agidana. Ni nabi shawarar kiyi zina da kaskantaccen talaka kuma yaron mijinki? Kafin asirinku yatonu kintaba fadamun halin dakuke ciki? Dan haka wlh kinji narantse maki baruwana acikin harkarku, fita nace. Tashi Medaki tayi tana kuka tafita waje. Wata irin dariya Gimbiya Zakiyya tasaka tace, uhmm dani kuke magana, anfada maku sarauta haukace? Kaima sarkin fada nasan kana tunanin katona asirina. Ni kuma zan nuna maka bakada wayau,duk duniyar nan babu wanda zeyarda da kai dan kafada masu munyi harka tare, domin kuwa babu wanda yasan munyi daga ni sekai, kuma agidan sarauta ba,a karbar shedar mutum daya, kuma shedar ma tabaki. Dariya tasa tashige daki. Saurin tashi Sarki Qaseem yayi yana kallon Gimbiya Suhailat, bayan tagama bashi labarin abinda yafaru. Kai yafara girgizawa ta kalleshi tace dan Allah kayi hakuri, wlh banyi haka dan in cutar dashi ba, kuma ni bansan Son dayake mata ya kai haka ba, kuma gani nayi nida kai munzaba mashi wadda ze aura shiyasa nayi haka. Murmushi Sarki yayi yace kinzaba mashi de, kuma ita Ayman din ai tasamu wanda take so, to koma bata samu ba, yarinyar dayakeso ita zanbashi sede ita Ayman tazo ta 2, domin kuwa kinso ki tabka babban kuskure, ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba, yarinyar da kika gansu tare da Areef jinina ce, kuma shima jininshi ce, bari inje asibitin inga halin dasuke ciki. Kuma kisani tunda har Ayman tasamu wanda takeso to bazata auri Areef ba, da ace tana sonshi, to zanbashi shawara ya aureta, amma tunda haka tafaru, kowa ze auri zabinshi. Kuma kisamu kalaman dazaki bama Jadiya Safeeya hakuri dasu, dan kinci mata mutunci, matar da ta sadaukar da jin dadinta domin takaremu. Matar da tabaro kowa nata, badan tana cikin talauci ba, a,a kawai dan tazauna damu da gaskiya. Juyawa yayi yanufi kofa zefita, da gudu tarugo tarikeshi tabaya tana kuka tace, dan Allah hubby kayi hkr kada kamun irin wannan horon, naji nayarda da duk abinda kace, kuma nahakura Yarima ya auri koma wacece amma dan Allah kafitar dani duhu, kuma kada kayi fushi dani kasan bamu saba haka ba. Murmushin jindadi yayi, sede bejuyo ba, yace ki kwantar da hankalinki, danki ze auri irin yarinyar da mukeso, yar gidan sarauta, albishir daya zan maki, wannan yarinyar da kika gani ba kowa bace se diyar Yaya da Fulani. Kuma wani abun farin cikin yanzu haka Fulani tana cikin gidan nan, sauran bayani sena dawo zakiji, yana fadin haka yayi waje. Wani irin yanayi tashiga, gaba daya tarasa mezatayi, ga kunyar abinda tayi yadameta, musamman idan ta tuno kalaman data fadama jakadiya, komawa tayi daki tana tunani. Cikin sa,a da kwarewa tare da temakon Allah beauty ta farfado, numfashinta ya dedeta, sede haryanzu bata bude ido ba, kuma bugun zuciyarta be dedeta ba. Likita yace sukaita dakin hutu, nan da wani lokaci zata dawo dede akwai abinda ya tsoratata shiyasa tashiga wannan yanayin. Adede lokacin Sarki da Waziri suka iso asibitin,kai tsaye office din likita suka wuce, bayan sun gaisa yayi masu bayanin halin da ake ciki. Sarki yace amma yaya jikin yarinyar? Likita yace insha Allahu babu wata damuwa, zata dawo dede. Amma Yarima jikinshi dasauki. Godiya suka mashi yasa aka nuna masu