saman
cinyarta tana murmushi.
Haisam yace tashi muje masallaci kada Abba yace
beganmu ba, Jakadiya tafita tace sekun dawo, akwai
abinci akitchen idan kundawo, suka ce to. Areef yaduka
kusa da beauty yace wato yau kinga yar uwa shine ko ki
kalleni ko? Kai tagirgiza ta tashi ta kalleshi. Dariya Haisam yayi yace beauty bakida matsala, kome akace kiyi sekiyi, gaskiya nan gaba zankoya maki bakomai zaki rika yiba.
Duka Areef yakaimashi yana fadin todan bukulu, ai seka
hanata, Allah yakashe yabani idan munyi aure base
narika magiya ba shine zakace wani tadena. Haisam yace
sosai ma, har wannan son jikin duk sena hanata. Dariya Areef yayi yanufi hanayar fita yace tunda kaine mijin ai se ingani, aini naji dadin wannan abu, sonjiki. Ai shine abinso, fita sukayi suna dariya.
Ayman tace sister da kikayi wanka kinyi alwala ko? Kai
tadaga mata, tace yauwa tashi muje kiyi sallah nima inyi alwala inyi, hannunta takama suka nufin daki.
Sarkin fada ne tsaye abakin kofar Gimbiya Zakiyyah se
waige waige yakeyi kamar marar gaskiya, wani abu
yadauko aleda yasa a idonshi, kafin yashiga gidan,
alokacin tagama sallah tafito falo, da sallama yashiga, cike da mamaki tace kai? Waya baka ikon shigowa part
dina? Ko kuma wani yace maka ina nemanka? Kai
yadago suka hada ido, wani irin abu taji ya tsikareta,
saurin rufe ido tayi, ganin halin data shiga yasa yayi
murmushi aranshi yace anzo gurin. Kallonta yayi yace
nadauka ai kinason ganina shiyasa nazo amma bari
inkoma.
Saurin bude ido tayi tasaki murmushi tace ni na isa nace ka koma? Shigo sannu da zuwa, zama yayi abisa kujera,
tace a,a muje daga ciki kada wasu suganka. Murmushi
yayi yatashi yana lashe baki aranshi yana fadin wayyo ni.
Daki suka shiga tace meza,a kawo maka? Murmushi yayi
yace bakomai zoki zauna kawai fira nazo muyi, wani irin yanayi taji tashiga, tahowa tayi kusa dashi tana wani
girgiza, kusa dashi tazauna tace togani, kallonta yayi
yakamo hannunta yace babu wanda zeshigo ko? Lumshe
idanu tayi alokacin taji wani bakon yanayi yashigeta, tace ina zuwa bari inbada sako akulle mun gidan kuma kada
abar kowa yashigo, yace akulle gida nida ba nan zan
kwana ba, wani irin kallo tayi mashi tace, kama isa, ai tunda kashigo sede da asuba kafita. Dariya yayi yace duk abinda kika fada dede ne rankiyadade, murmushi tayi
tafita. Wani irin tsalle yayi na farin ciki, hannunshi yasa a aljihu yaciro wani abu aranshi yana fadin saboda tsaro.
Bayan sundawo daga sallah part din Jakadiya Safeeya
suka wuce, anan suka samesu afalo beauty tana kwance
kan cinyar Ayman ita kuma tana ta wasa da gashinta
tana bata labari, da sallama suka shiga, Haisam yace to wlh baze yuwu ba, wannan matar taka zata sama Angel
dina taurin cinya, Areef yace wlh kai dan iska ne, agaban beauty kake wannan maganar sokake ka kangararmun
da ita, bacin kasan yarinya ce. Ai dasauri beauty ta tashi jin abinda Areef yafada, kafafuwa tafara durzawa akasa
tana turo baki tana kunkunai.
Dariya Ayman da Haisam sukayi, Ayman tajawota tace yi
hakuri, shine yace maki yarinya ko? Kai tadaga tana kara turo baki, kamar zatayi kuka, ai ganin haka yasa Areef ya matso yaduka kasa kusa da ita yana fadin yihakuri
beauty na wasa nakeyi kinji? Kai ta daga tana murmushi, Areef yace yauwa beauty na, tashi muci abinci in baki
tsara barki. Tashi tayi tanufi kitchen.