dakin Areef da beauty. Seda Sarki yafara shiga gurin beauty, kwance yasameta kamar matatta, Jakadiya Safeeya tana gefenta se kuka takeyi, sallamarsu ce tasa tayi saurin goge idonta, ta tashi tana mika gaisuwa, da kyar ya amsa, hankalinshi yana kan beauty, sak kamarta da Fulani da Areef yake gani afuskarta, wasu hawayen farin ciki ne, suka zubo mashi. Kusa da ita ya matsa, fuskarta ya shafa ya kalli Waziri yace tabbas ita ce, ko ba,a fadamun ba nasan wannan jinin Yaya ce, Allah sarki, Allah maji rokon bayinsa, insha Allahu ayau Yaya zesamu babban albishir, ayanzu base gobe ba. Kallon Jakadiya yayi yace kifadamun Ina Fulani take, inje da kaina inkaima Yaya ita?. Se alokacin Jakadiya ta tuna sunbarta agida, damma tasan barci takeyi, sede tana duba agogo taga lokacin tashinta yakusa, gashi basu kulle gidan ba, cike da tashin hankali ta kalli Sarki tace Rankai dade tana gida kuma yanzu zuwa wani lokaci zata iya farkawa, gashi bankulle gidan ba, ina tsoron tafito, koza,a sa amaidani gida kada tafito?. Waziri yace babu damuwa, muje muga jikin Areef semuwuce tare. Sarki yace a,a tunda ance jikin nashi dasauki kawai. Muwuce, Jakadiya tace to bari inma Ayman magana seta dawo nan tazauna kada tafarka. Waziri yace rankaidade muje gaba daya muga jikinshi semu wuce. Areef da Haisam suna cikin tsara yanda zasu hada plan, Ayman tana gefe duk tashiga damuwa se kallon Haisam takeyi tana tunanin idan aka rabasu bazata iya. Hakura dashi ba. Turo kofar da akayi ne. Tasa su saurin kallon kofa, Areef suna hada ido da sarki yayi saurin komawa ya kwanta tare da rufe ido. Dariya yakusa bama Sarki, bayan sun shigo Sarki ya matsa kusa dashi yace lallai yarona kai ragone tunda har zaka iya kwanciya asibiti saboda mace, to danazo ince maka na amince da zabinka amma tunda naga baka warke ba, nafasa, ai dasauri yamike yariko hannun Sarki yana fadin wlh nawarke koyanzu ma asallameni. Gaba daya dakin seda suka sa dariya, hada Ayman me kuka. Sarki yace ka kwantar da hankalinka babu wanda ze hanaka auren zabinka, kuma jininka, bari muje gida mudawo, kallon Haisam yayi yace ka kula dasu, ke kuma me kukan soyayya sekiyi shiru tunda zaki samu abinda kikeso, kitashi kije gurin Diyata kizauna zamu dawo yanzun nan. Juyawa yayi yafita suma suka bisu abaya. Cike da Mamaki Areef ya kalli Haisam yace Jinina, kuma diyar Abba? Tome yake nufi? Kafada Haisam yadaga alamun shima besani ba, yace mujira sudawo maji daga garesu. Jakadiya Karima se kuka take tana fadin tsakanina da Gimbiya Zakiyya Allah ya isa, muguwar mata tasamu cikin bala,i kuma gashi yanzu mune akulle, bamuda wata sheda dazata nunama mutane tanada hannnu acikin abinda muka aikata. Kaicona ni Karima, ban rike amanar da mutanan nan suka bani ba, naci amanarsu, nima kuwa Allah baze barni ba. Yanzu shikenan haka za,a yanke mana hukunci muna kallo abar Gimbiya?. Wata irin dariya Sarkin fada yayi yace kidena bata hawayenki abanza, waye yace maki itama zata kubuta? Aini bana barin baya da kura, inde zanyi aiki to dole se nasamu madafa nake farashi, ko anfada maki nima irin kwakwalwar jinin sarauta nakeda ita wadda bata da seti? Kawai malama kizuba ido kisha kallo gobe. Suna zuwa gidan afalo sukaci karo da ita tafito se raba idanu takeyi. Cak Sarki ya tsaya yazuba mata ido, tabbas ita ce, sede tarame, hannu yadaga sama yanama Allah godiya, Waziri yace Jakadiya kamota muwuce. Hannunta takama suka nufi waje. Ur's. NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 AMAKABARTA AKA HAIFENI 🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 95⚜100 Da sallama suka shiga falon Sarki Hasheem, yana zaune abisa kekenshi yana sana,ar tashi wato tunanin Fulaninshi, matsawa kusa dashi Sarki Qaseem yayi. Kafadarshi ya dafa ahankali yadago yana kallonshi, wasu siraran hawaye suka fito daga idanunsu su duka biyun, alamu Sarki Hasheem yayi mashi da lafiya? Murmushi yayi mashi yakama kekenshi yafara turawa. Seda yakawoshi kusa da su Waziri sannan ya sake shi, shide kallonsu kawai yakeyi, Jakadiya Safeeya takamo hannun Fulani wadda take boye abayanta, tafito, adede lokacin dasuka hada ido da Sarki Hasheem Fulani taji kanta yayi wani irin sarawa. Shi kam Sarki Hasheem besan lokacin daya mike tsaye ba bakinshi yana motsi yana nuna Fulani da hannu ba, itakam nan take ta kwala wani irin ihu tafadi kasa, shima jikinshi ne, yafara rawa yazube kasa idanunshi suna fitar da kwallah. Dasauri suka isa gurinshi, Jakadiya Safeeya kam gurin Fulani ta nufa, sede tana tabata taji babu alamun numfashi atare da ita, Waziri yakama Sarki Hasheem yadora kan cinyarshi jikin sarki se rawa yakeyi yana kara nuna Fulani da yatsa, da karfi yace Fulani. Jakadiya Safeeya takalli su Waziri tana kuka tace bata numfashi fa. Sarki Qaseem wanda duk yagama rudewa, yama rasa ina zeje, ya kalli Waziri yace yazamuyi ne? Waziri yace kawai muwuce dasu duka asibiti ina ganin zefi sauki. Sarki Qaseem yace ma Jakadiya taje takira Suhailat tazo sutafi tare, anan Waziri yakira wasu fadawa suka kama Sarki aka kaishi mota, Sarki Qaseem kuwa da kanshi yadauki Fulani ya kaita mota. Waziri yatara manyan fadawa kusan guda 20 yace nabaku umarnin bayan fitarmu kada wani ko wata yakara fita koya shigo masarautar nan, harse mundawo idan nabada umarni. Jakadiya Safeeya kam tana zuwa part din Gimbiya Suhailat, jikinta yafara rawa, dan batasan dawane ido zata kalleta ba, ganin zata bata masu lokaci yasa kawai tashiga, alokacin Gimbiya tana zaune falo tabuga tagumi. Saurin tashi tayi tana kallon Jakadiya cike da fargaba tace. Dan Allah kada kicemun narasa Yarima dan Allah, sunkuyar da kai tayi tace baki rasa shiba, sede memartaba ne yace infada maki kifito mutafi asibiti. Ai dasauri taje tadauko hijabinta tafito suka nufi mota, tana zuwa suka shiga wata mota ita da Jakadiya, su kuma suka shiga dayar Wazirri jasu zuwa asibiti. Azaune, Areef yake bisa gadon beauty ya rike hannunta idanunshi suna fitar da hawaye, kara kallonta yayi yace dan Allah beauty kitashi haka nan, wlh zan iya samun matsala idan har baki farka ba. Haisam ne ya matso kusa dashi yadafa shi, yace kayi hakuri abokina zata samu lafiya, bagashi kana kallo numfashinta yna tafiya dede ba. Addu,a zaka yimata zata tashi. Suna zuwa aka nufi emergency dasu, sede shi Sarki wani daki aka kaishi tunda dama likitan yasan cesa dinshi, akan Fulani likitoci suka taru suna bata