Haisam yace gsky kaci sa,ar mata wannan saurin sauka haka, to wlh kaji tsoron Allah, Areef yace da tsoronka
nakeji? Sarkin sa ido kawai, kuma badakai zanci abinci
ba, nida beauty zanci. Haisam yace Allah nagode maka
nima daka hadani da abin sona ayau, nadana shiga 3
agurinka, Angel muma tare zamuci ko? Kai tadaga tana
murmushi, lokacin da beauty tafito tasan alokacin ake
bama mamanta abinci, harta nufi dakinta se kuma ta
tuna da maganar Jakadiya Safeeya,,,,,,,, kada kisake
kishiga dakin can idan akwai mutane agidan nan, idan ba haka ba, kamata zasuyi bazaki kara ganinta ba. Maganar
Areef ce tadawo da ita, beauty mezakiyi awannan dakin
kuma?
Juyowa tayi tana murmushi ta girgiza kai, tanufo
gurinsu, ansar abincin yayi ta koma tadauko sauran,
atare yazuba masu yamika ma Haisam yace ganaku nan,
dariya yayi yajawo yazuba masu, Areef yace taho beauty
na muci, zama tayi kusa dashi, sede bega ta jingina dashi ba, murmushi yayi aranshi yace su beauty anfara girma
kenan, abaki yafara bata tanaci, shima yace nima bani
zakiyi ko? Kai tadaga tana murmushi, haka sukarika cin
abincinsu sun manta dawasu Su Haisam.
Dariya Jakadiya Safeeya tayi jin abinda Gimbiya Suhailat tafada, tace ai sundawo tundazu suna gidana, acan
nabarsu suna cin abinci ma. Wani murmushin jin dadi
Gimbiya tayi tace ai nasan Yarima zeso Ayman, gashi
lokaci guda har sun saba, wato kunyata sukeji shiyasa
suka tafi can. Jakadiya tace emana agida na za,ayi firar ai, kinsan Yarima. Naguri nane, ai, gimbiya tace aise suyita ta tafiya nima haka nakeso, Allah yabama Yaya lafiya
musha biki. Kallon agogo Jakadiya tayi tace bari inje gida seda safe Gimbiya.
Kallonta tayi tace haba de tunyanzu sallar isha,i ma
yanzu za,ayi, wai meyasa yanzu bakison zama anan sosai, musammamma da dare? Gaban Jakadiya yafadi, aranta
tace nasan Fulani tana can takusa tashi ai dole inkoma
kada su Yarima suganota. Dasauri tayi murmushi tace ai dole intafi inje inji inda aka tsaya amaganarsu,
murmushin jindadi Gimbiya tayi tace hakane fa,
Jakadiya tace nikam yanzu ai nasamu yan fira tunda de
kunya tahanasu zama anan, dan yarima ma cewa yayi
bayaso kusani harse Sarki yasamu lafiya yasan dayayi
maku magana za,a sa rana. Gimbiya tayi dariyar jin dadi tace kibarni dasu, zamu gwada masu bamusan komai ba
dakanshi zezo mana da maganar, bari hubby yadawo
infada mashi, sosai Jakadiya taji dadin maganar Gimbiya, sallama tayi mata tafita.
Koda taje kowa yana zaune tare da masoyiyarshi, Areef
yanata koyama beauty rubutu da karatu, kitchen ta
wuce ta dauko abinci tace sannuku da aiki, Yarima yace
Aunty har kindawo? Tace bari inshiga ciki inci abinci inyi wanka sukace to afito lafiya.
Haka rayuwarsu tacigaba da tafiya babu wanda yasan abinda yake tafiya atsakanin masoyan. Abangarensu
kuwa soyayya me karfi tashiga tsakaninsu, akoda yaushe
suna part din Jakadiya Safeeya, Areef yadage sosai yana koyama beauty karatu da rubutu, suna dawowa office
beda gurin zama se gurinta, dayake itama tanada basira
beda gurin zama se gurinta, dayake itama tanada basira
kome yakoyamata take daukeshi, ayanzu har rubutu ta
iya, dan tana hada kalmomi.
Ganin haka yasa hankalin Jakadiya yafara tashi, samunta tayi tafada mata kome Yarima ya tambayeta kada
tabashi amsa, idan ba haka ba, duk ranar da yasan
labarinta bazata kara ganinshi ba kuma zesa akoresu,
kada kisake kice mashi A MAKABARTA AKA HAIFEKI,
kawai kifada mashi abinda nafada mai, kinji ko? Ta daga kai, da wannan hankalin Jakadiya Safeeya yadan kwanta,
kuma akaci sa,a shima be cika yimata tambayoyi ba.