temakon gaggawa. Gimbiya Suhailat da tambayoyi suka cika cikinta, gashi tana son ta tambayi Jakadiya Safeeya amma kunya ta hanata, ganin haka yasa Jakadiya tace Gimbiya muje kiga jikin Yariman mana, kamar jira takeyi ta tashi cike da kunya tace muje de infara ganin jikin surikar tawa ko?. Bakaramin dadi Jakadiya taji ba, dajin furucin Gimbiya, tace to muje, Gimbiya tace dan Allah kiyi hakuri da abinda namaki, wlh idona ne yarufe, har na furta maki wadan nan maganganun, amma kiyafe mun, kuma Hubby yayi mun bayanin komai nagane. Tabbas soyayya baruwanta dawani mulki ko sarauta, kudi ko talauci, wlh nayarda da zabin Yarima dari bisa dari, ada kam nayi kuskuren cewa dole dan sarauta seya auri jinin sarauta, segashi tun ba aje ko inaba Allah ya nunamun ishara, kuma nayarda da abinda nagani. Murmushi Jakadiya tayi tace haba ai babu komai, nice yakamata innemi yafiyarki, dan na rufe maki abubuwa da yawa wanda ba laifina bane, amma muje kiga jikin nasu, daga baya zakiji komai. Hannun beauty dake cikin na Areef ne yafara motsi, saurin kallonta yayi yana fadin Haisam wlh beauty motsi takeyi, kara matsawa kusa da ita sukayi, Ayman tace aiko Yaya ga idonta nan yana juyawa, Areef yace beauty bude idonki nine akusa dake, babu wanda ze rabamu, dan Allah kitashi Abba ma yana dubaki kuma shima ya amince. Kallon Ayman yayi hawaye suna zuba a idonshi yace dan Allah kuce ta tashi. Adede lokacin da su Gimbiya suka turo dakin babu wanda ya kula dasu dan hankalinsu yana gurin beauty, tsaye Gimbiya tayi tana kallonsu, gaba daya tausayinsu yakamata, gani takeyi duk itace tasasu awannan halin, matsawa Jakadiya tayi kusa dasu. Adede lokacin beauty tabude idonta, bata sauke su akan kowa ba se akan Gimbiya Suhailat, ai kawai gani saukai ta tashi cikin tsorata ta kwala kara daga karshe tace Mama............ gaba daya dakin seda suka firgita dajin abinda beauty tayi, saurin shigewa jikin Areef tayi jikinta yana rawa, kara rungumeta yayi yana shafa bayanta. Se alokacin ya juya yaga Momynshi ce ashe beauty tagani, saurin daure fuska yayi yace Momy dan Allah kifita, kina ganin yanda beauty ta tsorata daga ganinki, tunda beauty take bata taba magana ba, amma ayau ta dalilin tsoranki datakeyi gashi magana tafito abakinta. Dan Allah kifita tunkafin takara ganinki tarasa ranta, wlh nima mutuwa zanyi. Cike da tashin hankali Gimbiya tajuya tayi hanyar waje tana kuka, Jakadiya tayi saurin kamota tana fadin kada kifita kidawo zanyi mata magana, kai kuma Yarima ka nutsu kasan dawa kake magana. Jawota tayi suka matso kusa da gadon beauty wadda take kwance ajikin Areef, ahnkl Jakadiya ta dafa kafadarta tace tashi kiji wani abu Yar Baba kinsan de bazan cutar dake ba ko? To idan har kinyarda da hakan inaso kitashi kuma kada kiji tsoron komai, Gimbiya tazo dan tadubaki kuma tafada maku tayarda zakuyi aure keda Yarima. Ai dajin haka beauty ta tashi sede bata rabu da jikin Areef ba, shikam murmushi kawai yakeyi, yana kallon Momynshi. Kusa da beauty Gimbiya ta matso takama hannunta, tace diyata kiyi hakuri kinji wasa nakeyi maku, babu wanda ze rabaku, nima inasonki, jawota tayi ai kamar jira takeyi tashige jikin Gimbiya, ai gabavdaya dakin aka sa dariya. Da wani irin ihu Fulani ta farka tana fadin wayyo nashiga 3 zasu kasheni, haka tayi ta ihu, ganin taki natsuwa likitocin suka leka suka kirawo su waziri, addu,a Waziri yayi ta tofa mata shida Sarki Qaseem, cikin lokaci kankani ta nutsu, sede gaba daya afirgice take. Wani likita yace da alama tunaninta yadawo, sede agskiya atsorace take, kila mutanen dasukayi mata sanadiyar shigarta wannan halin sun tsoratata sosai, dan haka shawarar dazan baku idan har akwai malami, to ku kaita yayi mata addu,a insha Allahu zata dawo dede. Waziri yace mun gode sosai, amma kana ganin za,a iya sallamarta ayau? Likita yace kwarai ma kuwa, ai babu sauran wani abu dayake damunta, dan ta dade tana shan magani, duk da ba mune muka bata ba, amma mungane ana bata magunguna masu kyau. Sarki yace mungode bari muduba jikin Yaya. Shima Sarki Hasheem jikinshi yayi sauki, dan soyake abarshi yaje yadubo Fulaninshi, amma likitan yahana, turo kofar dakin sukayi tare da sallama, aibyana ganinsu Sarki yace ina Fulani ya jikinta? Gaba daya seda sukayi mamakin maganar data fito daga bakin Sarki, dan yau shekaru 18 da watanni beyi magana ba. Da sauri Srki Qaseem yaje gurinshi yana murmushi ya rungumeshi yana fadin Yaya wlh itama ta warke ayau ma zamu koma gida. Cike da fara,a Sarki Hasheem yace da gaske? Waziri yace sosai ma, runtse ido yayi wasu hawaye suka zubo mashi yace Allah nagode maka daka dawomun da Fulanita, ya Allah katona asirin duk wanda yayi ma Fulani hakan ni kuma nayi alkawarin wlh bazan barshi ba. Likita yayi gayran murya yace Alhmdull, dama nace maku yawancin irin wannan matsalar idan har mutum yahadu da ita ta dalilin rasa wani abunda yakeso, to aduk lokacin daya ga wannan abun alokacin da beyi tsammanin ganinshi ba, to inhar Allah yaso ze iya samun sauki. To hakane yafaru da memartaba, jikinshi yasamu lfiya, nan da wani lokaci zefara tafiya kamar kowa, amma kada yayi garaje, gurin fara tafiya, yanzu haka zamu bashi sanda wadda zata temaka mashi gurin tafiya. Kuma zaku iya tafiya ayau, sede dole seyasha magungunan dazamu bashi, suna zasu temaka mashi jikinshi yayai kwari. Sarki Qaseem yace yanzu kam tunda farin cikinshi tadawo ai ba magani ba, komai zesha. Dariya suka sa gaba daya, Sarki Hasheem yace yanzu de ku kaini inga Matata ko kuma intafi da rarrafe, dariya sukayi likita yace a,a ga kujera nan kuturashi yaga farin cikinshi. Kwance take idanunta akulle, amma ba bacci takeyi ba, tanaso tayi tunanin,sede data fara setaji kanta yana sarawa, da sallama suka shigo, lokaci guda ta bude idonta, bata sauke su ako ina ba, se akan mijinta, jan jiki tayi ta tashi zaune, fuskarta dauke da murmushi, turashi sukayi har kusa da gadonta, sannan Waziri yakamo hannun Sarki Qaseem sukayi waje. Hannunshi yasa yakamo nata, fuskarshi dauke da murmushi, saukowa tayi daga bisa gadon ta durkusa kusa dashi ta shige jikinshi tana kuka, kara rungumeta yayi yana shafa bayanta. Dakin beauty suka nufa, azaune suka samesu se fira sukeyi, suna dariya, beauty kuwa tana jiin Gimbiya, se dariya takeyi, sede haryanzu tun maganar datayi tafarko bata kara cewa komai ba, Areef ma kasa matsawa yayi yana manne da ita, wani irin farin