Abangaren Gimbiya Zakiyya kuwa ta kwace ma Medaki
Sarkin fada, dan duk dare agurinta yake kwana, wani irin sonshi takeyi, har bataso yayi nisa, sosai Medaki tashiga damuwa sede tunda Jakadiya Karima tayi mata bayanin
komai, shima Sarkin Fada yace mata yayi hakane dan
kawai yarama irin cin mutuncin datayi masu ne, kuma
kudinta yakeci sosai, kuma yana kawoma su Medaki,
hakan yasa hankalinta ya kwanta idan yasamu lokaci
kuma yana zuwa gurinta.
Haka rayuwar gidan tacigaba da tafiya Waziri akullum
yana kara sakama Sarkin fada ido, dan sunyi waya da
malam yace mashi yayi kokari yagama hada duk wata
sheda daza,a fara tuhumar Sarkin fada yana nan zuwa
tunda jikin Sarki yafara sauki, yanaso akawo karshen
matsalar gidan.
Gimbiya Suhailat ce tafito tana neman Ayman, ganin
bata ganta ba, wata baiwa tace sunfita bagaren Jakadiya Safeeya. Murmushi tayi tace yaude bari inje da kaina
inga wata wainar ake toyawa, kuma in nuna masu nasan
abinda suke boyemun, ai gara azo ayi bikin nan kowama
yahuta. Allah nagode maka da zaka cikamana burinmu,
bari indawo in bama Yaya albishir medadi, itama nasan
zataji dadi ace Ayman dinta zatayi aure. Fita tayi wasu bayi suna take mata baya, suka nufi bangaren Jakadiya
Safeeya.
Zaune suke afalo, Areef da beauty suna zaune bisa
doguwar kujera, sungama karatu, yana bata biscuit
abaki, suna ta firar su gwanin ban sha,awa, Haisam da
Ayman suma suna zaune kasa yana bata ice cream tana
ta zuba mashi shagwaba.
Jakadiya kam tana dakin Fulani tagama yimata wanka
tana sa mata kaya, tayi kyau sosai, hutun datake samu
kyanta yafito har kiba tayi. Jakadiya tace insha Allhu
komai zezo karshe da malam yazo kema kije gurin
mijinki koze samu sauki.
Wazirine da Sarki Qaseem suka fito zasuje bangaren sarki Hasheem, dede gurin part din. gimbiya Zakiyya
zasu wuce, sega Jakadiya da Sarkin Fada sunfito daga
gidan, Sarkin Fada se gyara wando yakeyi, suna fitowa
suka kwashe da dariya, hannu yamika mata suka kashe,
yace kai wlh yau nasha roman Gimbiya, sosai, kinsan
tundazu naso infito ta hanani, ashede haka Sarki yakejin dadinshi. Jakadiya tace ba dole sunemeka ba, tunda kana dauke masu nauyin abinda musakin mijinsu yakasa ba,
ai wlh..........
Maganar ce ta makale sakamakon idanu data hada dasu
Waziri. Hannu tasa ta tabo sarkin fada dayake shirin yin magana. Wata irin zabura yayi alokacin da idanunshi
sukaga abinda take nuna mashi, wani irin kallo Sarki da Waziri suke binsu dashi,,,, kuttt suka hadiyi wani miyau me daci, ga wata irin zufa datake fito masu.
Shinko su waziri sunji firarsu? Kubiyoni anext page
danjin abinda yafaru.
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
www.NabilaLady5@gmail.com
Season 85 ⚜90
Idan ran Sarki Qaseem yayi dubu to yabaci dajin irin
kalaman Sarkin fada da Jakadiya Karima, Waziri ne,
yajuya ya kalli Sarki Qaseem, shi kanshi ya tsorata da
ganin yanayinshi. Cikin sauri yataboshi, yana kallonshi yayi mashi alamu da ido.
Juyawa yayi murmushi dauke afuskarshi yakalli su Sarkin fada yace dama gurin memartaba zamuje kuma segashi
munhadu, ko kuma daga can kuke? Dasauri Sarkin fada
yace wlh kuwa shinema mukashiga gurin Gimbiya muyi
mata albishir naganin halin da Sarki yake ciki.