cike ne yaratsa zuciyar Sarki Qaseem ganin yanda yasamesu. Sarki yace waini ina Areef marar lafiya ne, munje dakinshi mabu ganshi ba? Dariya suka saka, Areef yace Abba ai nawarke, Gimbiya tace ba dole ya warke ba, tunda yasamu abinda yakeso, dariya sukayi. Waziri yace ai seku tashi mufara shirin tafiya gida tunda kun warke dare yayi sosai. Sarki yace gaskiya kam, yaude asibitin tazama ta masoya. Haka likita yabasu sallama tare da magungunan Sarki Hasheem dana Fulani, suka kama hanya zuwa gida, sede haryanzu Sarki Hasheem bega beauty ba, dan seda suka fara shiga mota sannan suma suka fito. Lokacin dasuka isa gida kuma dare yayi sosai, hakan yasa Gimbiya taja Ayman da beauty tace ma Jakadiya kema kitaho mukwana anan kisan de Yaya baze baki Matarshi ku kwana tare ba. Dariya tayi tace hakane, muje kawai. Kallon su Areef tayi tace Haisam kaima kafada ma su hajiya anan zaka kwana gurin budurwarka kada suji shiru. Rufe fuska yayi yana dariya yace ai nafada masu, tace yauwa maganata tayi dede kenan? Adede lokacin da motar su Waziri da su Sarki tashigo harabar gidan, suna haskawa jikin wata bishiya suka haske fuskar Medaki, ai dasauri takara labewa, domin ta dade agurin jiran dama kawai takeyi tasamu tagudu, hannunta rike da dan kullinta, sede babu wanda yaganta daga Sarki Qaseem , se Waziri wanda dama shine yake jan motar, Sarki da Fulani suna baya, wani murmushi Waziri yayi , yawuce. Bayan yayi parking motar yayi saurin fita yakirawo masu gadin gidan, ai Medaki tana ganin haka tayi surin komawa part dinta, kara jaddadamasu yayi akan su kula da tsaron gidan, kuma akulle kofa babu wanda ze kara shigowa bare fita. Haka suka raka Sarki da Fulani har falo, Fulani ta kalli Waziri tarike kanta kamar me tunanin Sarki yace lafiya Fulani ko kanki yake ciwo? Kai ta girgiza, can kuma tayi saurin bude ido tace ina yarinyata? Sarki yace kina nufin kin haifi cikin jikinki kuma yana raye? Kai ta girgiza tace dan Allah kubani diyata wlh nasan na haihu, kada kucemun ta mutu. Waziri yace ki kwantar da hankalinki, diyarki tana nan, araye asalima babu abinda yake rabaku, atare kuka zauna, babu abinda yasameta, sede yanzu tana gurin Gimbiya Suhailat, kuma nasan sun kwanta kinga dare yayi kibari seda safe zaki ganta. Murmushin jin dadi tayi ta daga mashi kai, sallama sukayi masu suka fita. Sarki yace turani muje daki muyi wanka, murmushi tayi tafara turashi, atare sukayi wanka tana temaka mashi, bayan sunfito sukayi sallah sannan suka kwanta suna me cike da farin cikin ganin junansu, sun rungume juna kamar za,a rabasu. Suna fita Waziri yakalli Sarki yace kaga abinda nagani kuwa? Sarki yace nagani, kabari kawai Allah yakaimu gobe nasan zamu gano sauran munafukan gidan nan. Sallama yayi mashi kowa yanufi part shi. Washe gari da misalin karfe 10 Malam na darazo ya iso, aka saukeshi amasauki, bayan yagama cin abinci aka kawoshi fada, alokacin su Sarki Hasheem da fulani sun iso gurin tasha kyau sosai, tana zaune agefen Sarki, bayan sungama gaisawa da Malam, ya tambayi jikinshi yace Alhamdulillahi ai jiki yaya sauki, dama akwai dalilin dayasa kuma yanzu nasamu maganin akusa dani. Dariya malam yayi yace to mungodema Allah, amma abinda nakeso da akai, sekayi hakuri da duk abinda zakaji ko zaka gani, ayanzu, nasan zaka shiga cikin damuwa, amma munaso mukawo karshen muna fukan gidan nan, kuma kaima nasan zaka so kasan wadan da sukayi ma Fulani haka. Sarki yace hakane, babu komai, Allah yasa inji alkhairi. Malam yace amin, adede lokacin su Gimbiya Suhailat dasu beauty, Ayman, Jakadiya , Areef da Haisam suka shigo, ai beauty tana ganin Mamanta da gudu taruga tafada kanta tana dariya. Itma tana ganinta tayi saurin rungumeta tna fadin yarinyata, Sarki da mamaki ya kamashi dasauri ya kalli fulani yace wannan ce diyata? Kai tacdaga mashi, besan lokacin da kwalla tacika mashi ido ba. Waziri yabada umarnin afito dasu Jakadiya Karima, sannan yasa Jakadiya Safeeya takirawo su Gimbiya Zakiyyah da Medaki, wani bafade yasa yakirawo Baban Fulani da Baban Darazo, kowa yasamu guri yazauna yana kiran abinda za,ayi. Nima nace bara in anje alkalamina injira shigowar su Sarkin Fada. Ur's NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 AMAKABARTA AKA HAIFENI 🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 100⚜105Cikin isa da mulki Gimbiya Zakiyyah tashigo, ko sallama ma da kyar tayi, guri tasamu gefen Sarki tazauna, dan batasan yasamu lfy ba. Kallonshi tayi fuskarta dauke da murmushi tace barka da asuba memartaba yajikinka?. Sanin ko anyi mashi magana baya amsawa yasa tadauke kanta bata kula da motsa bakin dayayi ba. Kallon malam tayi tace malam barka da asuba, yace yauwa kintashi lfy. Medaki ce tashigo jikinta duk yayi sanyi kamar antsamota daga ruwan zafi. Akusa da bakin kofa tazauna duk tagama rudewa, cikin rashin jindadin abinda tayi Sarki Hasheem yace medaki dawo nan mana. Ai Gimbiya Zakiyyah batasan lokacin datace yaushe kafara magana memartaba?. Murmushi yayi kawai yayi shiru, haryanzu babu wanda ya kula dasu Fulani, bayan medaki tazauna kusa da Gimbiya Zakiyyah, kallonta tayi tadan duko kusa da kunnanta tana murmushin mugunta tace ina fatan kinyi kwanciyar karshe agidan sarauta? Seki shirya karbar hukunci. Sallamar su Sarkin fada da Jakadiya ne tasa Medaki tayi saurin tashi tana hawaye. Wani murmushin jindadi Sarki Hasheem yayi, ganin Jakadiyarshi, dama yana so ya tambayeta domin ita yakeso yayima albishir na samun diya da yayi, domin yasan tana daya daga cikin masu son yasamu karuwa. Da fara,a yace Jakadiya matsonan infara baki albishir medadi, ai jitayi kamar yan hanjin cikinta zasu fito, kamar ance Fulani tadago kai, ai tana dagowa sukayi ido 4 da Sarkin fada. Wani irin ihu tasaka ta ture beauty, tashi tayi kamar zata ruga tana fadin gashi nan yazo zasu kasheni. Waziri da Sarki Qaseem bakaramin mamakin abinda take fada sukayi ba, duk da dama suna zarginshi. Jakadiya Safeeya da Gimbiya Suhailat ne suka rike Fulani, Sarki Hasheem kuwa jiyayi kamar yatashi, gaba daya jikinshi rawa yakeyi, ganin haka Sarki Qaseem ya matsa kusa dashi yadafashi yana bashi baki. Gimbiya Zakiyyah kuwa batasan lokacin data mike tsaye ba tana nuna Fulani, Medaki kuwa kukanta har yafito fili, duk da sanyi da falon yakedashi be hana zufa keto mata ba. Gaba daya sauran mutanen Falon sun shiga rudani, Areef kuwa matsawa yayi kusa da