Gaskiya munji dadi sosai, jikinshi yayi kyau, yanzun nan nashiga ko kinti 2 banyi ba, shine ma muka fito da
Jakadiya. Amma ai kuma yanzu kukazo nan, ko kun dade
tsaye anan? Waziri yayi murmushi yace ai ko second 2
bamuyi anan ba, kuka ganmu, bari mukarasa. Wata irin
ajiyar zuciya suka saki, har suna hada baki gurin fadin to adubashi, Jakadiya Karima tajuya tanama Sarki Qaseem
kirari, hannu yadaga mata tare da kakalo murmushi
sannan suka wuce.
Sarkin Fada yace wai! Allah yasomu damun kama kanmu
ashema basujimu ba, Jakadiya tace kaide bari, nidama
nasan dakyar idan sunjimu, dan Sarki Qaseem mutum
ne wanda beson jin abinda bedameshi ba. Sarkin Fada
yace haka ne, shima ai Wazirin na Allah ne, babu
ruwanshi dajin gulma, akwai addini, muje gurin Medaki
itama inkwashi rabona. Jakadiya tace to amma gaskiya
yau nima inaso muje dakina.
Wani kallo yayi mata, sannan yace haba Jakadiya da
girmanki kike fadin haka, ai kibarma Gimbiyoyin Sarki,
ke kam yanzu ai kinwuce wannan matsayin. Hade rai tayi
tace amma ai duk tsufa na ban kaika ba ko? Dariya yayi
yace haka ne, amma kinmanta namiji baya tsufa? Kawai
kibar wannan maganar muje inyi abinda zefishsheni.
Wani guri kafin akai part din Sarki Hasheem suka samu
suka zauna, idanuwan Sarki Qaseem har rufewa sukeyi
sbd bacin rai, da kyar ya iya daga baki yace, dan Allah Waziri kace abinda naji ba gsky bane, nabama mutanen
gidan nan amana musamman wadannan 2, acikinsu
Yaya yafison Jakadiya Karima, nima haka, dan Allah
Waziri. Wani irin tausayinsu ne yakama Waziri, ganin
idanun Sarki Qaseem sunyi ja yasashi matsawa kusa
dashi tare da dafashi yace.
Memartaba wane irin matsayi kabani azuciyar ka?
Kallonshi Sarki yayi yace aduk gidan nan kaine mutumi
nafarko damuka fara aminta da kai, kawuce kowane irin
matasayi agurinmu har ka kai matsayin dan uwa
agurinmu. Bari kaji aduk fadin duniyar nan kai kadai
muke iya fadama sirrinmu, shiyasa bama jayayya da duk
wata shawara dazaka kawo mana.
Kawai kafadi abinda ke ranka namaka alkawarin
komenene zankarbe shi, nasan bazaka taba fada mana
abinda ze cutar damu ba. Gyaran murya Waziri yayi,
fuskarshi cike da annurin kalaman dayaji daga bakin
Sarki Qaseem, ahankali yafara fada mashi duk irin
abubuwan daya fara gani agurin Sarkin fada, har firar
dasukayi seda yafada mashi, daga karshe yace zakayi
mamakin idan nafada maka Gimbiya Fulani tana cikin
gidan nan tsawon watanni 3?.
Seda Sarki yakusa kwarewa saboda firgita, kai waziri
yadaga alamun da gaske yake, sannan yacigaba, akwai
abubuwa da yawa wanda bakusansu ba, daga ni se
Malam, se Jakadiya Safeeya kadai muka sansu, amma
inaso abari se gobe idan Malam yazo zeyi maku bayanin
komai, sede abinda nakeso kasani bawai munboye
Fulani da wata manufa tamu bane, a,a wannan umarnin
Malam ne.
Kuma alokacin da muka kawota gidan nan, babu wanda
yasan itace, dan tun lokacin data bace tsawon shekaru
18, har zuwa yanzu tana cikin yanayi na hauka, kuma
wahala data sha ne yasa muka kasa ganeta, acikin yan
kwana kin nan dayake tana samun kulawa agurin Jakadiya Safeeya, dan agurinta take zaune, tofa alokacin ne, tafara dawowa kamanninta, sbd tana samun tsafta,
shine Jakadiya ta ganeta.
Bayan tafada ma Malam, yace kada tafada ma kowa,
kuma yakirani yafada mun, nima yace kada infada ma
kowa, dan wadan da suka aikata mata wannan laifin
suna cikin masarautar mu, dole semunbi asannu zamu
iya ganosu.
Ajiya mukayi waya dashi yace mun zezo gobe domin
yanaso yakawo karshen halin da masarautar mu take
ciki. Babban abin farin ciki tahaifi cikin dake jikinta, Allah ya azurta ta dasamun diya mace, aranar data bar gidan
nan kamar yanda su Malam suka sami labari daga gurin
wadan da suka tsinceta, to aranar ta haihu, kaga yanzu
Yarinyar tana da shekara 18 da watanni.
Babban abinda yasa nataboka alokacin damu kaji abinda
su Sarkin fada suke fada shine, kasan idan baka iya kama barawo ba, to shine zekama ka. Nadade dasanin halin da
Sarkin fada yake ciki shida matar Sarki Medaki, suna
aikata kazamar harka, kusan kullum agurinta yake
kwana, nasamu wannan bayanin ne daga gurin daya
daga cikin bayin dana sa ya kular mun da duk wani
motsi na waziri.
Dan haka ayanzu base gobe ba, inaso kabani dama nasa
akama Sarkin Fada da Jakadiya akullesu har zuwa gobe,
idan Malam yazo se afito dasu, nasan idan aka maimaita
masu laifin dasukayi, zasu tona duk abinda sukayi.
Hawayen dake idanun Sarki Qaseem yagoge, saboda
bakaramin kaduwa yayi dajin labarin Waziri ba.
Da ace beji abinda suka fada dazu ba, kuma ace ba
waziri bane yafada mashi dabaze taba yarda da abinda
aka fada ba, kallon Waziri yayi yace ayanzu bani da
sauran bakin magana, da kai da Malam nabaku damar
ku aiwatar da duk wani abu da yayi dede da hukuncin
masarautar nan, sede abu daya nakeso, inaso akawo ma
Yaya Fulaninshi yagani, kila ta silar haka yasamu sauki, banaso afadi wani abu harse yasamu sauki, dan yaji duk
irin abinda mahintan makusantanmu suka aikata. Waziri
yace godiya nake, bara inje insa akama su, kafin wani
tunanin yashige su sugudu. Sarki Qaseem yace shikenan
bara inshiga gurin Yaya kada yaji shiru.
Da sallama su Gimbiya Suhailat suka shiga falon Jakadiya Safeeya, adede lokacin da Beauty tana karbar biscuit
ahannun Areef shi kuma yana ta mata wasa da hankali,
se dariya sukeyi, hannu tasa zata karba, cikin rashi sa,a tafada jikinshi. Kwanciya tayi saman cinyarshi tana ta
dariya shima haka.
Cak Gimbiya ta tsaya da sauran Sallamar data fara,
tsayawa tayi tana kallonsu cike da mamaki, da takaici,
sam bata kula dasu Ayman ba, sede kawai taji dariya
agefenta, saurin kallon gurin tayi, ai jitayi kamar tazube
dan takaici, Haisam ne, yake kokarin saka ma, Ayman sweet abaki, sunata dariya abinsu.
Kamar daga sama sukaji wata irin tsawa, wadda tasa
beauty saurin kankame Areef, tayi,wani Uban ashar
Gimbiya tasaki, wanda ita kanta batasan ta iyashi ba.
Gaba dayansu hankalinsu atashe suka juyo suna
kallonta, cike da kaduwa Haisam da Ayman suka sauko
kasa, shikam Areef sam abun be daga mashi hankali ba,
kara rungume Beauty yayi saboda kukan datasa mashi,
sam bata taba jin wata aba wai ita tsawa ba, tunda take, hakan yasa tayi mugun tsorata.
Gimbiya cike da bacin rai tace kai dan Ubanka bazaka
saketa ba, kabani hankalinka? Jakadiya ce tayi saurin
fitowa daga dakin fulani, dan dama tayi bacci ta tsaya
gyara mata dakinne kafin tafita, tana cikin gyara taji
wannan hayaniya.
Alokacin data fito saura kadan tazube saboda kaduwa,
cak ta tsaya bakin kofa tana zaro ido tare da kallon
Gimbiya. Areef yakama beauty suka sauka kasa, dan
shima alokacin da Gimbiya tamashi wannan zagin
bakaramin kaduwa yayi ba, dan tunda yake betaba jin
irin zagin abakin momynshi ba, ko fada bata taba
yimashi ba.