beautynshi yari keta sosai, yadora kanta saman kafadarshi, dan yasan batason hayaniya, ita kam kuka tasaka tunda Fulani ta tureta. Malam da kanshi ya matsa kusa da Fulani datake kwance akan cinyar Jakadiya tana ta kuka, addu,a yafara yimata yana tofa mata. Sarkin fada kuwa da Jakadiya zaman yan bori sukayi suna rarraba idanu. Sarki Qaseem ne yayi gyran murya sannan yace ya isa, kowa yasamu nutsuwa kuma azauna domin muyi abinda yakawomu. Malam yadade yanama Fulani addu,a kafin tasamu tadawo cikin nutsuwarta. Sarki Hasheem kam gaba daya kanshi yagama daurewa shiru kawai yayi yana karanta addu'oi, hakan yasa yafara samun nutsuwa, sede haryanzu idanunshi suna kan Jakadiyarshi data kasa kallonshi. Bayan kowa ya nutsu Waziri yatashi yace ma malam yabude masu taro da addu,a. Bayan angama Waziri yafara magana. Alhamdulillahi da farko zanfara dayima Allah godiya daya kawomu wannan rana mecike da farin ciki da kuma bakinciki. Da farko zanfara gabatar da matar Sarki, kuma amarya agurinshi wadda akafi sani da Fulani. Bayan shekaru 18 da wasu watanni bata gidan nan, inda aka samu wasu marassa imani suka shigo har cikin dakinta suka dauketa........ Sallamar Su Baban Fulani ce ta tsaida Waziri daga jawabin dayakeyi. Fulani tana ganin Babanta ta tashi tanufi gurinshi, ai shima yana ganinta yabude hannuwa tashige jikinshi tana kuka. Shima kukan yakeyi seda suka bama kowa tausayi. Bayan sun natsu suka zauna, Baban beauty kuwa gaba daya mamaki yagama cikashi ganin abin al,ajabi. Waziri yaci gaba da magana. Kamar yanda nace ba,asan wadan da sukazo suka dauke Fulani ba, amma tunda Allah yasa gata tadawo kuma tana cikin hankalinta. Kuma zata iya nuna wadanda suka aikata haka akanta to duk wanda yakasance cikin masu laifi, tabbas ze fuskanci hukunci me tsanani, kuma kowane irin matsayi gareshi a masarautar nan. Ai kamar daga sama sukaji Medaki ta tashi tana fadin shikenan munshiga 3 wlh, ba laifina bane, duk kutsaya wlh zanfadi iyakar gaskiyar dana sani. Gimbiya Zakiyyah tayi wani murmushi aranta tace lallai zaki sha mamakina,ni nasan babu wanda zeyarda idan kikace hadani. Waziri yayi murmushi yace rankiyadade munajinki. Tashi tayi tana kuka tafada masu duk abinda sukayi itadasu Gimbiya Zakiyyah, akan batan Fulani, sede bata fada masu abinda suke aikatawa da Sarkin fada ba. Gaba daya falon aka dau salati, Sarki Hasheem kuwa zama yayi kamar dutse, kallon Jakadiya Karima kawai yake idanunshi na zubar da ruwa. Waziri yace da kyau, tashi Gimbiya Zakiyyah tayi tafara magana cike da mulki. Inada ja agame da maganar Medaki, wannan maganar datayi kawai tafa deta ne sbd wani dalilinata, amma kowa yasan bana shiga harkar talakawa taya za,ayi inhada baki dasu mu aikata irin wannan shirmen. wanda kowa yasan duk wanda yafito daga gidan sarauta bazeyi haka ba. Idan kuma har tace dani, ni nayarda sukawo sheda, idan har aka sameni da hannu aciki nayarda da duk wani hukunci daza,amun. Waziri ya jinjina kai, alamar gamsuwa, ya kalli Medaki yace kina da wata shedar dazata nuna mana tana da hannu acikin abinda kika fada? Wata zufa ce takara keto mata, hawaye suna zuba a idonta tafara girgiza kai, tace a,a amma wlh dama

Chapter 9 of 13