Wani irin murmushin takaici Gimbiya tayi, ta kalli
Jakadiya, rai abace tace sannu munafukar Allah,
mayaudariya, maha inciya, ashe dama abinda kike
kullawa kenan? Kinaso ki batama yarona tarbiyya tunda
ke baki dashi? Wato duk ginin da nakeyi kece kike rushe shi? Kinje kinsamo wata matalauciyar yarinya kin hadata da Yarima, ita kuma diyata kin hadata da abokinshi.
Ashe dama duk zaman damukeyi zaman munafurci ne ?
Wai meyasa duk wanda be fito daga gidan sarauta ba,
zaka sameshi maci amana ne? Lallai zamanki yazo karshe
agidan nan, bazan kara amincewa da banzan halinki ba.
Kai kuma Haisam kake kowa? Inaso kasani Ayman
Yarima zata aura, garama ka tattara soyayyarka kayi
waje da ita, ko kuma kaima kaje kasamu diyar dan siyasa ka aura, danmu bama auratayya da yan siyasa, domin
Sarauta gado ce, kuma ajininmu take, kufa?.
Mulki ne, da lokacinku yacika ko kunaso ko bakwa so,
dole kusauka kubama wanda yaci, dan haka kada inkara
ganinka agidan nan, bare kuma tare da Yarima ko
Ayman. Ke kuma kisaurari hukuncinki, matsawa tayi ta
ture beauty wadda tundazu take kuka.
Hannu Areef yasa yariketa sosai shima hawayene suke
zuba a idonshi, da kyar yace Momy dan Allah kiyi hakuri wlh beauty itace rayuwata, idan kika rabani da ita
mutuwa zanyi, ture ta tayi takama hannunshi dana
Ayman wadda itama kukan takeyi, Haisam ne kawai
medauriya acikinsu, amma har jakadiya kuka takeyi.
Jansu tarikayi kamar yara har suka fita daga falon,
dasauri Jakadiya ta matsa takamo beauty ta dagata zasu
shiga daki, kuka kawai, takeyi harda sheshsheka, tana tashi takoma tazube kasa sumemmiya.
Abakin kofar falon Areef ya toge, duk yanda Gimbiya
taso tajashi kasawa tayi, hannunshi ya fisge alokacin
dayaji Jakadiya tasa wani irin kuka tana fadin munshiga 3 Yar Baba dan Allah kitashi, dasauri yakoma falon,
Gimbiya tabishi tana fadin kadawo nace maka ko. Yana
zuwa yaga beautynshi kwance akasa babu alamun rai
atare da ita, wata irin kara shima yasaki tare da dafe
kanshi yazube kasa asume.
Urs.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
www.NabilaLady5@gmail.com
Season 90⚜95
Da gudu Gimbiya da Haisam sukayi kansu, tana zuwa
takama Areef hankali tashe tafara jijjigashi tana kuka, Jakadiya Safeeya ma beauty tarika jijjigawa tana kuka.
Haisam ne yayi kokarin fita waje yakira wasu bayi maza, suka dawo tare.
Su suka dauki Areef shi kuma yadauki beauty suka fita,
Jakadiya, Gimbiya da Ayman suna binsu abaya, cikin
mota yasakasu, Jakadiya tashiga tare da Ayman ya kulle
kofar ko kallon Gimbiya beyi ba yaja motar suka barta
nan tsaye dan babu halin tabisu, tunda Sarki Qaseem
besani ba.
Komawa tayi part dinta tana kuka, kara tunano kalaman
Areef tayi,,,, Momy wlh kika rabani da beauty nima
mutuwa zanyi. Hannutasa tarufe duka kunnuwanta tana
fadin bazaka mutu ba Yarima, kaine farin cikina, dan
Allah kar kamun haka. Saman kujera tafada tana kuka
bayinta se hakuri suke bata.
Waziri ne, tare da wasu manyan bayi maza suna binshi
abaya, hanyar lambu suka nufa dan yafi zaton suna can,
koda sukaje basu same su ba, tunawa yayi da Medaki,
hakan yasa suka nufi can.
Alokacin Sarkin Fada da Medaki suna cikin daki, ita ko
Jakadiya Karima tana zaune falo tana kallo ta tasa
farfesun kaji tanaci. Wata baiwa ce tashigo falon, ai
dasauri Jakadiya tace Uban wa yabaki izinin shigowa?
Bana hanaku idan muna gidan nan kushigo ba?.
Dukawa tayi tace Allah yabaki hakuri, dama Waziri ne, ya tambayeni ko keda Sarkin fada kuna ciki, shine nace
masa kuna nan, shine yace amaku magana. Cikin
Jakadiya ne yayi wani kara, nan take zufa tafara keto
mata, batasan lokacin data saki cinyar kazar datake
hannunta ba.
Cike da tashin hankali tace ubanwa yace kifada masa
muna ciki? Innalillahi wainnailaihirraji,un. Munshiga 3
kada de ace asirinmu ne yake shirin tonuwa? Tashi kiba
mutane guri munafuka. Hanyar dakin Medaki tanufa, har
tuntube takeyi, tana zuwa tafara bubbuga masu,alokacin
sunyi nisa cikin harka, dade sukaji bugun yayi yawa,
shine Sarkin Fada yayi saurin zira babbar rigarshi, ko wando besa ba, haka yaje yabude.
Ai yana fitowa Jakadiya tajawoshi tana fadin munshi 3
gasu Waziri can abakin kofa suna jiranmu. Zaro ido yayi yana fadin waya fada masu muna nan? Tace kaide
kawuce muje, bawannan bane agabanmu, yanda zamu
kare kanmu bakamar ma kai, danni wlh tawa mesauki
ce, tunda ni macece kuma kowa yasan inada hakkin
shiga duk inda nakeso amasarautar nan.
Sarkin fada yace kiwa Allah kije kice ke kadai ce, bakisan inda nayi ba, nasan zasu kyaleki. Zaro ido tayi tare da dafe kirji tana fadin Jar Uban nan, ai wlh baka isa ba, ai gara ma kai, kome akayi maka kasha dadi, nifa?
Menasha, kun hadani da naman kaza da kallo kunshige
daki, ai wlh inde nafita kaima seka fita.
Bugun kofar falo ne, ya sasu saurin kallon gurin alokacin Medaki tayi saurin fitowa da daurin gaba ajikinta, kanta ko dan kwali babu, tana fadin wai meke faruwa haka?
Shigowar Waziri ce tasata yinshiru, idanu 2 suka hada
dashi, hakan yasa yayi saurin kauda kanshi, ai dasauri
takoma daki, kallon Sarkin Fada yayi wanda ko rawani
babu akanshi, dagashi se babbar riga,, jikinshi kam ko
wando babu.
Hannu Sarkin Fada yadora akanshi yana fadin shikenan
yau kuma ahaka tazo mani. Waziri cike da bacin rai yasa fadawa sukamashi, Jakadiya Karima tace ai dama kullum
ina fada maku kune bakwaji, yau ga irin ta nan, nikam
baruwana, Allah yakara, hanyar waje tanufa tana shirin
fita. Wani kallo da Waziri yayi mata yasa dole taja burki tana raba idanu.
Wazirin yace ku kamosu dukan su akaisu kurkutu zuwa
gobe, kuma inaso kusaka kwakkwaran tsaro agidan nan,
yanzu zan fadama sauran masu tsaro, kada abari kowa
yafita daga gidan nan koda kuwa matar Sarki ce, koma
waye dole akirani kafin yashigo ko yafita. Haka aka tasa keyarsu zuwa kurkutu. Medaki kuwa tana daki tarasa
inda zata sa ranta.
Suna zuwa asibiti aka karbesu akayi emergency dasu,
kowa aka fara bashi temakon gaggawa, cikin lokaci
kankani Areef ya farfado, sede beauty ko alamun motsi
batayi, hakan yasa likita yace akai Yarima dakin hutu, nan suka cigaba da duba Beauty.
Tunda Areef ya farfado yafara kiran beauty, kuka
yasakama Haisam da Jakadiya Safeeya, se lallashin shi
sukeyi, Areef yace wlh idan wani abu yasami beauty na,
nima Momy zata rasani. Haisam yace kadena fadin haka
Areef insha Allahu zata warke. Karar wayar Haisam ce ta katsesu, Areef yace idan Momy ce kace mata ban farfado
ba dan Allah.
Yana dagawa tace Haisam yaya jikin Yariman? Wani irin
haushi yaji, wato ita ta danta ma kawai takeyi. Ahankali yace Momy Areef yana cikin wani yanayi, addu,a kawai
zakitayashi. Cike da tashin hankali tace ina likitan banishi, yace suna can akanshi suna bashi temako.
Dan Allah Haisam kace ma likita yayi duk yanda zeyi kada dana yarasa ranshi, ko wani abun yasameshi dan Allah.
To kawai yace mata, yakashe wayar. Runtse ido Haisam
yayi yana karajin haushin kalaman Momy, Areef yace
hankalinta yatashi ko?.
Kai kawai yadaga mashi, yace ina ganin matsalar mu
zatazo cikin sauki, sbd Momy tana sonka sosai, dan haka dole muhada mata plan. Murmushi Areef yayi yace haka
ne, abokina nagode, yanzu muje inga jikin beauty na.
Jakadiya Safeeya tace a,a Yarima ka kwanta jikinka babu kwari, likitoci suna kanta suna nema mata sauki.
Komawa yayi yakwanta zuciyarshi tana zafi.
Sarki Qaseem ne, afalonshi hankalinshi tashe da abinda
Waziri yafada mashi sungani apart din Medaki, haka
yazauna yadafe kanshi da hannu 2, jin haryanzu shiru
bega Gimbiya Suhailat tafito ba, yasa yatashi yanufi
dakinta, kwance yasameta tana ta kuka, cikin sauri
yakarasa gurinta tare da kamota ya rungume.
Kara rungumeshi tayi tasaki wani sabon kuka, shafa
bayanta yafarayi yana fadin meyafaru kike kuka haka?
Kanta tadago, tana share hawaye tace shikenan
munshiga 3 Hubby, zamu rasa danmu guda 1 da Allah
yabamu. Cike da tashin hankali Sarki yace bangane
mikike nufi ba, meyasamu Areef din ? Ko hadari yayi? Kai tashiga girgiza mashi, tace yana can asibiti likitoci ma sunkasa samo kanshi. Sarki yace dan Allah kitashi
kifadamun abinda yafaru, wlh zuciyata gab take da
bugawa, bakisan irin tashin hankalin daya sameni ba,
kifadamun abinda yafaru tunkafin nima kirasani.
Ai dasauri Gimbiya ta tashi tana kallonshi, se alokacin ta kula da yanayinshi, idanunshi sunyi ja sosai,cike da
kaduwa tace hubby dan Allah meyafaru, kallonta yayi
dan yafara kulewa da ita, tureta yayi cike da bacin rai, yace ya ina tambayarki kina tambayata dan kin rai nani, kawai kifadamun abinda yafaru idan bahaka zanbar
maki gidan. Matsowa tayi ta rungumeshi tana kuka, dan
tunda suke betaba yimata irin wannan ba, asalima bata
taba ganinshi cikin irin wannan yanayin ba.
Dagowa tayi tajawoshi suka zauna bisa gado, kanshi tajawo tadora saman cinyarta tana ta shafa kanshi,
lumshe ido yayi, yana sauke ajiyar zuciya. shiru sukayi nawani lokaci, jinyayi shiru yasa tadagshi ta tashi takawo mashi ruwa mesanyi, dakanta tabashi, kofi guda ya
shanye, sannan takara jawoshi yakwanta akan cinyarta.
Ahankali tana shafa kanshi tace hubby karika fadin
Innalillahi Wainnailaihirraji,un, kayi haka harso 5,
sannan infada maka abinda yafaru, amma ina fatan
bazakamun fada ba idan kaji abinda nayi?
Cike da fargaba Medaki tashiga falon Gimbiya Zakiyyah,
alokacin tana zaune tana hutawa, kallonta tayi tace
kekuma lafiyarki zaki shigo mani gida ahaka, ko Sarki ne ya mutu? Medaki tazauna tace ai da mutuwa yayi zefi
sauki da halin dazamu shiga nida ke, da su Jakadiya,
cinkin lokaci kadan.
Tashi tayi daga kishingiden datake tana yamutsa fuska
tace bangane abinda kike nufi ba? Anan tafada mata duk
abinda yafaru, har halin datake ciki ita da Sarkin Fada seda tafada mata, dan ita tariga da tagama yarda da ita, tunda taga halinsu daya ne. Wani irin miskilin murmushi Gimbiya Zakiyyah tayi, tayi mata wani irin kallo, tace.
Lallai bansan ke Jahila bace se
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 13